Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ko'ina cikin jikinta, dole ta wartsake ta karɓi mijinta hannu bibbiyu suka dinga farantawa juna cikin farin ciki da ɗokin juna, ALLAH ya taimakesu yaron ya basu haɗin kai domin shi ma kanshi a gajiya yake shiyasa yake ta baccinshi su kuma suna ta shan soyayyarsu kan kari, don Safwan ya susuce akanta sosai sai zuba santin daɗi yake yi yana nishi saboda irin bala'in daɗin da yake ji yana ratsa koina na jikinshi, sun daɗe suna abu ɗaya har sai da Sayyid ya falka sannan suka haƙura ba don sun so ba.

Da safe ma ba ƙaramin rawar jiki ya yi akanta ba don ma yana kawaici baya don Zee ta ganoshi, gudun janyo wata sabuwar fitinar yasa kwanansu biyu a Yola ya tattara Matarshi da ɗan shi suka koma Abuja, inda suka ci gaba da jiyar da junansu daɗi tare da tarairayar juna kamar yanzu ne suka yi sabon auren, a gefe ɗaya kuma suna renon yaronsu da ko kaɗan basu son ganin kukanshi don inda hali ma ƙuda basa son ya hau kanshi.


Watan Sayyid huɗu Dije ta fara zuwa school saboda ƙulafucinta akan makarantar, dole aka nemo mata wadda zata dinga kula da Sayyid saboda hidimar karatun ba wasa ba.

*****

Bayan shekara biyar Dijen Baffah ta yi karatunta ta ƙare har ta sami aiki a wata babbar Asibitin da ke Abuja, sannan ALLAH ya sake bata wata haifuwar inda ta sami ƴa mace aka saka mata sunan Hajiya Mama ta ci sunan Sayyada, Zee ma ta yarinyarta ɗaya mai suna Ummusalmah itama tana aikinta acen Yolar cikin amincin ALLAH, Fiddo ma anyi mata aure har ya haifi ɗanta masha ALLAH, Surayya ma yaranta uku Husnah ma ta yi aure da ƴarta mai sunan Nasiba.

Zamansu lafiya har lokacin saboda akwai fahimtar juna sosai a tsakaninsu, shi ma kanshi Uban gayyar ya zama ƙaton Alhaji don kuwa daga shi har Matanshi duka sun sauke farali, Inna da Baffah ma da Gambo da Maigari duka sun je, a gefe ɗaya kuma Dije daga lokacin da ta fara karbar salary ne ta fara asusun gina makarantar boko da islamiya garin na su, ga alkhairin da take yi wa yan garin da guminta bayan na Maigidanta, izuwa lokacin su Ladiyo kansu sun zama wata tsiya a sanadin Ƙawarsu Dijen Baffah, sai dai kwatsam ALLAH ya aikowa Gambo rasuwa bayan gajeruwar jinyar da ta sha, Dije ta yi kukan rashin Gambo saboda wani jigo ce ta rayuwarta, akan hakane ta yi ƙudurin gina masallaci a ƙauyen hadiyya zuwa gareta, ALLAH ya taimaketa Alhaji Safwan ya dafa mata ta cika gurinta, mutanen garin sai sambarka suke yi tare da godiya ga Ubangiji da ya sanya Dijen da suke aibatawa a baya itace yanzu ta zamo silar jin daɗinsu, Usmanu ma ya zama babban ɗan kasuwa yana samu daidai gwargwado don ya riki kanshi da Iyayenshi har ma wasu suna jin dadi ta sanadinshi.

Dije ma Cikin ƙashin kanta da shekaru suka ja ta biyawa Usmanu da Hansai Hajji, bayan sun dawo ne wata shekara suka yi haɗaka da Malaminta suka biyawa ƙawayen Dijen, Ladiyo Jummala Lanti da Mune tare suka je da su ma ɗin kansu suka sake komawa tare da su.

Wata shekara ma da kanta ta biyawa uwargidan Maigarin hajjin ta je don har abada bata mance karayar da ta janyo mata ta yi a lokacin gudun kura da suka yi.

Hajiya Dije da ALHAJI Safwan a ƙauyensu Dijen mutane sai turuwar zuwa gayar da su ake yi a ƙofar gidan Maigarin da suka fara zuwa domin su gayar da shi, sai ga wasu yan bautar ƙasa an turo tare da doguwar takardar da aka ce akawowa Maigarin, Maigarin ya karɓa yana kallon Dijen da ke dariya cikin ƙasaita saboda tuno abunda ya faru a baya, Dije ta karɓa ta dinga karantawa cikin harshen turancinta irin na ƴan America, bayan ta kare ta fassara masu duk abunda takardar ta ƙunsa, gaba ɗaya wurin manya da yara samari da ƴanmata aka dinga yi mata tafi ana yi mata kirari irin na mutuntawa da zayyano irin halayen kirkinta ita da Mijinta, zuciyarta cike fess da farin ciki ta tashi ta fara nuna jin daɗinta a fili sannan ta yi kira sosai ga mutanen garin akan su jajirce su dinga saka ƴaƴansu a makarantar boko da islamiya, saboda su ma su waye su zamo dai dai da kowa adaina yi masu kallon ƙauyawa, ta yi masu nuni da kanta da irin nasarar da ta samu duk a sanadin bokon wanda su kansu shaida ne ba sai an sanar da su ba, sannan ta yi kira ga iyaye sosai akan su dinga haƙuri da halayen ƴaƴansu musamman marasa ji, Baffah'nta ma ya tashi ya yi dogon jawabi akan alfanun yi wa ya'ya addu'a kuma kada a gaji da yi madu addu'a aduk wani rashin ji ko wani abu mara kyau da suka aikata, don ALLAH maji roƙon bawanshi ne kuma aduk lokacin da aka roƙa zai amsa sai dai jinkirin sakamakon a wani lokaci, mutane da dama sunyi alwashin jajircewa sosai akan karatun ƴaƴansu, kuma sunyi godiya da abun alkhairin Dije da Mijinta garesu, nan suka fito da kuɗi suka rarraba wa mutane duk wanda Allah ya sa da rabonshi ya samu, don ko yan bautar ƙasar ma sai da Suka wankesu da alkharinsu da suka saba.




Tammat bi hamdullah anan na kawo karshen littafin na *Dije ƙarangiya* masu comments masu masu yiman addu'a da masu yiman sharing book din a groups Kuma na gode sosai sai mun hadu a littafin na kuɗi mai suna *GIDAN AURE* littafi ne wanda ya kunshi rigingumun gidajen aurenmu a yau da kuma ma wasu abubuwa da baki bazai iya faɗa ba, masoyana masu son bin books ɗina a Koda yaushe idan kuna buƙata zaku sameni ta wannan numbar sai mu yi magana 09032685442 sai kuma na Free da zanyi don ku masoyana shi ma mai suna *SHAGALLIYA* wanda shi ma ɗin cike yake da barkwanci da nishaɗi ba kaɗan ba kusan ince fiye ma da Dijen Ƙarangiya, don haka ku ci gaba da bibiyata Ni *HADIZA IBRAHIM D/AUTA wadda wasu suka fi sani da PRINCESS DIJA* zaku iya nemana ta wattpad kamar haka *Princessdija246*


INA SONKU SOSAI MASOYANA ADUK INDA KUKE KUMA A DUK INDA KUKA KASANCE🤝🏻






Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment