Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

girma sai sabuwar sangarta ke shigarta"


Murmushi Zayyan yayi "dole na jira. Ya batun abincin mutanen nan?"


Mairama tace masa an kusa saukewa. Waya ya dauko ya kira Emzee da suke tare da Awwab da yace su jira ko a gonar Malamijo ne sai ya kirasu. Mairama ce ta karba ta fada masa inda su Radhiya suke tace su daukosu su dawo gidan.


Zamanta tayi suna ta hira da Zayyan a ciki kuma Salame ta shige tsohon dakinsu da Mairama zuciyarta sai zafi take ta rasa inda za ta saka ranta taji dadi. Duka fadin gidannan kowa baya sonta tayi bakinjinin da ita da kanta ta rakitowa kanta.


***********


Mota bata karasawa kofar gidan saboda haka daga can nesa kadan Emzee yace Awwab yayi parking ya karasa a kafa. Ya shiga suna gaisa da mutane Radhiya da Rahima a tare suka ji muryarsa. Radhiya ce ta fara fitowa daga dakin da suke da sauri Emzee yayi kamo hannunta a dan birkice saboda fuskarta da ya gani tayi ja.


"Adda ina da ina ne yake miki ciwo? Kun koma asibitin? Sun baki magani?"


Murmushi tayi "kai Emzee irin wannan tambayoyi"


"Da kyar na wayi gari inata tunanin ko yaya kika kwana. Zo mu tafi tare muke da Hamma" yace yana kallon Rahima dake tsaye a bayanta ta janyo hijabinta ya rufe mata fuska.


Mamaki ya kama Radhiya duk da tasan  cewa dama zai damu saboda rashin wayarsu jiya. Yau kuma tun safe take gwada tasa wayar a kashe ashe yana sane. Murmushi tayi dimple dinta ya shige ciki sosai ta kamo hannun Rahima tana ce masa itama fa akwai ciwon a jikinta.


Tabe baki yayi "Allah Sarki"


Wata irin fargaba taji a take ta dago kai ta kalle shi sai ta ga yayi gaba abinsa yana yiwa mutan gidan sallama kamar bai san da zamanta a wurin ba.  Idanunta suka cicciko da kwala tana mamakin wannan abu. Yaki daukar wayarta tun jiya yau kuma ya ganta ya share. To ko dai yana fushi ne saboda Ummansu ta daki yayarsa ta tambayi kanta. Babu mai jinta bare ya bata amsa haka ta fito a sabule ta bi bayansu.


Tun kafin ta karaso wurin motar Awwab ya fito ya dora hannu a jikin kofar bangaren da yake yana kallon yadda Radhiya take tafiya tana dan cije lebenta na kasa. Gashi wurin da mutane dole ya daure ta karaso.


Gaba Emzee ya tafi zai shiga Awwab ya hade fuska cikin wasa yace "haba inlaw koma baya ka barni naji ya kwanan iyali"


Murmushi Emzee yayi Radhiya na dariya idanunsu suna cikin na juna Rahima tayi murmushi ta shiga baya. Ga tsananin mamakinta wata muguwar harara Emzee ya doka mata yana ganin kawai da gangan tazo masa shiyasa taki fada masa wace babarta.


"Hamma bari kawai zamu taho a kasa ga Halifa can na hango ya fito"


"Wasa nake fa shigo mu tafi kada mu bar Daada da jiranmu"


Ai baya jin yana kaunar zama inuwa daya da Rahima. Ayatul kursiyyu ya shiga karantawa yana son idan ma wani abu aka yi masa Allah Ya bashi lafiya. Ko da yaji, wannan soyayya da yake mata daga haduwarsu a ranar ko baccin kirki bai iya yi ba sai aikin tunaninta. 


"Ina biye daku dama babu nisa fa" yace kawai ya taka ya riski Halifa. Awwab ya ja motar tare da kamo hannun Radhiya ya rike gam. Ba magana suke yi ba sai dai kallon da suke yiwa juna kawai mai cike da shauki. Rahima bata kula da abinda yake faruwa a gaban ba saboda tashin hankalin da take ciki. Me ya sami Emzee kamar bai san ta ba.


Suna zuwa gidan ta sauka daga motar ta shige ciki. Awwab ya dago hannu ya shafa fuskar Radhiya ta lumshe idanu. Jinginar da ita ya yi kokarin yi yana cewa "bayanki bazai sage ba kin zauna kinyi gaba Schatzi"


Da sauri ta dago jin zai hada bayanta da kujerar tare da yin kara cikin wani irin sautin wahala "aashhh Chèri da zafi"


 Gabadaya Awwab ya rude "mu gani" yace yana shirin kwanto da ita jikinsa ta matsa da sauri tana rufe idanu.


"Silly girl" ya ja hancinta "ashe ciwon ba na gaske bane tunda bai hanaki jin kunya ba"


Kyabe fuska tayi kamar me shirin kuka "Hammana ina kayan dubiya?"


"Bayan kin fada min kika yi sai a wurin Mami naji."


"To kuma sai ka taho hannu na dukan cinya" 


Kai ya girgiza yana dariya "wata maganar idan kika yi sai ta tuna min wata yarinya da na hadu da ita shekara uku da suka wuce a falon Mama mai kwalkwalin kai"


Shan kunu tayi tana kumbure kumbure "sai na fadawa Daada kana tsokanata"


Dariya yake mata ta cukule fuska "baki san yadda hoton kan yarinyar ya zauna min bane a kaina"


"Kaga bana so"


"Idan baki so a bani janbaki na shanye ki gani idan zan sake tsokanarki" ya kare da lumshe idanu yana budesu a kanta.


Kunya duk ta kamata shi kuwa kamar ya cusata a zuciyarsa kawai yake ji saboda yadda komai nata yake burge shi. Hira suke yi a nutse yana ta tsokanarta daga baya ya kare da bata shawarar a matsayinta na babba kada ta bari ko kadan su Rahima su ga wani chanji daga garesu. A irin wannan lokacin ne mutum yake kwasar lada domin ya rama sharri da alkhairi. Sosai take jindadin shawarar tasa kafin daga baya su gangara kan shirin dinner din da za ta daki Abuja nan da kwanaki.


Halifa da Emzee basu dade ba suka isa gidan inda suka shiga dakin da iyayen nasu da kakanni suke. Emzee yana kallon Umminsa ya hango Rahima a jikinta Ummin kamar tayi kuka tana kallon fuskarta.


"Ni dai ko asibiti zan kaita ne a Kano wannan idon yayi kwanciyar jini" tace tana juya fuskar Rahiman yadda su Innawuro zasu gani.


Kirjin Emzee yayi wata irin dokawa saboda yadda fuskar Rahimansa ta koma...Rahimansu dai ya gyarawa kansa da sauri tare da saurin barin wurin. Yana tafe fuskar tana masa yawo a ka cike da tashin hankali. Ba zato yaji ance "Karami"


Juyawa yayi yana kallon Salame tayi wani iri. Fuskar Rahima ya tuna yaji ransa ya baci amma albarkacin Ummi sai ya gaisheta. Kasa boye mamakinta tayi saboda tasan bata kyauta musu ba amma yaran suna da ladabi duk da fitinarsu da ake gani musamman Radhiya.


"Uhmmm dama...nace...dama...uhmm"


"In tafi ne?"


"Cewa nayi ko za ka kira min su Radhiya da Halifa"


"Radhiya ko Rahima?"


"Radhiyan dai" kunyar ganin Rahima take ji sosai kuwa.


Wayarta ya kira sannan ya tafi kiran Halifa wanda tun a hanya yake bashi hakuri yace kada ya damu magana ta gama wucewa.


Radhiya da Halifa sunje sun sameta sai ta rasa abin fada sai da Halifa yace zai tafi ta iya hada kalmar hakuri ta baiwa Radhiya. Murmushi kawai tayi tace babu komai saboda yadda bata sakewa a gabanta. Bayan tafiyarta ne ta dan sassauta murya tace da Halifa


"Me kanwarka take cewa game dani?"


"Me zata ce kuwa Umma banda kuka"


Shiru tayi na rashin sanin abin yi kafin daga baya tace "wai fuskarta ta kumbura?"


Shi gabadaya ya kosa da tsayuwar ma "bari na kirawo miki ita ki gani"


"Dawo Halifa" tace tana yafito shi da hannu bai tsaya ba sai da yaje kofar dakin da suke.


"Rahima kizo inji Umma"


Duk wanda yake wurin ya ga firgicin da ya bayyana a fuskarta ta kankame Mairama sosai har ta soma kwalla.


"Tashi kije Rahima" Nene ta umarceta.


Tamkar wadda kwai ya fashewa haka ta mike tana kallon Ummi ko zata ce mata ta zauna sai ta ga tayi mata alamar taje. A tsorace take sosai ta fito ta bi bayan Halifa. Tana zuwa daga nesa ta zube a kasa ta gaisheta. Salame ta amsa yau babu wannan hura hancin.


"Dama jiranki nake yi mu tafi"


A kidime tace "ina?"


Murmushi Salame tayi wai nan ita gyara za ta yi "muje gidana kiyi min kunshi saboda Kamun gobe. Amma ki fara dauko kayan da zaki saka goben sai mu shiryo daga can"


Abinka da rashin sabo Rahima sai jin abin tayi bambarakwai ta kasa cewa komai sai faduwar gaba. Halifa take kallo tana neman agaji.


"Umma ita za ta yiwa Radhiya kunshi fa ko?"


"Eh da su Anti Laila" ta ce cikin sauri.


Salame ta fuskanci akwai tsoronta a tattare da Rahima to amma so take ta gyara ya kamata su bata dama.


"Nima ina nan din zan jira ki sai ku fara da wuri saboda yau nice da girki." Ta murmusa hakoran nan masu gansa kuka suka bayyana "yau sai ki tayani muyi girkin tare"


Qut...Rahima ta hadiyi yawu Halifa ya kalleta ya danne dariya saboda yasan karshen takura da tashin hankali tana cikinsa. Salame ta bar wurin batare da Rahiman ta amsa ba can kasan zuciyarta tana jin wani iri game da yadda idon yarinyar ya koma.


Yarfe hannuwa Rahima ta shiga yi tana kallon Halifa "yaya zanyi?"


Tausayinta yaji a ransa yana murnar shi namiji ne don gaskiya bai hango yadda zai iya kwana da ita ba da shine Rahima. Babu wata sakewa ko shakuwar uwa da 'ya kawai sai ku kwanta kusa da juna. 


Kiranta taji Radhiya tayi bayan tafiyar su Emzee suna wurin Ummi tace a kira wata mai lallen Rahima babu wanda zata yiwa saboda idonta. Radhiya dama a yatsu kawai zata yi saboda dai kada ace amarya ba kunshi. Gidan ya soma kaurewa da hayaniya Ummi ta fadawa Rahima ta tafi gidansu ta hado duk wani abu mai mahimmanci musamman takardun makaranta da ita zasu koma gabadaya. 


"Ummi gabadaya kika ce?" Ta kasa boye farincikinta. Tana son Mairama tsakani da Allah saboda a dangin mahaifiya babu inda ta ga soyayya da kulawa kamar a wurinta. Bayan la'asar kuwa ta sulale ta fice a soro ta hadu da Salame "yauwa dama ke nake jira muje" ta nuna mata kofa.


A tsorace tace mata kaya zata debo a gida. Salame ko a jikinta tace idan ta dauko ta taho gidanta gobe sai suyi sammakon fitowa.


Yau Rahima an shiga tsaka mai wuya. Yanzu idan ta rufeta da duka tana cikin bacci fa.


"Naji ance jibi zaku wuce ne kinga zai kyautu mu kwana muna hira tunda zamu jima bamu hadu ba"


Jiki a sanyaye tace to tayi hanyar gidansu. Baffanta da Iya basu ji dadin ganin yadda idonta yayi ba ta hada 'yan kayanta masu kyau ta fada masa inda zata kwana. Nan yayi tsalle ya dire yace ba dashi ba babu inda zata je. Iya ce tace ya kyaleta tunda babu mai rabata da mahaifiyata. Ba don taso ba haka taje gidan. Kanenta na binta da ido shekeke Salame ta daka musu tsawa tace bazasu gaishe da yayarsu ba.


 Rahima da yaran a tare suka firgice Salame ina ma ta kula sai fada take wai basu da tarbiyya basu san girman na gaba dasu ba. Murhu ta hada ta dawo ta kirata wai ta tayata tankade. Tare suka yi girkin tana ta dararewa saboda kada jikinta ya gaya mata.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Tare suka yi girkin amma Rahima ce karfin aikin. Yaran gidan sai binta suke da kallo ita dai kanta na kasa har suka kammala. Baffanta ne ya kira Ummi ya sanar da ita inda zata kwana kada suji shiru. Addu'a ta rinka yi Allah Yasa kada wani abu mara dadi ya biyo baya. 


Lura Salame tayi da yadda Rahima take tsakurar abincinta. Tuwon masara ne da miyar karkashi sai tashin daddawa take yi ga sukunbiya an saka saboda ita. A cikin kwanon silva ta zubawa Rahima ta kwarara miyar a kai. 


Sai da ta gama lashe hannunta ta bi irin abin miyar nan da ya kan makale a tsakanin hakora da harshe tana sakato shi sai ji kake tana tsk-tskk da baki ta kora da ruwan rijiya sannan ta tabe baki.

"Abincin namu bai kai na 'Yan Abuja dadi bane naga kina ta yafita kamar bakya so?"


Kafin ta kai karshen maganarta Rahima ta zunduma wata katuwar loma wadda ta kasa hadiyewa saboda bata kaunar karkashi ko kadan. Da gudu taje bakin rariya ta zubar ta dawo tana jiran Salame ta soma fada sai taji tayi mata magana babu wannan fadan.


"Ba kya cin tuwo ne?"


"Miyar...miyar ce dama...dama karkashi ne....bana sha"


"Yo maimakon ki fada nayi miki hadin mai da yaji sai ki cuci kanki? In kin fada min ai ba dukanki zanyi ba" tace da ita amma idan kaji yadda muryarta ke fita sai ka dan tsorata. Takaicin yadda yarinyar ke zabura duk motsinta ne yake damunta. Kwanon ta dauka ta mikawa sauran yaranta da gudu suka far masa dama sun cinye nasu ita kuma taje kitchen ta dibar mata wani cikin sauran da zasuyi dumame dashi da safe. Mai kwantirola ta yaryada mata da gishiri ta dauko yaji da rabin maggi a dakinta ta saka sannan ta bata. Ko kadan wannan hadi bai yiwa Rahima dadi ba saboda man danye ne sai karni ke tashi amma kyautatawar da mahaifiyarta ta gwada mata karon farko tun wayonta yasata yin kwalla ta janyo farantin ta cinye shi duka. 


Basu wani jima da gamawa ba Alh Indararo ya dawo gida Salame ta kai masa nasa abincin. Kayan jikinta tun na jiya ne babu zancen wanka a ajandarta duk kuwa da cewa da murhu tayi girki ga kauri ga datti. Tunda ta shiga banda harara da habaici babu abinda yake mata ya gama cin abincin yace ta fita kada ta sake zuwa turakarsa da sunan kwana sai idan da kansa ya nemeta. Abu na biyu kuma ya bata lokaci kankani ta san yadda zata yi su daidaita da Mairama a basu ko da mutum biyu ne cikin yaran shi ma a rage masa nauyi.


Kallon raini ta bishi dashi "wannan shi ake kira karfin hali barawo da sallama."


Hannu ya kawo da sauri zai sauke mata ta fita ba shiri yana ta fada kuma wai kashin tsiya gareta kada ya kuma ganin kafarta a dakin. Dama waye ya aiketa bayan jiya ya mata dukan nan jiki yayi tsami. Dakinta ta koma aka yiwa yara shimfida Khadi tana gado tace da Rahima.


"Kwaba lallen kizo ki yayyaba min dashi zan kwana saboda ya kamu sosai"


"Kada ya cabe ko ba mai ado kike so ba?"


"Ado kai 'yan nan. Kada ki damu zan iya kwana dashi."


Duk yadda idonta yake damunta bata nuna ba ta kwaba lallen nan ta zauna. Wayarta ta soka a gaban dankwalinta bayan ta kunna torchlight saboda rashin wuta sannan ta kamo kafar. Dandakuwa sunan wani abu. Ga datti da wani maiko maiko ga yalwataccen  kaushi yabi ko ina a cikin kafar babu inda babu. Kamar ta ce mata ko zata wanke kafar amma babu fuska sai uwar hamma da Salamen take yi. Ba yadda ta iya haka tasa kasan zaninta ta goge kafar sosai sannan ta baje basira ta soma zane. Goma ta wuce ta gama Salame tace mata ta kwanta a daya gefen ya zamana Khadi na tsakiyarsu. Da kyar ta iya bacci saboda rashin sakewa da sabo. Asubar fari kuwa ta mike ciwon ido yayi sallama ya kara nauyi tana ruwa. Alwala ta dauro ta zo ta tashi Salame ta kwashe mata lallen ta goge hannuwan da kafafu sannan itama tayi alwalar. Tun a lokacin tana iya ganin yadda lallen nata ya fito radau yayi kyau musamman hannuwanta. A sannu sannu gurbin da ta danne Rahima a zuciyarta ya fara neman nuna kansa ga duniya. Sai take jin wani takaici da haushin kanta na kin sakarwa yarinyarta tun farko.


Sunyi sallah Rahima ta gaisheta ta amsa tare da cewa ta bude idon da ta rufe mana. Ai kuwa tana ganin yadda ya kuma hadewa gabanta ya fadi. Hakuri ne tun jiya ta kasa bawa Rahima sai yanzu take sake ganin rashin hankalinta. Ruwan kunu taje ta dora da ya tafasa ta debi wani a bokiti tazo ta gasa mata wurin. Babu wani sauki da taji amma abubuwan kyautatawar da Ummanta ke yi mata kadai sun isheta farinciki. 


Kafin ta dawo daga dama kunun Rahima ta soma janyo kayayyakin da suke soke a lungu da sakon dakin babu wadatar isa ga zarni da wari duk ya hada. Gari guda ta hada wanki sannan ta soma shara Salame ta shigo. Tunda take dan cikinta bai taba yi mata shara ba. Na gabanta banda cin tsiya da fitsara basu san komai ba. Halifa namiji ne, macen da zata yi kuma ta dauki karan tsana ta dora mata. Bata ce mata komai ba Rahima ta aikatu sai wuraren shabiyu ta gama gyara dakin. Wankin kuwa Salame tace zata yi da kanta.


"Lokaci na kurewa shirya ki tafi gidan Malamijo zan taho anjima ki bar min wankin"


Wanka taje yi bandakin babu kanta sai kawai ta shafa ruwa a fuska da kafa ta fito sauran ta wanke musu bandakin. Da sauri ta shirya suka yi sallama ta fito. Sai yanzu ta saki ajiyar zuciya ta sami nutsuwa saboda duk a tsorace take.


Da zuwanta gidan tayi sa'ar samun bandakin da babu kowa ta nemi ruwan zafi tayi wanka. Ido suntum ta shiga daki wurin Ummi hankalinta ya sake tashi. Abinci ta sa ta ci suka tafi asibiti a cikin garin. Sai bayan azahar suka dawo anyi mata allurai tasha magani ta kwanta bacci.


Biki yayi biki gida ya cika da dangi abin farinciki harda wasu cikin mutanen Sakkwato banda na rugar Barkindo zuga guda. Anci an sha babu kwandalar Mairama ko ta mijinta. Malamijo ne yayi kusan komai sai kuma kannen Mairama su ma wasu katan din lemo, akwai wadda tayi zobo da ginger aka kulla a leda, cincin da meatpie kowa dai ya nuna da gaske sun gaji da zaman doya da manja zumuncin suke muradi ayi.


Amarya Radhiya sanye take da leshi mai dan karen kyau ja da adon duwatsu anyi mata dinkin buba ta daura zamin a kai. Kafarta babu lalle sai yatsu kawai haka ma hannu amma tasha ado ba kadan ba. Sarkar beads aka yi mata shirin ya kayatar matuka tana tsakiyar fili ita da Mama da 'yan uwa ana kidan kwarya. Rawa take tana juyi karaf idanunta suka gano mata shigowar Gwaggonta Salame tana tafiya tana dafa bango saboda takalminta. To da yake Allah baiyi ta mutum mai riko ba indai anyi abu ya wuce to fa ya wuce kenan a wurinta sai dai dan abinda ba'a rasa ba. Shiyasa take kaifi daya babu munafurci ayi komai a wuce wurin. Tana takun rawar a girgiza 'yan mata da masu kidan suke yi taje ta riko kafadun Salame ta kawota tsakiyar fili. Ba laifi tayi kyau atampa ce a jikinta ta sako wani takalmi da bai tsufa ba tun na lefe saboda bata sakawa sosai yayi mata tudu. Yau kuwa dole a dama da ita kowa yasan cewa bata karewa Salame ba.


Bata gama gyara tsayuwa ba Radhiya ta rinka juyi da ita ana girgiza jiki ana rawa. Salame tayi wuri wuri ta jigata 'yan uwa aka basu fili ba abin ta gudu ba ace bata son zumunci tafi kowa laifi. Wata kanwarsu ce ta leka dakin da Mairama take zaune da Rahima mai bacci tace mata ta leko tasha kallo. Daga bakin kofa ta hango rawar da suke tika harda su Hajjo amma Salame jikinta yafi na kiwa girgiza saboda Radhiya ta matsanta mata. Me Mairama zata yi kuwa banda dariyar yadda suke yi. Daidai lokacin Salame ta dago kai suka hada ido Mairama ta daure fuska kamar ba ita ke dariya ba ta shige dakin.


Kwafa Salame tayi cike da takaici a zuci take ta babatu "jimin rashin mutumci fa, tana kallo 'yarta za ta ballani maimakon ta tsawatar shine ta koma daki, yanzu kayi magana a hadaka da sojoji saboda rashin gata"


Wani kanin Mairama ne mai hoton yazo aka fara sannan fa Salame ta samu damar sabulewa. Malamijo ma yazo ansha hutuna yana rike da 'yan biyunsa. Kyautar saniya da sa ya yiwa Radhiya babbar jika yace amma a barsu a gonarsa ya cigaba da kiwata mata. Abu yayi kyau zukata sun haskaka da farinciki.


Bayan isha ne Salame ta gama shirin tafiya ta shiga neman Rahima. Haka kawai take son su tafi tare jiya taji dadi har ranta ko da bata iya nunawa ba. Tana daki wurin Mairama tana faman lallabata taci abinci. Gobe da sassafe zasu tafi saboda a kaita asibiti. Yanayin idon ya soma bata tsoro. 


Daga jikin kofa Salame ta coge taki yiwa Mama da Ummi magana sai Rahiman ce tace mata "Umma inzo mu tafi ne?"


Keyar Mairama kawai take gani amma jikinta ya bata gara ta hakura kafin wani abu ya biyo baya. Duk da haka ta ga yana da kyau ta tunawa kanwarta wace tayi ciki da goyon Rahima.


"A'a yi zamanki Rahimata, gobe zan shigo da wuri kafin ku wuce mu karasa hirarmu ta dazu. Kayanki kuma zan bayar a kawo miki yanzun nan"


Dariya ce ta ciwo Ummi wai Rahimata...to dama waye yace ba tata bace? Ita kadai ta nesanta kanta da yarinyar kuma zata fi kowa farinciki idan taja ta a jiki ta sami soyayyar uwa kamar kowa. Sake maimaita kalmar tayi sai dariya tana ta kokarin dannewa amma yadda Salamen tayi magana dole mutum ya dara. Mama na ganin haka ta tace Rahima ta kawo ruwa kwarewa tayi. 


Tana fita ta kalli Salame da ke tsaye har yanzu "dan bubbuga mata bayan mana Adda Salame kina tsaye tana tari"


Idanu ta zaro kamar zasu fado tace "wa? Ni....shegiya inji dan daudu. Rufa min asiri ina tabata yanzu zaki ji dirin motocin sojoji ana kiran Salame"


Kan kace kwabo ta fice abinta ko da Rahima ta dawo bata nan. Washegari sammako suka yi saboda yadda Ummi ta matsu suje asibiti kullum idon kara kumburi yake yi. Ta yiwa Malamijo zancen masu zuwa biki yace kada ta damu zai turo wasu Abujan wasu kuma su bisu Sakkwato har zuwa kai amarya Katsina sannan wasu daban suje Nijar. Hakan yayi mata kuwa sosai.


A ranar Mami itama da nata gayyar suka wuce Abuja. Abinda ya bata mamaki bai wuce biyosu da Fauziyya da Bilal suka yi ba. A take ta nunawa Fauziyya bata son yawo ta bari har sai ana gobe Bilal yace shine yake son su tafi saboda akwai abinda zasu yi da Raji da angwayen. Bata matsa son jin ko meye ba suka kama hanya.


**********


A Abuja azahar ta riskesu saboda sammakon da suka yi. Dan kwana biyun da babu Mairama Daada yaji jiki saboda har yau gani yake ko daya bisa dari na fanshe rashin matarsa baiyi ba. Yana falonsa na kasa suka iso Radhiya ta makalkale shi yana dariya. Ita kuma ta lura hakan na masa dadi sai yaji kamar bai rasa komai ba na rayuwar 'ya'yansa shiyasa take yi. Rahima na gefe tana murmushi ta gaisheshi ya sakar mata fuska fiye da yadda yake yi kwanakin baya da ta zo.


"Auta bakya laifi wannan daurin har ido na meye?"


Ummi ce tayi masa bayani Radhiya ta kwance ya ga idon ransa kuwa ya baci kamar ya ga Salame a gabansa ya saita mata fuska. Da kansa ya kira Emzee da ya bar gidan tun safe kuma saboda zuwan Rahiman ne yace yazo bayan la'asar ya kaisu asibiti. Bai ma san waye za'a kai ba amma dolensa ya amsa umarnin mahaifinsa.


Karfe hudu da rabi ya iso Ummi ta sauko sanye da riga da zani da hijab ta tura mai aiki kiran Rahima. Tamke fuska yayi bayan sun gaisa tunda yaji sunanta. Doguwar rigar atampa ce a jikinta ta dora rigar sanyi mai zip ta gaba mai dan fadi tare da hijabi fashion wanda ya zarta kafadunta da kadan. Idonta kuwa hankici tasa ta dafe shi bata son haske na ratsa shi.


"Ina wuni" tace da ta iso kusa da shi da Ummi.


Waya ya shiga dannawa baji ba gani yana a'uziyya a zuci wai kada a sake makalo shi da wani nau'in siddabarun a cikin muryarta da take masa dadi har yau. 


"Baka ji ana gaisheka ne?" Ummi tace tana nufar kofa za ta fita.


Sai da ya harari Rahima mamaki ya sake kamata sannan yace "na amsa Ummi baki ji bane"


"Wai haka Rahima?"


"Ummi ya amsa" tace tana murmushi. 


Emzee na ganin Ummi tayi waje ya dawo kusa da Rahima kamar gaske ya kuma daure fuska "babu kunya kike yi mata karya, ni nace ki rufa min asiri ne?"


Jikinta ne ya soma rawa saura kadan ta fashe da kuka tace kasa yayi hakuri kawai ta wuce. Da ta karasa bakin motar ma baya ya bude duka bangare biyun yana cewa wai su shiga baya tare zasu fi jindadi. Ummi bata ce komai ba tayi zamanta yaji dadin hakan saboda don bai san karyar da zaiyi mata ba idan ta tambayeshi.


Asibitin Samu Wadata su ka

Please Login or Register in order to submit comment