Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tace.
"To muje ki hau gado ku kwanta ni kuma sai in kwanta a ƙasa kam carpet ɗin.
Gyada tayi cikin gamsuwa da hakan.

Haka sukayi Ummi ta kwanta a ƙasa ita kuma Hibba ta konta gefenta a ɗan tsorace.

Ita kam Shatu batama san sunayi ba, domin bacci mai nauyi takeyi.


Haka dai Ummi tai shiru saida ta tabbatar Hibba tayi bacci kana ta koma ɗakinta.


Washe gari da safe bayan Ummi, Saratu, da Hibba sun gama karyawa ne.
Shatu da tunda tai sallan asuba ta koma ta konta kan sallayar sai yanzu ta fito.
Tayi wonkanta fes ta ƙenƙesa ado da kolliyar ta ba irin mai ramɓatsau ɗin nan ba.
Komai dai-dai tayi abunta.
Riga da siket ne na Mateyal mai taushin gaske, White Coffee mai kyau.
sai ɗan ƙaramin gyale ta yafa a kanta, cikin nitsuwa ta fito.
A falo ta zauna tare da juyowa ta kalli Ummi dake shirya abinci a Dinning table.
"Ina kwana Ummi".
Tace cikin muryarta Normal.
Cikin kulawa Ummi ta juyo tare da cewa.
"Lafiya lau Shatu. Kin taso kenan".
Murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"Ummi meyasa baki tadani ba, kika shiga kitchen da kanki".
Kai ta jinjina tare da ɗaukan cup mai ɗan girma,
Tea mai kauri ta haɗa a ciki kana,
ta taho inda take miƙa mata cup ɗin tayi tare da cewa.
"Gashi amshi kisha, aiki kam ai saida lfy".
Amsa tayi tana murmushi a hankali tace.
"Lfyata lau ai Ummi kawai dai baccin ne ban san meyasa nake ta yinshi ba".
Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata,
Kana ta juyo tace.
"Hibba kawo mana namu abincin nan muci.

Najiyo Muryar Jamil suna zuwa, kuwa wata ƙil dasu Imran zasu zo".
To tace kana ta ɗauko musu nasu Foodflaks ɗin da plate and spoons da ta kawo musu.

Jolof ɗin taliyace da kifin banɗa dasu Kabeji da karas da green beans da dai sauran kayan haɗin.
Sai kuma, ferfesun kayan ciki.
A plate ɗaya Hibba tasa musu, da ita kana ta sawa Ummi.
Kana tasa musu fork, tare da cewa.
"Bismillah Aunty Shatu sauƙo muci ko".
To tace kana ta sauƙo,
suka fara cin abincin.
Amman ina tayi loma ɗaya sai ta kusan 4 minute bata kuma sawa a bakiba.
Sai dai ta shanye tea ɗin ganin hakane yasa Ummi ta ƙara haɗa mata wani shayin.
Shima ta shanye abinta fes, taliyar kuma baifi cokali biyar ba tayi.

Su Jalal kuwa suna shiga suka wuce Dinning area suma sukayi breakfast ɗin kana suka fita, sabida hidimomin salla. Domin yau za'ayi hawan daba, Jalal kuma mayene mai zaman kanshi a kan sarrafa, doki, ɗan daga Affan sai shi.
Bayan Sheykh a iya sarrafa doki kab Masarautar Joɗa .
Amman shi Sheykh ya daɗe da cewa shi ya girma da yin wannan sakarcin.

Su Ummi kuwa, kitchen Suka kuma shiga.
Sanin yau tabbas akwai baƙi masu ɗimbin yawa da masarautar Joɗa zata amshi baƙoncinsu.
Domun ƙananan sarakunan wasu garuruwanma duk zasu zo da tawagar su.
Haka yasa suka shiryawa taron haiƙan ƙadaran ko wani Side dake gidan za'ayi abinci a ciccika manyan kuloli a kai fadar Lamiɗo, wani a kai sashin bayi.
Kana kuma ko wani Side da baƙin su.
Haka yasa su Ummi da Saratu da Larai zagewa.
Sukayi abinci kala-kala kana suka ciccika kulolin aka kai fada akai wurin bayi.
Sannan sukayi nasu kuma suka sassaka a Foodflaks masu ɗan karen kyau suka jera a Dinning table,
tare da plate, spoons, and forks. Kana sun cika Fridge kuma da drinks kala-kala.
Sun kuma yi Pepper Checken mai zafi na zabbi.

Sai kusan ƙarfe ɗaya suka gama komai,
Su Saratu suka kimtsa komai kana suka tafi.

Su kuma duk suka shiga ɗaki da nufin yin wonka.
Tuni zuwa lokacin Masarautar Joɗa ta fara ɗinkewa da baƙi tako wani sashin.

Sheykh Jabeer kuwa, tunda ya tashi.
Ya nufi cikin Garden ɗin nan da ababen tarihin masarautar Joɗa yake.

Zazzagayawa yakeyi yana dubawa, dan tabbatar da babu wani abun da zai cutar da wani ko wata.
Sabida yasan yau manyan baƙi zasu shigo ciki.
A nuna musu ababen tarihi da dai sauransu.

Gefen da curin da macijiyar nan yake ya nufa.
Ya dudduba ƙofofin ba hayaƙi ba komai.
Sai dai in mutun ya kasa kunne zaiji sautin numfashin macijiyar ka da ƴan ƙanana kuka irin na ƙananan macizai.
A hankali ya ƙara matsowa bakin curin. Cikin nitsuwa yayi gyaran murya.
sai kuma yaji sautin kukansu da kuma numfashin uwar ya ƙaru sosai.
A hankali yace.
"Assalamu alaikum, ya ke wannan halittar Ubangijin sammai da ƙasai".
Gyara tsayuwarshi yayi jin numfashin na ƙara matsowa.
A hankali yace.
"Ba cewa nayi ki fitoba, nazo in roƙeki ne kamar yadda Manzon Allah ya sanar mana, dukkan halitta tanaji.
Kuma ina kaga wani abun cutarwa a gidanka ka haɗashi da Allah da Manzonsa kace ya fita.
Manzon Allah ya bamu tabbacin.
Muddin ba mai cutarwa bane zai fita.
In yaƙi fita kuwa ka kasheshi".
Ɗan zagaitawa yayi jin kukansu ya kuma tsananta, cikin sanyi yace.
"Ni bazan roƙeku kan ku fita ku bar muhallin zamanku da ban san tsawon shekara nawa kuke rayuwa a wurinba.
Kuma bansan dalilin zamanku a wurinba.
Shiyasa bazance ku bar Masarautar Joɗa ba.
Kuma bazan kasheku ba,
Sai dai roƙana garemu.
Munada baƙi a Masarautar Joɗa kuma yau zasu shigo, dan Allah da Manzonsa, kada ku fito ku baiyana kanku ga baƙinmu kada ku razana mana baƙi kada ku cutar mana da mutanenmu.
Kuyi zamanku a muhallin ku".

Shiru sukayi tsit alamun sun jishi kuma sun gamsu".
Fahimtar hakane yasashi cewa.
"Na barku lfy".
Yana faɗin haka ya juya, Lamiɗo da Galadima ya gani tsaye a bayanshi.
Murmushi sukayi tare da matsowa inda suke.
Galadima ne yace.
"Kada ka damu da fitarshi da zamanshi da yaranshi
Domin kai ke ganinshi a nan, amman duk in da wani mugu ya shigo masarautar Joɗa da nufin yiwa Lamiɗo wani abun zai ganta da yaranta a gabanshi.

Amman wanda yake jinin wannan gidan bazai ganshiba.
In kaga mutun ya ganshi saida sahalewar Lamiɗo".
Shiru yayi yana kallonsu.
Shi kuwa Lamiɗo a hankali yace.
"A ƙalla yafi shekaru ɗari biyu da arba'in a cikin wannan curi a wannan Masarautar tun zamanin baban kakana Joɗo yake nan, ba kuma tsafi bane, ba sihiri bane, kamar yadda kowa ya sani shi maciji curi gidan zamansa ne, to bulalin caɗin masarautar Joɗa kuwa suma asali nan suke da zama curin ne ya binnesu, kana macijiyar ta shiga ciki, shine ma dalilin hana shaɗi to sai dai lokaci zuwa lokaci in an sarki maici yazo wurin yayi sallama macijiyar kan fito, in zata fito takan fito da balalin a binɗinta. Sai daga baya ta fara fita ita da ƴaƴanta suna yawo cikin masarautar Joɗa ne, muka gane yunwa ke sata fitowa, sai ta shiga cikin kaji tasha kwayaye ta haɗi ƙananan kaji.
Lokacin da muka fuskanci haka sai muka fara kawo mata kwai a matsayin abincinta.
Daga baya muka fahimci in mutun ya shigo da mugun nufi tana razanashi".
Taɓa bakinshi yayi cikin rashin yarda bare gamsuwa yace.
"Ni dai ban tambayeka ba, inma tsafine kaidashi Ni nan Muhammad Jabeer bani dalaifi a ciki nayi-iya yina in rabaku da wannan tsarabe-tsaraben na masarauta kun ƙiya".
Ya ƙarishe mgnar yana juyawa ya nufi wurin da tsuntsayen wurin suke.
Gefenda aku yake ya nufa.
Tana ganinshi ta kaɗan fiffigenta tare da cewa.
"Sheykh Jabeer ya dawo".
Murmushi yayi tare da shafa kan akun yace.
"Ya dai tsuntsuwa mai daraja ya gida".
Cikin irin mgnarsu na Ali tace.
"Lfy Sheykh ya madina garin Manzon Allah".
Ta ƙarishe mgnar tana kaɗa kanta da jelarta alamun yiwa sauran tsuntsaye rigimar ance mata tsuntsuwa mai daraja.
Murmushi mai faɗin Sheykh yayi ganin.
Ɗawisun nan tazo gabanshi ta tsaya ta buɗe dogon jelanta ta kaɗashi tayi sama dashi.
har yana taɓa gemunshi cikin sanyi yace.
"A a kekyawar tsuntsuwa mai kyan ado da tafiya".
A hankali ta karkaɗa jelan kana ta fara zagayashi.
Tana nuna mishi kyan tafiyar.
Su kuwa sauran tsuntsaye kuka suka farayi.
Murmushi mai faɗi ya kumayi tare da cewa.
"Tsuntsaye masu zaƙin murya da sauƙin firewa".
Aifa nan suka tashi sama suna shawagi a wurin.
A hankali ya juyo ya kalli tarin tattabarun dake gabanshi mazan ciki suna ƙotowa wa matansu.
Kai ya rausayar tare da cewa.
"Iyayen soyayya duk cikin tsuntsaye bayaku a soyayya".
Ai sai suka fara irin kukansu nan guggdu-gudduu guuu".
A hankali ya fita yankin tsuntsayen bakin ƙoramar dake gudana a tsakiyar Garden ɗin ya nufa.
Inda agwagin ruwa keta shawagi a bakin wurin.

Zama yayi yana nazartan lamuran halittun ɗan adam.
Ko wanne halitta akwai mace akwai na miji.
Kuma ko wanne halitta namiji baya iya rayuwa saida macce.
To shi menene matsalarsa da duk manyan likitocin duniya suka kasa ganowa, kowa sai yace mishi lafiyarshi lau.
Shi kuma yasan baida lfyar maza, tunda bai taɓa jin wani abu ya motsa a zuciyarshi bare yasa wani sashi na jikinsa motsawa ba yana dai jin shi wasu lokutan a namiji jim kadan lbri zai sauya.
Gefenshi Lamiɗo da Galadima sukazo suka zauna.
Bisa wani carpet da hadimin da ya shigo yanzu ya shimfiɗa musu.
Yana fita wani ya shigo da kayan abinci.
Cikin kula Lamiɗo yace.
"Taho nan muci abinci Ustazu".
Hannunshi yasa ya shafa cikinsa.
Sosai yakejin yunwa hakane ya sashi gyara zama nan sukaci abinci su ukum su.

Gani. Ƙarfe ɗaya tayine, lokacin salla ya ƙara to.
Ga ɓaki nata shigowa masarautar Joɗa.
Yasa suka tafi.

Shi yana shigowa bathroom ya wuce. Wonka ya fesa mai rai da lfy kana yayi al'wala.
Kana ya fito ya kimtsa cikin wasu tattausan riga da gajeren wondo 3 qtr yasaka kana yasa tattausar rigar mai guntun hannun. Duk kalarsu Royal blue ne, sai ya ɗauka farar jallabiya. Fara mai ɗan karen kyau.
Kana yasa baƙar al'kyabbar jikinshi tare, dasa hirami mai fari da ja, yayinda hakama takalmanshi fari da ja.

Wasu sabbin turaran da ya seyo ya fesa a kan sabbin kayan da ya saka masu ɗan karen kyau.

Wani irin ƙamshi yakeyi mai daɗin shaƙa.

A hankali ya fito falonshi, kallon abinci dake jere kan Dinnin yayi kana ya wuce ya fita.
A falon ya samu su Jalal da alamun da al'wala a jikinsu.
Can falon Shatu yajiyo muryarta tana kiran Hibba dake ɗakin Mama.
Sai yanzu da yaji muryarta ne ma shi ya tuno da ita a gidan.
Kai ya kaɗa yasa ƙannenshi a gaba suka tafi.
Suna isa masallacin akayi sallan azahar.

Ƙarfe ɗaya da mintu arba'in suka firfito masallacin da ya cika yayi maƙil mafi akasarin matasa suna cikin shigar sukuwane.

Yana fitowa gida ya nufa sabida bai son yawan hayaniya, kuma zaiyi baccinsa da ya saba dashi, baccin tsakanin azahar da la'asar.

Su Jalal kuma cikin abokansu suka nufa.

Yana dawowa Falon Hibba kaɗai ya samu ta kunna tv tana kallon Film ɗin India kamar zai hanata kuma dai sai ya wuce.
Bayan tayi mishi sannu da dawowa.

Yana shiga ɗakin ya tura ƙofar ɗakin ya rufe ba tare dasa key ba.
Kana yasa hannunshi ya kashe fankar, tare da kashe wutan ɗakin.
A hankali ya iso bakin gadon. Zare Al'kyabbar ajikinshi yayi ya ajiyeshi bisa gadon.
Kana ya zare jallabiyar jikinshi itama ya ajeta kan gadon ya rage dagashi sai 3 qtr da ƙaramar rigar.
Dan sosai yake jin bacci, sanadin ɗan zafin hadarin dake haɗuwa yayi yawane yasa ya ƙara gudun AC kana.
A hankali yayi taku zuwa, gefen gadon agogon hannunshi ya cire ya ajiye a kan Bedside drower'n dake kusa dashi.
Konciya yayi a nan a ƙasa bisa tayis babu shimfiɗan komai bare pillow.
Wannan tsarinshi ne da yakeyi, wanda yanayin hakane dan tuna konciyar ƙabarin da wata rana zai riskeshi.
Wani lokacin ma, harda AC'n yake kashewa.
Yana konciya ya fara tasbihi yanayi a hankali idonshi na rufuwa, wannene yasa yakeyin bacci a lokacin da yaso.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa.
Cikin wani irin farin ciki Jalal Jamil suka nufi Side ɗin Hajia Mama jin labarin Ya Affan ya dawo daren jiya karfe biyun dare, a bakin Imran

A falo suka samu Hajia Mama cikin tarin bege da kewar ɗan uwan nasu Jalal yace.
"Mama wai Yah Affan ya dawo?".
Cikin murmushin tace.
"Eh ya dawo".
Da sauri Jamil yace.
"Yesss Jalal zomu tafi tafi Side ɗinshi Aunty Mami an shawo turai an dawo".
Da sauri suka tsaya jin Mama na ce musu.
"Basa nan tunda safe Aunty Mamin naku ta matsa ya kaita gida wai Abban Yusuf ba lfy, to sun tafi can, Aryan ma yazo bai sameshi ba shima ya tafi can duk sun haɗe a can".
Da sauri Jalal yace.
"Muje mu ɗauko shi dan wlh su Hamma Yusuf da Ya Aryan bazasu barshi ya dawo da wuriba".
Cikin murmushin Jin yadda yaran ke son Juna tace.
"Yanzu kuwa zasu dawo, dan kunsansu duka uku da son daba, sun girmama su basu bar hawa doki da tsereba kuma kasan Yusuf zaice suzo wurin uban gidansa Malam Jabeer".
To da hakane suka ɗan gamsu suka nitsu.

A can Dou Gire kuwa samun jikin Abban Yusuf da sauƙine yasa.
Suka shirya suka nufo Masarautar Joɗa.

Ummi ma tayi kolliyar sallanta tayi kyau ta fito falon, inda Hibba take.

Shatu kuwa tana ɗakinta lokacin ta gama yin kolliya tasa wani damdatsen Shadda lace mai masifar kyau, Royal blue ne mai kyau da ɗaukar hankali sai zaren lace-lace ɗin da akayi da red and pink guava mai masifar kyau, sai wani irin sheƙin shaddar takeyi tana fidda maiƙon kyau.


Doguwar rigace inrin fitet ɗin nan na zamani mai ɗan karen kai duk inda sirin yanken fisis ɗin yake an bishi da jerin duwasun shuwa riski masu sheƙin Daimond, cib-cib rigar tayi a jikinta.
Murza ɗauri ɗan kwali tayi irin mai stpes ɗin nan
Kana ta tura ɗan kwalin kaɗan wannan tattausan saje da suman dake konce a goshinta ya fito ras.
Sai ta baya kuma ta tsakiyar ɗan kwalin ta bar rami ta fito da jelan gashinta ya konto har kafaɗanta ba tare da ta kitseshi ba.
Wasu ƴan kunne da sarka na azurfa ta saka a wuyanta,
sai wani kekyawan agogon fata rea ƙirar Gucci ta manna a tsintsiyar farin hannunta da yake, ɗanɗase da zanen jan lalle mai kyau.
Gyale rea color mai masifar kyau ta ɗan yafa a kafaɗunta.
Wasu turaruka kala biyu ta fesa, kana ta kalli muskarta da jikinta a madubin.
Wayarta ta ɗauka ta ɗan kaikaice ta ɗauki kanta hoto ta cikin madubin tayi kyau sosai.
Wasu takalma marasa tudu tasa suma rea color ne.
Tana riƙe da wayarta ta fito falon.

Da sauri Hibba ta miƙe tare da cewa.
"Wow! Wow!! Wow!!! masha Allah Aunty Shatu kin ganki kuwa masha Allah."
Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Kai gsky amaryar Sheykh ta fito da madarar kyau masha ALLAH".
Ita dai sai murmushi takeyi dace musu.
"Ngd".
Cikin jin kunya.
Hibba kuwa duk takun da motsin da zatayi sai ta ɗauke ta hoto.
Daga ƙarshe ta rinƙa yi musu selfi su duka huɗu.
Saida suka gajine kana suka zauna suna hira.


Nan suka kira Umaymah suka sha hira.

Suna cikin hira Ummi ta juyo da sauri jin muryar Affan yana sallama tare da cewa.
"Assalamu alaikum. Ina Umminmu ina amaryar Hamma tuzuru".
Miƙewa da sauri Ummi da Aunty Juwairiyya sukayi tare da cewa.
"La Affan yaushe ka dawo".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Jiya da tsakiyar dare, ina Auntyn nawa".
Ya ƙarishe mgnar yana shigowa cikin tsakiyar falon.
Tafa hannu Ummi tayi tare da cewa.
"Suwa nake gani kamar Yusuf da Aryan".
Cikin dariya sukace.
"Muɗin ne dai Ummi".

Cike da jin daɗi Ummi da Aunty Juwairiyya ke cewa.
"Kai maraba lale lallai yau munada manyan baƙi , oh duniya Yusuf da Aryan kamar ba kuba".
Dariya sukayi tare da zama a kujeru.
Hibba kuwa tuni ta isa gaban Affan lakace hancinta yayi tare da cewa.
"Sakaliyar Umaymah ashe kina nan bana zakiga shagalin sallan Masarautar Joɗa".
Cikin sauri ya kalli Shatu dake ce musu.
"Sannunku da zuwa".
Da sauri ya juyo ya kalli Ummi kana ya kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa.
"Wannan ce Auntyn nawa amaryar Sheykh Ustaz Malam Dr Jabeer akarmakallu".
Murmushi Ummi tai tare da cewa.
"Eh itace".
Cikin dariya ya kalli Yusuf da Aryan da suke gaisawa da ita yace.
"Kan bala'i ashe dama Sheykh Hamma Jabeer yana kallon mata kalli yadda ya zaƙulo zankaɗediyar sarauniya".
Yusuf ne ya daki kafaɗarshi tare da cewa.
"Kaifa Affan ɗan iskane baka da mutunci, baiyi aureba kace mishi. Shugaban tuzuran Afirka.
Yanzu yayi auren kuma zakace yana kallon to dama ce maka akayi shi makaho ne?".
Dariya sukayi baki ɗayansu,
Aryan ne yace.
"Bar Affan da shegiyar surutu".
Dariya suka kumayi kana duk suka zauna.

Suka gaisa cikin tsokana Affan ya kalli Shatu dake danna wayarta tana kallon hotunan da sukayi yanzu yace.
"Aunty Amarya Hamman namu yana nan ne, ayi mana iso wurin shi mu kwashi gaisuwa".
Shiru ta ɗanyi tare da kallon Ummi.
Da sauri Hibba tace.
"Eh yana nan yanzu ya shiga".
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
"To Aunty Sayyada ayi mana sallama dashi ace ɗaliban shi ne, Affan, Yusuf, Arya,".
Cikin tsoron kada Shatu ta kuma zuwa ɗakin abun da ya faru jiya ya sake faruwa Ummi tace.
"Ai yana bacci ne yanzu ko".
Da sauri Affan yace.
"No ba matsala in ance masa Yusuf ne, tashi kice muna sallama dashi."
Cikin murmushin jin Yusuf da Aryan sunce.
"Eh gsky gwara mu gaidashi kada ya gammu a wurin sukuwa yace bamu nemi izininshi ba".
A hankali tace.
"To bari a gaya mishi".
Ta yunƙura zata tashine Ummi ta riƙe hannunta tare da cewa.
"Shatu kadafa".
A hankali tacewa Ummi.
"Ba komai fa Ummi".
Ganin hakane yasa Ummi ta sake mata hannun tare da cewa.
"To Allah yasa".
Amin Amin Juwairiyya da Hibba sukace.
Shi kuwa Affan cewa yayi.
"Allah bazaiyi faɗaba in yaji mune".
Kai Ummi ta gyaɗa sabida basu san me take tsoron ba.

Ita kuwa Shatu a hankali ta nufi Side ɗinsa.

Su kuwa hirarnsu sukaci gaba dayi a falon.

A hankali ta tura ƙofar falon nashi ta shiga.
Shiru babu kowa babu komai sai sautin ac dake tashi fuuuhhh.

A hankali ta lumshe idonta kana cikin sanyi ta nufi ƙofar ɗakin nashi.
Tare da cewa.
"Salamu alaikum! Salamu alaikum!! Salamu alaikum!!!".
Shiru babu motsin komai, hakane yasa a hankali tasa hannun hagun ta dafa ƙirjinta dake bugawa.
Kana tasa hannun damanta ta tura ƙofar Bedroom ɗin.
Sai kuma gashi ta buɗu ƙofar.
Wani sassanyan ajiyan zuciya ta sauƙe jin wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi daya ratsa mata jiki da zuciya.
Sallama ta kumayi shiru ba amsa.
A hankali ta cusa kanta cikin ɗakinta da yake duhu.

Wani irin bugawa ƙirjinta keyi kana.
Kanta na sarawa da masifan ƙarfi.
A hankali ta juya gefen mashigar ɗakin hannun tasa ta lalubi abin kuna wutan ɗakin danna ɗaya daga ciki tayi,
hakan yasa ƙoyin wutan ɗaya mai kalar Sky blue ya kawo wuta.
Sanadin hakane ɗakin ya kawo wani irin haske mai ƙayatarwa.
Yanayin wutan ɗakin labulayen da kayan jikinta dana jikinshi sukazo iri ɗaya.
Juye- juye tayi tare da cewa.
"To ina yak".
Shiru tayi bata ƙarisa rogowar mgnar ba hangoshi can ƙasa yana konce rigingine yayi pillow'n da tafukan hannunshin.

A hankali tayi taku uku zuwa biyar ta matso kusa dashi cikin sanyin da ya fara yimata yawa ga cikinta dake tsuma a hankali tace.
"Salamu alaikum".
Ko motsi baiyiba bare tayi zaton zai amsa.
Sallama ta kumayi shiru ba amsa.
Ganin hakane ta matso a hankali take takun saɗab-saɗab take taka sawunta a hankali har ta isa kusa dashi.

Da sauri ta zubawa ƙafar damanshi ido.
Ajiyan zuciya tayi mai sanyi tare da mgnar zuciya.
"Uhumm ashe dama yana komciya a ƙasa haka babu shimfiɗan komai ba pillow, da kuma ƙaramar riga da wondo iya guiwa."
A hankali ta iso gab da kanshi,
Cikin yin numfashi a hankali wai karya jita, ta rusuna ta zauna bisa sawunta irin zaman yin tahiyan salla.
Cikin ƙurawa babbar yatsar ƙafar damanshi inda ta rinƙa biyo wannan zanen macijin dake kwance lib a ƙafarshi.
Da ido tabi zanen har kan guiwarshi inda iya nan wondon 3 qtr ya rufe.
A hankali ta ƙara sunkuyowa ta kurawa wurin ido, tare da mgnar zuciya.
"To iya ina wannan zanen tafiyar macijin ya tsaya ne a jikinshi?".
Jim kaɗan tayi kana a hankali.
Ta miƙa hannunta, cikin sanɗa a hankali hankali tasa yatsunta biyu ta kamo bakin ƙafan wonɗon ta ɗan jawoshi a hankali tayi sama das...!




Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 in Kuma special Group kikeso wanda a mako biyu ake gaba part 1 kuma abiyu za'a gama Part two da izinin Ubangiji yimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. sai ki turo screenshot shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.



By
*GARKUWAR FULANI*
Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake.
Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar.
Pat ya fetti a jikinshi.
Ganin ya motsa.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta,
Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow'n da yayi dasu.
Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu.
Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta.

Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya.
Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta.
A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin.

Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje.
Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu.
Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi.

Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace.
"Allah shi ƙara".
Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta.
"Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye".
Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta.

Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace.
"Yah Sheykh!".
Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi.
Sai dai ko motsi baiyi ba,
A hankali ta kuma ce.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh!!".
Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta.
Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka".
A hankali ya buɗe idonshi,
Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo.
A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta,
Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi.
Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya.
Da sauri tace.
"Wash Allah na".
Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani.
Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya.
Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi.

"Harda zuba min maruka".
Ya faɗa a ransa.

Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta.
tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi."

A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine,
ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni.

Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone.
Cikin muryar bacci yace.
"Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?".
Cikin tura baki tace.
"Cinyana, nagaji kanka nauyi".
Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta.
tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa.
"Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?".
Cikin tura baki tace.
"Nifa tada kai a bacci kawai nayi".
Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace.
"Masha Allah, kinyi kyau."
Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi.
Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace.
"Nagode".
Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata.
Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace.
"Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle".
Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba.
Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace.
"Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar".
Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye.
A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa.
Ita kuma binshi da ido tayi,
tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya.

A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili.

Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito.
Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba.

Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi.
Sannan ya fesa turare.

Duk inda yayi tana binshi da ido.
Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa.

Sannan

Please Login or Register in order to submit comment