Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

je inda suna zaune Ummi ta saka shi ya bada numbar katinsu aka dauko sannan suka yi zaman jiran a kira su. Basu jima ba kuwa aka kira Rahima da Ummi suka shiga wurin likitan. Bayan ya duba idon sosai yace musu wasu jijiyoyi ne suka toshe sakamakon jinin da ya daskare a ciki shi ya kawo kumburin idon. Magani ya rubuta mata na sha da digawa domin sace kumburin sannan zasu dawo bayan kwana biyar a auna lafiyar idon.

**********


Kwana biyun bayan dawowarsu an cigaba da gyara Radhiya sosai. Mama ce da aikin hadata da kayayakinsu na Sakkwatawa da kuma na wata kawarta Maman Farida. Sai kuma takunkuminta na hana Awwab ganin amarya. Tun ranar da su ka dawo daga Sumaila ta fada masa da kanta. Manufarta bai wuce samun lokaci da kyau a gyare mata 'ya ba. Sannan kuma tasan cewa idan ba haka tayi musu ba haka zaiyi ta zuwa kullum yana bata show tunda yasan matarsa ce. Idan kuwa sai da komai ya kammala ne dole ya fi ganin tasirin aikin.


Ba wani damuwa yayi sosai ba saboda shima bashi da isasshen lokaci. Tun safe suke kulle gidan Mami idan ta fita shi da Bilal, Yousuf, Raji, Emzee da Ibrahim sai wani mutum guda daya da yake zuwa sai dare ya tafi. Mama tayi juyin duniya Mami ta fada mata me suke yi taki su ma kuma kowa ya rufe bakinsa. Yau da yake neman alfarmar son ganin Radhiya lallabowa yayi yana mata magiya. Wasa yake yiwa DK da yake hannunsa yana mata magana.


"Ko awa biyu bana jin zamuyi don muma abinda yake gabanmu akwai cin lokaci"


"Na yarda amma da sharadin sai ka fada min me kuke yi kai da 'yan uwanka"


Dariya yayi don kowa yasan tana binsu daidai suna zillewa ne.

"Big surprise ne Mamanmu ni dai a taimaka kada zuciyar......"


Da sauri tace "Ahhhh dena kiran zuciya yanzu zan kira na sanar da ita."


"Allah Ya ja da ran Mama. Nagode" yace tare da ajiye DK a cikin wani abun kwanciyar yara yana murmushi.


Bayan fitarsa ta kira Ummi ta fada mata gobe zai zo daukar Radhiya zasu je yin hotuna wanda za'ayi amfani dasu a wurin dinner din. A wurin Ummi Radhiya taji zancen ta kama yi masa mitar bai fada da wuri ba yanzu wane kaya zata saka yace ita kadai yake bukata goben komai is ready.


"Hammana da ya ka shirya komai ban sani ba?" Tace cikin jindadi.


Murmushi yayi mai sauti "ke dai ki shirya around 12 zan zo. Love you...sai munyi waya anjima ana jirana"


Saroro tayi da wayar a hannu tana tunanin me yake dauke masa hankali ne yanzu bashi da lokacin hirar kirki. Da dare kuma ba wani jimawa suke ba yake kwanciya. Washegari kafin ya iso ta gama shiri tun daren jiya sunyi magana da Arifah itama Yousuf ya fada mata zasu je kuma kada ta tanadi kayan sakawa. Zahra ce ta yi mata light make up mai kyau fuskarta kamar ka dauke ka dasa ga wani irin kamshi mai rikita kwakwalwa da sanyaya ruhi. A kitchen ta yiwa Ummi sallama saboda yace bazai shigo ba sai sun dawo gudun bata lokaci. 


Awwab kasa dauke ido yayi daga kanta tun fitowarta har ta iso gaban motar inda yake tsaye rike da kofa ya bude mata. Murmushi tayi tana sunkuyar da kai haka kawai wani irin nauyinsa take ji. Tana shirin zama ya duko daidai kunnenta "you look sweet"


Fadada murmushin tayi ta rufe fuska da tafukan hannayenta. Sai da ya zauna ta soma gaishe shi idanunsa a kanta kamar zai cinyeta.


"Hammana ina wuni?" Tace da karamar murya tana jin faduwar gaba.


"Lafiya kalau my baby."


Yanzu ma murmushi kawai tayi kamar ba ita ba wani salihanci ne yayi mata dabaibayi yayin da kwanakin barin iyayenta da zama cikakkiyar matar Awwab suke gabatowa. Tayar da motar yayi ya kama hannunta ya rike yana magana a hankali amma idanunsa na kan titi.


Cikin muryarsa mai tafiya da zukata wadda har yau idan Radhiya taji sai ta sanyata cikin wani irin yanayi na tsanananin son mai muryar yace "kinsan wani abu?" Kai ta girgiza ya cigaba da magana "yau inspecting dinki zanyi"


Mantawa tayi da shiru shirun ta kwace hannunta da sauri tare da zare idanu, baki na rawa tace  "me...me ne?"


Kin kallonta yayi har yanzu saboda ya san sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba "Inspection nace ko ban isa ba?"


Da rawar murya tace "ka isa amma ni ban taba jin anyi bane"


"To ke me kika sani game da aure dama. Kafin amarya ta tare ango yake yi domin tabbatar da cewa tana da tsafta."


Katse shi tayi da sauri "Hammana wallahi ina wanka kullum kuma ba ma sau daya ba"


"Dan kin fada da baki shikenan ni kuma sai na yarda?"


Gabanta ke matsanancin faduwa ta kwantar da murya tace "Kasan dai bazan yi maka karya ba...ka tambaya kaji" 


Murmushi ya juya yayi mata sannan ya gyara muryarsa domin ta saki jiki yana dariyar yadda ta tsorata "na yarda dake Schatzi, kuma nima gaskiya da aka fada sai da naji kunya nace bazan iya ba...."


Wani irin numfashi yaji ta sauke saboda samun relief ta gyara zama harda kwantar da kanta akan seat. Murnar da ta fara bata yi dogon zango ba taji yace "..to amma kwanakin nan duk kin chanja I really miss my Alheran."


Wani abu taji har zuciyarta yana bin dukkan jikinta soyayyarsa tana karuwa a cikin ranta.


Idanu ta lumshe lokacin da ya dan kalleta yana yin kwanar gidansu Arifah domin a nan zasu dauki hotunan. Akan Radhiya ya gaskata soyayya ya kuma san dadin kasancewa da masoyi. Rabuwarsu ta shekaru ukun nan kuwa shine lokaci mafi radadi a zuciyarsa. Dawo dashi tayi daga duniyar da yake neman tafiya ya barta ta hanyar cewa  "Chèri nice fa har yanzu"


Sun shiga gidan har yayi parking amma bai bude musu su fita ba ya zuba mata idanunsa "Gaskiya a'a shiyasa dole zanyi inspecting dinki na tabbarar ke din ce da gaske"


Baki ta shiga turawa kamar karamar yarinyar ya kasa hakuri sai da ya saka yatsansa yana shafar dimple dinta a sanyaye yake cewa "tawa Alheran din bata ganina ta kasa magana...I miss wannan 'yar kauyen me yawan kuka da dariya akan Hammanta, Schatzi dina da muke ci daga plate daya da spoon daya, muke shan abu mu ragewa juna. I miss 'Yar soja saboda ni ita ce wadda na kamu da sonta lokacin da na fara hada ido da ita. Idan zaki dawo min da ita yanzu I promise you babu wani inspection da zanyi....atleast for now" ya kare da kashe mata ido.


Kalamansa sun tsaya mata a rai taji kamar su dawwama a cikin wannan yanayin. Kallon da yake mata mai kashe jiki ne ta gaji dashi saboda yadda ta rasa sukuni gabadaya ta hura masa iskar bakinta daf da idonsa ya kifta idon tayi baya da sauri tana masa dariya.


"Gaskiya ta kare maka sosai Hammana"


"Na sani Alheran, daga ranar da na ganki da wannan kwal....."


Saurin fita tayi daga motar don tasan me zai ce. Ita kuwa babu lokacin da ko tuna shi idan tayi sai taji matsananciyar kunya kamar farkon haduwarsu a falon Mama. Fuskarta da alamun bacci ga kai a aske. Bayanta ya biyo yana cewa ta saurare shi ita kuwa ta ki suna dariya wata mai aiki ta kaisu falon da Yousuf da Arifah suke baje kolin soyayya suna jiransu.


Arifah rungume Radhiya tayi suna murna sannan ta ja hannunta zuwa dakinta inda wata mai kwalliya take jiransu. Jaka ce guda biyu iri daya sai dai kala da ta bambanta Arifah ta mika mata farar ita kuma ta dauki cream. 


"Ga kayan da zamu saka kuma an nanata min yadda suke a jere har kasa haka zamu rinka dauka" tace tana murmushin yadda suka yi da Yousuf kafin zuwan su Awwab.


"Ina mamakin yaushe suka sayi kayan da dinki" cewar Radhiya.


"Nima tambayar da nayi kenan. Amma wurin telan nan da muka kaiwa dinkin biki suka kai. Yanzu dai tashi mu shirya"


"Muje na fara gashe da Mom tukunna"


"Tun safe ta fita maybe ta dawo kafin mu gama"


Kayan saman suka fara daukowa tare da fadawa mai kwalliyar kada tayi musu heavy make up. Atampa ce ja da zanen fulawa manya navy blue anyi musu riga da skirt fitted a cikin kayan akwai dan karamin kwalin fashion sarka da dankunne ja sai mayafansu kashka mai stones navy blue. Kowacce cikinsu ta kasa boye farincikinta suna murna kai kace yara ne. Duka kayan da mahadinsu na mayafi da sarka. Babu bata lokaci aka tsara musu kwalliya kowacce tayi kyau. Daurinsu ma iri daya ne mai hawa hawa su ka dora mayafan a kafadunsu.


Ga mamakinsu Awwab da Yousuf suna sanye da blue jeans da red shirt mai dogon hannu. Radhiya dai hawaye take neman yi saboda yadda Awwab yayi surprising dinta yayi matukar burgeta da shiga rai.


Mai hoto yace idan sun shirya shima fa ya shirya. Hotuna suka yi sosai kowanne couple sunyi su kadai sannan anyi musu tare. Kayansu na biyu shadda ce ta matan orange ta mazan kuma combination din orange da fari sun sha hula. Nan ma kamar wancan kowa yayi da matarsa sannan sunyi tare. Sai kaya na uku matan lace  doguwar riga anyi aiki a gaban na mazan ma irinsa ne dinkin yarbawa harda hularsu. Wannan gudunmawar Raji ce mijin Zahra kayan sun amshi kowa aka yi hotuna ana zolayar juna. Kayan karshe abaya ce hadaddiyya kowa ya nemi kalar da matarsa tafi so amma design iri daya. Na Radhiya light green na Arifah light  purple (lilac). Ango Awwab yasa yadi irin mai shara sharan nan light green amma babu hula shi kuma Yousuf lilac. Idan ka kansu kamar kada ka dauke ido. Sunyi matukar kyau aka karasa musu hotunan Yousuf ya nanatawa mai hoton zasu zo da daddare su nuna masa hotunan da su ka zaba da kuma jerin yadda suke son ayi musu slide show din.


Ko a nan kawai amaren sun san mazansu sun karramasu sun nuna musu soyayya. A daki Arifah take fadawa Radhiya abinda Dad dinta yake yawan fada mata tun bayan da aka daura auren.


"Akwai ranar da zaki ji wai me ya sameki ne kika rasa mijin aure sai wane saboda kawai ya bata miki rai. Shima watarana zaiji kamar ya rufeki da duka don takaicin wani abu da kika yi ba daidai ba. A irin wannan lokacin babu abinda ke rike igiyar aure kamar idan kuka tuna memorable moments din da kuka gina lokacin ganiyar soyayya. Saboda haka kowa ya sami dama yayi kokarin nunawa dayan cewa they are special"


Radhiya ta jinjina kai tace "Sis to mu me zamuyi musu?"


"Ki bari a gama biki yanzu dai sunyi mana one-zero."


Wayar Awwab ta katsesu Radhiya tayi hanzarin mayar da kayan da tazo dasu ta dauki jakar kayanta ta sauka. Abinci aka gabatar musu wanda Arifah tasa aka shirya amma kunya ta hanasu ci. Plate Awwab ya samu ya zuba musu shi da Radhiya ya rike hannunta su ka koma wurin wasu kujera daga can gefe guda. Yousuf yace masa ya kyauta dama bashi da niyar barin Arifah ta tashi bata ci komai ba. 


Yadda suka saba kama-kama da spoon daya Awwab da Radhiya suka yi a haka aka ci abincin sannan suka tafi tare da Yousuf ya sauketa a gida.


***********


Ana saura kwana biyu fara events din Jos wanda kowa zaije banda Radhiya ance itama amarya ce. Tayi magiyar har Awwab ta roka yace tayi hakuri ba yinsa bane amma idan ta shirya ya kama musu masauki shi da ita sai su tafi tare. Da jin haka tasan hakuri ya zame mata dole ta gama rigimarta da shagwaba ta sallama. Sai gashi Zayyana da Rahima suka ce mata zasu zauna da ita su ma sun fasa zuwa. Ummi kuwa tace basu isa ba ya zama dole a karrama iyalin Excellency. To karshe dai Fauziyya ce ta fake da laulayi ta zauna tunda kwana biyu ne zasu yi kuma dai ba son tafiyar take ba. An gama wannan shawarar washegari ya kama ranar da za'a mayar da Rahima asibiti. Ido ya sace kamar bashi ba amma kuma yana ta ruwa.


Ummi ta shirya zasu tafi da Emzee da Ibrahim shiru bata sauko ba Emzee ya hau sama kiranta. A falon saman ya ganta zaune akan kujera ta dafe kai tare da runtse idanu.


"Ummi..." yace a tsorace ganin tana ta runtse ido "baki da lafiya ne?"


Hannunta ta dago masa tana son ya taimaka mata ta tashi "tun dazu nake jiran wani ya hawo, taimaka ka mayar dani daki jiri ke dibata sosai"


Da taimakonsa ta karasa dakin da kyar kanta yana ta juyawa kuma ta kafe bazata bisu asibitin ba wai stress ne kawai da rashin zama.


"Kaje ka kai min yarinyata a duba mata idon nan idan kun dawo sai ku karbo sakon nan da na fada maka wanda zamu tafi dashi Jos gobe"


Ba haka yaso ba don har Daada ya kira a waya ya fada masa. Sanin halinta na kin asibiti yace su tafi da Rahiman ya kusa tasowa zai kaita da kansa.


Yana saukowa ya nemi Ibrahim ya rasa. Can ya hango shi da Zayyana suna hira an nutse a cikin soyayya. Tsaki yaja tuni ya dawo daga rakiyar 'yan mata. Zayyana ya tura ta kira Rahima su tafi Ibrahim ya kyabe baki


"Ni dai gaskiya babu inda zata je ka kira wayarta mana ko kaje ka kirata da kanka. Dawo ki zauna kinji"


Emzee ya rike haba "ashe da gaske akwai ranar da zan ga kana tale baki? Kanwata kiyi a hankali kada ya fiki iyawa a kasa gane wace Zayyana waye Ibrahim"


"Banda abinka ga Zayyanan ai" Ibrahim ya nuna kansa sannan ya nuna  Zayyana yace "ga Ibrahim".


Murmushi tayi tana jin kunya ta je kiran Rahima. Dama a shirye take gudun bacin rai daga Emzee yasa tayi zamanta sai Ummi ta sauko. Lokacin da ya fadawa Radhiya Ummin bata jindadi tana daki bata sani ba. Zayyana  tace bazata bisu ba saboda anyi printing takardunta na admission da ta samu a Nile University akwai wuraren da zata cike Mami zata turo dreba a karba. Ibrahim kememe yaki bin Emzee da yaji haka.


"Kuje ku dawo Zee-zee ina jiranka a nan" ya nuna inda yake zaune.


Haushi ya kama shi kuwa saboda ganin yanzu su biyu ne kadai zasu shiga motar. Gaba tayi nufin shiga tunda su kadai ne yace "koma baya".


Bayan ta zaga ta zauna abinta batare da tayi masa magana ba. Yana zama ya kula kamar mudubinsa a saitin fuskarta yake don duk motsinta yana gani maimakon ya hango titi.


"Koma gefe" ya umarceta.


Gefen ta koma ta rakube zuciyarta tana zafi. Ba komai yake damunta ba sai rashin sanin aihinin abinda tayi masa wanda ya bata masa rai har yake mata haka. A gaban mutane bama ya shiga shirginta sai ya zama dole. Idan su kadai ne kuma dalili ya janyo sai yayi mata magana to ba mai dadi yake yi ba. Ba karamin azabtuwa yake da yin hakan ba domin kuwa har yanzu ya kasa rabata da matsayin da ya bata na Rahiman Muhammad. Ga tausayinta da yake dawainiya dashi saboda ciwon idonta.


Ko tari taki yi a motar ya kunna karatun Qur'ani kira'ar Mishary Rashid Al-Afasy cikin suratul Kahf. Da kadan da kadan yake jin tashin muryarta tana bin karatun a hankali sai ya sami kansa da rage volume batare da tayi la'akari ba. Idanunta a rufe sai dai lokaci lokaci tana sanya tissue ta goge ruwan da yake fitowa kamar hawaye daga dayan idon nata. Bakinta yake bi da kallo ta mudubi can cikin zuciyarsa yace "Rahima".


Wani mugun horn yaji yayi saurin kallon gabansa tare da taka burki da karfi kadan ya rage ya dokawa motar gabansa. Rahima ta bude ido da sauri ya juyo suka hada ido sai harara yake maka mata.


"Wato ta nan kika bullo kuma? Bari mu koma gida addu'a zan ce Ummi ta rinka yi min saboda na fuskanci abin naki da gaske ne."


Bata fahimci me yake nufi ba shi kuwa bai fasa cewa zai tsananta addu'a ba wai tunda an biyo ta can asirinsu ya tono shine ake neman sake tafiyar da tunaninsa gashi daga kallonta ta mirror ya kusa yin accident. Idan ka ga yadda yake fadan abin dariya kuma ya kasa hakura da kallonta ta mirror din. Sun kusa isa asibitin yayi parking a gefen hanya saboda abin ya ishe shi yace ta dawo gaba. Ita dai bata da ta cewa sai fatan idan ma wata lalurar ya gamu da ita da ta janyo masa chanja halaye Allah Ya yaye masa. Yanzu ta dena jin haushinsa sam sai tausayi.


A asibitin tare suka shiga wurin likitan. Tambayoyi yayi mata game da yadda take jin idon ya haska ya gama bincikensa sannan yace ta rufe idon mai lafiyar ta karanto masa ABCD da aka hargitsa daga can karshen wani office inda ake gwajin ido. Zuciyar Emzee ta tsinke kuka ne kawai baiyi ba jin Rahima guda biyar kadai ta iya fada daidai sauran kuwa sai dai ta kalli Q tace O ko ta kira K da E. Abin gwanin ban tausayi sai da mutum yayi mata haka sau uku ya tabbatar abinda yake zargi ne ya sami idon. Ita kuwa ganin yana maimatawa har cewa tayi dashi tana gani fa. Sai dai sakamakon toshewar da jijiyoyi suka yi da jini aikinsu yayi matukar rauni duk da cewa an magance toshewar kumburin ya warke gabadaya. Ko idon zai yi lafiya da wahala ta sake gani sosai dashi. Yatsunsa ya shiga nuna mata yana cewa ta fadi ko nawa ne. Nan Rahima ta rikice inda bata tantance biyu da uku. Hawaye sosai ta soma yi da likitan ya soma bayani. Duk yadda Emzee yake kokarin nesanta kansa da ita ba karamin tausayinta bane hake bin ko ina a jikinsa. Wasu magungunan ya rubuta mata sannan ya auna karfin idon yace zaiyi mata glass ne su dawo nan da kwana uku.


"Babu yadda za'ayi mu samu gobe da safe saboda tafiya zamuyi a goben" cewar Emzee.


"Zaku iya samu amma sai ka kara kudi. Kayi magana da cashier din idan ka fita"


Nan suka gama komai ya biya kudi cikin wanda Ummi ta bashi. Maimakon su tafi gida wani babban shago ya wuce da ita ya sa salesgirl din tayata neman frame mai kyau. Wani round ta zaba ya dace da fuskarta babu dai me yiwa kowa magana ya biya kudin suka koma asibiti. A mota ya barta yace ya kai musu sannan suka tafi gida.


Zayyan na komawa gida ya sami Mairamansa a kwance Radhiya ta bata tea taki sha wai bacci kawai take son yi ta rabu da ita. 


"Jeki abinki Alheran ajiye min tea din" yace da ita.


Tana fita ya cire rigar khakinsa ya rage singlet da godon wando ya kwanta a kusa da ita tare da janyota jikinsa.


"Fillo me yake damunki ne kwanakin nan na lura kamar baki da lafiya."


"Stress ne Sojana kuma kaima kasan dole ne tunda kun dauko mana abinda yafi karfinmu."


Dariya yayi yana shafa kwantaccen gashin kanta da yake nadewa da kansa saboda laushi. Dinner ce angwaye suka tsara abarsu Baban Arifah yazo ya chanja komai. Abokansa 'yan siyasa da manyan mutane wasu ba zuwa Jos zasuyi ba shine suke ganin kawai gara ayi wata a Abujan. Sai kuma bangaren sojoji da suke yiwa Zayyan kallon wani celebrity suma kowa yana son zuwa bikin 'yarsa. Excellency yace bai ga amfanin ayi taro gutsi-gutsi ba alhalin mutane daya ne zasu zo. Kuma dama bikin ya rabu kashi kashi ayi ta tara gajiya da barnar kudi. Hakan da yayi ya kara masa kima a idanun su Baba Hadir da Daddy domin ya nuna yasan zafin nema ba kamar yadda yake a wurin 'yan siyasarmu ba ayi sati ana biki ana barin kudi. Shiyasa su Mama kullum suna tafe ana ta shiri domin suyi taron da zai kayatar ya fitar da mazajensu kunya.


A cikin kunneta Zayyan yace "ni kuwa sai nake ganin kamar na tureki ne Fillo"


Da saurinta ta tashi zaune "rufa min asiri da abin kunya Sojana. Muna bikin 'ya ka tureni da wane ido zan kalli mutane."


"Kin fiye tsoro kamar ba matar soja ba. Ina ruwanki da mutane. Iyaka ki goya namu ta goya nasu ba shikenan ba"


"Ni dai ka dena wannan fatan" tace tana sake narke masa.


"Yanzu ma na fara, kinsan irin farincikin da zanyi kuwa idan gaske ne? Hmmm Fillo kiyi fatan Allah Ya amsa domin ki ganewa idanunki babban matsayin da zaki kara takawa a zuciyata"


"Kana nufin akwai inda ba ni bace dama?"


"Ko daya, sai dai zan kara mata fadi ne domin a haka kinyi mata yawa" yace yana kara rungumeta tare da addu'ar cikar burinsa.


A nata bangaren itama hasashen cikin take yi amma kunyar kasancewarsa take. Ina zata boye kanta ace tayi ciki bayan ta aurar da 'ya. Ga tarin fargabar yadda Zainab ta haihu.


Sai dare ta iya saukowa Emzee yayi musu bayanin abinda likita yace. Mairama taji babu dadi sosai. Wata kiyayya ta banza da Salame ta dorawa kanta ta janyo ta makanta 'yarta da bata yi mata laifin komai ba. Kuka sosai Rahima take yi Zayyan yace kowa ya fita ya barsu da ita. Daga shi sai ita da Ummi ya rinka yi mata nasiha akan hakuri da karbar kaddara. A nutse yake janta karshe ya nemi jin me take son karantawa idan ta gama makaranta tace Nursing take so. Murmushi yayi yana yabawa zabinta sai dai wani hanzari ba gudu ba shine makarantar da aka sama mata sun ce sai sunyi mata gwaji kafin ta shiga SS3. Idan bata sami result irin wanda suke bukata ba sai ta maimaita ajin.


"Daada repeting fa kenan a wayance" tace a sanyaye da guntun hawayenta.


Ummi tayi dariya "kin ganni fa tare muke tafiya da yayyenki Ibrahim da Karami. Yanzu nan da sati biyu zan koma makaranta ina level 4 suna level 4"


Murmushi tayi kafin tace "Nasan ma sai sunyi min ko don English da Maths" 


Kwantar mata da hankali Daada ya cigaba da yi yace ko me ya faru kada ta damu. Ummi kuma tace za'a daukar mata lesson teacher a gida. Bayan ta koma wurin Radhiya wayar Malamijo Ummi ta kira ta fada masa.


Fada yayi kamar ya ari baki karshe yace "Mairama kinga hakkinki ko"


Hawaye ta soma yi "Malamijo ka dena fadin haka kaddararmu ce daga ni har Rahiman"


"Ai ko ban fada ba hakan ne. Salame ko kadan bata da hankali. A da bata damu da Rahima ba yanzu kuma hakkin yarinyar nan bibiyarta yake duk inda ta zauna bata da zance sai Rahima kamar wata sabon kamu. Tayi ta nunawa mutane kafarta wai ita tayi mata lalle..."


Dariya ce ta nemi kwacewa Mairama tace "Kayi hakuri ba da niyar bata maka rai na fada ba"


Albarka ya rinka saka mata yace ba da ita yake fushin ba yana dai jira ya gani ko wannan dalilin zai sa Salame ta dawo hayyacinta sosai. A yadda ya tsara Na'e da wasu ne cikin yaran zasu zo Abujan. Yadikko taje Sakkwato ita kuma Hajjo taje Nijar. Maman 'yan biyu dai banda ita a wannan yawon yaranta kananu ne ga zaman mota.


**********

Bikin kwana biyu suka halarta a Jos tare da su Tante Nasara da wasu daga Nijar da suka taho tare. Kudi dai yayi kuka to amma ba abin mamaki bane duba da cewa biki ne na 'ya daya tilo ga gwamnar jihar tasu.


Gabadaya aka dunguma suka koma Abuja wasu a mota wasu a jirgi. A hanya Ummi ta rinka amai kamar zata fitar da kayan cikinta don sosai ta galabaita. Mama tana sannu tana murmushi wanda ya janyo Ummi kai kararta wurin Mami. Hakuri Mami ta bata tana gargadin Mama da ido saboda birkici musu da Ummin tayi. Zuwa yanzu ta gama tabbatarwa ciki ne duk da bata je asibiti ba hankalinta duk ya tashi ina za ta kai abin kunya a cewarta. Da su ka isa gidan Daada su duka ukun suka sauka a nan ana lallaba patient. 'Ya'yan nasu basu san me yake damunta ba sai hawa suke ana mata sannu. Sai da ya rage su hudu a dakin da Tante Nasara sannan Mama ta kasa hakuri ta soma tambayarta.


Doki ne ya isheta tana dariya "Ummin Awwab anya baki harbu ba?" 


Ummi ta gama aika mata sakon harara kamar ido zai fado "kin manta bindigeni akayi"


Su duka ukun suka sa dariya ta sake hade rai lokacin da Tante tace "abar zancen wasa matar Yaya kamar

Please Login or Register in order to submit comment