Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tunda sbd na banza yazo sau guda hakan bazai saka ta dena fita tad'i ba"gaba d'aya yarinyar nan na rasa meyasa da'an mata zancen Aure ko saurayi na kiranta take canzawa zuwa damuwa?".....shidai tunda ta fara fad'anta be tankataba"saida ta gama sannan ya mik'e tsaye "ba Abincin zaka ciba ne?" na k'oshi! ya fad'a yanata cin magani ya fita daga cikin parlourn"mamy ta tab'e baki tana fad'in da zaku burgeni kaida ita shine ku Auri juna "da zaka nuna ka goyi bayanta kar Allah yasa kaci Abincin.....shidai besan tanayi ba"sashen su mama ya wuce sbd yasan itace ke girki "yana shigowa ya sami maman Atsakar gidan tana rabon Abinci daga gefen kitchen nata"Abba na parlourn sa dabai jima da shigowa ba"sau biyu yayi sallama"mamah ta Amsa tana murmushi tace" ka dawo daga masjeed d'in?"Eh mama Asaman Abincin nan"dato ta Amsa ya wuce parlour ya zauna"beyi cikakken mintina biyar da zama ba"Asma'u ta shigo rik'e da plate da bowl na Alkubus da miyar taushe,data wadatu da naman saniya da man shanu"saida ta gaishesa ta Ajiye masa,kafin ta shiga cikin kitchen d'in dake parlourn ta d'akko masa goran ruwa da cup ta Ajiye ta fita...cikin jin dad'i ya fara cin Abincin dama yasan mama ta iya Abincin gargajiya"koda ya gama cin Abincin zamansa yayi yana Amsa tsirakun tambayoyi na mutane dake turowa"jefi jefi yana Amsa wayar mutane sbd ya baro Isma'il ya tafi chemist d'in nasa"can yaga har ukku da mintina 5 saiya mik'e tsaye ya fito tsakar gidan rik'e da plates d'in Ahannunsa"ke Amshi kayan can dama, bakije kin fito dasuba sai kika bari shine zai fiddo?"cewar mamah dake zaune tana gurzan kubewa ta miyar dare"no mama bara na kaisu kitchen ya fad'a yana wucewa ya Ajiye ya fito "sai lokacin ya lura da ummah Atake ya d'aure fuska "Khadija dake zaune sai gaidashi takeyi yayi kamar be jiba....wai dan ubanki ba zaki dena gaidashi ba tunda yanaji ya miki banza"zai baki Abinda Allah be baki bane?"ke ko kishin tankamun da Aka hanashi yayi Ai ya saka ki dena gaidashi.....lafiya keda baki gajiya da k'ananun mgn?"cewar Abba daya fito daga cikin parlourn sa"shidai Dr darma tsaki yaja Azuciyarsa yama Ida ficewa daga tsakar gidan....dole kace haka mana"k'iri k'iri yaron nan nurah ke nuna wariyar launin fata tsakanina da zainab"bayan haka ta hanashi gaidani ko tanka y'ay'ana "ko jiya kan idona ya shigo da leda ya bata kaza ta soya"cinya da k'ashin k'ugu ta bani nace bazan ciba..... Abba dai yayi tsaye yana saurarenta yana toshe hanci sbd warin jab'a da yaji tanayi"saima daga bisani ya juya ya koma parlourn sa"yayinda mamah ke Aikinta ta nuna kamar bata san meke faruwa ba??"saidai fa ran ummah ya b'aci da Abba yak'i mgn ya wuce ciki....

*2 days ago*
Tun ranar Friday da Dr darma yacewa Ahyaan ta wuce ciki be koma tanka taba"itama haka daga nata b'angaren tayi biris dashi"dukda cikin kwana biyun week end ne Amma yayi busy sbd Monday zai fara fita office,ga zuwa chemist ga Aikin ginin gidansa da Aka fara babu wanda yasanar mawa"sai ya zama tun safe idan ya fita sai yamma yake dawowa"mamy na lura Acikin 2 days d'in break fast da lunch wajen mama yake zuwa yayi"saidai tayi murmushi kawai sbd ta lura fushi yakeyi da ita sosai .... Ayau yakama ranar monday! Abinka da sabon ma'aikaci tun 7:00 am ya gama zazzafan shirinsa ,sbd ba break fast zaiyi ba "kasancewar yana Azumi "kuma yayi Alk'awarin 8 am a office zata dinga yi masa"k'ananun kaya ne riga da wondo na t shirt da jeans Ajikinsa "sai ya Aza jacket Asama"ba k'aramin kyau yayiba"yasha sabon Aski jiya da gyaran fuska"sajen nasa har walkiya da d'aukar idon me kallo yakeyi tsabar yadda yaji gyara"ga wani irin k'amshi me kashe jiki da zuciya daya zaunah Ajikinsa"shidai sau guda ya kalli kansa ta cikin mirror ya d'auke kansa yana koma d'aure fuska "dan yau da y'an jin kan yatashi"hakan kuma ba k'aramin kyau yayi ba...wata jaka ya d'auka da Aka bashi laptop ya saka ciki "sai kuma ya nufi gaban mirror ya duk'a ya saka takalminsa sawu ciki coffee brown irin kalar suit jacket d'insa, yana k'ok'arin tashi tsaye....wani irin harbawa da dokawar k'irji ce ta samesa duk a lokaci guda, Adalilin jin sautin zazzak'ar muryarta me kama da busar sarewa tana yi masa sallama"d'aure fuska ya k'arayi yana jin wani iri"sanye take da hijab har k'asa me hannu wacce ta lafe Ajikinta ta fiddo shape d'in jikin nata, sbd kayan dake jikin nata robber ne,kuma sun matseta.....kanafa jina nayi sallama shine ba zaka Amsa munba?"yayi shiru yak'i tankata"Kai wai mika d'auki kanka ne??.
   “Duk yanda zuciyarki ta baki?.yafada cikin cool voice ya nufi bakin k'ofar d'akin"ta d'an kallesa"kaje daddy na kiranka"bayan hakan kaima kasan Akanme zan wani shigo cikin wannan tsamin d'akin naka?
“Mittsoww! banda lokacin ki"Ak'ule tace " ban hanya na wuce" idan nak'i fa?"rayuka su b'aci "tunda Ai naga gaba kakeyi dani ko? nike gaba dake ko kece kike gaba dani?? wlh duk ranar da nake miki mgn kika koma yimun tsaki sai kinyi nadama"Agabana kike gaida su khaleel"ni meyasa bakya girmamani Ahyaan?"shine zakiga laifinah sbd na fita harkan ki kamar yadda kika nuna bakiyi dani?"bana cusa kaina inda Aka d'aukeni Awulak'ance kin gane ko?"wai yanzun duk dan sbd na maka tsakin kake wannan fad'an?"ya mata banza"okay yayi kyau bani hanya na wuce"duk tana maganar ne bata re data yadda ta kallesaba "shi kuma gaba d'aya ita yake kallo"ganin yak'i tankata kuma yak'i ya gyara saita saka k'aramin kuka tana fad'in wai ba zaka gyara na wuce ba?"sai kin bani hak'uri sannan zaki tafi"kanta ta d'ago suka had'a Ido "harara tayi jarumtar watso masa tana d'auke kai"sai kuma tace"ba yau zaka fara fita office ba shine kakeso kayi latti?"to ai kece kika ja"ki bani hak'urin shine kike jin girman kai? naji shikenan kayi hak'uri "banida sunane?"to broth kayi hak'uri "dama shine sunana?"shi mu'az kina kiransa yaya ni banda ni?"murmushi ta saki har beauty point d'inta na lub'awa tace"kaima kasan Ai ya girmemu ko?"sannan kaiba k'an....kina k'arasa fad'a Ina falla miki Mari"ya fad'a yana tsareta da manyan idanunsa ya wani tsuke fuska"hmm !wlh da Anyi y'ar mare mare kuwa"kadai ce nadena maka tsaki na baka hak'uri ko?"kuma duk na baka"to nima karka koma cemun yarinya ko kuma K"idan nak'i fa meye zaki iya yimun?"banza ta masa tak'i mgn saiya matsa suka fito"zata wuce yace jirani mana"ta wani turo baki batace komai ba tana satar kallonsa sbd ba k'arya yana bama wanka lokaci"bayan ya rufe ya mik'a mata jakar ungo rik'emun ki jirani gefen mashin nawa. sai nazo na Amsa na wuce"nidai gaskiya bazan iya jiraba muje dai je cikin gidan mana"shikenan ki barsa"wai broth meye haka ne?"yayi shiru yabi ta gefenta"shikenan kawo na rik'e kaje wajen daddyn zan jiraka "beyi mgn ba ya juyo ya mik'a mata jakar ya wuce"ita kuma ta nufi bakin get wajen flowers ta hango mashin nashi"tsaye tayi tana d'an murmushi sbd idan badan itama tana son Amfana dashi ba da babu wani hak'urin da zata bashi "d'an renin wayo "duk ta Ayyah na Aranta murmushi na sub'uce mata"kamar Ance ta juyo ta hangosa yana nufota cikin shegiyar tafiyar nan tasa ta k'asaita "d'an nutsuwa tayi batace komai tana kallonsa ta gefen Ido yajawo mashin d'in dake wanke goge ya hau"ta d'an lumshe Ido sbd k'amshin turarukan sa ba k'aramin dad'i yake mata ba"matsowa tayi ta Aza masa jakar daga gabansa tana fad'in to ustazah Allah yabada sa'a"sai kayi Addu'a idan zaka fara duba patient "dukda bansan ta wane sashen ka karantaba"idanunsa Akanta yace"fannin mata ne! yamutsa fuska tayi sbd haka kawai taji bata so hakan ba...ko zaki bini ne? yafad'a can ciki"Allah ya tsareni da koma hawa wannan mashin d'in naka kaje ka kayar dani ko?"idan Allah ya bamu motar daka ce saina dinga binka koma inane"uhmm !idan na tashi fita dake a mashin saiki hana"bak'ar mgn taso yab'o masa Amma sbd tuna zata Aikesa saita fasa....ga key nan ki gyaramun d'akina "batace komai ba ta Amsa Ahankali tace"broth dama pls zan baka sak'o idan zaka dawo?sak'on meye?"ta sunkuyyar dakai k'asa"idan bazaki fad'amun ba matsa na wuce"cikin shan mur tace wlh Dana maka rashin mutunci"to kimun ko yanzun mana"yafad'a yana tayar da mashin d'in"dama cream shaver nakeso pls"gashi sauka siyomun"meye zakiyi dashi?"me kasan Anayi dashi?"ta k'are maganar tana mik'a masa 2k"sai yak'i tankata yaja mashin d'in ba tare daya k'arbi kud'in ba ya wuce"yana d'an murmushi sbd yayi mamakin yadda ta nuna kunya"ya d'auka marar mutuncin batada kunya sai rainin wayo ta iya.....
Kwance take saman 3 seeter Acikin wani had'ad'd'en katafaren parlour na Alfarma ,wanda yaji kayan more rayuwa...."idanuwanta Alumshe tana tunani"tayi iya bakin k'ok'arinta na ganin ta yakice guy d'in nan A cikin ranta Amma Abin yaci tura"ko muryarsa taji sai ta samu nutsuwa balle kuma uwa uba tayi tozali da kyakykyawar fuskarsa"taso ta hak'ura dashi ,kodan sbd taga Alamar beda kirki ,zafin kai had'e da shan k'amshi da Aji,duk tana lura yana dasu"k'ilan sbd yanada kyau yake hakan?"saidai ta saka wad'anda ta Amince dasu da suke kusa da chemist nashi sud'an bibiyesa taga ko watace ta janye hankalinsa"Amma yadda take jinsa Azuciyarta zata iya komai sbd ta mallakeshi..... Anty Ikhkhee! taji muryar sultan d'an yayanta"tashi tayi zaune saima lokacin ta lura shida daddynsa yake"hannun yaron ta kama ta janyosa saman cinyarta tana d'an murmushi tace"yaya Abubakar! Uhmm Autar Hjy"tunanin meye kikeyi haka yaronki na miki mgn Amma baki jiba?"waskewa tayi tace" kaina ke ciwo ne yaya Ina wuni?"lpy qlau"Mr mahuta ya Amsa yana zama kan kujera yad'an lumshe Ido yana girgiza k'afafuwansa "yaci burin zuwa guda zai komayi gidan su Ahyaan daga nan muddin babu nassara to wlh kota wane hali sai hak'arsa ta cimmah ruwa....itadai bilkisu na zaune tana satar kallonsa tana jin kamar ta sanar masa da matsalarta tasan yayanta yadda yake sonta zai iya komai Akanta"saidai ita bata so Arok'i Dr Nura Darma ya sota, tafi son ta jashi Ajiki tayi Amfani da k'irsan mu ta mata ta janye hankalinsa....shigowar hajiyar su cikin parlourn yasaka ta sauke Ajiyar zuciya.....saida Ahyaan ta gama Abubuwan gabanta sannan tana surutai da gulmarsa wai yacika takurata da yawan saka Aiki"2 days taji kasiririt da basu mgn shine yanzun daga sun koma mgn zai fara matsa mata"kasancewar tunda ya dawo Nigeria sai yau ne dataje kiransa ta shiga d'akin,sai kuma yanzun"komai na d'akin ya burgeta sosai"bama wani datti yayi ba"Anutse ta gyara masa saman bed d'in,ta goge mirror da table d'in da yake aza books na Addini "sannan tayi shara da mopping"kafin ta shiga bath room d'in "wow! wato gyara dai ya saka Aka masa shine sbd son kai mu be saka mana bath tub ba ko?"ta fad'a tana k'arema cikin toilet d'in kallo komai Atsare"ga kayan wankansa masu k'amshi"ko wane saida ta duba"in bacin taga rashin dacewar tayi wanka Anan datayi"Amma dukda haka saida ta wanke fuska da k'afafuwanta "data gama wanke bath room d'in"sannan ta fito ta sami turarukansa ta faffesa "ta kuma turare d'akin da turaren wuta"sannan ta rufe ta wuce cikin gidan "da farko mamy tama d'auka shine ya shigo da taji k'amshin turarensa saida taji maganar Ahyaan sannan ta fahimci itace ke k'amshin"mamy meye za'a girka?"ki bari sai Anjima Ahyaan kwanta ki huta"inaga fa mamy broth yauma yana Azumi ?bazan iya ganewa ba sbd yanzun wajen mamah yake cin Abinci mu nan laifi muka masa Ai"murmushi kawai Ahyaan tayi tama d'auka kodan sbd ta dena masa mgn kuma mamy na goyon bayanta ya saka yake fushin"saidai batace komai tayi kwanciyar ta har bacci ya d'auketa.....
bayan sallar la'asar uban gayyar ya shigo cikin gidan Agajiye sbd rashin sabo da Aiki "ga chemist ma yad'an je ya zauna yaduba mutane da sallamar masu siyan magani"duk yad'an fad'a sbd gajiya da yunwar Azumi "koda ya kafe mashin d'in d'akinsa ya fara nufa sbd ya watso ruwa yad'an kwanta kafin time d'in shan ruwa yayi"kan wasu kujeru dake gefen barandar da d'akunan mazan gidan suke Anan ya zauna yakira mamy yasanar mata Ahyaan ta kamasa keys d'in d'akinsa "kasancewar beda contact nata"kuma zafin kansa ya hanashi ya nema"beyi zaman mintia biyar ba Awajen hamza ya iso wajen da gudu yana sanye da yunifoam farare na islamiya"yadda ya kallesa ya had'e rai ya saka yaron ya nutsu yana gaidashi ya mik'a masa"wato ita tafi k'arfin zuwa ta kawo shine ta Aiko?"ya fad'a Azuciyarsa yana Amsar key d'in tare da fad'in Ina Ahyaan d'in?"tana kitchen tana girki"be koma mgn ba ya mik'e tsaye ya wuce ya bud'e k'ofar d'akin ya shiga.....k'amshin turarukan sa dana turarukan wuta yafara shak'a "Allah ya shirya ki *Aminatu* shine Abinda ya fad'a yana maida k'ofar ya rufe" ya kalli saman mirror ya girgiza kansa,sbd ya fahimci ta faffesa masa turaruka"ya fad'a saman bed d'in yana sauke Ajiyar zuciya "saidai k'afafuwansa na'a k'asa ko takalminsa be cire ba"sai y'an kalle kalle yakeyi ko Ina fes dashi"yafi mintinah goma Akwance kafin yayi jarumtar tashi ya bud'e ward rope ya d'akko towel ya fara rage kayan jikinsa"sannan ya shiga wankan.....cikin mintina 25 ya fito sanye da wondo 3 quarter fari da riga Amles sky blue"idanunsa sun rage haske sun d'an yi ciki sai lumshe su yake yawanyi"kai tsaye sashen su mamy ya nufo yana dariya Azuciyarsa da Abinda yaga Ahyaan ta masa a bath room "zai tambayeta idan tana son kayan wankan saiya siya mata irinsu,dukda yasan itama da irin wa'anda take using dasu....k'amshin girkin daya cika haraban gidan har zuwa main parlour yadaki hancinsa "yad'an shafi cikinsa sbd tsabar gajiya shi yau bema da zab'in Abinda zaiyi bud'a baki dashi"mamy na zaune itada bak'uwa Atsakar gidan "mamy sannunku da gida"yauwa ya Aikin?"Alhamdulillah"yafad'a yana gaida bak'uwar ya wuce cikin parlourn rik'e da leda bak'a irinta shopping "ba kowa sai motsin Ahyaan dake kitchen ta kusa kammala had'a masa Abin bud'a baki da mama ce ta kirata taje ta Amso dawon Awara tace" taje ta had'a da wani abun ta shirya masa Abin bud'a baki.....cikin kitchen d'in ya nufa ya toge daga bakin k'ofar yana hangota tana tsaye tana juya Awarar data ji k'wai tare da doya cikin pripan "yad'an kauda kansa"batada Aiki sai saka k'ananun kaya "yafad'a Azuciyarsa tare da shan Alwashin zai take mata burki"rasa meye zaice yayi sai kawai yamata gyaran murya"ta juyo da sauri"Ido suka had'a ta d'auke kanta tana tambayar kanta meyasa wai idan ta gansa take jin fad'uwar gaba?"sannu da Aiki *Amun dago*"uhmm yauwa kadawo ne ?"bakiga Alama bane?"shiru tayi tak'i mgn"ya matso yana fad'in ga sak'on naki"ki shirya Anjima zan miki Allura"ta juyo Ak'ule ta wurgo masa harara tana fad'in tunda nace maka banida lafiya ko?"ko kuwa kaje kaduba mata nima Akace maka irin sune?"tabbas na duba su harma da haihuwa duk yau na Amsa"ta yamutsa fuska tak'i mgn"yad'an tab'e baki ya matso ya fisgo hannunta data rik'e k'ugu dashi"batare daya kalletaba ya saka mata ledar hannunsa yana fad'in ki dafa mun ruwan shayin me karanfani"be jira cewar taba yasa kai ya fita"ta tab'e baki tana Ajiye ledar ta cigaba da Aikinta "bayan ta idar ta shirya masa komai cikin basket ta d'akko tare da ledar ta fito daga cikin kitchen d'in"mamy na kallonta tace sannunki da Aiki Ahyaan"yauwa mamy"ta fad'a tana Ajiye basket d'in saman center table ta wuce d'aki"gefen bed ta zauna ta duba ledar"cream shaver d'in ne cikin kwalinsa sai ledar pads guda 4, kowace leda guda 12 pieces ce Aciki"ga kuma man kitso babba"sai kuma 2k daban"da mamaki ta d'auki 2k d'in "sannan ta cire cream shaver d'in ta maidasu cikin ward rope tana d'an murmushi Afili tace wani time d'in broth yanada kirki"bara naje naji kud'in meye ?"ta fad'a tana fitowa cikin d'akin"tana fitowa shi kuma yana shigowa cikin parlourn "kusan Atare suka zauna kan kujerah"mamy dai batayi mgn ba tama wuce tsakar gidan sbd tayi Alwallah ta fara Azkhar"Ahankali tace" broth !naga sak'on nagode sosai"Amma kud'in dana gani na meye?"ya kalleta yaga bashine take kallo ba"sai yayi shiru "kanafa jina?"kina mun mgn kina kallon wani wajen "na lura baki son kitso Any time gashinki Atsefe"kuma kina yima mutane girki"gobe in Allah yakaimu kije Amaki kitson da kud'in......✍️
ikon Allah wannan shi Ake kira k'arfin hali 😂🫣🤭

wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251

dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba

Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn

Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba

#Mommyn fareesa
#Dr Nura Darma
#Ahyaan
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: 🧍 *AGE MATE'S* 🧍‍♀?

*19&20*




*Littafin kud'i ne!*

.......cike da mamaki Ahyaan ke sauraren kalaman nasa har yayi shiru"sai ta saki murmushi irin na rainin wayo tana d'age kafad'a tace"sannu yaya babba! idan nayi girki Anga gashi sai mutum ya cire ko kuma mutum ya hak'ura da cin girkin nawa"nidai nasan gidan nan babu wanda ya tab'a mun k'orafin hakan sai kai"sbd haka ni ba zanyi kitson ba"haka kawai naje Ajamun gashina kaina yazo yayita mun ciwo ko?"tunda ba damuwa kayi da Abinda nakeso ko bana so ba....tamkar wanda ta danne bakinsa da dannau ya kasa iya furta komai sai binta da kallo kawai yakeyi har tayi shiru"sai kuma ganin yak'i tankata ya saka ta mik'e tsaye da nufin ta wuce d'aki"*bani kud'i nah* ! yafad'a tamkar bayaso"yi tayi tamkar bata jiba ta kama tafiya"taku biyu tayi yace"zonan nace miki Ahyaannnnn! ya kirayi sunan nata cikin wani irin salon taushin murya mai Amo da ratsa zuciyar mai saurare"A bazata taji saukar muryar tasa"gaba d'aya saima ta kasa juyowa"idan nazo nan baki zoba komai na miki ke kika ja"nifa gaskiya broth bazan baka ba ai kyauta ka bani"kaga zanci faran 500 yau da dare,gobema ta 500 har na cinye kud'in"bece komai ba ya mik'e tsaye yafara tunkarota"kamar Ance ta juyo ta ganshi yakusan isowa inda take "Azabure taja baya"ki tsaya ki bani nace ko?"menene zata baka?" kaida baka gajiya da tak'alarta"cewar mamy data shigo jikinta da lemar ruwan data yi Alwallah "da sauri Ahyaan ta matsa bayanta tana fad'in wai mamy cewa yayi naje Amun kitso"ni kuma kinsan bana son kitson zafi ke Akwai"shine wai saina basa kud'in daya bani na kitson"ta k'are maganar cikin shagwab'a"mamy ta kallesa yayi tsaye ya wani sha mur yana kallon Ahyaan da tak'i yadda ta kallesa"ita mamy dariyama yabata"tana d'an murmushi tace"Ahyaan ta fika gaskiya "na baka ta rabaka da mutum"nifa ba kyauta na bata ba mamy "kitso nace taje Amata tunda ban Isa da itaba ta bani kud'i nah na wuce mana"k'in tankashi mamy tayi ta kalli Ahyaan tace"wuce muje ciki kiyi Alwallah rabu dashi"ba zaki bayar d'in ba"da kake sakata Aikace Aikace baiwarka ce ita ko kuwa Ajiyeta kayi ne?"bece komai ba ya fita"sbd shine kawai yasan meya keji ga jikinsa"Ahyaan kuwa sai taga kamar bata kyauta masa ba"musammun data tabbatar siyayyar Abinda ya mata zasufi 10k, dama kawai sbd ta jashi ta nuna bazata bayar da kud'in ba.....Bayan An gama sallar magrib d'in tana zaune tana Azkhar ya shigo cikin d'akin"saida gabanta yafad'i dataji sallamar sa"ta d'ago kanta suka had'a Ido, saita kawar da kanta tace"barka da shan ruwa"barka kadai"taso muje! Ina kenan?"bece komai ba ya juya ya fita"ta tab'e baki tana zare hijab d'in jikinta Afili tace na shiryama duk wata fitinarka"komai zakayi bazan bayar da 2k d'in nan ba"ta fad'a tana fitowa daga cikin d'akin "ta samesa zaune kan carpet yana zuba ruwan zafin dayace ta dafa masa"ga wata leda bak'a Ajiye gefensa"Agefensa nesa kad'an dashi ta zauna tana fad'in gani"ya mata banza"matsalata dakai shine k'yaliya"nanma be tanka taba ya kurbi shayin"sannan ya zaro plate ya warware ledar gabansa ya juye balango me zafi yanata tashin k'amshi"yau dake zamuyi bud'a bakin sarkin mita"kai kuma sai Ace maka sarkin shariya ko?"ya mata shiru"tayi d'an murmushi tana fito da kular data zuba masa doya da k'wai da Awara soyayya"kafin tace"zan dai taimaka maka na tayaka rannan Ai baka mun tayi ba saima Ina maka mgn ka wani Amsa Awulak'ance"ta k'are maganar tana gallah masa harara "ya tab'e baki yana fad'in wlh zan koraki d'aki"hmm ! lallai ma "dad'in Abin kirani kayi bani ce nazo ba balle ka gayan mgn "kuma Allah babu inda zani"kamun mugunta na had'aka da daddy Ai yadawo"bece komai ba yaci gaba da shan tea d'insa harya gama ya Ajiye cup d'in ,ya d'auki fork yafara cikin Abinda ta zuba musu a plate"ita kuwa bata fara ciba"shinkafa da miyar kifi tafara zuba masa ta turo masa gabansa"sannan ta d'auki wani fork d'in tad'an koma matsowa gabansa suna ciye ciyensu babu me mgn "saidai dasun had'a Ido zata hararesa koshi ya harareta"da naman yazo k'arshe ta janye plate d'in tana fad'in ni za'a barmawa broth nice fa k'arama "dariya yadinga b'abb'akawa yana kallonta"Ahaka mamy ta shigo ta samesu"ba k'aramin mamakin ganinsu Ahakan tayiba" tamkar irin mata da miji suna cin Abinci haka taga sum mata.... y'ar rainin wayo kawai "Ashe kin yadda dai na girmeki da sati gudan ko?"ta gallah masa harara tana fad'in dama sbd ka barmun ne na fad'a"Amma mamy ba nice babba ba?"murmushi kawai tayi ta zauna kan kujerah "shi kuma Dr darma be koma mgn ba yaja plate d'in Abincin ya fara ci"ita kuwa saida ta cinye sauran naman duka , sannan ta d'auki plates d'in da cup d'in da yasha shayi ta wuce kitchen dasu "bata jumaba ta dawo rik'e da goron ruwa Ahannunta"ki koma ki d'akko mun fanta na gwangwani"dato kawai ta Amsa sbd ganin idon mamy"koda ta dawo samunsa tayi yana Amsa wayar wata mata dake neman shawarah sbd matsalar gidan Aurenta "gefensa ta Ajiye masa da cup kafin ta zauna kan kujerah tana tab'e baki Aranta tana ganin rashin dacewar Abinda matar tayi"Ace duk duniya ta rasa wanda zaya bata shawarah sai wani da bata saniba,Ina y'an uwanta maza da mata da Aminnan Arzik'i?? shiru tayi sbd jin yadda yake jawo mata hadisai da Ayoyi yana fassarasu da bata hak'uri,bisa ga tayi biyayya ga mijinta ta hak'ura da Auren dazai k'ara indai zaiyi Adalci, kuma yanada halin d'aukar nauyinsu"bayan ya Ajiye wayar mamy tace Allah ya kyauta! dama kana Amsa kiran nasu ne?"ah ah sak'o dai ta turo tafiso muyi mgn"shiyasa data kira na d'auka"mijin nata ne zai k'ara Aure"murmushi Ahyaan tayi tace"wlh mamy ta bani haushi"miye ribar kiran wani kisanar masa da sirrinki?"wlh idan nice dashi da yarinyar duk sai kowa yaji ga jikinsa"wasu matan lusarai ne wlh.... murmushi kawai mamy tayi,yayinda doctor be saka musu baki ba yana dai saurarenta yana cin Abincinsa"shi kansa yana ganin nan gaba zai karya layin da Ake turo tambayoyin gaskiya sbd be san takura "musammun wasu ma da ba sbd Allah suke turo tambayar ba"yana wannan tunanin ya gama cin Abincin "ya kalli Ahyaan ya mik'e tsaye yace"kina jin Ana kiran sallah kikayi zaune?"banza ta masa"shi kuma be koma mgn ba ya fita"......washe garin ranar misalin karfe 7:21 am Dr darma ya shigo gidan cikin shirinsa me matuk'ar d'aukar hankalin duk wanda ya kallesa "yadi ne sabo ash colour Ajikinsa, ya Aza hula k'ube wacce tayi daidai da kakar kayan"yayinda har Ana ganin lallausan gashin kansa ta baya sbd ya kashe hular"mamy na zaune tana had'ama Autah tea sbd karya makara a skul"kasancewar sun gaisa da Asuba "zama kawai yayi yamata sannu ta kallesa da kulawa tace"harka fito? uhmm! ga break fast d'in can "tamkar yace"Ina Ahyaan Amma saiya basar ya nufi wajen madaidai cin dining table d'in da mutum hud'u ke iya cin Abinci yaja kujerah ya zaunah"kunun tsamiya ya zuba da soyayyar planten da fanke "Anutse yayi break d'in ya gama,kafin yayima mamy sallama ya fita"Ahyaan kuwa bacci takeyi"kasancewar yanzun kullum da safe data sha ruwan maganin da rubutun zata fara jin ciwon kai"daga nan kuma saita kwanta tayita bacci"ita kanta mamy ta kasa nutsuwa da hakan data ke gani ga Ahyaan Acikin y'an kwanakin"saida Dr darma na fita ,ita kuma ta wuce cikin gidan sbd suyi zancen sauyawar Ahyaan d'in itada mamah.....sai yamma Dr darma yakoma shigowa cikin gidan yana sanye

Please Login or Register in order to submit comment