Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

daga bakin sa ba. Cikin kuka mai fitowa tun daga karkashin zuciya ta ce,
“Idan sama da kasa za ta hadu, ba zan baka ‘yata ba ka kaiwa Mami....….”
Ai ba ta idasa rufe bakinta ba ta ji saukar marin da ya tafi da jinta da ganinta na wucin gadi, har sai da ta ga wuta da gilmawar taurari, kafin ta farfado ya sake shimfida mata wani, ya fizgo yarinyar dake bayanta, wadda a take ta soma canyara kukan da ya ratsa har cikin kwakwalwar Ibrahim…..

Rayhanah na durkushe tana regaining consciousness. Ta rasa a duniya take ko a lahira. Ibrahim ya kara da cewa,
“Idan don lasisin da na baki na soyayyata a gareki ne yasa za ki wulakanta min UWA, to kin yi kadan Rayhanah! Son ya ci uwatar! Soyayyar ta ci abu kazan.....ubanta. Ki gaida mutanen TAKAI”.
Ya raba ta gefenta ya wuce rungume da ‘yarsa, wadda har zuwa lokacin ba ta daina tsala ihu ba.
Wata Nurse ce dake bangaren Nursery, wai ita Regina ta karbi jaririyar daga hannunsa ta sanya mata kan feeding bottle a bakinta (nipple), sai ta yi shiru. Ta mika masa ita tana tambaya.
“Where is her Mum?”
Sai ya wuceta zuwa motarsa bai bata amsa ba.
Ya bude motar ya shiga ya zauna ya bude tawul din ya rufeta sosai ya kwantar da ita a kusurwar kujerar baya, ya dinga jan motar a hankali kamar mai tafiya akan kwai kada ya jijjigata.
In ka kalle su shi da jaririyar sai sunyi bala’in baka tausayi. Idanun shi sun kada sunyi jawur amma ba hawaye yake ba. Bakin ciki ne da fushi mai tsanani, yana mamakin halayen mata.
Kai ka so su, ka kaunace su da zuciyarka daya, ka so nasu har fiye da yadda kake son naka, amma ba za su saka maka da komai ba sai raini ga mahaifiyarka, wadda itace silar komai na zamowarka in existence har kayi girma da balagar da suka samu suka aura suke mora, ba don komai ba sai don saboda sun sameka a hannu.
To Allah wadaran soyayya! Shi ya sanya bai taba yiwa kansa sha’awar auren soyayya ba da farko saboda gudun irin wannan fiffikar.
Ga wadda yake murna da halayenta, dabi’unta da ginin da suka soma yiwa rayuwarsu, ta nuna masa itama bata da bambanci da sauran mata.
Har ya iso gida tunanin da yake ta yi kenan.

*****
[12/30/2019, 20:24] Takori: Sanda Rayhanah ta samu dawowa hayyacinta daga gigitattun marin Ibrahim sai ta mike tsaye hajijiya na dibarta. Dai-dai lokacin likitanta da Nurse suka shigo, cikin mamakin abinda ya kawo ta bakin kofa haka ko hutawa ba ta gama yi ba.
Haka suka sata gaba da lallami da ban baki har ta hakura ta koma gadonta ta kwanta. Suka ci gaba da abin da ya kawo su, suka bata magungunanta ta sha suka sanyata ruwan zafi suna ci gaba da kula da ita, kulawa ta musamman albarkacin Dr. Ibraheem.
Likitan ya tambayi babyn, tana kuka ta ce Babanta ya tafi da ita. Cikin mamaki suka ce
“Ina?”
Ta ce, “Ba ta sani ba”.
Sai kuka.
A take Dr. Aziz, Musulmin Lebanon ya kira wayar Dr. Ibraheem, magana suka yi mai kama da jayayya. A karshe ta tsinci maganar Dr. Aziz inda yake cewa.
“Wannan Issue dinku ne kai da iyalinka babu ruwan baiwar Allah, kada ka kwareta ka kawo ta uwarta ta shayar da ita ko in kai maganar kotu wallahi”.
A wajen Bature yaro ya fi komai muhimmanci, kuma gwamnati na da ikon raba Da da iyayensa idan irin haka ta faru, ko in an ga za su cutar da rayuwar yaron musamman kasar Amurka da Ingila.

Ba ta dai ji me Ibrahim din ya ce ba, Dr. Aziz ya ci gaba da bincikar lafiyarta. Ya yi rubuce-rubuce cikin file dinta, sannan ya iso gabanta a hankali ya ce,
“Ko mene ne ya hadaki da Dr. Ibrahim ki kwantar da kai ki amshi laifin, ki karbi jaririyarki ki shayar da ita kin ji? Babu abin da take bukata a halin yanzu sai ke da dumin jikinki, idan fa har kina son soyayyar uwa da Da ta kasance tsakaninku, kar ki bari a rabaku, kin ji?”
Tana share hawaye ta daga masa kai. Ya ce ta zo ya kaita gida in ji Ibraheem.
Ba ta da zabi in ba komawa gidan ba, jiki ba karfi babu passport ina za ta je? Sai dai ita ma ta yi fushi da Ibrahim a kan marin da ya yi mata, fushi irin wanda ba ta taba yinsa a kan kowa ba, including MAMI.
Shine ya danna bell a flat dinsu, Ibraheem ya bude daga shi sai farar singilet da wandon wanka gajere, ya bata hanya ta wuce inda ta jiyo babyn nata tsala kuka. Tsikar jikinta ta tashi gaba daya ta saurara don jin daga inda kukan ke fitowa, master bed room ne.
Ba ta bi ta kan wani Ibraheem ba ta je ta sunkuto ‘yarta ta fito. Dr. Aziz na nan falo tare da Ibraheem suna ta ragargazar Turanci kamar an bude CNN. Da alama mukabala suke yi, Dr. Aziz na tausarsa.
Ta zo za ta wuce dakinta ya ce,
“Come here Rayhanah”.
Tana matukar ganin kimarsa kasancewarsa consultant na gynecology din Illinois baki daya, kuma aboki ne na jiki ga Ibrahim, domin tare suka yi karatu duk da suna fanni daban-daban.
Ya mika hannu ya ce,
“Bani ita”.
Tana share hawaye ta mika masa, Ibrahim ya yi kicin-kicin ko kallon ta ya ki yi.
Dr. Aziz ya ce,
“Durkusa ki ba shi hakuri”.
Sai ba ta yi musu ba ta durkusa din.
“Ka yi hakuri Ya Himu, bai kamata ka yi hanzarin yanke hukunci a kaina ba, ba tare da ka tambayeni dalilina ba.
Na san abinda baka sani ba. Mami ba ta sona, shi yasa Daddy yake boye mata aurenmu.
To kuma ga zuri’a ta soma taruwa ina so Mami ta sani…. ina tsoron..,. ina tsoron… kada ta ce ba za ta amshe ta a matsayin jika ba…. tunda ba ta san da aurenmu ba”.

Cikin harshen Hausa take yin maganar cikin kuka da karkarwar murya, kada Dr. Aziz ya fahimta.

“Wannan statement da kika fada wai bata son ki, kamar ya ya ba ta son ki, ban gane mata ba? Wane irin so kike so ta yi miki bayan wanda ta yi miki tun kina Rahanen ki?
Da bakina mun yi fada da Mami a kanki, da na ce ban yarda da zamanku tare da su Abida ba. Cewa ta yi ita babu ruwanta, Da na kowa ne, za ta rike ki tsakaninta da Allah.
Sannan don yanzu na ce zan sawa ‘yata sunanta ki nemi wulakanta min ita Rayhanah? Sam, ba zan dauka ba wallahi. Ki yi mana duk zabin da kika gama dama, a shirye nake da karbar duk hukuncin da kika yanke. Sunan ‘yata Asma’u, Rayhanah ki yi duk abin da za ki yi….”
Ganin cewa ba ta da hujjar da za ta kare kanta a kan wannan bayani na Ibrahim a kan mahaifiyarsa, sai ta bi shawarar Dr. Aziz wanda ke ta daga mata kai da kada mata ido alamar ta dauki laifin, sai ta kama kafarsa….
“Na yi kuskure Ya Himu, don Allah ka yi hakuri….”
Ta ci gaba da rera masa kuka mai nuna MARAICIN ta.
“Ba ni da uwa, bani da uba, bani da komai sai kai da Baba Dacta, sai ‘yar da Allah ya bamu yau din nan. Idan ka rabani da ita ka ki ni saboda kuskurena ina za ni? Ibrahim ina zan sa kaina???”.
Ta kwantar da kai a kan gwiwoyinsa tana sauke ajiyar zuciya.

Ga mamakinta sai Ibrahim ya mika hannu ya dago habarta yana share mata hawayen da ‘yan yatsunsa zara-zara guda biyu. Sai Dr. Aziz ya yi gyaran murya don su san da zamansa a falon, domin ga dukkan alamu suna bukatar fiye da hakan wajen lallashin junansu.
Rayhanah ta mike ta zauna kusa da Ibrahim, ya mika hannu ya sarkafo kugunta. Dr. Aziz ya ce,
“Kin iya breast feeding?”
Ta girgiza kai cikin jin kunya wato “A’ah”.
Sai ya hau nuna mata,
“Haka za ki rike ta, ki dago ta haka…. Ki sanya nipple din a tsakanin yatsunki biyu, sai ki sa mata a baki. Amma ki dinga yi da lura kada ki toshe mata hanci.
Idan ta sha da yawa sai ki dagata ki dora a nan…. (ya nuna mata) har sai ta yi gyatsa”.
Rayhanah ta daga kai. To ungota yi in gani. Ta karbi ‘yar, amma don kunya sai ta yi dakinta, ba za ta iya wannan rashin kunyar ta likitoci ba.
Ba Dr. Aziz kadai ba, Ibrahim ma ya yi dariya. Ya raka Dr. Aziz har motarsa ya dawo ya rufe gidan bayan ya sallami Benjamin.
A yadda ya shigo ya same su, ta takarkare tana aikata yadda Dr. Aziz ya koya mata ne, har ‘yar ta kama hungrily tana ta tsotso. Sai suka ba shi sha’awa da tausayi, duk da har lokacin bai gama warewa sosai ba.
Itama din kuma a shake take, bata huce ba daga marin barin makauniyar da yayi mata. Kawa-zucin ‘yar dama shi ya fi damun ta, tunda ga abarta a hannu, to babu laifi ko Ibraheem ya ci gaba da dukanta.
Sai ga hawaye sur-sur! Suna tittidowa. Ibrahim ya zauna a kusa da ita a hankali, ya turmutsa yatsunsa cikin kwantacciyar sumar kanshi ya lumshe ido a hankali, sannan ya bude yana kallon yadda ‘yarshi ke zukar nonon uwarta, ya tabbatar ya dau alhaki, ya san Rayhanah kuka take, amma bai yi yunkurin komai a kai ba.
Wata irin soyayya ce mai yawa ta tsakanin uba da Da ke ratsa shi. A lokaci guda kuma tausayin Rayhanah, yana tuna kalaman da ta gaya mishi dazu.
Wannan shine a doke ka a hanaka kuka. Shi kansa ya san Abida ba ta son Rayhanah, amma bai san da Mami ba.
Haka nan ya yi mamakin dalilin da yasa Daddy ya hana shi gayawa Mami aurensa da Rayhanah, in haka ne akwai ayar tambaya a tsakanin mu’amalar Rayhanah da Mami. Ya tuna cikin kalamanta tace

“nasan abinda baka sani ba!”

Har kuma zuwa inda yau ke motsi, daga Daddy har ita babu wanda ya yarda koda cikin raha ko subutar baki ya gayamasa dalilin fasa auren Rayha da Khalipha. Saidai su ce
“Allah bai yi ba!”.
Eh, gaskiya ne komai sai Allah ya yarda, amma babu abinda ke faruwa a duniya babu dalili.
Sai ya ji jikinshi ya yi sanyi, mai daki shi ya san inda yake masa yoyo. Zuciyar Rayhanah mai kyau ce, ba za ta fadi sharri ko batanci haka kawai a kan kowa ba, balle a kan uwar da ta haife shi.
Tukunna ma, shi shekarunsa nawa baya tare da su? Ya san irin rayuwar da suka yi cikin tsayin shekarun ne?
Da wannan tunanin ya mika hannu ya rungumo matarsa, ya kwantar da kai a kafadunta, zuciyarshi cike da nadamar saurin kai hannunshi ga lafiyar jikin wadda ta ba shi farin cikin rayuwar da bai taba tsintar kansa a ciki ba. A kuma ranar da ta ba shi farin cikin ko hutawa ba ta yi ba.
Jinta gaba daya jikin Ibrahim kamshin jikinsa na ratsata sai ta idasa narkewa, hawayen suka kara shimfidowa a kan kundukukinta.
“Ki yafe ni Rayhanah, kin yafe min Rayhanah?”
Ta daga kai….
“A’a, wannan bai gamsar dani ba, bude bakinki ki gaya mini….”
Ya fada a lokacin da ya dago habarta. Sai ya soma dauke hawayen da harshensa. Runtse ido ta yi, amma jin Ibrahim na neman zafafa al’amarin sai ta kwace.
“Malam yi a hankali, dinkin likita ce”.
Ibrahim yasa dariya ya sake kamo ta.
“Ba sai a sake dinkewa ba???”

Ya fada da muryar da ta gaya mishi hakan shekaru biyu a baya. A take ta tuno da first night dinsu. Ta juya masa keya cikin jin kunya tana jijjiga babyn.
Ibrahim ya sake binta ya ce,
“Ko kwaryar ba masaka tsinke ne inda za a sake soka allurar?”
‘Yar ta aje cikin ‘yar katifarta, ta dau filo ta danne shi tana bugu. Sai ya hantsilota ya koma samanta ya mamayeta yadda ko motsi ba za ta iya ba. Cikin dariya da shaukin bege mai yawa ya ce,
“Wallahi ki bini a hankali, in ba haka ba wannan dinkin farkashi zan yi yanzu”.
Ganin ya soma zarce Zaria ta soma lallashi, wanda ba ta san yaushe ta iya ba, har da su dadin baki, kirari da bambadanci.
“Haba dan Ibro na…. angon Rayhanah Baban Asma’u….. dan gaban goshin Baba Dacta.....likitan likitocin kodar Rayhanah......” Ibrahim dariya yayi yace
“har kin tunomin da Ado, oh su Rahane da yanzu fa anada ‘ya’ya goma” ta shaka tayi fus, kamar alkubus. A ranta tace “yanzunnan zan rama”.
“Ai dai duk da kaki bani shayin da Baba Dacta yace ka bani, ka turo inyamuri ya bani, kuma arzikin kalma ko ta sannu ce ban taba samu ba, na ganka kana mazari kana tsuma kana gwada ‘yar kashi da Adon don yana kokarin shimfidar ni.....”
Inda abin da ya tsana a tayar ko a tuna masa a duniya to wannan zancen ne. Ai kuwa a take ya koma serious. Fuskarsa tayi kicin-kicin kamar ba shi yake rahar da yake yi yanzun ba.
“Rayhanah zamu bata, uwar Asma’u zamu bata……”
“Na tuba….. na bi Allah na bika Baban Asma’u. I’m in nostalgia (ina cikin begen gida)”.
“Nima gidan nake so Rayhanah, amma bari Mamina ta yi dan kwari zuwa watanni biyar haka”.
Har cikin ranta ta gamsu da hakan.
******

WELCOME TO THE WORLD ASMA’U IBRAHEEM MANSUR

Rubutun da za ka fara cin karo da shi kenan a kasan tangamemen hoton da za ka fara cin karo da shi da zarar ka shigo falon nasu, mai kama da fadar wani gwamnan a Nigeria.
Uwar da Uban ne cikin ‘Native Hausa Attire (shadda da Atamfa) shi dinkin Mohammed na shudiyar shadda sheraton da hula Damanga shudiya mai duhu, sun sa buleliyar ‘yar tasu a tsakaninsu kowa ya rungumo bari daya, wadda ta washe ta yi haske ta zama kamar ‘yar Sudanese, dukkansu bakinsu a washe, fararen hakoransu a warwaje kamar masu tallan colgate. Itama ‘yar bakinta kamar ya tsage da dariya, cleft da beauty point din Mami da Ibrahim duk sun lotsa.
Hoto ne wanda Ibrahim ya turawa Baba Dacta copy dinsa cikin wayarsa, ta hanyar BlackBerry Messenger. A lokacin yana kan hanyar komawa gida daga wajen aiki.
Ya ji shigowar hoton amma bai bude ba, sai da ya shiga get Mal. Dahiru ya rufe ya adana motar a rumfar adana motocinsu.
Ya dauko kwat dinsa da bakar jakarsa tukunna ya bude. Sai da ya jingina da motar kada kafafunshi su kada shi. Kwallar farin ciki ta tsiyayo daga idanun Dr. Mansur. Ya tsura musu ido dukkansu ukun kamar ya hadiyesu don kauna.

Wannan rana yake jira, ya maidawa Asma’u martanin bakin cikin da ta kunsa masa shekaru uku da suka wuce. Ai bai shiga gidan ba, mota ya koma duk da gajiyar dake jikinsa ya sake fitowa ya nufi Arewa Studio dake Tarauni ya basu suyi mishi window size guda biyar zai dawo gobe ya amsa, bayan ya biyasu.
Wani abin mamaki a washegari bayan ya karbo hoton sai ya dasa a falonsu, daya a bed-room dinsa, daya a dakin su Abida, a lokacin duk basa nan. Jawahir tana Hurghada, Mimtaz ta sake haihuwar da namiji again. Mami na office, Abida da Aziza suna makaranta.
Bayan ya kakkafa enlargements din ya yi tafiyarsa office dinsa da nasa copy din da zai sa a office dinsa, zuciyarsa kal kamar madara. Duk inda ya gitta cikin ward din su an san Dr. Takai yau yana cikin farin ciki. Sai raha yake yi da likitocin da ke karkashinsa da marasa lafiyansa.
Dr. Kofar Mata ya kasa shiru ya ce, “Wai Dr. Mansur hala amarya ka yiwa Dr. Ma’u?”
Bakin Dr. Mansur har kunne ya ce, “Eh, kamar ka sani kuwa wallahi Dr. K/Mata, gata”.
Ya mika masa hoton da ya yi saving a fuskar wayarsa.
“Zo muje office ka ga amaryar tawa sosai”.
Ai kuwa ya mike ya bishi office ya nuna masa tangamemen hoton. Dr. K/Mata kamar yau bai ci abinci ba, haka ya bude baki yana ta kallon hoton.
Ya ce,
“Wannan kamar Ibraheem, ‘yar kamar Asma’u, matar ce ban sani ba”.
Murmushi ya yi ya ce,
“Ita ma ‘yata ce, ni nake rikon ta”.
Dr. K/Mata ya ce, “Masha Allahu, Allah ya albarkaci little Asma’u ya rayata cikin tafarkin Islama, amma ban san sanda Ibraheem ya yi aure ba”.
“Auren ne ya zo a kurace, amma abu wajen shekara uku”.
Haka suka yi ta zancen Ibrahim da iyalinsa, suka manta da patients dinsu.

A take Daddy ya turawa Hakimi da Haj. Karima da Inna Juma, wadda ba ta yarda ta zauna a Farm Center ita kadai ba, tana gidan Hakimi, can aka ba ta daki take zaune. A take kuwa suka hau kiran wayar Dacta suna neman karin bayani, baki har kunne Daddyn ke amsa musu.
Tafi-tafi zance ya yadu cikin gidan Hakimi da wajensa Ibrahim matarshi ta haihu, ‘ya kamar Asma’u. Wannan kadai ya isheta aya, idan fa har tana da hankalin tsinkayen hakan kenan.
Abida da Aziza ne suka fara dawowa gidan a gajiye tubis, suka baje a falo suka kure A.C. Kamar an ce da Aziza daga kanki ta yi arba da tangamemen hoton, ta hau zubawa Abida duka a cinya.
“Yaya Abida….. Yaya Abida ....sister…. Sister kin ga… kin ga”.
Abida ta juyo a fusace domin har ta samu barcin gajiya ya sureta Aziza ta katse mata. Tana niyyar mangare Azizah sai ta ji tana fadin.
“Kamar Ya Himu da RAYHANAH da ‘Cute Baby!”.
Abida ta daga ido ta kalli side din. Ai da sauri suka mike dukkaninsu suka runtuma ga hoton suna kallo sosai. Iyakar rikicewa da firgita Abida ta yi.
A take ta ja waya ta kira Mami.
“Mami ki taho gida maza – maza yanzu ki ga wani abin mamaki”.
“Mene ne?”
Ta fada da dan karfi.
“Ke dai ki taho Mami za ki sha mamaki, idan fa har baki suma ba”.
Ta kashe wayar ta kyale Mami.

Dr. Asma’u ta dade tana juya kan wayarta a hannunta. Ita ba ta son irin wannan sam, a ce ta yi abu, amma ba a gaya mata dalilin yin shi ba. Tana da ayyuka masu yawa a gabanta amma dole ta ture ta mike don Abida ba ta taba yi mata haka ba.
Abida jikinta bari yake, saboda kaduwa da razana. Azizah tsalle take, tsallen murna tana fadin
“A perfect match! Miskila, sai miskili dan’uwanta. Daddy the matchmaker! What a beautiful daughter I’ve….. wayyo ni dadi kashe ni.
Come soon baby Asma’u in goya ki in miki rawa in cillaki in café ki”.
Ta isa ga hoton ta sumbaci yarinyar daidai lokacin da Mamin ta fado falon. Abida ta janyota ta isar da ita ga hoton tana fadin
“Mami dubi rainin hankalin da aka miki, har aure Ya Himu ya yi da tsintacciyar yarinyar nan har sun haihu baki sani ba saboda an raina ki…..”
Ba ta kai ga rufe bakinta ba Daddy ya fito daga dakinshi yana ba ta amsa da cewa.
“An raina ta ko ta raina kanta annamimiya? Ba tun yau na kwana da sanin mugun halinki ba, to ki sani, ita wannan da kike kira tsintacciyar mage ta zama jininki, dolenki, uwar ‘ya’yanki ko ki mutu, ko ki yi rai ba abin da zai sameta da ikon Allah, wai don kun wulakanta ta.
Babu yadda za ku yi da ita, sai dai ku ci gaba da raina kanku, domin KAINUWA ce dashen Allah, kuma murucin kan dutse baka fito ba sai da ka shirya!!!
Idan kuna da hankali wannan ya isheku ishara. An gaya muku ana yiwa Allah shisshigi ne cikin al’amarinsa?”
Ya juya ya shige dakinsa.
Abida ta yi tsumu-tsumu, ita kuwa Dr. Asma’u sai ta zube a doguwar kujerar falon tana kuka, kukan da dukkansu basu san dalilin da yasa take yinsa ba, na bakin ciki ne ko na nadama? Allah kadai ya san me ke a zuciyar bayinsa.
Cikin zuciyarta Allah ya isa take wa Dr. Halima da ta goga mata bakin fenti a idanuwan wanda ya fi kowa sonta a duniya, ya yarda da ita, ya ba ta amanar gidansa. Ya yi mata kyakkyawar shaida a zuciya da bakinsa na uwargida ta gari. Yanzu wane bayani za ta yiwa Daddy ya saurare ta?
Babban bakin cikin Mami kullacin da Dacta Mansur ya yi mata a kan ikon da ta nuna a kan Khalipha da cewa da ya yi ta nuna masa yau ba shi ya haifi Khalipha ba….. tabbas ta dade da manta wannan

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment