Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata da laifi insha Allahu zan kula da ita tamkar Yasmeen ka gaisheta kace nace dole ayi kamu".
"zataji Mum sena dawo".
"toh seka dawo Allah ya tsare".
"Ameen ".
nanya fita yabar Mum da Yasmeen sunata yabon Inteesar.




Direct unguwar su Inteesar ya nufa ya tsaya daka ɗan nesa da gidansu yayi parking yayi hakan yayi daidai da fitowar Hauwah zata shiga gidansu Inteesar daga nesa ta hangi kamar motar Zaid mamakine yakamata ganin ya tsaya nesa da gida shiga gida tayi cikin sauri Jameelah dake raɓe a zaure tana ganin wucewar Hauwah cikin sauru ta fice ta nufi inda yayi parking tashiga yaja suka ɗauki hanyar oasis.




Samun Inteesar tayi ta fito daga wanka se ƙamshi ketashi sakamakon anfara yimata gyara cikin girmamawa tace"Ummih sannu da hutawa".
"yauwa Hauwah".
"Inteesar kunyi waya da Uncle Zaid ne naga motarsa a ɗan nesa da gidannan".
"a'ah mekika gani ".
"motarsa nagani aɗan nesa da gidannan ".
"ko ɗaya wataƙila gurin Abbah yazo zasuyi wata maganar".
"ƙila kuwa".
nan suka cigaba da hirarsu batare da zargin komai ba.




Suna isa Oasis yana gama parking cikin shaukin so yace"ƙanwata bara na buɗemiki saboda banaso kina aikin wahala".
"kaji Yayah daka barshi ma na buɗe aiki ni nake aikin abincin gidanmu gabaki ɗaya".
"eh dai kidaibari na buɗemiki".
"toh".
nan ya fita ya zaga ya buɗemata suka fito suka nufi cikin gurin ɓangaren Namijin duniya ma baƙaramin siyayya yayiwa su Rahama ba shikuma yasamu seat ya zauna yasa sukayi oder duk abinda sukeso aka kawomusu bayan sun gama cine yabawa Rahama atm card ɗinsa aka ciri kuɗin abubuwan da suka siya yayi gaba suna binsa a baya necklace ɗin dake hannunsa ce ta faɗi ya duƙa da niyyar ɗakkowa kafin yakai ƙasa Zaid ya rigasa!!!!!!!!!





*Kuyi haƙuri Sisters bani da lafiya se yau na samu sauƙi dan Allah ku sakani a addu'o'inku .*




Votes and Comments





_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_# Real eeshow



_*Paidbook ,Amount Nml grp 300,Vip 800, pc 1k, Account Detail 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank, or Vtu mtn or airtel ga ƴan Niger kuma zaku turo da katin Airtel na daidai kuɗin da kikeson shiga aiko da shedar biyanka/biyanki ta wannan number 08108362334.*_


Book 2


4️⃣1️⃣➡️4️⃣2️⃣



Yana ɗagowa da niyyar basa sukayi ido huɗu da Namijin duniya kallon-kallo suka shiga yi yayinda Namijin duniya ke jifansa da kallon tuguma cikin inda-inda Zaid yace"Ina yini Yah Abdallah".
"lafiya ".
yana gama faɗin haka ya miƙa hannu ya anshi necklace ɗin hannun Zaid ta gefan ido ya kalli wadda ke gefan Zaid a zuciyarsa yace"kenan yaudarata yakeyi".
rasa me basa amsa ne yasashi fara tafiya yana mamakin abinda idanunsa suka ganemasa lokaci ɗaya yaji wani abu na tasomasa daga zuciyarsa se huci yakeyi yayinda yakejin haushin kowa direct gurin da yayi parking ɗin motarsa yashiga tare da jingina da jikin seat yanajin zuciyarsa na mugun tafarfasa a zuciyarsa yace"meyasa zeyimata haka seda yarinya ta aminta dashi shine ze zage yariƙa cin amanarta aiko yazama dole na ɗauki babban mataki akansa ".
wata zuciyarce tace"tokai meye naka na damuwa da yarinyar da bata ganin darajarka yaje yayita yaudararta matsalarsu".
wata zuciyar ce tace"yazama dole ka kula da rayuwarta tunda a ƙarƙashinka take kaje kawai ka faɗamata koda zata gwasaleka shine kawai mafita".
jin shigowar su Rahama ne yasashi buɗe rinannun idanunsa da yaketa ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yashiga yiwa motar key dafa kafaɗarsa Rahama tayi tare da cewa"Yayah meyasa naga gabaki ɗays mood ɗinka ya canza daka haɗuwa da Yah Zaid lafiya".
ba tare daya kalleta ba yace"bakomai sweetheart muje nakaiku gida inada wani mahimmin aiki a office ".
"toh mutafi tare man Yayah".
"a'ah bari na kira Salisu driver yazo yamaidaku gida".
"toh".
nan yayi dialing number Salis yayimasa kwatancen ta hanyar da zasu haɗu yabada su ya nufi office ɗinsa cike da zaƙuwar son yaganta.




Ɓangaren Muhseen ko yana isa gida ya nufi part ɗin Abbansa zaune ya sameshi yana karanta jaridah Amminsa na haɗamasa tea ƙarasawa yayi cikin falon ya zauna kusa Abbansa yayi ƙasa da kansa kamar me neman wani abu yace"Ammih sannunku da hutawa".
"yauwa Auta waya taɓamunkaine ".
cewar Abbah yana aje jaridar dake hannunsa yajawo Muhseen jikinsa kwantar da kansa yayi a cinyar Abbansa tare da cewa"ba Zaid bane".
"me aminin naka yayimaka".
cewar Amminsa tana miƙawa Abbansa tea turo baki yayi kamar wani ƙaramin yaro yashiga zayyanewa su Amminsa duk abinda yafaru har abinda Zaid yayimasa be rage komai ba seda ya faɗamusu murya a raunane yace"Abbih dan Allah inaso kuyimun wata alfarma".
"faɗi Auta kota mecece indai munada halin yimaka zamuyimaka".
sauke numfashi Muhseen yayi tare da cewa"Abbih batama fi ƙarfinku ba dan Allah ku temakeni kuyimun ".
"faɗi munajinka".
cewar Amminsa dake maida hankalinta garesa ƙasa yayi da kansa yana wasa da ƴan yatsunsa tare da cewa"dan Allah Abbih inaso indai Zaid ya fasa auren Inteesar ku ɗauramun aure da ita a ranar kuma misalin lokacin ɗaurin aurensa da ita banaso a fasa komai".
shiru gurin gabaki ɗaya ya ɗauka zuciyar Muhseen se bugawa takeyi da sauri-sauri gani yakeyi dakyar idan iyayensa zasu yadda gyaran muryar da Abbansa yayine yasa jikinsa ƙarayin sanyi a zuciyarsa yanata addu'ah muryar Abbah ce ta katseshi daga dogon tinanin daya shiga yaji yace"indai wannanne Auta ka kwantar da hankalinka indai yadda ka faɗamana zancennan haka yake insha Allah zan nemamaka aurenta".
cikin farinciki Muhseen ya rungume Abbansa tare da cewa"nagode Abbana maganin kukana ina alfahari da samunka a matsayi mahaifina I love you Abbah".
murmushi Ammih tayiwa tilon ɗan nata ganin yadda yaketa farinciki tace"wato ni baka alfahari dani ko".
saurin sakin Abbah Muhseen yayi tare da rungume Ammih yace"niko nake alfahari da uwata datafi ta kowa a duniya amma Abbah karka faɗawa kowa wannan zancen a gurin ɗaurin aure idan yafasa sena aureta domin banaso duniya tayimuj kallon maci amanar abokinsa".
"toh Allah ya nunamana".
"Ameen".
nsnsuka cigsba da hirarsu daka bisani Muhseen ya nufi part ɗinsa ya kwanta a makeken gadonsa tare da kara wayarsa a kunne tare da cewa"ƙawar amarya se yanzu naga miss call ɗinki".
"eh dama kira nayi naji ya zancen schedule ɗin biki najiku shiru kuma abu se matsowa yakeyi ko ƙunshi bamuyiba".
murmushin takaicin abubuwan da abokinsa keyi yayi tare da cewa"turomun da account number ki nasakamuku kuɗin ƙunshi shaf na manta ne muna cikin hidima munata tsara event ne".
"okay toh bara na turomaka ".
"tom".
nan sukayi sallama yanamaijin tausayin Inteesar.





Yana shiga Comphanynsa ko parking beyi mekyauba ya buɗe ya fita ko takan masu gaidashi bebiba ya nufi gurin elevator yashiga ya nufi office ɗinsa mutane se gaidashi sukeyi bemasan sunayi ba ya tura ƙofar office ɗinsa da ƙarfi kalloj kujerar Sakatariya yayi yaga ba kowa hakan yasashi cikin sassarfa ya buɗe ƙofar da zata sadashi da office ɗinsa yana buɗewa sansanyan ƙamshin room freshner daya haɗe da sanyin ac ya bugi hancinsa lumshe sexy eyes ɗinsa yayi yana shaƙar daddaɗan ƙamshin tare dabin ko ina na office ɗin da kallo gani yayi ko ina fes dube-dube yashigayi koze ganta ganin beganta anan bane yasashi nufar toilet direct ya buɗe nanma beganta ba jiki ba kwari yakoma kan ɗaya daka cikin kujerar office ɗin yazauna tare da tinanin ta inda zefara nemanta yabata shawara kan karta yarda ta auri Zaid ba mutumin kirki bane ganin bashi da wata mafita yasashi fita ya shiga motarsa nufi unguwar daya taɓa ajeta yana tinanin koze ganta ya daɗe a cikin mota ya dube-dube ko Allah zesa yahanta amma bega kome kama da ita lokaci ɗays yaji kansa na mugun ciwo tsintar kansa yayi da jin haushin kansa na nemanta da dayayi yaja motarsa yanata tsaki ya nufi gida.






Washe gari suna tashi da sassafe suka shiga aikace-aikacen gida ita da Khadija sunkusa gama wanke -wanke Jameelah ta fito tana miƙa alamun tashinta bacci kenan kama baki tayi cikin iya bariki tace"Aunty meyasa baki tasheni nazo munyi ba kuketa gumurzun aiki ku kaɗai".
hararta Khadijah tayi a zuciyarta tace"tsinanniya sekace yin aikin dama takeyi ".
murmushi Inteesar tayi cike da soyayyar ƴar uwarta tace"ai aikinma ba yawa harma munkusa gamawa kije ki shirya idan muka gama semu tafi gurin ƙunshi".
"toh Aunty".
nanta koma ɗaki tana yiwa Inteesar dariyar tagama da ita a zuciyarta tace"toh a ina tasamu kuɗi bayan Yayah Zaid yacemun ko biyar be bataba ". ƙumƙunai Khadijah tashiga yi harara Inteesar ta watsamata haɗe cewa"kinga Khadija inbaki fita idonaba wallahi zakiga yadda zanyi dake koke zaki biyamat".
nan taitayiwa Khadijah faɗa har suka gama wanke -wanken suka shirya gabaki ɗayansu suka tafi gidan ƙunshi.




Ɓangaren Namijin duniya ko kobaccin kirki besamu yayiba Allah,Allah yakeyi gari ya waye ya nufi comphany ɗinsa ana kiran asuba yana fitowa daga masallaci yana komawa bedroom ɗinsa ya faɗa wanke yana fitowa a gaggauce yashiga shafa mai yana gamawa yasaka wasu haɗaɗun ƴan kanti sunyi matuƙar amsar jikinsa ya ɗauki phones ɗinsa ya shiga sauka daga bene cikin hanzari kaciɓus sukayi da Abbih ɗinsa daya dawo daga masallaci kallonsa yayi cike da mamaki yace "ina zaka haka da sanyin safiyar nan ".
cikin girmamawa yace"Abbih ina kwana dama office zani inada wani aiki me mahimmanci ne shiyasa zantafi da wuri".
"lafiya ƙlau amma dai ka tsaya ko tea ne kaɗansha kafijin kwarin yin aikin".
"ai da wuri zan dawo idan na dawo nayi breakfast".
"ok seka dawo ina fatan dai ka tuna yaune ranar da alƙawarinmu ze cika".
"eh Abbih idan na dawo zan falamaka".
yaƙarasa zancensa yana ficewa dankar Abbih ɗinsa yaƙara tayo da wata maganar murmushi Abbih yayi ya wuce .



Yana fita ta anshi makullin ɗaya daga cikin sababbin motocinsa yashiga yaja ya nufi comphany ɗinsa lokacin daya isa tsirarin mutane ne suka isa ya nufi office ɗinsa yana shiga ya zauna tare kunna syatem ɗinsa yashiga duba abubuwa yanayi yana duba lokaci wasa-wasa har 11am ba Inteesar ba alamunta ɓangaren Namijin duniya ko yarasa meke damunsa se tsaki yakeyi yana duba cctv camera koda zega ɓullowarta amma shiru bata bs labarinta har ƙarfe huɗu jiki ba kwari haka ya nufi gida yanata tinanin meya hanata zuwa!!!!




Votes and Comments




_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_# Real eeshow



_*Paidbook ,Amount Nml grp 300,Vip 800, pc 1k, Account Detail 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank, or Vtu mtn or airtel ga ƴan Niger kuma zaku turo da katin Airtel na daidai kuɗin da kikeson shiga aiko da shedar biyanka/biyanki ta wannan number 08108362334.*_


Book 2


4️⃣3️⃣➡️4️⃣4️⃣



Yana isa gida direct y part ɗinsa ya nufa a ya zube akan haɗaɗen gadonsa ya lumshe sexy eyes ɗinsa ya lula duniyar tinani dakyar ya iya tashi yashiga toilet yayi wanka yafito yana fitowa ya shirya cikin ƙanan kaya marasa nauyi ya nufi hanyar fita domin samawa cikinsa abu mara nauyi a falonaa yayi kaciɓus da Rahama datazo kiransa tana ganinshi tayi saurin juyamasa tana kukan shagwaɓa murmushin daya ƙarasamasa kyau yayi tare da kawota jikinsa cikin tausasa murya yace"sorry Sweetheart nasan nayi laifi na fita da wuri ".
yaƙarasa zancensa yana kama kunnensa alamun bada haƙuri murmushi Rahama tayi tare da yin hugging ɗinsa cikin shagwaɓa tace"indai kanaso in haƙura seka faɗamun sunanta".
"wakenan".
"wadda ta zautarmana dakai kaketa zabga smiling jiya wadda ka siyawa necklace".
murmushin dabe shirya yi bane ya suɓucemasa ya lakacemata hanci tare da cewa"zaki santa amma ba yanzu ba".
bubbuga ƙafa tashigayi alamun bata yardaba kama hannunta yayi yace"muje yunwa nakeji idan nagama cin abinci zan faɗamiki kinji amma sekin dena kuka".
"yauwa Bro na Abbih na nemanka a part ɗin Granny".
damm ƙirjinsa yabayar domin yasan kwanan zancen jiki ba kwari yace"muje".
"toh".
nan suka nufi ɓangaren Granny yayinda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri.




Suna isa falon Granny suka tadda Abbih da Granny suna hira cikin girmamawa suka samu guri kan carpet suka zauna ƙasa da kansa yayi cikin girmamawa yace"sannunku da hutawa".
"yauwa sannu mesunan Manya ".
cewar Granny tana kallon Abdallah kallon Rahama Abbih yayi cikin nuna alamun rashin wasa a fuskarsa yace"ki shiga ɗaki zamuyi magana".
"toh Abbih".
nanta miƙe tashige bedroom ɗin Granny shiru ne ya biyo baya naɗan lokaci kafin daga bisani Abbih yayi gyaran murya tare da tattara hankalinsa ga Abdallah dake wasa da zara-zaran ƴan yatsunsa yace"kai muke saurare inafata dai yanzu kasamu daidai da ra'ayinka ko?".
cikin dakiya tare da basarwa kamar besan me Abbih yake nufi ba yace"bangane ba Abbih".
murmushi manya Abbih yayi domin yasan halin ɗannasa yace"kasan dai yaune ranar ƙarshe dana ɗibamaka akan ka fito da matar aure shine zaka nuna kamar bakasan inda zancena ya dosa ba to yanzu na tunamaka kasamu ko kuwa haryau bakasamu daidai da ra'ayin naka ba".
jiɓine yashiga ketomasa dukda sanyin ac dake falon abinka da Namijin duniya seya make ya sosa ƙeya yace"eh to gaskiya har yanzu bansamu wadda ta kwantamunba amma aɗan ƙaramun lokaci zuwa lokacin dazan samu wadda tayi daidai da ra'ayina".
"aiko kayi kaɗan yaro kayi ƙarya ka kwana da yunwa jiƙaka kakeso muyi musha yau ni Indo naga abinda ya isheni anyako wannan katon ba aljana ce ta aureshi ba kuwa yaza'ai ace duk irin zuƙa-zuƙan matan dake sonsa yace duk basuyi daidai da ra'ayinshi ya yaro da anyi maganar aure seyace a ƙaramasa lokaci inbaka da lafiya ka faɗamun in nemamaka magani domin so nike naga masu yimun addu'ah gaskiyar Meramu tacemun jifan jikana akayi shiyasa yaƙi aure naƙi yadda aiko kowaye senayi maganinshi ungo kiramun Meramu mutafi Malam na bayan tsauni ya bincikamun domin banga ta zamaba za'ah kassaramun jika".
taƙarasa faɗa tana miƙawa Abbih waya yakiramata aminiyartata ansar wayar Abbih yayi tare da cewa"Innah ki kwantar da hankalinki ba wanda yayimasa wani abun basekin tafi wani gurinba".
"yo ina hankalina ze kwanta anjefi jikana bakaga yadda idonsa yakoma kamar gautaba daka yin maganar aure oh ni Indo ka tashi ka miƙani gidan Meramu mutafi gurin wannan mutumin na bayan tsauni".
"naji Innah amma inda kike ƙoƙarin tafiya ba gurine mekyauba Malami baze zauna a bayan tsauni ba sede boka kuma babu kyau zuwa gurin boka".
matsar kwalla Innah tashiga yi tana jan majina tana cewa"yanzunan Iro ni kake ciwa zarafi kan zanje samowa ɗanka lafiya shine zakayimun sharri a ina nafaɗamaka gurin boka zani to nabarka da ɗannaka magautan su kasheshi insuna iyawanz zame hannuna akan ɗanka kuma ku barmu sashina tunkafin nima naci zarafinku".
murmushi Abbih yayi ganin yadda Innah ta haƙiƙance wai ita ala dole an nunamata iyakarta lallashinta Abbih yashiga yi dakyar ta sakko tabarsu su zauna a falonta kallonsa Abbih yayi naɗan lokaci sannan yace"tunda kace har yau bakasamu wadda ta kwantamaka ba to ni dakaina zan lalubomaka".
damm ƙirjinsa ya buga yayinda yaji yawun bakinsa ya ƙafe lokaci ɗaya kai kawai ya ɗagawa Abbih nan Abbih ya miƙe yayiwa Granny sallama ya tafi .




Yana ganin fitar Abbih yasaki wata nannauyar ajiyar zuciya miƙewa yayi tare da zama kan kujera ya lumshe idonsa kamar koda wannan lokaci tinanin kyakyawar fuskarta yashiga yi wani ɓangarena zuciyarsa se tsukulinsa yakeyi daya kira Ahmad daya turomasa da numberta yaji ko lafiya batazo ba jin muryar Innah yayi tana cewa"mesunan Manya ka rabu da wancan sakaran uban naka bawani boka wallahi Malami ne gobe da safe zanje gidan Meramu ta rakani in ansomaka kasha abunka ba tare daya sani ba duniya ba gaskiya kai baka damu da mutumba shiya damu dakai kodai baka da lafiya mesunan Manya".
jin abinda tacene yasa Namijin duniya yin wata dariyar dabe shirya yinta ba jin waiko bashi da lafiya a zuciyarsa yace"Granny dakinsan yadda lafiya tayimun yawa da bikice haka ba domin ina tausayawa yaran mutane domin nikaina nasan nakama ɗiyar mutane nasan bazataji da daɗiba".
a filikuma ɗagamata kai yayi alamar eh bashi da lafiya riƙe hannunshi tayi tare da cewa"aikoda naji aiko gobe zansa Barirah ta tafi ƙauyensu tasamomin magunguna kafara sha shiyasa kenan naga kamar kana tsoron mata ashe ga inda matsalar take doleko kaji tsoron mata ashe ba kayan aiki aiko ba zance yanzu dai ka kwantar da hankalinka insha Allahu zaka samu lafiya kaima kamar sauran maza".
dariya Namijin duniya yaƙarayi jin wai shike tsoron mata yace"Granny ya mutum yake gane yafara soyayya".
washe baki Granny tayi tare da cewa"Mesunan Manya wata ka kamu da sonta ne".
"a'ah abokina ne yakamu dason wata shine ya tambayeni".
"ayo aina ɗauka kai ka fara soyayya ".
"a'ah".
"zakaji kana son ganinta akowanne lokaci baka da buri sena ganinta komai nata ze riƙa burgeka kodako rashin kunya tayimaka bazakaji haushi ba zaka kasance mejin tausayinta akowanne lokaci".
ƙirjinsa ne yabada damm jin abinda tace a zuciyarsa yace"kenan sonta nike".
wata zuciyarce tace"Allah ya kyauta inrasa wadda zanso se ƙasƙantacciyar cleaner tausayinta kawai nakeyi ".
a fili ya furta "no tausayinta nakeji domin ni bani da lokacin ɓatawa".
kallonsa su Granny sukayi Rahama tace"intayi wari maji".
hararta yayi tare da miƙewa ya fice yabarsu.




5:00pm
Zaune kowa yake a ɗakin taro kowa yasha kwalliya ta alfarma ba abinda ke tashi a gurin se kiɗa zaune take akan kujerar higher table ita kaɗai tasha make-up harta gaji inba farin sani kayimata ba bazaka ganeta ba domin tayi kyau sanye take da wata rantsatsiyar gown white me adon stone red se net ɗin da aka rifemata fuska daya kasance red komai na jikinta red ne shiru-shiru ba ango ba alamarsa se amarya tsu kan step ɗin Hauwah tahau ta nufi gurin Inteesar da idanunta sunfara tara ruwa ta sunkuya daidai kunnenta tace"Besty ki kwantar da hankalinki insha Allahu ba abinda yafaru dashi".
maida hawayen dake ƙoƙarin fitowa tayi tare da yin murmushin yaƙe tace"Allah yasa Besty kinga irin abinda nake faɗamiki kinƙi yadda kikayo uwar gayya gashi ba lallai yazo ni bikinnan wallahi duk yaficemun daka rai domin jikina duk sanyi yakeyi".
"dan Allah kiriƙa haƙuri wataƙila wani abun yatsayayi bakiga abokansa duk sunzo ba shima yana hanya".
"Allah yasa".
nan Hauwah takoma seat ɗinta na babbar ƙawar amarya.



Dariya Jameelah tayi ganin Inteesar kaɗai akan kujera tare da kallon ƙawarta Hindatu tace!!!!!!!!




Votes and Comments




_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_# Real eeshow



_*Paidbook ,Amount Nml grp 300,Vip 800, pc 1k, Account Detail 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank, or Vtu mtn or airtel ga ƴan Niger kuma zaku turo da katin Airtel na daidai kuɗin da kikeson shiga aiko da shedar biyanka/biyanki ta wannan number 08108362334.*_


Book 2


4️⃣5️⃣➡️4️⃣6️⃣



"Hmmm kalli tsinanniyar se zare kurma-kurman ido take a kujera ita kaɗai kamar kazar da aka tsoma cikin ruwan zafi ai wallahi tunda tace zata jadani tana tare da wahala domin muddum Ummanmu na numfashi bazata taɓa barinsu suyi aure gidan jindaɗi ba sede suganmu muna hutawa suko sede su ƙare dayin aikatau da wanke-wanken gidan mutane da shara domin ni idan na auri Zaid ko kwancen kaya bazan temakesu dashi ba".
"gaskiyane Mrs Zaid Cheif judge aikinki na kyau mudai idan abunnan ya tabbatu Allah yasa kar a manta damu domin nasan halinki dakinsamu duniya kike shafawa idanunki toka ki babbake komai".
"haba ƙawata kisha kuruminki wannan karon zanbaki mamaki domin so nike kema kiyi ramm da zuciyar babban amininsa Muhseen kinga shikenan amincinmu yaƙara ɗinkewa".
"Allah ƙawata ammafa kinaja sosai amma kina ganin ze kulani kuwa domin gayennan naga alamu kamar yanada girman kaifa".
"ke da Allah jacan girman kanshin banza munada Umma fa faɗuwar gaba asarar namiji ai ba'ah shiga dawa dan ƙarya kedai kawai ki kwantar da hankalinki zakiga yadda jikinsa ze riƙa tsuma akanki ai ina tinanin duk girman kansa bekai ɗan gogana ba amma dayasha aiki idan yaganni kamar ze lasheni haka yakemun shima zakiga yadda ze koma kai gaskiya nagaji so nike naɗan fita shan ice cream bara na kira Sweetheart yakaimu gurinnan yacika zafi".
dariya Hindatu tayi tare da tafawa da Jameelah daketa faman yatsuna tace"lallai ƙawata gaskiya kin ƙaro wulaƙanci wato angon da amaryarsa ke jirama keshi zakisa ya kaiki shan ice cream baki da case kina cin duniyarki da tsinke wallahi".
"sosaima kuwa idan banci lokacina ba yanzu yaushe kikeso naci koko so kike nayi ƙara'ih shekaran jiya da muka fita yasiyamana layin me &u dan yariƙa jina a waya suko wa'incan gaulayen da kikaga sunata faman kiranshi aikin banza sukeyi domin nina sakashi ya kashe wayarsa bazasu taɓa samunsa ba sa ƙaraci nacinsu su haƙura inbada abin namiji mezeyi da ɗiyar marasa asali bayan ga ƴar dangi gaba da baya itakuwa fa waya taɓa sanin dagin wannan me farar ƙafar".
"gaskiya ne tawajena kici lokacinki".
"yauwa tawajena".
nan ta ɗakko wayarta daka jaka murmushi tayi tare da cewa"oh kinga ɗan halak yanzu muke maganarsa sega kiranshi ai bara naɗauka".
"yadai kamata tawan".




Ɗagawa tayi tare da yin ƙasa da murya tace"hello Dear yakake".
"lafiya ba lafiya ba tunda banji lafiyar sarauniyar birnin zuciyata ba tunɗazu naketa kiranki kinyi bakiyi picking ba lafiya".
murmushin daya ƙara narkar dashi a duniyar soyayyarta tayimasa tare da cewa"tuba nake My King ina gurin shagalin aurenku ne".
"kingaki ko zaki farako kinsandai na faɗamiki banaso kina haɗani da wannan me warin jaɓar shine kike ƙara lanƙayamun itako ko sokike na fara miki kuka to ".
wani daɗine yaƙara kamata zuciyarta tace"sorry My nadena karkamun kuka wasa nake maka idan ba wani abun kakeyi ba inason muje shan ice cream inba damuwa".
"kinji sweetheart ai koda aikin da nikeyi na bari nakaiki kisha kina ina nazo na ɗaukeki mutafi".
jinjina Hindatu tayimata alamun aikinta na kyau kashemata ido ɗaya Jameelah tayi tare da cewa"Sweetheart ina gurin kamu ".
"ok gani nan zuwa amma sede ki fito waje domin banason aganni a zata gurin abun nazo".
"tom shikenan inka iso ka kirani sena fito mu wuce".
"toh gani nan zuwa".
yaƙarasa zancensa jikinsa na tsuma kashewa tayi tare da cewa "bara inje inɗan nuna alhinin rashin zuwan ango dankar a zargeni".
"aiko dai".
nanta miƙe ta nufi step tashiga nuna alhininta .




Zaune yake a falonsa ya zubawa tv ido kamar wanda yake gane abinda akeyi ba abinda kemasa yawo se kalaman Granny na tambayar daya yimata hannunsa ɗauke da glass cup yana shan coffee turo ƙofar da akayine yasashi dawowa daga duniyar tinanin daya lula kallo ɗaya yayiwa aminan nasa tare da amsamusu sallama yacigaba da shan coffeensa hankali kwance zama sukayi akan kujerar dake facing ɗin tashi tare da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya murmushi Ahmad yayi tare da yaɓa Adam dake gefansa suka saki murmushi taɓe baki Abdallah yayi tare da cewa"kwagama munafuncinki a gidanma mutum be tsiraba se anbi mutum da gulma".
dariya Adam yayi tare da cewa"ai gwara mu munafunafunci mukeyi da wanda yakeson abu yana hana zuciyarsa abunfa yariƙa basarwa waishi ala dole bayason raini fa".
"mekake nufi".
dariya Ahmad yayi tare da cewa"abinda kunnenka yajiyemaka saura kwana biyar afara tafiya gurin seminer nan kaikuma kaƙi motsawa wallahi mudai tafiyarmu zamuyi tunda muba gwauraye bane irin wataƙil baka da rabo idan mundawo maɗan sanmaka riba".
"bangane saura kwana biyar ba har abun yazo".
"eyi badai munbaka shawara kaƙi ɗauka ba da yanzu seka tafi da ita inmundawo ka saketa kaga riba biyu ga sauro ga revenge ga ribar seminer".
shiru yayi secan yace"to yanzu meye abunyi kasanfa banason rasa wannan seminer ".
"bara nakira Hauwah naji yadda za'ayi tabamu number Aishatun".
"ok ".
dialing number Hauwah yayi tare dasata a hansfree yadda kowa zeji bugu ɗaya ta ɗauka tare da komawa gefe saboda hayaniyar kiɗa tace"salamu Alaikum Sir".
"wa'alaiki salam".
"ina yini?".
"lafiya ƙlau Hauwah dama number Inteesar mukeso inba damuwa".
shiru gabaki ɗaya sukayi danjin mezatace daga ɗaya ɓangaren Hauwah tace"Sir yanzu haka muna gurin kamun Inteesar gobe ake ɗauramata aure".




Lokaci ɗaya hankalinshi yayi mugun tashi ya rasa mekemasa daɗi amma dake namijin duniya ne seya dake kamar beji komai ba har suka gama wayar bayan sungama Ahmad yace"tokaji irin abinda muke gujemaka tunfarko da yanzu ba wannan zancen akeyi ba yanzu sede a nemi wata".
ɓangaren Man of the world ko kasa magana yayi sakamakon wani kullutun abu dayazo ya tsayamasa a maƙoshi lokaci ɗaya sexy eyes ɗinsa suka rine zuwa ja yayinda jijiyoyin kansa suka tashi sukayi ruɗu-ruɗu ba abinda ke ketowa a jikinsa se zufa yayinda kansa ke mugun saramasa ganin zasu ɗago jirginsa ne yasashi lumshe idanunsa ganin halin daya shiga ne yasa Adam zungurar Ahmad ya raɗamasa"mutuminmu fa ya auka ba tare daya sani ba".
"hhh aini tun kwanakin baya na lura yanzu dai yakamata muyi wani abu akan aurennan nata".
"hakane kam".
nan suka miƙe suka yimasa sallama kai kawai ya ɗaga musu sakamakon wani ciwon kan dake barazanar tarwatsamasa kai ba abinda ke kai komo a ciki zuciyarsa se kalmar Hauwah na cewa"gobe za'ah ɗaura mata aure ".
a zuciyarsa yace"ashe zata iya aure batare data sanarmun ba".
wata zuciyarce tace"to waikai meye naka naseta sanarmaka ".
rasa me bashi amsa ne yasashi miƙewa yana haɗa hanya kamar wani ɗan

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment