Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://NovelsHQ.com
to download more hausa novels visits our site at www.NovelsHQ.com

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/NovelsHQ

Twitter : https://twitter.com/NovelsHQ

Telegram : https://t.me/NovelsHQ

Compiled By Umar Dalha Funtua.

Copied By Ummee Yusuf.

[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAKE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_💃🏻NBA SONTA NAKE BA💃🏻



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana gwiwa a wajen rubutu._


*BA SONTA NAKE BA* littafi ne daya kunshi darrusa na yau da kullum,ina rokon Allah kaman yanda na fara lafiya yasa na gama lafiya.
Da fatan zaku bani hadin kai kaman yanda kuka saba.

حَدَّثَنَا يَحْيَى بْنُ يَحْيَى التَّمِيمِىُّ وَأَبُو بَكْرِ بْنُ أَبِى شَيْبَةَ وَمُحَمَّدُ بْنُ الْعَلاَءِ الْهَمْدَانِىُّ جَمِيعًا عَنْ أَبِى مُعَاوِيَةَ - وَاللَّفْظُ لِيَحْيَى أَخْبَرَنَا أَبُو مُعَاوِيَةَ - عَنِ الأَعْمَشِ عَنْ إِبْرَاهِيمَ عَنْ عَلْقَمَةَ قَالَ كُنْتُ أَمْشِى مَعَ عَبْدِ اللَّهِ بِمِنًى فَلَقِيَهُ عُثْمَانُ فَقَامَ مَعَهُ يُحَدِّثُهُ فَقَالَ لَهُ عُثْمَانُ يَا أَبَا عَبْدِ الرَّحْمَنِ أَلاَ نُزَوِّجُكَ جَارِيَةً شَابَّةً لَعَلَّهَا تُذَكِّرُكَ بَعْضَ مَا مَضَى مِنْ زَمَانِكَ. قَالَ فَقَالَ عَبْدُ اللَّهِ لَئِنْ قُلْتَ ذَاكَ لَقَدْ قَالَ لَنَا رَسُولُ اللَّهِ -صلى الله عليه وسلم- « يَا مَعْشَرَ الشَّبَابِ مَنِ اسْتَطَاعَ مِنْكُمُ الْبَاءَةَ فَلْيَتَزَوَّجْ فَإِنَّهُ أَغَضُّ لِلْبَصَرِ وَأَحْصَنُ لِلْفَرْجِ وَمَنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَعَلَيْهِ بِالصَّوْمِ فَإِنَّهُ لَهُ وِجَاءٌ ».

*It was narrated that `Alqamah said: "I was walking with Abdullah in Mina when he was met by Uthman. He stood and talked with him and Uthman said to him: `O Abu Abdur-ur-Rahman, shall we not marry you to a young girl who can remind you of the times past?` Abdullah said, `If that is what you are telling me, (let me tell you that) the Messenger of Allah (s.a.w) said to us: O young men, whoever among you can afford it, let him get married, for it is more effective in lowering the gaze and guarding one`s chastity. And whoever cannot afford it should fast, for it will be a shield for him."*


Sahih Muslim


*BISMILLAHI RAHMANIR RAHIM*



________Hmmmmm bansan ta ina zan fara baku labarin na da yake cukuikuiye ba *BA SON TA NAKE BA* wannan Kalmar da na saba ji kenan a gidan mu har zuwa gidan aure na, bari dai in fara muku daga d'an farko yanda zaku fi fahimta.


Suna na Fatima. Amma Inna ta na kira na da Zareefa a halin yanzu shekaru na basu fi 10 zuwa 11 ba muna shirye-shiryen rubuta common entrance a makarantan mu na boko sai dai yau tunda na shigo kuka nake sosai saboda cin mutuncin da akayi min yau har yayi yawa duk da ba yau aka fara min ba sai dai na yau d'in ya tsaya min a rai.


Uniforms aka zo dasu ana rabawa daga gwarzon Governor mu professor Babagana Umara Zullum, harda jaka wadda ya kunshi note books, tex books crayon pen da sauran tarkacen da d'alibi zai bukata gefe d'aya kuma ga sandal da socks amma aka tsallake ni wai dan ban biya 200 na PTA ba duk da kasancewar nafi kowa bukatan wa'yan nan kayan domin uniform d'ina ya gama yagalgalewa.


Basa tab'a ganewa Inna ta ina zata samu gudan 200 ta bani in kawo musu Ita da kyar take samo 30 da safe ta bani 20 in sayi alale wajan Maman Dije dake gidan mu 10 kuma ta bani a matsayin kud'in tara, toh a wannan halin 200 ba karamin kud'i bane a wajan mu.



Kudin taran ma in na zo dashi sai in rasa abun saya dashi, gashi kiri-kiri ana mana girki a makaranta a rabawa kowa banda ni da ban san me na tare musu ba, bakin jinin Malamai prefect harda monitor nake dashi akan wannan 200 da bana kawowa yasa duk suke jin haushi na, ina ji ina gani za'a tsallake ni a hanani abincin nan wanda nake masa kallon kaman naman kaza suke ci sai randa suka ga dama suke bani bani, duk ranan da na samu ci nake kaman in had'a da hannu na.


Abinci ne da ake rabawa ko kwatankwacin sa babu a gidan mu, dan wata ran alale mai kwai da hanta ake rabawa wata ran kuma jallof d'in doya ko macroni ko kuma na shinkafa da wake yaji manja, toh ina mu ina cin wannan kayan dad'in a wannan gidan namu na yawa.


Abban mu matan shi 3, dan haka in gari ya waye kowa shi zai nemawa cinsa da 'ya'yan sa abinda zai ci babu ruwan Baban mu da d'aukan nauyin ahalin da Allah ya bashi duk ranan da Allah ya bashi zai sayo masara ko dawa a nika dayawa a rinka tuwo da daddare da safe da rana kuma kowa yaji da kan shi dan haka duk yayuna da kanne na wanda muke uba d'aya da cousins d'ina duk tallah suke dan rufin asiri amma ni Inna ta bata yarda da tallah ba duk da ni kad'ai ce wajan ta tana iya kokarin ta wajan ganin ta sauke duk wani nauyi daya rataya akan ta dai-dai karfin ta shiyasa kaf gidan mu babu masu zuwa boko ko islamiya sai ni kad'ai wanda 'yan gidan mu sukewa lak'abi da iyayi ne sai dare kuma muke zuwa makarantan Allo gaba d'ayan mu amma banda 'yan matan da suke tsayawa zance abin su.



Kona dawo makaranta wata rana babu abinda zanci in Inna bata samu wankau tayi ba sai dai ta tura ni gidan su da yake makotaka da namu inci duk abinda ya sauwaka a wajan kakata kasancewar suma kaman gidan namu suke babu wadata sai dai su basu da yawa kaman gidan mu,ranan da ta samu kud'in wankau kuma ta kan bani hamsin in sayi garau-garau nan wajan Gwaggo Aisha ta d'an yarfa min a roba dan mugunta ko mai da yajin kirki bata zuba min kuma in na fita waje na saya ya zama abin magana da habaice-habaice shiyasa ko zan fita saya a waje Inna ta ke hanani.



*BA SON TA NAKE BA* shine kullum Kalmar da Baban mu yake fad'awa Inna ta in wani abu ya faru a cikin gida kuma kayan takaici a gaban kowa yake fad'a mata hakan sauran matan gida suyi ta shewa ana kara habaice-habaice tun bani da wayo har nayi wayo na gane me hakan ke nufi kuma a bakin matan gidan mu na tsinta wai Kakana Abban Inna ta tsohon soja ne in ba'a biya su fensho ba wajan Baban mu yake neman rance har kudin suka taru ya kai Kakana ba zai iya biya ba wanda yasa dole ya bashi Inna ta shiyasa ko kad'an bamu isa mu d'aga murya kaman kowa a gidan ba,Inna ta in ba wani abu take ba kullum tana cikin d'akin ta dan matan duk sun had'e mata kai har yaran su duk raini suke mata sai wajan matan kanin Baban mu Maman Dije take samun sauki dan babu ruwanta da hargitsin gidan mu sai kishiyarta itama tana shiga cikin sauran matan Baban mu tana taya su wulakanta Inna ta.




Haka na fito daga cikin makarantan ina kukana na karin takaicin ma 'yar silifas da nake lallab'awa kuma nake shan bulalan rashin sandal akai ina zuwa bakin gate ya tsinke, ban tsaya neman leda dan gyarawa ba na rike a hannu na nufi titi ido rufe na manta da akwai motoci kan titin burina kawai in ganni a gida.



Karan takawan brick ne ya dawo dani hayyaci na, ganin mota ya nufo ni gadan-gadan yasa na rasa yanda zanyi saboda firgita nan na durkushe ina jiran ta Allah ta kasance min.


Motan daya ja brick Allah ya taimake ni bai kad'e ni ba amma motan bayan shi sai da ya fasa mishi danger, shima na bayan shi ya buga mishi a takaice dai motoci kusan 5 sukayi hatsari duk a dalilina, kuma duk abinda ake ina nan durkushen ban mike ba.



Wani wanda motan shi yafi na sauran bugawa ya fito a zuciye ya janyo ni yana bala'i yana zagina ya d'aga hannu zai yarfa min mari, ihu na yi na rufe fuska ta da d'ayan hannuna ina jiran saukan marin amma na ji shiru ina bud'e idona naga ashe mutane ne suka rike shi suna bashi hakuri, ina jin ya sake min hannu na kama hanyan gida da gudu dama tsakanin makarantan mu da gidan babu wani nisa sosai.




Ban iya tsayawa a ko ina ba saboda zafin rana da yake kona min kafa ina shigowa Hajara na fita da katon tire da aka jera mata robobi da aka zuba garau-garau hamsin hamsin a ciki, ni dai ban san ya akayi ba kawai sai gani nayi munyi karo kayan kan ta sun zube kamin kice kwabo almajirai sun fara wawaso nima ganin haka na wawasushi roba 2 na kama ci dama na kwaso yunwa ta na fitan hankali.




Ihu Hajara ta fasa tana "Wayyoo Gwaggo zo ki gani zo kiga abinda Zareefa tayi min" jin an ambaci suna na yasa matan gidan da yaran su lekowa dukan su, ni kuwa ko a jikina ina gefe sai zabga loma nake yau na samu shinkafa da wake daya ji mai da yaji har roba 2.


Salati manyan suka fara suna bina da kallo yanda baki na yayi nasha-nasha da mai,Gwaggo Aisha da fitowar ta kenan tace" kan uba ke Hajara meke faruwa ya akayi kika min b'arin abinci haka?"



"Wallahi Gwaggo kin gan ta nan Zareefa ce ina fita ta shigo a guje ta ture ni har nayi barin, kuma tun kamin almajirai su zo ita ta fara wawason min abinci" Hajara ta karasa tana harara ta yanda nake ta sud'e roba dan ban san ma sunayi ba sam.



Wani maka da Gwaggo ta kai min a gadon baya ban san lokacin da na saki roban na gatsare tare da fasa ihun azaba ba, wuyan matattacen uniform d'ina ta kama ta jani zuwa ciki tana" lalle na yarda wannan 'ya ta gado mugunta, hasada da tsiya yo banda tsiya yanda kuke ke da uwar ki baku da allura a cikin d'akin shine ta koya miki yanda zaki na yi min barna kina jawo min asara??


Ke Bintu koki fito wallahi kabo na ba zaiyi ciwon kai ba duk inda zaki shiga ki fita sai kin bani kudina yanzu kuma wallahi ba sai anjima ba, ki fito na ce ".



Kallon yanda wuyan uniform d'ina yake kara yagewa yasa nace" Gwaggo ki sake min uniform d'ina kinga kina kara......" Ban samu karasawa ba sakamakon buge min baki da tayi tana huci tace" inifon din banza inifon din wofi ke iskanci uwar taki take koya miki ko boko shegiya yarinya duk wani gantali kin iya wai an likawa boko da baida baki"



"Ni ai abin nasu dariya yake sakani haka masu bokon suke ko akan su aka fara oho, dubi kiga ko takarda d'aya bata dashi balle fensir,ko da uwar me take rubutun?" Cewar Inna Asabe.




Inna ta duk tana jinsu amma ko lekowa bata yi ba balle ta tanka musu, hayaniya sosai ya kaure a gidan mu harda mokota masu zugi sai yi suke harda masu cewa a gaban su ma abin ya faru, dole yasa Inna ta fitowa daga d'aki jin abin yaki ci yaki cinyewa.



"Yauwa daddawa uwar zaman d'aki dole ai yau ki fito azo a biyani kud'ina naira dubu daya da dari biyu ciff wallahi ko biyar d'ina ba zaiyi ciwo ba".



Dariya suka fara suna " keko Aisha ina wannan taga har dubu da dari biyu sai dai in 'yar zata sai da ta biya ki" ko kuma kije wajan tsohon soja" wani tsohon soja sai dai ayi sata" ire-iren kalamai da suke jifan Inna ta dashi kenan.



Kaman yanda ta saba bata kula kowa ba ta koma cikin d'akin ta sai gata ta fito da dubu d'aya da dari biyu ciff da Gwaggo Aisha ta ambata ta mika mata babu kunya ta sake min riga ta karb'e kudin tana lissafi tana mamakin ina Inna ta ta samu wannan kud'i ita da burin ta yau sai ta wulakan tamu yanda taga dama amma cikin ikon Allah ta biya.



Duk watsewa suka yi cike da mamaki wasu ko cewa suke dama bar raina mutum baka san sirrin sa ba.



Ana cika min rigata na shigo d'aki ina kallon wuyan rigata na ce, "Inna dubi fa yanda ta maida min wuyan rigata gobe ya zanyi in tafi makaranta?"



Inna da ta had'a rai sosai ta ce, "ba wuyan riga ya kamata kiyiwa kuka ba, gobe kika ce za'a rufe karb'an kud'in common entrance ko?"


Gyad'a mata kai nayi ina cire kayana.



"Toh kud'in da nayi wata 3 da wani abu ina tara miki na common entrance d'in su na bada a maimakon abincin mutane da kika zubda, gobe ma in kin taso daga makaranta kada ki rinka kula da gaban ki".




Yawan comments yawan typing.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```


*_And now_*


*_💃🏻UWANI💃🏻



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*Addu'a Ga Wanda ka zage shi:*

Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce;

اَللَّهُمَّ فَأَيـما مُؤْمِنٍ سَبَبْتُهُ فَاجْعَلْ ذَلِكَ لَهُ قُرْبَةً إِلَيْكَ يَوْمَ الْقِيَامَةِ.

Allahumma fa'ayyuma mu'minin sababtuhu, faj'al zalika lahu kurbatan ilayka yawmal qiyamati.

Ya Allah! Duk wnai mumini da na zage shi, to ka sanya wannan ya zamanto sababi gare shi na samun kusanci zuwa gare Ka ranar kiyama.

*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


*2*

Kasa cire rigan nayi na zaro ido waje ina kallon Innara na ce," Inna kud'in common entrance d'in kika basu?"


"Ya kike son inyi? Kin san halin Aisha sarai a gidan in ta fara fitina zata kai awa goma tana yi ba tare da ta gaji ba,ni kuwa kin san ba iyawa zanyi ba gwara in bata a rabu lafiya gobe ma idan zaki shigo gida kada ki natsu " Inna kenan ta bani amsa.


Zama nayi da rigan a wuyan na ina hawaye na ce," shikenan za'ayi banda ni kenan,ko yau ina kallo akayi ta rabon abubuwa a makaranta ni ban samu komai ba akan 200 balle 1500 nasan gobe ko class ba za'a barni in shiga ba".


"Haka Allah ya kaddara ba zaki rubuta ba a wannan shekaran amma kiyi hakuri zuwa shekara mai zuwa ko kuma muyi addu'an Allah ya kawo wata hanyan,kinji ko?" Inna ta fad'a min cikin rarrashi.


Goge hawayen fuskan ta nayi na tashi na cigaba da cire uniform d'in na ba tare da na kara cewa komai ba.


"Ki d'auki hamsin cikin d'ari ukun daya rage kije ki sayi wani abin kici" cewar Inna.



Dariya na fara kyakyalewa da shi harda rike ciki sai da nayi mai isa ta sannan na ce," ai inna ciki na kaman zai fashe saboda koshi, dan lokacin da Hajara tayi b'ari almajirai suka fara wawaso nima roba 2 na wawashe na cinye tas abina Gwaggo Aisha data ji haushi kinji yanda ta zuba min dundu a baya Wallahi ko jin zafi ma banyi ba".



Cikin tsuke fuska Inna ta ce," wai ya akayi kika yi musu b'ari? Kullum inayi miki fad'an ki natsu amma ba kya ji ko?"



Daina dariyan nayi sannan nayi kalan tausayi na fara bata labarin abinda ya faru a makaranta har zuwa yanda mukayi karo da Hajara,ajiyar zuciya Inna ta sauke tana mai jin tausayin na ta ce," hakuri zakiyi Zareefa insha Allah wata rana sai labari,karatu kuma da yardan Allah zakiyi shi".



Gyad'a kai kawai nayi na fita yin alwala zahar a lokacin duk yaran gidan anyi musu abin sana'a duk sun fita talla,ina idar da sallah na fara shirin islamiya shi kam cikin dokin zuwa nake shirin na kasancewar a can bana takura kaman boko.



Akwai wani Malamin mu da yake d'aukar mu Qur'an shi ya tsaya minsosai sabo kokarin na dan har kudin wata 500 shi yake biya min domin kullum dai-dai nake kawo hadda ta yanzu haka mun bawa izufi 30 baya.


Ina gama shirin na nayiwa Innata sallama na tafi.



Ina fita Inna ta kwaso uniform dana cire ta hau wanke min da sauran Omo da ta rage jiya,tanayi tana jin su suna ta haice-habaicen su ta gama ta shige d'aki ta rabu dasu.


Mun taso a islamiya ni da kawayen na muka nufi gida muna d'an wasan su na yara,muna zuwa dai-dai gidan mu na fara jin muryan Baban mu yana ta masifa kaman zai ari baki.


Dariya sauran yaran suka fara har suna lekowa ta rububben ginin daya zagaye gidan.


Jiki a sanyaye na nufi cikin gidan namu dan nasan yanda Baba yake d'aga muryan nan nasan da inna ta yake,muryan Gwaggo Aisha naji tana kara zuga Baba da fad'in karya da gaskiya.


"Toh ai Mallam dan ma baka ga irin rashin kunyan da yarinyan nan tayi min a waje ba,inda zaka san da gayya ta b'arar da kayan sana'a shine,itace farkon daka wawa sannan sauran almajirai suka bi bayanta.


Koda yake b'ata baki na nake ina gaya maka abinda ya faru na san babu wani hukuncin da zaka d'auka tunda 'yar amayar ka ce abin sonka".



A fusace Baba ya juyo kanta yana," wannan wani irin maganan banza kike min matar da *Ba sonta nake ba* aka lika min ita dole yasa na karb'a dan kar inyi asaran kud'i na,amma wallahi Aisha kin cuce ni"..


Gwaggo Aisha ta saki shewa dama Kalmar da take son ji kenan.



Baba ya cigaba da fad'an shi inda yake cewa," duk kin bi kin b'ata yarinya bata ganin kowa da darajan a gidan nan da anyi magana kice wai boko take sai kace ki d'in bokon kikayi aikin banza kawai zata zo ta same ni a gidan sai jikin ta ya gaya mata"


Yana juyowa muka had'a ido ina can makure karshen bango ,aiko baiyi wata-wata ba ya nufo ni zai sake min wannan rankwashin sa nan da sai yasa kullum na saki fitsari a wando.


A guje nayi d'akin mu na shige kamin ya kama ni sanin cewa in ba wani babban dalili ba baya shigowa,cikin sa'a kuwa bai shigon ba ya tsaya a tsakar gida yana cigaba da fad'an,sam na daina jin me yake cewa domin ganin Inna ta na kuka abinda ban tab'a gani ba kenan tun tasowa ta dan komai akayi mata a gidan ko Baban mu ko matan gidan sai dai tayi murmushin mai ciwo tace akwai Allah.



Toh tana furta wannan kalman duk yanda za'ayi da ita ba zata kuma tankawa ba na sha tambayan ta me yasa itama ba zata ke rama cin fuska da ake mata ba sai dai tayi wannan murmushin nata mai ciwo ta ce," bakomai Zareefa akwai Allah" daga nan kuma ba zata kara cewa komai ba.


Zuwa nayi har gaban ta na durkusa a gaban ta tare da d'aura hannu na kan guiwoyin ta na ce," Inna kuka kike,meya same ki?" Duk na jero mata wayan nan tambayoyi a lokaci guda.


Murmushin nan nata mai ciwo tayi min kana ta ce," babu komai ba kuka nake ba wani abu ne ya shiga ido na".


Ba dan na yarda ba nayi shiru nasan ko abinda ake mata a gidan nan dole tayi ta kuka kullum,komawa gefe nayi na zauna ina kallon ta tana dinke min wuyan uniform d'ina daya yage bata kuma yarda ta zubar da hawaye ba.



Da washe gari da safe bayan na sayo alale na naci Inna ta bani 200 a cikin kudin daya saura ta ce in kai makarantan nima a bani bani sabon uniform d'in inya so ko shekara mai zuwa sai in zana jarrabawan.



Cikin matukar farinciki na nufi makaranta yau nima za'a bani kyautan kayan makaranta kaman sauran d'alibai.



Direct office d'in principal na wuce ina jin kaina yau kaman bani ba,bayan na gaishe shi na bashi kud'in na ce ni jiya ban samu daman zuwa ba shiyasa ban samu komai na rabo ba.


Tambayan shekaru na yayi na fad'a mishi ya ko duba ya ciro uniform sabo dal ya miko min,murna fal jikina na karb'a amma sai na kasa tafiya ina jiran jaka da sauran tarkace.



Ganin na ki tafiya ya ce," me kike jira kuma?" Kasa nayi da kaina na ce," Sir su jaka da takardu suma ban samu ba".



"Okay toh sai gobe ko anjima dan suna store,ya suna ki kuma a wani class kike?"



"Suna na Fatima Hassan,kuma ina class 6A" na bashi amsa.



"Toh kije anjima zan sa akai miki" cike da farinciki na juya na koma ajin mu feeling proud.


A wajan assembly akayi announcing cewa duk wanda bai biya kud'in common entrance ba ya koma gida dan zuwa nan da awa 2 za'a fara kuma ba barin mu za'ayi mu shiga ba,nan take murna ta ya koma ciki.


Jiki a mace na kama hanyan gida dan nasan zaman nawa bashi da amfani,ina tafiya ina hawaye saboda na kwallafa rai na akan jarrabawan,shikenan inaji ina gani mates d'ina zasu wuce ni.



Ina tafiya cikin tafiya naji horn a kusa dani ,matsawa gefe na karayi maimakon ya wuce sai naga ya tsaya kusa dani yana kallo na ya ce," kanwata meya same ki kike kuka akan titi?"


Kallon shi na tsaya yi d'an kyakkyawa dashi duk da ba fari bane.


"Kiyi magana mana kanwa ta?"ya katse ni.


"Kud'in common entrance ake nema shine aka kore ni dan ban

Please Login or Register in order to submit comment