Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

musu yawa amma kowacce rana sai munyi waya kuma tana neman inje in taya ta wasu abubuwa sai dai kwata-kwata bana cikin natsuwa kasancewar Yaya na yau kusan kwanan shi 5 kenan da yin tafiya amma shiru bai dawo ba kuma wayar shi bata shiga balle inji lafiyar shi.

Wannan dalilin yasa bani da kwanciyar hankali sam shiyasa na kasa zuwa gidan su Maryam d'in, haka kawai kuma nake jin yawan fad'uwar gaba har na kasa daurewa na fad'awa Inna tace min inyi ta addu'a ba abinda zai faru.

A haka na daure nake dan al'amura na har ta kai gobe ne dinner gidan su Maryam kuma tun safe ta matsa min da waya kan yau bata son wani excuse lalle inzo da safe dan akwai abubuwan da zamuyi, ba dan ina so ba na amsa mata da toh kawai na katse waya ta dan rashin jin labarin Yaya na ya sanya bana jin dad'in duniya sam.

Da washe gari ma Inna ce ta matsa min akan in tafi tun safen tunda haka ta bukata ko akwai ayyuka da zan kama musu itama tana zuwa anjima kad'an,dole na na shirya nayi mata sallama na fita.

***********************

Tun jiya yaje tsadadden saloon da yake zuwa aka aske mishi gashin da ya tara kuma akayiwa askin zamani, sanin cewa in Abba shi ya gani ba zaiyi mishi da sauki ba , ko da yaji Abban nashi ya dawo duk daukin son ganin shi da yake sai da ya d'auko natsuwa da jarumta sannan ya nufi part din iyayen nasa cikin fargaban kada yayi mishi maganan aure.

A parlour ya tadda su zaune suna hira Abba na shan fruit salad da Momy ta had'a mishi da kan ta.

Kusa da kafafun shi ya karasa ya zauna tare da d'aura kan sa akan cinyan Abba ya kwantar, cikin tsantsan kaunar tilon d'an nashi ya hannu yana shafa kan a hankali fuskar shi d'auke da murmushi yana matukar son d'an nashi sai dai wasu halayan da ya kwaso marasa kyau ya d'aurawa kan shi yasa basa shiri, ganin sa cikin shigar kamala kad'ai yau yasa shi farinciki.

Babban burin shi yanzu shine yaga d'an nashi yayi aure ko zai natsu ya daina abinda baya so sannan shima girma ya fara zuwa mishi yana bukatan hutu yana son d'aura shi kan d'inbin dukiyar shi da shi kan shi bai san iyakar su ba.

Cikin girmamawa yayiwa Abban nashi barka da zuwa shima ya amsa cikin kulawa, zama ya gyara ya d'auki spoon d'in da Abba shi ke shan fruit shima ya fara sha yana kai na farko baki ya lumshe ido yace" Mom ji yanda wannan fruits din yayi dad'i amma ni in nace ki min ba yayin dad'i haka".

Mom tana dariya tace" kayi aure matar ka zata yi maka wanda yafi wannan dad'i".

Ras yaji gaban shi ya fad'i meya kai shi fad'in haka gashi har an tabo zancen da baya so ayi ta agaban Abba, shima dariyan yayi da son kawar da zancen yace" yauwa Mom abokinaboki na shamsuddeen nan da kike ta yabon shi kullum gobe ne fa auren shi anjima kad'an ma zan je dinnern kuma dasu Sadiq....."

"Aikin kenan zuwa dinnern wasu amma kai baka tab'a tunanin kaima kayi settling down, ko har yanzu kana tsamanin yaro kake komawa?" Abba ya katse musu zancen cikin daure fuska da zaka san ran shi a bace yake.

"Anyway duk ma laifi na ne da na zuba maka ido ina kallon ka da sunan ina jiran ka kawo min matar da kake so da kan ka,but tunda baka fahimta ba let me make my self clear, kwana 3..... Wallahi kwana 3 kacal na baka in baka fito da wacce kake so ba kauye zan je in samo maka mata cikin 'ya'yan dangi, in kuma ka d'auka wasa nake maka ka jira kwana 3 ka gani" Abba yana gama maganan shi ya mike fuuu ya bar musu parlon.

Cikin wata irin murya mai cike da tashin hankali ya rarrafo gaban Mom ya fara magana" Mom pls ki bashi hakuri wallahi ni banida wacce nake so a yanzu dan Allah ya kara min lokaci wallahi zan kawo ta har nan ku gan ta".

"Wannan karon nima babu hannu na a ciki saboda ka kai Abban ka makura sannan ni kaina ina son ganin auren ka ko dan jikoki su cika mana gida, so count me out of this" itama tana gamawa tabi bayan mijin ta suka bar Zafar cikin fargaba da tashin hankali.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹

🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*16*

Zafar ya kai kusan 30 mins a zaune wajan sai share gumi yake duk da sanyin A.c dake parlor amma bai hana shi jikewa da gumi ba, ta ina ma shi zai nemo mata cikin kwana 3 kacal, shi fa ya raina 'yan mata 9ija kuma koda yayi karatu abroad bai samu wacce ta kwanta mishi a rai har yace zai iya auren ta ba.

Ringing d'in waya ne ya dawo da shi hayyacin sa amma ya kasa d'aga hannu ya d'auki wayan balle ya amsa,sai da akayi mishi 2 missed calls a na 3 ne ya d'auki wayan ya kai kunne yayi shiru.

"Zafar kana ina ne baka karaso ba, tun d'azu Shamsuddeen ya dame ni da na kira ka wai har an kusan tafiya hall" muryan Sadiq yaji cikin wayan yana magana, bai iya bashi amsa ba ya cire wayan daga kunnen shi ya mike a hankali ya fara tafiya cikin kasaita daya zame mishi jiki.

Part d'in shi ya shiga bai tsaya a parlour ba ya wuce bedroom ya fad'a kan makeken gadon shi da a kalla zai lashe mutane 7 ba tare da wani takura ba, tunani kawai yake tayi dan komai na duniyan ya fice a ran sa bare zuwa bikin nan, bai dad'e da kwanciya ba d'ayan wayan shi ya fara ringing shima kaman ba zai d'aga amma ya daure ba tare da ya lura da sunan mai kiran ba ya amsa wayan, muryan ango Shamsuddeen yaji yana mishi magana.

"Haba Zafar yanzu ka kyauta min kenan, har an fara shagalin biki na baka ciki?"

"No Shams it's...., No just ba zan iya zuwa ba saboda wani dalili nd......"

"Dan Allah mana kada kace haka please ko minti 2 ne Zafar we really need u here ,pls I'm begging..."

"Stop that mana sai ka roke ni ne zan zo bikin ka, aiko saboda Sadiq zan zo ko yanzun ma wani issue ne yake son shige min gaba but gani ni nan zuwa tunda kace ko minti 2 then I will come sai dai ba zan dad'e ba" yana gama fad'in haka ya katse wayan tare da mikewa zuwa bathroom.


Can b'angaren su Ango kuma sadiq yana kallon Shamsuddeen daya gama waya yace" ya zai zo d'in?"

Gyad'a kai shamsuddeen yayi yana murmushi suka cigaba da shirin su.

******"""""*******

Tunda nazo gidan bikin na daure zuciya ta ake ta hidima da ni sai kai komo muke, cikin wannan yanayin ban fasa trying number Yaya na ba sai dai amsar daya ce a kashe har a wayan Maryam na gwada wai ko daga layi na ne a natan ma switch off ake ta maimaita min, bayan munyi sallahn la'asar Maryam ta takura min muka tafi saloon inda akayi mana gyaran gashi lalle sannan aka mana kwalliyan mu.

Muna dawowa daga saloon muka saka ankon mu na material Les dark blue da tie milk color sosai kayan suka zauna a jiki na, nayi wani kyau ina haske sai ka zata nice ma Amaryan , Maryam itama tayi kyau sosai abinta,

Lokaci yanayi mutane suka fara tafiya ga motoci birjik sai wanda ka zaba zaka shiga wasu kuma a nasu suke tafiya, duk yanda Maryam tayi min nasiha kan in saki raina cikin jama'a in kwantar da hankalin na Yaya na yana lafiya amma na kasa.

Ko da muka isa ma banyi wani abu ba na nemi waje na zauna kan wani table da babu kowa saboda ina bukatan kad'aici na fad'a duniyar tunani anya Yaya na lafiyan shi kuwa Allah yasa haka Allah ya kare min shi duk inda yake Ameen.

Haka na cigaba da tunanin shi ina yi mishi addu'a Allah ya kare shi yasa yana cikin koshin lafiya tare da kokuwa da hawaye cikin ido na da suke ta bara zanan zasu fito ina maida su ciki.

****************

A hankali yake takun sa cikin natsuwa da kasaita ya nufi wata bakar latest Honda wanda zai fita dashi, tsab yake kaman wani basarake yayi matukar kyau cikin half jamfa na wani arnanen voile milk color mai duhu wanda ya kara haska farar fatan sa, bai saka hula ba,gashin kan shi da sajen shi sun sha gyara sun kwanta lub sai sheki suke sai kamshin tsaddaun perfumes d'in shi yake, bai yiwa iyayen nashi sallama ba ya fad'a motan shi yaja ya tafi.

Sowan abokan sa sosai ke tashi a lokacin da ya iso na murnan zuwan nashi dan wasu sun fidda ran cewa zai zo, bai biye musu ba hannu kawai ya d'aga musu ya wuce ya samu waje ya zauna yana auna maganan Abban shi wai shi zai had'a shi aure da 'yar kauye shida na birnin ma basa burge shi in aka aura mishi ita ko Ina zai kai ta, oho.

Yana cikin zancen zuci yaji an dafa mishi kafad'a a dan razane ya d'ago yaga Sadiq ne tsaye a kan shi yana mishi murmushi yace " lafiya kake kuwa tun d'azu ina tsaye s kan ka ina maka magana baka ji ba har sai da na tab'a ka, kuma baka je kun gaisa da Shams din ba kazo ka zauna kai kad'ai".

Zafar kallon shi kawai yayi ya d'auke kai ba tare da yace mishi ci kan ka ba kuma bashi da niyyan tankawan.

A zuciye Sadiq ya mike zai bar wajan yana fad'in " d'an rainin hankali kada Allah yasa kayi maganan ai dama ka saba wulakanta mutane...".

Caraf yaji Zafar ya riko hannun shi ta baya tare da dawo da shi baya fuska a had'e yace" seat"

Ba musu Sadiq ya koma ya zauna yana mai nazarin yanayin Zafar d'in ,duk da bai cika faran-faram da mutane ba amma yaga tarin damuwa da tashin hankali a tare da shi kasancewar shine mafi kusanci dashi bayan iyayen shi.

"Wats wrong u look so disturbed?" Sadiq ya tambaya cikin kulawa.

Hannun shi duka 2 ya d'aura a goshi yana murzawa kaman ba zai amsa ba can kuma yace" ina cikin damuwa Sadiq kasan yau Abba ya dawo da naje...."

"But naga kayi aski ai ko an bashi labarin kaje wani party ne?" Sadiq ya tambaya yana dariya.

"Shut up just shut up it'ss not a joke ina gaya maka damuwa na nd u e making fun of me" Zafar ya katse shi a hasale.

"I'm sorry sorry pls I don't mean it naga kawai shine matsalan ka da Abba most time" cikin rarrashi da kwanantar da murya Sadiq yake magana yaga da gaske abokin nashi ya fusata.

"In wannan ne da sauki kaima kasan ba zai dame ni ba cos I'm used to it " sai da ya sarara yana had'iyen zuciya alaman abinda zai fad'a ya mishi zafi yace "can u imagine abba ya bani 3 days wai in kawo matar da zan aura ko ya had'a ni da 'yar kauye".

Dariya Sadiq ya kwashe da shi harda rike ciki yace" kai nagodewa Abba yayi min maganin ka Wallahi ba ka raina 'yan matan Nigeria gaba d'aya ba, shikenan anyi maka mai kankat waya ga Zafar da village girl.

Kasan me on ur wedding day ko kuma on ur dinner with d village girl nine zan....."

A fusace Zafar ya mike ya koma wani table ya bar Sadiq na kwasan dariyan mugunta, yana zaune a wajan sai saka da warwara yake na yanda zai zillewa auren da Abba keso ya lik'a mishi idon shi ya sauk'a a kaina da nake zaune a gefe ni kad'ai kai na a sunkuye kan waya ta sai neman layin Yaya na nake da bata shiga.

Ido ya zuba min ko kiftawa baya yi harda tagumi yayi kana ganin shi kasan yayi zurfi cikin nazari ni kuma ban san wainar da ake toyawa ba.

Tab'a shi da akayi ya dawo dashi daga dogon tunani daya tafi ya juya yaga Sadiq ne, gira daya ya d'aga mishi yana murmushi yace " da alama dai Abba ba zai had'a ka da village girl ba".

Cikin sauri shima ya amsa yana" yes I won't let dat happen Sadiq, look at dat girl Sadiq" yace tare da kallon inda nake zaune, bin wajan da kallo Sadiq yayi kamin yace" yes na ganta tun a can nake kallon yanda ka tsare 'yar mutane da ido, so finally Zafar got d love of his life,love at first sight huh"

Buge mishi kafad'a Zafar yayi yana hararan shi yace " dallah can who told u I love her kaima ka san abinda ba zai tab'a yiyuwa bane *BA SONTA NAKE BA*. I just have plan on her dat will free me from Abba".

Masu tambayan karshen Uwani ku kara hakuri shima zan cigaba nan bada dad'ewa ba.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*17*

Komawa yayi ya zauna bayan ya tsurawa Zafar ido sannan yace" ban gane me kake nufi ba, *ba sonta kake ba* pls ka warware min ka saka ni a duhu" cewar Sadiq kenan.

Ajiyan zuciya ya sauke mai nauyi irin ya samu relief d'in nan yace" well ba wani abu bane just zan kai ta a matsayin wacce zan aura wajan Abba in akayi auren shikenan I'm a free man ba mai takura min akan rashin aure in tayi 1 or 2 month sai in sallame ta, that's all".

"What!! " Sadiq ya fad'a cikin zare ido sannan ya cigaba "Zafar me kake nufi da cewa zaka aure ta bayan wata d'aya ko biyu ka sallame ta, rayuwar 'yar mutane zaka lalata saboda cikan burin ka, haba my friend kada ka zama mai son kan ka mana wannan abinda kake yunkurin yi kuskure ne Babba".

Wani kallo Zafar ya watsa mishi na irin ka raina ni nan ya kawar da kan shi gefe kaman ba zai tanka ba ya bud'i baki yace " did u expect har wani abu zai shiga tsakani na da ita ne?

Zata amsa sunan mata tane a idon duniya but a zahiran ce ba haka bane kaima kasan irin wa'yan nan yaran ko kallo basu ishe ni ba balle ace zan so irin su ko kayi tunanin ni Zafar zan had'a shimfid'a da ita" ya fad'i hakan yana yatsina fuska kaman yaga kashi, shi dai Sadiq bai katse shi ba illa zuba mishi ido da yayi yana sauraron shi.

"Zanyi hakan ne kawai dan samowa kai na mafita dan haka stop dreaming cos ni *Ba sonta nake ba* as I said earlier" ya karasa fuskar shi d'auke da sansayan murmushi.

Har yanzu Sadiq ya kasa samun kalma ko d'aya da zaiyi amfani da shi ya gane abinda yake babban kuskure ne, shi kuwa hankali kwance ya zuba min ido yana kare min kallo a lokacin Maryam tana tsaye a kaina kan lalle sai mun shiga cikin masu rawa muyiwa Ya Shamsuddeen liki amma nace mata ba zan shiga zan koma gida saboda zazzab'i da naji yana son rufe ni.

Bata yarda ba sai da ta d'aura hannun ta kan goshi na taji zafi rau, a take taja kujera dake opposite da nawa ta zauna fuskarta d'auke da dumbin damuwa ta kama hannu na tace" Zareefa pls ki kwantar da hankalin ki nasan damuwa da kika saka a ranki shi ya haifar miki da zazzab'in nan,addu'a ya kamata muyi tayi Allah ya dawo dashi lafiya" duk cikin sanyin murya da tsigan lallashi take maganan.

Cikin son sakani dariya tace " ke nifa nafi ki damuwa Yayan mu ya dawo musha biki kin ga da bikin ku ne da muna can high table ba nan ba"

Ta koyi nasara dan murmushin da ban shirya ba ya tsubuce min tare da hawayen da nake shanye su tun d'azu, Maryam ba zata tab'a ganewa ba ni kad'ai ce na san yanda nake ji a cikin zuciya ta.

Rarrashi na Maryam ta fara da kyar ta samu nayi shiru ina ajiyan zuciya duk su Zafar suna kallon mu daga inda suke zaune, mikewa nayi ina gyara head tie dake kaina nace mata " zan tafi Maryam dan Allah kada ranki ya b'aci yanzu haka har na fara jin sanyi yana son rufe ni".

"No babu komai muje in raka ki but tayaya zaki tafi bayan baki da lafiya?" Maryam ta tambaya cikin kulawa.

Zan iya kada kiji komai" na bata amsa ina dafa kaina da nake jin kaman ya fashe.

"Thats d right time " cewar Zafar tare da shuran car keys d'in shi akan table , ba tare da ya juyo ba ya cewa Sadiq" zo muje".

Biyo shi Sadiq d'in yayi yana son yaga mai zai yi da yake cewa wannan shine right time, can gefen wasu flowers ya samu ya tsaya bayan ya fito daga cikin hall, Sadiq shima gefen shi ya samu ya tsaya.

Ko minti 3 basu yi da tsayuwa ba muka fito muma daga cikin ina tafiya a hankali ,har muka iso inda suke ni ban san da mutane a wajan ba naji muryan Maryam tana " Ya Sadiq ina wuni ku"

Sadiq d'in ne kad'ai ya amsa da " lafiya lau Maryam ya kuka fito lafiya kuwa?"

"Wallahi k'awa tace bata da lafiya shine na rako ta zata tafi gida"

"Subhallah Allah ya bata lafiya, amma ba zata iya driving a wannan yanayin ba ko da driver tazo?" Sadiq ya kara tambaya.

"No zan rakata bakin hanya ta hau napep ne".

"Allah ya bata lafiya" yace tare da kallon Zafar daya d'auke kan shi kaman baya jin me suke cewa alhalin duk hankalin shi yana kan mu.

Zungurin Sadiq yayi tare da yi mishi magana da ido, cikin sauri Sadiq yabi bayan mu ya tsaida mu yace " nan anguwan abin hawa yana wahala bari mu sauke ta tunda muma fita zamuyi"

Cikin farinciki Maryam ta fara musu godiya tare da jan hannu na zuwa wajan wata mota daya bud'e mana, da ido nakewa Maryam nuni da ba zan shiga motan su ba ita kuma ta min nuni da babu komai 'yan gida ne, rashin karfin jiki da hajijiya da nake ji ya bata daman tusa ni a bayan motan ta rufe tana d'aga mana hannu.

Kwantar da kaina nayi a jikin seat d'in tare da lumshe ido na fara shak'an wani fitinannen kamshi da ban tab'a ji ba a rayuwa ta, ina ji motan ya fara tafiya amma na kasa bud'e ido na can naji Sadiq d'in yana tambaya ta wani anguwan zasu sauke ni? Sai da naji a jiki na alaman ana kallo na ban damu da in bud'e ba saboda nasan sunan anguwan mu da na fad'a ne ya bashi mamaki kasancewar duka gidajen talakawa ne a anguwan.

"Sai ki nuna mana inda zamu bi mun shigo anguwan naku" muryan Sadiq ya katse min tunani, a hankali na bud'e ido sannan na nuna mishi hanya da zamu bi can nesa da gidan mu nace ya sauke ni anan.

Parking yayi daga gefe na bude kofan na sauka sauka a hankali cikin muryana mai sanyi da baya fita sosai nace " nagode jazakallahu khairan" na kama hanyan gida ina layi,da ido Sadiq ya rakani har na shige ciki.

Gyaran murya Zafar yayi wanda ya dawo da hankalin Sadiq ya juyo yana kallon shi yace" sai ka gaya min ma'anan kawo ta gida sannan dan wulakaci kaja baki kayi shiru na tabbata bata san mu 2 muka kawo ta ba.

"Mu tafi Mallam ba wai ka kama min tambayoyi ba" Zafar yace hankalin sa na kan wayan shi, girgiza kai kawai Sadiq yayi yaja motan suka fita daga layin dan wannan halin abokin nashi ya ci ace ya saba.

Da kyar na kai kaina d'akin mu na zube a gefen Inna da take kwance a kan gado,a firgice ta tashi zaune saboda ta fara bacci kuma bata ji shigowa ta ba.

"Wani irin rashin hankali ne wannan zaki shigo min d'aki ba sallama sannan kuma ki fad'o min a ka sai kace wata 'yar maye, ko daga wajan bikin kika

Please Login or Register in order to submit comment