Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Menene gaskiya? Shin ma wanenen Aseef ɗin?!!! Idan baku manta ba Josephine sun canza ɗaya daga cikin TRIPLETS, kuma Lion yana zargin Aseef ne, hakan na nufin Aseef ɗin ne da gaske? Kenan shi ba mutun bane? Kada fa ku manta a gida suka baro shi yana kukan rabuwa da su! Kenan dama Aseef zai iya kashe TRIPLETS nasa? Ko dai yaya ne, wai wanenen shi!!!!!!!!!!!!!!, Ko dai ba shi bane? Amma dai Areef ba zai taɓa iya kasa gane Aseef ba gaskiya, tun da ya ambaci sunansa, to ba makawa shi ɗin ne!!!! Tirkashi, yau ake yinta, wata sabuwar cakwakiya mai ƙulle kai🧠. Na barku lafiya, har kullum taku ce PRINCESS TEEMA ta amana mai salon ban mamaki da ruɗa kwakwalwa!.

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥

*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔
ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.

*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA,
INFECTION KILLER,
COLACCA,
SAI KAYAN GYARA PAGE.
KACA KACA.
YALLAGWADA.
JIGIDA.
RUWA RUWA.
BANI BANI.
WOMEN JELL BATA BATA.
DAFIN KAXA.
TANTABARA.
XABUWA.
CICCIƁI.
AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER
09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH,
BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.


❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥


https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S


❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥




TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️

❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)


*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*




Date: 23/4/2024

E13



"Aseef what are you doing here?". Ya yi maganar cikin tsananin fitar hayyaci, da ruɗu, dan ko a mafarki bai taɓa tunanin zai ga Aseef a Daular Mutuwa ba, kuma a nan ɗin ma yana ƙoƙarin kashe shi, wlh zai iya rantsuwa har ga Allah wannan Aseef ne ba gizo ba.

Shiru Aseef ɗin ya yi bai amsa mashi ba, sai ma sanya hannu da ya yi ya mayar da handkerchief ɗin face nasa, sannan ya ɗaga wukar da gaske zai datse mashi wuyar, cikin kwanciyar hankali da kwarin gwiwa yake aikwatar da komai nasa, ga kuma tsantsar nutsuwa a tattare da shi, ba zaka taɓa cewa Heartbeat na TRIPLETS da ya kasance rago mai shagwaɓar tsiya bane, a nan ya zama mai taurin zuciya, mara imani da tausayi.

"Aseef before you kill me, talk to me fist pls, duk da nasan cewa kai ne, amma ka kara share mani tantama kafin ka yi abin da zaka yi".

In a cool voice ya ce "Yeah Areef, it's me, what's next that you want me to tell you before the time of your death". Cikin kwarin gwiwa, jarumta, da nuna isa ya yi maganar, sam babu shagwaɓa ko ɗigo a muryarsa.

Tashin hankali, ai shi Areef ganin Aseef ɗin da kuma tabbatarwa da shi ɗin ne yafi kashe shi ɗin da za'ayi ɗaga mashi hankali, yanzu dai da gaske Aseef ɗin me babu tantama, kuma da kansa zai kashesu? Innallilahi wa inna ilahirrajiun, ya ilali ya lillahi. Godiya ga Allah Areef ɗin ya fara yi da Allah yasa shi ne ya kalli Aseef ɗin ba Lion ba, da Lion ne zuciyarsa zata buga, yanda yake tsananin kaunar Aseef ɗin fiye da kansa, sai dai bai san cewa Lion ɗin ma yana a kan hanya ba.

"Babu wani abin kuma da nake son sake sani face na ce maka kada ka cutar da Lion, kome zaka yi mana ni ka yi mani ni kaɗai, please ka bar Lion ya huta, ya wahala a kanmu ɗan tahalikin nan, tun muna yara, a kanmu ya koyi faɗa, a kanmu ya koyi zafin zuciya, ka fi kowa sanin cewa saboda kai Lion ya koyi faɗa, a primary school shi yake tare mana faɗa, komai muka kwaso shi yake tare mana, ya tsaya mana a kan maraicinmu na rashin uwa, ya bamu farinciki fiye da kansa, ya kula da mu fiye da rayuwarsa, burinsa kawai ace muna yin yanda muke so, please Aseef ka kashe iya ni kaɗai, ka bar Lion, ka barshi ya huta, kada ka ci amanarsa". Ya kai karshen maganar idanunsa sun yi jajir tamkar jini.

Cool murmushi Aseef ɗin ya saki, daga bisani kuma ya ɗaure fuska tamau, cikin muryar shagwaɓa tamkar yanda yake magana a gida ya fara magana yana turo baki "I can't kill you my Areef, i can't do anything to you my TRIPLETS, ku ne ni, kune bugawar zuciyata, kune farincikina, haka zalika ba zan iya bari ko kuda ya taɓaku ba, kamar yanda Lion ya tsaya mana tun muna yara har izuwa yanzu, bai yarda ko kuda ya taɓamu a rashin son ranmu ba, to nima a yanzu Allah ya ara mani lokaci da dama na taimake ku, na ceceku my TRIPLETS!" Ya kai karshen maganar tare da juya wukar hannun nasa ya datse kan ɗaya daga cikin matasan dake tsaye a gefe da gefensa, nan take matashin ya zube kasa bai shura ba, sai jini dake malala a kasa kamar an buɗe bakin fanfo.

Kafin sauran su yi wani yunkuri, ya sake datse kan ɗaya. Cikin zafin nama sauran suka yi kansa, ita kuwa Queen dake kallonsu, a zabure ta mike tsaye, dan bata taɓa tunanin cewa ba mutuminta dake yanka mutane bane, tambayar kanta take yi ina wancan mutumin nata mai yanka mutanen kenan? Tashin hankali, wato gaba ma da gabanta, wai aljani ya taka wuta, Queen ta iya bibiyar su Lion tun da suka baro Kaduna, har suka shiga Enugu, har izuwa Daular Mutuwa, amma bata iya gane ya aka yi mutuminta mai datse kan mutane ya sauya ba, bata iya gane shi ɗin ina yake ba, bata iya bibiyar Aseef ba, shin ta yaya aka yi Aseef ma har ya shigo cikin Daular Mutuwar ba tare da ta sani ba? Ya aka yi har ya kashe ainahin mutuminta mai kashe mutane ba tare da saninta ba? Ya akayi har ya shiga cikin tawagar mutanenta ba tare da saninta ba? Wanenen shi ɗin to? Wai wanenene Aseef?!!!!!!.

Idan kuwa da gaske Aseef ya zo taimaka masu ne, to kenan hakan yana nufin da wata manufa na daban Josephine ta sanya shi a cikinsu? Ke nan ba ta canza ɗayan TRIPLET'S ɗin bane dan ta cutar da su? Ko dai yaya abin yake ne? Amma to tun farko ma menene makasudin canza TRIPLETS ɗin? Manene yasa suka kawo Aseef suka ɗauki na ainahi? Ina na ainahin yake? Shi Aseef ɗin su waye iyayensa? Dole dai akwai wani dalili mai mugu mugun karfi na yin hakan, akwai babbar cakwakiya da kulla kulla a wannan lamarin, wanene mai gaskiya a cikinsu Josephine? Alkalamin PRINCESS TEEMA ce kawai zai warware maku gaskiya, dan haka ku kasance da ni taku PRINCESS TEEMA mai abin ban mamaki.

Babbar magana, a tsananin razane Queen ta mike daga saman kujerar mulkin nata, sai dai kafin ta yi yunkurin yi wa mutanenta dake faɗa da Aseef ɗin wani tsafi, tuni Aseef ɗin ya kashe su dukka, babu imani babu tausayi ko ɗigo a tattare da shi, haka ya yi masu kisan kiyashi, tamkar ba Heartbeat namu ba. Babban abin da ya girgizata ya kuma jijjiga tunaninta, bai wuce yanda ta ga Aseef ɗin ya buɗe Areef daga lock da suka sanya shi ba, ita dai tasan cewa bayan ita babu wanda ya isa ya buɗe waɗan nan locks ɗin, to ya aka yi Aseef ya buɗe shi? Kuma dai da tsafi ake buɗewa, hakan na nufin shima yana da tsafi kenan?.

Ta saki baki tana mamaki, bata ankara ba sai gani ta yi dukkansu biyun sun miƙe tsaye, Areef sai tambaya yake yi ina Aseef ya samu karfi haka? Shi kuma Aseef ɗin sai tambayarsa yake yi ina Lion nasu yake? Wannan shi ne cakwakiya....... JAMA'A NI KAI'NA INA SON SANIN WANENE ASEEF FA? DAN A GASKIYA WANNAN ABIN AKWAI ƊAURE KAI.

Ganin Areef ɗin zai ɓata masu lokaci wajen tambayarsa wanene shi, sai ya riko hannunsa tare da jansa suka fita, har sun fita ɗakin, sai kuma Aseef ɗin ya dawo ya ɗauki jakar da Areef ya zo da ita. Ita kuwa Queen sai kallonsu take yi ta cikin ruwan tsafin, bata ɗaga hankalinta dan sun fito daga ɗakin ba, dan a cewarta, ai tana da zararan mukarrabanta da za su yi gunduwa gunduwa da su, su cinye namarsu ɗanya, dan haka sam bata wani damu ba, bata san cewa abin ba haka yake ba, ko a tsafin ma ai akwai iyayenka wajen yin shi, gaba ne da gabanta, ita har yanzu a iya Africa take tsafinta, su kuma tsafinsu bugawa suke yi da manyan kasashen duniya masu faɗa aji, su ba kananan kwari irinta bane, iyayenta ne a iskanci da bala'i. E KAM BABU SHAKKA IYAYENTA NE, GA ALAMA TA FARKO, ASEEF YA IYA SHIGOWA HAR YA KASHE MUTUMINTA MAI YANKA MUTANE, YA KUMA SHIGA CIKIN JAMA'ARTA DUK BATA IYA GANEWA BA, BABBAN ABIN TAMBAYAR MA SHI NE, TA YAYA YA SHIGO CIKIN DAULAR?.

Suna fitowa harabar wajen, wasu jiga jigan maza masu kama da su barbushi ne suka kewayesu, zaratan maza ne majiya karfin gaske, yanayin nunfashinsu ma kawai abin tsoro ne, dan suna numfashi yana fitar da hayaki tamkar waɗan da aka ɗaurasu a saman garwashin wuta mai tsananin zafi, wasu jibga jibga da su, ga gashin kansu kamar jijiyar bishiya, a tsai tsai kamar kawon shaiɗan, idanunsu kawai abin tsoro ne, tamkar ba idanun bil adama ba, wasu jajir dawu tamkar sun zuwa jini ne a ciki, hannunsu kawai abin kallo ne, wasu dama dama da su, kirjin nan nasu a tsaye tamkar bishiyar kuka, sam yanayin halittarsu ya fita daban da ta mutane, kai daga gani kasan da tsafi suke amfani, da tsafi suka mayar da halittarsu hakan, jikkunansu babu riga, sai dai ta kasa ne kawai suka rufe, sun kasance su goma ne cif.

Hakika Areef ya tsorata da ganin waɗan nan halittu, ya girgiza na ganin munin halittarsu, sai dai bai sare ba, bai ji sanyin gwiwa ba, dan hukumar C.I.A idan ba gani suka yi an kashe su ba, to wlh basu taɓa tsarewa a kan abu, komai gani suke yi za su iya, haka Areef yake ganin kamar zai iya faɗa da su, yana ganin mutane tamkar gunguma gungumar kumaka da aka sassaka da dafaffiyar karfe, amma hakan bai sa ya ji ba zai iya yakarsu ba.

A tare waɗan nan gunguma gungumar mutane suka nufesu, suna taku kasa na amsawa da dib, dib, dib. Su kuwa suna tsaye suna kare masu kallo.

Sai da suka isa wajen ne Aseef ya ciro da wata sharɓeɓiyar wuka daga kugunsa, shi kuma Areef ya yi bismillah dan su fara yaki, sai kuma me? Yana ambatar wannan bismillahi gabaɗaya dakarun Queen ɗin suka ja baya da su, tamkar waɗan da aka janye da tsafi.

Ita dai Queen tana cikin faɗarta har wa yau, sai kallon abin al'ajabi da mamaki take yi, wani irin zaro shegun idanun tan nan ta yi na ganin yanda mukarraban nata suka ja baya daga tunkarar su Areef ɗin, irin wannan jan baya kamar an janyesu haka? Abin ya ɗaure mata kai. Amma bata sare ba, sai ta sake yin amfani da tsafinta ta sake turasu suka tunkari su Areef ɗin.

A karo na biyuma bismillahi Areef ya yi, dan su TRIPLETS komai za su aikata, to fa da bismillah suke farawa, sunan Allah shi ne a farko kafin su yi komai, kun tuna lokacin da Lion zai shiga gidan Queen? Sai da ya yi bismillah, ko zama za su yi a saman sofa, sai sun yi bismillah, ta yanda koda akwai wani abin da aka kullah masu, to wannan sunan Allah da suka kira, zai zama sanadiyar warwarewar komai, idan suka yi bismillah za su zauna a waje, to duk wasu shaiɗanun dake zaune a wajen za su watse, kowa zai kama kansa, hakan zai sa da wuya su zauna a waje kuma kuga sun yi faɗa ko makamancinsa, saboda da sunan Allah suka fara zama, babu wani shaiɗani a wajen da zai iya zugasu su yi faɗa, shiyasa kuke ganin kullum cikin Kaunar juna suke, babu faɗa babu kyaran juna.

A karo na biyu da ya yi bismillah ma, a dubu ɗari jakarun suka sake ja da baya, abin ya yi matuƙar girgiza Queen ba kaɗan ba, dan haka sai ta miƙe tsaye, cikin nuna isa da izza ta sanya hannu a saman ruwan tsafin nata, tare kuma da fara surutansu irin na matsafa, nan take ruwan nata ya fara juyawa kamar fanka.

Shi ma Aseef ya yi mamakin ganin yadda mukarraban Queen ɗin suka kasa iso su, sai dai bai nuna ba, kuma already shi ma kun san musulmi ne, akwai dai wata a kasa, amma ban da haka, duk wata addu'ar da Areef zai yi, shima zai iya yinta, so dama kunsan already shi bai yi nisa a karatun addini bane, bai san ma'anonin wasu adduo'i ba, ya dai iya karantawa ne kawai, ita kanta bismillahi bai san me ma'anar yinta ba, ya dai san sunan Allah ne.

Wannan surutai da Queen take yi ba komai bane face karawa jama'ar tata karfi, da kuma dakiya. Haka kuwa aka yi, bayan ta gama surutanta, sai ta sake turasu ga su Areef ɗin, bayin Allan, su kuma suna tsaye gam, babu alamar tsoro ko sarewa a tattare da su, sai ma kwarin gwiwar da suka sake ji mai karfi yana kara ratsasu.

Da wani irin mahaukacin zafi mukarraban Queen ɗin suka nufosu a karo na uku, dafe kai Areef ya yi yana faɗin "La ilahaillah anta subahanaka inni kuntunminazzalumin, wai ku idan za ku zo mu kashe juna kawai kuzo mana, amma saboda walaƙanci sai ku tinkaro mu, sai mun shirya kuma ku sake ja da baya, wannan abin fa ya fara kona mani rai, wani irin abu ne wannan? Ku yi maza ku karisu in ma kashe juna ne sai ayi komai a wuce wajen, ban son jan rai, zuciyata ta fara hasala".......faka faka kenan.

Bai kai karshen surutan nashi ba ya ji an taɓa shi, da sauri ya ɗago kansa, Aseef ne ya taɓa shi, yana ɗagowa ya ce mashi "To ai sai ka dai'na surutun haka ko? Mutanen da sun ɓace kamar haske, kai katsaya sai wani zuba magana kake yi kai kaɗai".

Zaro idanu ya yi yana faɗin "Ban gane sun ɓace ba? Ina kuma suka je? Ba kashe mu suka zo yi ba wai? Yaushe suka ɓace?". Duk waɗan nan tambayoyi ya jerosu ne da mamaki a saman face nasa.

Shiru Aseef ɗin ya yi na ƴan sakanni kafin ya ce "Oho time da ka fara surutanka mana, ni muje hai". Shiru Areef ɗin ma ya yi yana tunanin to a kan me za su ɓace kuma?. Bai san cewa wannan kalma ta lailahaillah anta subahanaka inni kuntuminazzalumin da ya faɗa bane yasa gabaɗaya suka yi wani irin ɓacewa ɓat, ita kanta Queen ɗin sai da kalmar ta sanyata ta yi wani irin baya baya ta faɗa a sama kujerarta na mulkin, karo na farko a rayuwarta da har wani jiri jiri take gani, kanta har wani sara mata yake yi...........

My peoples, wannan shi ne banbancin duk wata shirka da kuma sunan Allah, idan mutun zai yi shirka, ko wani saɓon Allah, to ba makawa sai ya ɗauki lokaci yana haɗa abubuwa, sai ya sha wahala kafin ma ya iya aiwatarwa, kuma ko da ya yi bata taɓa ɗorewa, misali, mushiriki, sai ya haɗa abubuwa da dama ya sha bakar wahala kafin ya iya yin tsafin nan nasa, ya azabtar da kansa ta hanyar shan jini da sauransu, kuma koda sun yi tsafin, baya taɓa tabbata, haka za su yi ta shan wahala, amma ba zai tabbata a jikin wanda suka yi wa ɗin ba, domin annabi ya ce tabbas tsafi bata tabbata a jikin bawa, dole akwai time da zai warware, lokaci gare shi, ɓarawo, sai ya sha wahala wajen yin sata, yana yi zuciyarsa tana bugawa da karfi karfi, saboda yana tsananin tsoron kada a kama shi, idan rana ta ɓacin mashi, to fa har kashe shi ana iya yi, idan kuma ya tsira, to abin da ya sata ɗin ba zata taɓa yin albarka ba, kamar iska haka zata wuce, kunga a nan ya sha bakar wahala sosai a banza, mazinaci, yana yin zina zuciyarsa na dukan uku uku, tsoron kada a kama shi, ko kuma wani abin ya faru yake yi, sannan idan har ya yi zina sau ɗaya, to kofa ce ta wahala da talauci a rayuwarsa take buɗe mashi, mashayin giya, idan ya sha giya, ya shiga cikin maye, ya fita a hayyacinsa, zai iya zuwa ya hau babban titi mota ta take banza ma ba tare da ya sani ba, babban musiface mutun ya gusar da hankalinsa daga jikinsa, masu yin luwaɗi, su maɗigo da sauransu, duk suna kasancewa cikin mufisa da wahala, masu yin lesbian a hankali hankali za su fara wari, ana tafiya ana tafiya har gabansu ta lalace, saboda sun kauce hanyar yadda Allah ya ce ayi, masu bada bayansu ayi zina da su ta wajen, su lalacewarsu ma tafi munin gani, dan har tsutsa suna yi, Allah ai ba abin wasa bane, Allah yana son bayinsa fiye da yanda suke son kansu, dan haka ba zai taɓa hana bayinsa wani abin na jin daɗin rayuwa ba, duk abin da kuka ji Allah ya haramta, to ba makawa wannan abin cutarwa ce ga bayinsa, masu yin bleaching wlh har wani irin wari suke yi, suyi ta zuba turare a jiki, amma kamshin perfume ɗin daban, warin jikin nasu daban, komai za su yi wa jikinsu, wlh ba za su dai'na wannan wari ba, saboda me? Saboda sun kauce hanyar Allah, Ubangiji ya fi kowa sanin abin da zai dace da bawansa, bai yi ki a bakar fata haka kawai ba, haka zalika bai halicci fararen fata haka kawai ba, yasan da cewa shi ne yafi dacewa da kowa daga cikinmu, amma ku ƴan iya, ƴan bani na iya, fit kin daka tsalle kina baka kice sai kin dawo fara, Allah yasan da farar fatar, amma ya baki baka, sai ki gode mashi ba wai ki ra'ina yanda ya yi maki har kina ƙoƙarin canzawa ba, a takaice dai duk masu aikata aikin saɓon Allah, to wlh a wahale suke, su kuma waɗan da suka ce Allah ya isar masu akan komai, wlh ko barci suke yi Allah yana isa masu ɗin, nafi jin daɗi a koda yaushe na yi maku misali a aikace ba wai da baki ba, dan ta hakan ce kawai za su fi ganewa, yanzu misali, ita dai Queen kunsan ba karamar wahala ta sha wajen gina waɗan nan dakarun nata ba, ko da ido ku kunsan dakare ɗaya ya isa ya kashe TRIPLET'S gabaɗayansu, ya isa ya cinyesu gabaɗaya, amma su TRIPLETS ɗin kuma sun ce Allah ya isa masu a kan komai, kuma ga shi ya isa masu ɗin, ƴar ƙaramar kalma ce a baki wajen faɗa, amma babbace a aikace, wato bismillahi munfara da sunan Allah kenan, ga shi su basu sha wahala ba, da iya bismillahi suka ruguje dakarun, ku sani bawai kankantar kalmarce abin dubawa ba, girman abin da ta kuntsa ce abin dubawa, bismillahi, mun fara da sunan Allah, tun da kuwa suka fara da sunan Allah, to ba makawa Allah zai tsaya masu, dan shi suka sako a gaba, shi ne kuma zai shige masu gaban a komai, abin da nake son nuna maku a nan shi ne, duk wani mai aikata saɓon Allah, to wlh a wahale yake har karshe raywuarsa idan bai tuba ba, idan ka ruke Allah, ka gama komai, ba zaka taɓa shan wahala ba, babu wanda zai iya kareka a kan komai a duniyar nan sama da Allah, to ni dai PRINCESS TEEMA na ce Allah ya isa mani akan komai da na saka a gaba a duniyar nan, kuma shi ne a kan gaba a komai nawa, shi na ruke babu wani ja in ja, saura ku kuma my READERS?.

STORY.

Wucewa gaba Aseef ɗin ya yi yana faɗin "Kai Areef ka cika tambaya". Ya yi maganar a tsananin shagwaɓe, yadda dai yake yi masu magana a gida.

Harararsa Areef ɗin ya yi yana faɗin "Kai ni kazo ka gaya mani ta yaya aka yi kazo nan wajen, ba zan yi mamaki da wannan karfin da ka samu ba, dan nasan kai jininmu ne, dole dama kana da karfi, shagwaɓa ce kawai ta cinye karfin, amma ya aka yi kazo nan? Shi nake son sani".

Miƙa mashi jakarsa Aseef ɗin ya yi, ba tare da ya dakata daga tafiyar da yake yi ba ya ce "Kai kanka fa baka san ta yaya ka zo nan ba, amma kake tambayar wani ta yaya ya zo? To ta sama na faɗo, ni ka ruke jakarka na gaji ba zan iya ba, ya fi karfina". Ya kai karshen maganar tamkar zai saka kuka.

Duka Areef ɗin ya kai mashi a dantsen hannunsa. "Ba wani nan sai ka gaya mani ta ya aka yi kazo nan".

Kukan shagwaɓa ya sanyawa Areef ɗin yana faɗin "Kai fa mugu ne, to nima na san tayaya na zo ne? Kawai na ganni ne a kusa da kai, daga haka kuma sai ban sake ganina ba".

Jinjina kai Areef ɗin ya yi yana faɗin "Sarkin rainin wayo na duniya ba, yanzu Aseef ni zaka kalla ka yi wa wannan tatsuniyar na cewa kawai ka ganka ne, sai kuma daga baya baka sake ganinka ba, to yanzu kuma da waye nake magana kenan?".

Turo baki ya yi kamar zai sa kuka ya ce "Da Heartbeat na TRIPLETS kake magana mana, ni ka karɓi jakarka ya yi mani nauyi, ba zan iya rukewa ba". "Amma kuma ai ka iya kashe mutane rai shidda ko? Jaka ce ba zaka iya rukewa ba?".

Kuka ya saka yana ƙoƙarin fara bubbuga kafa a kasa, da sauri Areef ɗin ya karɓi jakar yana faɗin "Rigimamme kawai, ni bani kayana". Ya karɓi jakarsa tare da wucewa gaba abinsa.

Haka suka cigaba da tafiya, Areef yana gaba, shi kuma Aseef yana baya, sai wuce ɗakuna suke yi suna neman sojojinsu da kuma Lion.

"Aseef wai ina Lion ne?". Areef ne ya tambaya.

Shiru Aseef ɗin bai amsa mashi ba, ko da ya juyo dan ya ga meyasa ɗan uwan nasa bai amsa mashi ba, sai ya kalli wajen wayam, babu Aseef babu dalilinsa. Da mamaki ya juyo da kyau yana kallon hanyar, babu wata kofa dai da za'ace Aseef ya bi ya tafi, hanya ce doguwa, sai ɗakunan mutane da suke a rufe ruf. Shiru ya yi yana al'ajabin ina Heartbeat nasun kuma ya yi?.

Ina da tantanma a kan Aseef sosai wlh!!.

Ya jima a tsaye a wajen ya kasa motsawa, tamkar wanda ruwa ta cinye. Almost 20 mins yana tsaye yana ta tunanin abin yi, kwatsam sai ji ya yi daga ta bayansa an taɓa shi.

A razane ya juyo. Cool murmushi Aseef ɗin ya sakar mashi yana faɗin "Muje".

"Aseef ta ina kabi ka bar nan wajen?". Ya yi maganar on a serious note.

Turo baki Aseef ɗin ya yi tare da wucewa gaba ba tare da ya bashi amsa ba. Kamar ba lafiya ba Areef ɗin ya ji ya mance da tambayar da ya yi wa Aseef ɗin a yanzu, kuma ya mance da tambayar da zai sake yi mashi, haka ya sake bin bayansa suka cigaba da tafiya a wannan shegiyar doguwar hanyar, suna tafiya Areef yana ambaton sunan Allah a cikin zuciyarsa, dan shi dama baya rabuwa da yin tasbihi, wannan tasbihi da yake yi kuma shi ne ya yi mugu mugun taimaka masu wajen kubcewa daga kan idanun Queen, kwata kwata ta dai'na ganinsu a yanzu, gabaɗaya sun fita daga idanun tsafinta, dan

Please Login or Register in order to submit comment