Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

magana bayan da hira mukeyi". Yake kawai tayi tace "a'a ba fushi nayi ba ai nasan hakanan bazaka hanani zuwa wurin Hajiya ba dole kana da naka dalilin kuma ma ai ka fada cewar bani da lafiya. Babu komai wata rana sai naje idan na kara samun sauki".



Dole ba don taso ba ta ware take janshi da hira don ta kawar mishi da shakku a zuciyarshi sai dai har ga Allah bataji dadin hanata zuwa gidan Hajiya da yayi ba. Tunda aka kawota gidan a matsayin matarshi bata taba fita ba sai lokacin da sukaje asibiti kusan watanni bakwai.



Tana son zuwa gaya ma amma sanin cewar ba lallai ne ya barta ba yasa ta kasa tambayarshi bare kuma yanzu data samu cikinnan komai takeyi idonshi nakai, ita har mamakin son yaranshi takeyi.



Da safe ne bayan sunyi breakfast yake ce mata ta shirya taje gidan Hajiya amma karya dade don baya son kaiwa yamma a unguwa. To itama tasan policy dinshi ne tun lokacin Mami nada rai bata wuce karfe biyar a waje.



Kitchen ta nufa ta hada abincin rana. Alkubus tayi da miyar taushe sai farfesun kayan ciki. Bayan ta shirya warmers ne ta zuba wanda zata kaiwa Hajiya ta hada a cikin basket sai toma dkinta don ta shirya.



Kafin ta shirya dama sai da ta tura Zainab don ta fadawa Mallam Adamu cewa zasu fita. A sitting room dinshi na sama ta iske shi ta mishi sallama sannan ta fita.



Lokacin da ta isa harabar gidan sai ta iske babu Mallam Adamu babu motar kuma, cikin daurewar kai ta tsaya tana kallon wurin daya saba ajiye motar. To ko dai Zainab bata gaya mishi cewa zasu fita ba.




Komawa tayi cikin gidan, a zzaune a parlour Ruqaiya da Zainab ne suna kallo a tashar disney. "Zainab baki fadawa Mallam Adamu cewa zamu fita ba ne" ta tambayeta bayan ta zauna akan kujera.



Tace "na fada mishi, su Yaya Ummie da Yaya Farida ne suka ce ya kaisu gidan kawarsu kuma ya fada musu cewa tare zaku fita suka ce idan ya kaisu ya dawo ya kaiki".



Ok kawai tacewa Zainab. Tasan da gayya suka fita bayan sun sanccewa fita zatayi don a gabansu ta tura Zainab ta shaidawa Mallam Adamu zata fita shinw suka rigata ficewa ta kuma san ba lallai ne su barshi ya dawo yanzu ba.



Tashi tayi ta haya sama don ta sanarwa Daddy cewa bata tafi ba. Tana shiga sitting room din yace mata "ya kika dawo ko mantuwa kikayi", gyada kai tayi tace "a'a na samu su Farida sun fita tare da Mallam Adamun ne". "Baki gaya mishi zaki fita bane suka fita ba tare da sun jiraki ba", tace "na aika Zainab ta gaya mishi maybe sunyi zaton ba yanzu zan fita bane".



Cikin fada yace "zancen banza kenan yasan zaki fita amma ya biye tasu Farida ya fita dasu, wa ma ya basu izinin fita. Ko sun sanar dake zasu fita. Girgiza kai tayi tace "um-um maybe kuma ba nisa sukayi ba shi ya saka basu sanr ba".



Tashi yayi ya shiga daki ya canja kaya zuwa kaftan ya dauko kwy din mota ya fito. "Tashi mu tafi" yace mata. Tashi tayi tabi bayanshi suka sauka kasa. Suna shiga parlour ta cewa Ruqaiya da Zainab su dauko takalmi da gyale suzo su tafi.



Juyowa yayi ya kalleta jin abinda tace yace "dama dasu kika shirya tafiya" tace "a'a na gani ne gidan babu kowa sai su Lami kaga ai bai kyautu a barsu su kadai ba".



Bai kara cewa komai ba sai dai kuma har cikin ranshi yana Jin dadin yadda take kula mishi da yaranshi yasan hadda wannan yasa mishi sonta a zuciyarshi.



Suna saukowa suka fita, yaran na baya ita kuma ta kame a gaban mota. Jefi-jefi suna hira har suka isa gidan Hajiya. Yana tsaida motar yaran suka fita da gudu don ko motar basu rufe ba.



Murmushi kawai Aisha ta dauki basket dinta ta fita ta nufi hanyar cikin gidan. Horn din da yayi mata ne ya sakata juyowa. Fitowa yayi ya kulle motar sannan yace "ki jirani mana mu shiga tare".



Ita dai kunya takeji yanzu kawai sai Hajiya ta gansu sun jero, shine fa dalilin da yasa tayi saurin fita don ta rigashi shiga amma ya tsaida ita.



Gaba ya wuce ta bishi a baya. A tsakar gida suka iske Hajiya a zaune akan tabarma su Ruqaiya sunyi matashi da cinyarta. Haka nan yau sai taji tana kunyar hada ido da Hajiya.



Cikin sanyin jiki ta karaso ta zauna akan tabarmar tana gaida Hajiya ita kuma tana tambayarta jikinta. Sai da ya bri suka gam gaiswa sannan ya gaida Hajiya ya tashi yana mi kallon Aisha yace "zan tafi sai da yamma zan dawo, inasu Zanab ne suzomu tafi kunsan yau akwai islamiyya" tace mishi "to nagode Allah ya kiyaye".



Bayan tafiyarsu ne Hajiya tace mata "tashi ki shiga cikinima yanzu nima yanzu zan shigo, tashi tayi ta koma parlour ta zauna.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

19

Yau kwanankin Aisha uku a asibiti kuma yau dinne ake saka ran za'a bata sallama. A cikin kwanakin nan gaba daya su Farida sai wasan buya suke yi da Daddy ko da wasa basu bari sun hadu dashi ba.



Shima kuma baibi takansu ba don a yanzu ba abinda ke gabanshi ba kenan. A yanzu ta lafiyar Aisha yakeyi, ya bari ne sai sun koma gida sannan ya zauna dasu dukkansu don yaji miye musabbabin hatsarin daya faru.



Baya so ya zurfafa zarginshi akan yaran sai dai kuma yanayinsu a lokacin ya nuna tabbas basu da gaskiya. Gashi kuma tun ranar bai kara sakasu a idanunshi ba abinda ya kara assasa zargin da yakeyi na cewar sune ke da alhakin kada Aisha har ta kusa tayi loosing yaranta.



Mutanen gaya ma sun samu labarin haihuwar Aisha don haka sukayita tururuwar zuwa dubata, Yakumbo Dije kuma ta zauna don ta kula da lafiyarta data jariran.



Koda aka sallameta gidanta aka wuce da ita duk da dai Hajiya taso ta tafi da ita gidanta amma Daddt yace a'a tunda dai ga Yakumbo Dije babu bukatar sai ta koma wurin Hajiya.



Koda suka dawo daga asibitin su Ummie basu je sun mata sannu ba bare suga babies, Khalifa ne kadai ya shiga ya dubata a daren ranar sai kuma su Ruqaiya da suka tare a dakinta basa motsawa ko nan da can.



Bayan kwana biyu da dawowarsu daga asibiti ne Daddy ya tara su a parlourshi na sama, tun daga kan Khalifa da ba ma ya nan abin ya faru har zuwa kan Farida. Ruqaiya da Zainab ne kawai babu.



Hatta da Hajia a ranar sai da tazo don tun suna asibiti ya gaya mata cewa yana so za suyi magana amma bai gaya mata akan miye ba sai kuma a yau yayi mata waya yace ya tura Khalifa ya daukota.



Gaba dayansu sun taru a parlourshi har Aisha. Ga Mu'azzam da Farida kuwa gaba daya sun rude don sun tabbatar da wannan zaman akansu akayi shi, hatta da Ummie a tsorace take.



Kallon wurin da suke Daddy yayi yaga yanda sukayi tsuru-tsuru kwata-kwata basa cikin nutsuwarsu.



Bayan wasu 'yan mintuna ne Daddy yayi gyaran murya yace "abinda yasa na taraku duka anan shine dan na sanar daku abinda ya faru kwanaki biyar da suka wuce na samun Aisha da nayi kwance a cikin jini bata cikin hayyacinta sai kuma wadannan da na samu a tsaye akanta wanda bana raba daya biyu sune sukayi sanadin dana sameta a halin dana tarar da ita" ya fada yana mai nuna su Mu'azzam.



Yaci gana da cewa "shine yasa na taraku anan don ina son sanin asalin abinda ya faru, Aisha ko zaki gaya mini yanda akayi kika fadi akan cikinki har yayi sanadin da sai da aka miki aiki aka ciro babies?"




Sunkuyar da kanta tayi ta kasa magana don sai yanzu da yayi maganar ne ma taji ciwon abin sosai. Bata taba sanin kin da suke yi mata har yakai yanda zasu yi mata lahani ba sai yanzu.



Tasan da gayya Mu'azzam ya cilla mata ball dinnan a cikinta abinda bata taba zaton zasu iya yi mata ba. Jin shirun nata yayi yawa ne yasa Daddy yace mata "Aisha kiyi magana mana, nace ko zaki iya fada mini abinda ya faru a ranar na tarar dake a kwance cikin jini".



Girgiza kanta tayi sannan tace "a gaskiya bazan iya tunawa ba na manta". Hajiya ce ta ce "wanne irin kin manta kina nufin baki san yadda akayi kika fadi akan cikinki ba da har yay sanadin da akayi miki aiki aka ciro yaran dake cikinki, kenan kin samu shafewar tunani da bazaki iya tuna rayuwarki ta baya ba".



Nanma Aisha cewa tayi "a'a Hajiya ban samu shafewar tunani ba kawai dai na manta abinda ya faru ne a ranar". Hajiya zata sake magana Daddy yayi hanzarin cewa "kyaleta Hajiya tunda tace ta manta shikenan saukinta ai ba ita kadai bace a wurin da abin ya faru don haka kai Mu'azzam kaine babba ko zan iya sanin abin d yaru da har nazo na iske Aisha a kwance yayinda kuke tsaye akanta kai da kannenka".



Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci Mu'azzam don har ga Allah yana tsoron Daddy yasan cewa shine ya cilla mata ball a ciki duk da dai yana tunanin Daddyn yasan cewa sune shine ma dalilin da yasa ya tara su duka anan wurin.



Ganin yayi shiru ya kasa magana ne yasa Daddy ya juya akalar tambayarshi wurin Ummie, itama shiru tayi ta kasa bashi amsa haka ma Farida.



Ranshi yayi mummunan baci, shirunsu ya kara tabbatar mishida zarginshi na cewa sune sukayi sanadin da Aisha ta kwanta a asibiti.



Cikin masifaffiyar murya yace "kunsan me shirun ku yake nufi, yana nufin zargin da nake yi akanku ya tabbata don ko rantsuwa zan iyayi akan cewa kune kuka yi sanadin da Aisha ta fadi. Yanzun its either ku fada mini gaskiyar abinda ya faru ko kuma nayi bincike na gano yanda abin ya kasance don kada ku manta ba wai ku kadai bane a wurin a ranar da abin ya faru kun kuma san Zainab bazata gaya mini karya ba. So its better you start talking right now".




Mu'azzama ne yayi karfin halin cewa "Daddy don Allah kayi hakuri wallahi tsautsayi ne",cikin tsawa yace "comeon ka fada mini abinda ya faru don bawai na tara ku anan don kuyi mini yawo da hankali bane".



A haka dai Mu'azzam ya daure ya fadi abinda ya faru sai dai yayi kokarin ya nuna cewa laifin na Farida ne don ita ta kauce bata bari Aisha ta dafa ta ba abinda yayi sanadin data kifa akan cikinta.



Gaba daya Farida rikicewa tayi jin Mu'azzam na neman ya juya laifin kanta ita kadai bayan kuma da ace bai fara jefa mata ball dinba da duk haka bata faru ba.



Sosai ran Hajiya ya baci da jin abinda ya faru. Fada sosai ta hau yi tana cewa "wannan ai rashi imani ne ku jefi mace da tsohon ciki, me kuke so ku zama ne yarannan".



Khalifa ma ranshi ya baci dajin abinda sukayi, ya rasa me ke damun yarannan wai har Mu'azzam da yake babba kuma namiji ace yana abu irin na jahilai yana biyewa su Farida.



Daddy kam takaici ne ma ya hana shi magana sai zuwa can ya ce"yanzu magana guda daya ce zanyi bazan yi tolerating iskancinku ba acikin gidana dole ne kuyi respecting matata don disresoecting dinta yana nufin disrespecting dina. Aisha da kuke gani matata ce and its a must for you to accept her as a mother, babu ruwana da wani grudges da kuke holding against her wannan damuwarku ce.



Abinda na sani shine cewa nine mai gida kuma dukkanku a karkashina kuke so dole kuyi accepting ko waye na kawo na ajjiye a cikin gidannan, don haka this should be the first and the last time da wani abu makamancin wannan zai kuma faruwa.



Abu na gaba kuma shine ke Ummie da Farida ku fito da miji auren zan yi muku tunda na lura har da kyaleku da nayi kun zaune mini a cikin gida babu aure yasaka kuke mini iskancin da kuka ga dama, don haka sai ku shirya auren Khalifa da za'ayi tare da naku za'a hada".



Kai kuwa Mu'azzam babu abinda zan ce maka don kuwa a shekarunka idan har baka tsawatarwa da na kasa dakai ba bazaka biye musu kuyi abinda kukayi ba amma kuma unfortunately kai ne kake nuna musu ko miye ma sukeyi, abu daya zan gaya maka shine bazan dauki rashin da'a a cikin gidana ba. Bazan yadda da ganganci irin wannan ba ayi terming dinshi as tsautsayi".



"sannan kuma inaso dukkanku ku bawa Aisha hakuri tare da alkawarin makamancin irin wannan bazai kuma faruwa ba". Ummie ce ta dago kai tana sharar hawaye ta ce "Aunty Aisha don Allah kiyi hakuri In Sha Allahu wani abu makamancin wannan ba zai kuma faruwa ba" ita dai Ummie har cikin ranta tayi danasanin abinda ya faru duk da dai babu ita a cikin abin da ya faru amma kuma tasan cewa ita ma tanayi wa Aisha abubuwa.



Duk sai da suka bata hakuri sannan Daddy ya sallamesu, itama Aisha ta tashi ta koma dakinta.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

18
Daddy ne a zaune a parlour yana zuba idon ganin ta inda Ummie da Farida zasu shigo. Tun bayan daya dawo daga kai Aisha gidan Hajiya yake zaune a wurin sallah ce kawai ta tashe shi kuma yana dawowa daga masallaci ya cigaba da zama a wurin din baya so su dawo bai sani ba.



So yake yaji ina suka fita tun safe bayan sun san Aisha zata fita kuma da izinin wa, don duk da yana sake musu wannan baisa ya kyalesu suna abinda suke so ba komai zasuyi sai da saninshi hakanan idan zasu fita sai ya yardar musu.



Har yaje masallaci sallar la'asar ya dawo basu dawo ba. Yana son yaje ya dauko Aisha amma ba ya son su dawo ba ya nan. Yana zaune a wurin har kusan karfe biyar da kwata sannan suka shigo suna dariya, Farida na cewa "yau kam duk abinta wannan fitar kuma dolenta ta hakura da ita".



Turus sukayi ganin Daddy a zaune a parlour don basu zaci ganinshi ba. Allah yasa dai baiji suba. "Sannu da hutawa Daddy" suka ce mishi tare da russunawa. Banza yayi musu ba tare da ya amsa ba. Ganin haka yasa sum-sum suka wuce stairs zasu hau sama.



Wata irin razananniyar tsawa ya musu tamkar yana a barrack yace "ku zo nan". Jiki na rawa suka zo suka durkusa nesa dashi don sun bala'in tsorata da tsawar da ya musu.



"Daga ina kuke" ya tambayesu. Cikin in'ina Ummie tace "daga gidansu friend dinmu" yace "wa kuka tambaya da zaku fita" suka yi shiru. Wata tsawar ya daka musu yace "comeon ku bani amsa nacevda izinin wa kuka fita" suka ce "babu kowa".



Yace "kenan ku nan har kunyi girman da zakuyi gaban kanku ko, har kuna iya fita daga gida ba tare da kun sanar ba ko. Wai me kuke so ku zama ne a cikin gidannan, halayenku fa sun fara isata. Idan kuka cika mini ciki matakin dazan dauka akanku bazai yi muku dadi ba".



Fada sosai yayi musu irin wanda tunda suke dashi bai taba yi musu makamancinshi ba. Gaba daya Daddy ya canja musu tamkar ba shi ba. Tashi yayi ya fita don zuwa daukar Aisha amma kafinnan sai da ya jawa Mallam Adamu kunne akan abinda yayi yace don miye yasan zasu fita da Aisha amma ya biyewa su Farida suka fice yawo ba tare da ya sanar mata ba.



Tun daga ranar ta samu saukin iskancinsu, sunayi mata amma sai sun tabbatar Daddy ba ya nan don yanzu sun fahimci cewa bazai kyalesu su cigaba da wulakantata ba.



A yanzu cikin Aisha yana cikin watanni na takwas. Tana zaune a parlour tare da Zainab tana yi matavkarin karatu a cikin suratul jumu'at. Mu'azzam ne da Farida da Ummie suka shigo daga waje suna dariya. Ball ce suka shigo da ita suke passing a tsakaninsu.



Hayaniyarsu ce ta ishi Aisha ta tashi zata bar wurin kawai sai Mu'azzam ya saita cikinta ya cillo mata ball din. Wata iriyar azaba ce ta ziyarceta. Tayi taga-taga zata fadi tayi hanzarin kai hannu don dafa Farida dake kusa da ita sai dai kuma lura da Faridan tayi cewa zatayi garkuwa da ita ne yasa da sauri ta ja baya don haka Aisha ta fadi akan cikinta.



Wata irin razananniyar kara ta saki kafin numfashinta ya dauke. Gaba daya sun tsorata da jin karar da tayi bare kuma da suka ga jini yana bin jikinta. A gaggauce Daddy ya sauko daga sama don ihun da yaji anyi yasan bana lafiya bane sai dai ya kasa tantance muryar waye yaji.



Ganin Aisha kwance a cikin jini yasaka mishi mummunar faduwar gaba ga kuma yaranshi da sukayi tsuru-tsuru a wurin ko motsin kirki sun kasa yi baya raba daya biyu suna da hannu a cikin abinda ya faru sai dai yanzu ba lokacin da zai tsaya bin ba'asu bane.



Bai bi ta kansu ba ya sunkuya ya dauki Aisha yayi waje da ita yana kwalawa Mallam Adamu kira. Bude motar yayi ya sakata a gidan baya sannan ya shiga ya zauna ya tallabeta a jikinshi. Mallam Adamu kuma ya zagaya bangaren ya shiga suka nufi asibiti.



Suna isa asibitin yayi hanzarin fita yana dauke da ita ya shiga ciki. Likitoci sun rufa akanta suna kokarin ceto rayuwarta data abin dake cikinta. Sunyi nasarar tsaida jinin saidai kuma akwai bukatar ayi aiki a cire. Sun nemi Daddy da yayi signing inda bai bata lokaci ba ya cije dukkan takardun da ake bukata.



An shiga da ita theatre ya dawo reception ya zauna sai dai kuma zaman ma gagararshi yayi don kwata-kwata hankalinshi ba'a kwance yake ba. Yana nan a tsaye a wurin ne nurse ta fito ta bukaci daya kawo kayan baby.



Khalifa ya kira a waya yace mishi yaje wurin Lami yacevta duba dakin Aisha zata ga akwatin data shirya na zuwa asibitu ta bashi ya kawo.



Tambayarshi Khalifan yayi ko ta haihu ne Aishan. Bai tsaya amsa mishi ba kawai ya kashevwayarshi. Baifi mintuna goma da kiran Khalifa ba sai gashi ya shigo dauke da akwati.



Yana shigowa abinda ya fara tambayar Daddy shine ta haihu, Daddy yace mishi "a'a suna mata c.s ne su ciro baby".



Rufe bakinshi kenan sai ga nurse din ta dawo karbar kayan ta kuma shaida musu cewa anyi nasarar ciro mata yara biyu mace da namiji. "Ita kuma Aisha fa" shine abinda Daddy ya fara tambayarta. Tace mishi " don't worry she will be fine" ta dauki akwatin ta juya.



Sosai Daddy yayi farin cikin jin cewa ya samu twins, sai yanzu hankalinshi ya kwanta har ya samu ya kira Hajiya a waya ya shaida mata batun haihuwar.



Lokacin da Hajiya ta iso asibitin har an fito musu da jariran ita kuma Aisha an kaita wani dakin zuwa lokacin da zata farfado.


*****
Kuyi hakuri jiya kun jini shiru thruout jiya wayata babu caji ne.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

20

Anyi taron suna lfy yara sunci suna Maryam da Abdallah, sosai Daddy ya kashe kudi a hidimar sunan. Mutanen gaya suka tafi suna ta murnar yadda suka tarar da Aisha cikin daula gashi mijinta ya wadata ta da komai na bukata.



A yanzu haka shirye-shiryen aurensu Ummie ake yi. Dama dukkansu akwai masu zuwa wurinsu don haka da Daddy ya ce su fito da miji shine kowacce ta turo maneminta gida.



Ita dai Ummie wani lecturer dinsu ne ke sonta, bai taba aure ba amma yanada shekaru don akalla zaiyi shekara talatin da takwas.



Ita kuma Farida me mata ne ta samu, ya dade yana sonta tana share shi duk da son data ke mishi sai dai kuma rashin son auren mai mata yasa bata wani kula shi. Ganin Daddy ya dibar musu takaitaccen lokaci don su fitar da miji yasa ta amince da aurenshi.



Duka manemannasu sun turo magabatansu an tsaida magana don haka aka yanke lokaci watanni uku masu zuwa daidai da lokacin da aka yanke na auren Khalifa.



Tunda lokacin bikinnan ya matso Aisha bata samu zama ba don kuwa hidima tayi mata yawa. Komai na harkar bikin a hannunta Daddy ya damka shi duk da dai amaren basu so hakan ba to amma babu yadda zasuyi.



Kullum cikin fita sayyaya suke tun daga kan furniture zuwa kayan kitchen dasu rugs da labulaye har kan kayan decoration na gida da kuma kayan da zasu saka na biki.



Ita ma kuma Aisha bata bashi kunya ba don kuwa ta tsaya taga anyi musu kaya na fita kunya duk da dai kowacce ra'ayinta aka bi wajen sayen kayan.



A wajen karbar kudin events din biki ne Daddy yayi musu jan ido don kuwa kudaden da suka nema a wurinshi sunyi yawa don events suka shirya zasuyi na rashin hankali a kalla sun tsara yin events sunkai shida. Dole suka rage events din zuwa guda uku.



Kowanne event sun fitar mishi da anko tun daga kan kamu da yini jar luncheon da dinner da zasuyi kuma duka masu tsada nan ma da kyar Daddy ya yarda yayi wa su Ruqaiya don yace abin yayi yawa su kuma yaran ba tausayinshi suke yi ba sun manta cewar hidimar auren 'ya'ya uku ne a gabanshi.




An fara bikin ne da kamu inda suka shirya yinshi anan cikin gidan inda amare sukayi shigar atamfa super exclusive akayi musu dinkin zannuwa falle biyu sai polo shirt da suka hada da zanin suka rufa da dayan zanin. Suma 'yammata ankon Zanin atamfar Julius holland sukayi da polo shirt din.



Anci abinci na alfarma an zubarwa da makada naira inda amare suka zage sukayi ta tikar rawa tamkar dai ba amaren ba.



Kasancewar kamun da yamma akayi yasa Maman Farida ta shirya musu mothers night a meena event center.



An kawo wa Aisha cards guda biyar nata dana wadanda zata gaiyata, Farida ce ta tura Zainab ta kai mata cards din a lokacin tana kitchen tana aiki tana jin Faridan na fadawa Ummie cewa wai wallahi da Mummynta tayi shawara da ita bazata bawa Aisha kati ba don har yanzu da takaicinta a ranta duk lokacin data tuna cewa Daddy bai taba daga musu murya ba sai akanta.



Dariya kawai Aiaha tayi don tasan dama Farida ta sama mata lafiya daga rashin mutuncinta ne don tasan yanzu Daddy bazai yadda da iskancinsu ba.



Ko lokacin data basu gudunmawarta ta sarka gold kirar dubai data saya musu Farida karba kawai tayi babu godiya sai cewa da tayi ai dole ne ma ta saka tunda dai tasan da kudin ubanta aka saya, ko a lokacin Aisha bata kalleta ba don tasan duk abinda zata yi mata na dan lokaci ne.





Anyi mothers night din inda amare sukayi shiga cikin bridal lace da sukayi dinkin doguwar riga. Komai da suka saka iri daya ne sai colour data bambanta. Ita Farida tayi amfani da colour fari da blue yayinda Ummie tayi olive green da orange.



Tunda aka fara bikinnan Aisha bata zauna ba ga hidimar yara gata Daddy da kullum cikin yi mata korafi yake yana cewa tunda ta fara hidimar auren 'ya'yanta ta manta dashi.




Gaba daya hidimar bikinnan ta gajiyar da ita. A ranar asabar ne bayan an daura aure ta shirya musu walimah inda aka gaiyato malamai sukayi wa'azi sosai akan hakkin miji akan matarshi da kuma hakkin matar akan mijinta da zama da abokiyar zama.



Da yamma ne aka kai amare gidajensu. Ita dai Ummie an kaita redbricks ne yayinda Farida aka kaita lamido crescent. Ita kuma amayar Khalifa nan unguwarsu aka kawota gidanshi babu nisa da gidan iyayenshi.



*****
Asghar da Sajjad nayi muku barka da sallah da fatan Allah ya maimaita mana ya amshi ibadunmu. Sorry for the long silence wallahi tunda na Sligo kano sallah ban samu zama ba.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar



Please Login or Register in order to submit comment