Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dana wata mace ba, ko fadila yana sonta ne kawai saboda wasu dalilai amma ko kad'an bazaya iya had'a son da yake mata ba da Wanda yakema auta.


***** ****** ******


"Wai ni khaleed bangane me kake nufiba, Cikin gadara da nuna isa take maganar "kana nufin ka raina za6in danayima a matsayina na mahaifiyarka ban isa dakai ba, sai kawai inji labarin wai ansaka ranar aurenka da Autar Hajiya, dan Baku d'aukeni a Bakin kome ba kaida mahaifinka, kun maidani shashasha, to wallahi baka isaba, wato ka za6i 'yar'uwarka shikuma mahaifin naka dan yaga d'iyar d'an uwansa ce shine ya Amince hadda sa ranar aure ba tare da saninaba, sai bayan anyi anyi kome angama ranar aure kawai ake jira tazo sannan aka sanar dani.


Tinda matar tafara magana khaleed be ce uffan ba sai da tayi shiru sannan yafara magana cikin nutsuwa, da Alamar rarrashi, yace "kiyi ha'kuri Momy nasan idan na tinkareki bazaki yarda da maganar aurena da Zainab ba, shiyasa na ro'ki daddy akan kada ya sanar dake har sai an tsaida ranar, amma dan Allah Momy kiyi hakuri, badan banison Fadila nayi haka ba, kawai manufata shine bayan na auri Zainab da kamar shekara ita kuma sai in aureta daga baya.


Wani irin salati ta kwad'a Wanda yasa 'yan'cikin sa juyawa, sannan tafara magana cikin masifa, Wato khaleed ni zaka cima mutunci ka nuna dangin ubanka sunfi dangina daraja a gareka, to wallahi ban Amince da wannan manufar takaba, sai dai kafara auren fadila sannan daga baya ka auri Autar, dan bazan hanaka aurensuba, dan su duka 'yan'uwanka ne, kuma Addini be hanaka auren Mace biyu ba ko ukku, kai harma hud'u, Amma kasani Fadila, itace ta farko idan kuma ka'ki za6ina to wallahi sai dai kafasa aurensu su duka.


Khaleed rasa yanda zeyi yayi, dan yasan halin mahaifiyarsa sarai, zata iya wargaje maganar aurensa da Auta, wacce kuma itace macen daya fara so a duniya kuma har yakoma ga mahaliccinsa baze so wata mace kamar yanda yake sonta ba.


Cikin tsoron halin mahaifiyarsa, yace "na Amince momy zanyi yanda kikace, zan fara auren Fadila Daga baya sai in auri Zainab d'in.


Bata san lokacin da ta saki wani murmushi ba tace "yauwa to ko kaifa, murmushi yayi na k'arfin Hali dan gabaki d'aya ji yake Momy tagama takura rayuwarsa.


Amma dan Allah Momy ina Neman wata alfarma, tace "ina jinka
Yace dan Allah Momy idan antashi sa bikina da Fadila, asa wata d'aya saboda baniso a canja lokacin da aka sa bikina da Auta, cikin nuna rashin damuwa tace "wannan kuma matsalar kace, idan ma sati d'aya kace a sanya iyayenta shirye suke,kamar yanda kake shirye.


A ranar Momyn khaleed ta sanar da daddynsa, yanda sukayi da khaleed, be musa mataba, ya Amince da duka bayanin datayi mashi.


Anje Neman auren Fadila, wacce ta kasanece 'ya ce ga 'Kanwar Momyn khaleed, Fadila kwarkwararrar 'yar duniyace, wacce boko yagama zaunawa jikinta, da kwalwarta, wayayyace ajin farko, zata kai shekara ishirin da biyar a duniya.


Cikin sati d'aya aka gama magar auren khaleed dafadila, ansaka ranar biki wata d'aya da sati biyu.












_To fah jama'a kunsan dai ba abinda Auta Hajiya tatsana kamar namiji me mata kuma gashi sahibinta wanda tafi 'kauna zaya fara auren wata kafin ita tab, ๐Ÿค” lallai akwai bada'kala_


*kudai kubiyo Zee Mmn khdy dan jin yanda zata kasnce*


08166169254






Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 7:54 PM] โ€ช+234 816 616 9254โ€ฌ: [01/08 7:32 am] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_Page_ 41-45




*Bayan sati Biyu*




โœ๐Ÿฝ "Auta,....... Hajiya ce ta kwala mata kira tana daga kitchen, da sauri ta iso tace "gani, Hajiya ta mi'ka mata wani d'an karamin bokiti, "anshi ebo min ruwa nan in tsame d'an wakennan, sauri nake fita zanyi, da sauri Auta ta kar6a ta ebo ruwan takawo ta ajiye sannan ta d'auko kujera irin ta zaman tsakar gida ta zauna tace "Hajiya ina zaki ne?, Hajiya tayi murmushi tace kai lefe zamu koh, Auta ta kalleta cikin rashin Sani tace waye zeyi aure? Hajiya tace to waye zeyi aure kuwa in banda yayanki, Amma ay nasan dai ya sanar dake, Auta tace "Hmm Hajiya nifa ban gane wane yayana kike nufiba tukun,
_kwata-kwata Auta bata kawo khaleed aranta ba dan tasan ita kadaice za6insa kuma be had'a sonta dana kowaba_


Hajiya tace "yayanki khaleed mana, kina nufin be sanar dake nan da sati biyu za'a d'aura auren sa ba,


Jitayi kanta na juyawa, zuciyarta tayi mata nauyi, idanunta sun daina ganin haske, kanta yayi wani irin sarawa, lokacin kuma ta nemi numfaahinta ta rasa, Hajiya na daga kitchen kawai sai gani tayi Auta tafad'i kasa ba Alamar numfashi tattare da ita, da sauri tanufi inda ta fad'i tana furta Kalmar *Innalillahi,wa'inna,ilahirrajiun*
A d'imauce take gigizata tana kiran *Zainab*....... amma ko Alamun motsi batayi, cikin tsananin rud'ewa ta dauko waya takira me gidanta, ta sanar dashi Auta ce ba lafiya, gata kwance ko motsi batayi,


Cikin tsananin rud'ewa suka nufo gidan shida daddyn khaleed, dan lokacin da Hajiya tayi waya ta gaya Mashi suna tare.


Kusan minti sha biyar sannan suka iso, har yanzu Auta na kwance ba Alamun rai tattare da ita, Hajiya na tallabe da ita tana faman zubar da hawaye, batare da 6ata lokaci ba aka sakata mota sai asibiti, suna zuwa aka wuce Emergency da ita, kahleed shine likitan daya kar6e ta tare da taimakon wasu abokan aykinsa suke kokarin ceto rayuwarata,


Kusan minti talatin Amma Auta bata farfad'o ba, hankalin iyayenta yayi masifar tashi, ba kamar Hajiya wacce saboda tsananin kuka idanunta sun kumbura sunyi jawur, kallo d'aya zakayimata ka gane tsantsar tashin hankali tattare da ita.


An akai kimanin awa daya, sannan Auta ta farfad'o Amma duk da haka bata san inda kanta yakeba, haka aka fito da ita Daga Emergency, aka maidata wani d'akin, tare da sanar da iyayenta inshaAllah kome normal data farka, babu wani ciwo dake tartare da ita sumar datayima yanada Ala'ka da wani Abu daya d'aga mata hankali, amma muddin aka kiyaye zata cigaba da samun sau'ki, khaleed ne kema Hajiya wannna bayanin, dakuma daddynsa da Baban Auta Wanda su duka shi suke sauraro.










Zee Elkaseem
Mmn khady
[01/08 8:36 am] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_Page_ 46-50






โœ๐Ÿฝ Hajiya zaune gaban gadon da Auta ke kwance, ta zuba mata idanu tana kallon yanda take maida numfashi, ahankli tafara motsawa alamar farkawa daga baccin datakeyi, Ahankali ta bud'e idanunta ta 'karema d'akin kallo ta tabbatar da asibiti take, sannan Ahankali ta ri'ka tino maganar da Hajiya ta gaya mata, wasu zafafan hawaye suka zubo ta gefen idonta, A zuciyarta tana cewa.


_shikenan rayuwata batada wani amfani wanda nikeso yaci amanata ya cuci rayuwata bayan yariga yasan ba wanda nakeso kamarsa, bazan iya mallakama wani namiji kainaba bayan shi, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta_


Da sauri Hajiya ta matso kusa da ita tana yimata sannu, "auta kiyi hakuri ki d'auki 'kaddara, kisani duk me rai ba Wanda kaddara bata fad'amawa, kuma ki d'auki wannan Amatsayin jarabawa ce daga nahaliccinki, kawai sai kiyi fatan cinye wannan jarabawar.


Cikin disashshiyar murya, auta tace "Amma Hajiya khaleed ya cuceni yaci Amanata yagama da rayuwata, Allah ya Isah tsakanina dashi.


Ta fashe da wani irin kuka me ban tausayi, ta sauko daga kan gadon datake ta dur'kusa gaban mahaifiyarta, tace "Hajiya dan Allah ki gaya ma Baba bazanyi aureba har Abada, na hakura da aure, dan Allah Hajiya kada Ku 'kara tinkarata da maganar aure.


Kama hannunta Hajiya tayi ta mi'kar da ita tsaye, ta maidata kan gadon ta zaunar da ita, sannan tafara mata magana cikin sigar kwantar da hankali, tace
"Auta wannan maganar dakikeyi bame yiyuwa bace, ke kanki kinsan halin mahaifinki sarai ba saina sake maimaita makiba, kin San dai baze samaki ido ki zauna ba aure ba, kuma khaleed ba cewa yayi yafasa aurenkiba, maganar aurenki dashi tananan ba Abinda ya canja, ita wannan wacce ze aura d'iyar kanwar momynsa ce, kuma tin yana sudan mahaifiyar ita yarinyar tabashi ita, saboda haka inaso ki nutsu ki kwantar da hankalinki, kisani aurenki da khaleed ba fashi, idan kuma zaki tinkari mahaifinki da wannan maganar to kisani nidai ba ruwana.


A hankali aka turo kyauren d'akin, suduka suka maida hankalinsu gurin dan ganin me shigowa, khaleed ne yashigo da sallamarsa, sanye yake cikin milk d'in shadda wacce tasha ayki da zare copee, sai wani daddad'an 'kamshi ke tashi daga jikinsa, lokaci guda kamshin turarensa ya bige d'akin, kallo d'aya auta tayi mashi taji wani masifaffen sonshi ya'kara shiga zuciyarta, lokaci guda kuma ta tuno da cin Amanar dayayi mata, batasan lokacin data tashi Daga kan gadon datakeba taje ta cakumeshi, ta fashe da wani irin kuka, tace "Khaleed ka cuceni kaci amanata, Allah ya isah tsakanina dakai, kuma ka Sani bazan aurekaba koda Kaine auntan maza a duniya.


Da hanzari Hajiya ta mi'ke tana 'ko'karin 6an6are hannun Auta Daga jikin khaleed, amma hakan ya gagara dan Auta ba karamin ri'ko tayi Mashi ba, cikin 6acin rai Hajiya ke magana, "ki sakeshi nace auta, saima ta'kara rikeshi tana mashi wani matsiyacin kallo Wanda shi kanshi yakasa gane kona miye.


Ji kake tasss, Hajiya ta d'auke Auta da mari, hakan kuma yayi dai-dai da shigowar daddyn khaleed, da kuma babab ita Autar, cikin 6acin rai Hajiya take magana, "waike Auta wace irin shashashar yarinya ce da ina maki magana amma kin raina maganata, cikin sanyin jiki Auta ta saki khaleed tafad'a kan gado ta fashe da kuka,


Ko kad'an khakeed beji dad'in marin da Hajiya tayima Auta ba, dan dama yasan duk ranar dataji labarin aurensa zatayi abinda ma yafi wannna dan yanda take gaya mashi batason kishiya, ta tsani kishiya.








Zee Elkasee
Mmn Khady
[10/16, 7:55 PM] โ€ช+234 816 616 9254โ€ฌ: [02/08 5:24 pm] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_Page_ 51-55









โœ๐Ÿฝ "wannan zancen banza ne zancen Wofi, abinda baze ta6a yiyuwa bane,
Wato Zainabu kinaso ki maidamu 'kananan mutane ko? ko kinaso ki haramta abinda Allah ya hallata, duk namiji Allah ya halatta mashi Auren mace daga d'aya har zuwa hud'u, saboda haka ke baki isa ki haramta Abinda Allah ya halatta ba.


Mahaifin Auta ne keta faman fad'a tinda suka shigo asibitin shida mahaifin khaleed, Hajiya tabasu labarin abinda ya faru tsakanin Auta da khaleed.


Cigaba yayi da fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,
Auta kuma banda aikin kuka ba abinda takeyi, kwance take kan gadon asibitin ta juya fuskarta dan bazata iya had'a ido da khaleed ba, dan ita kanta sai daga baya tayi danasanin abinda tayi mashi, cikin zuciyarta kuwa cewa take.


_Allah kasa kada Abinda na aikata yazama silar fasa Aurena da khaleed inason khaleed son da bazan ta6ayima wani namij iirinsaba_....


Wani sabon kuka ta fashe dashi lokacin data tsinkayo muryar daddyn khaleed yana cewa, "A'a Alhj baza'ayi hakaba kada fa atakurama yarinya, yakamata atambayeta aji ra'ayinta, tinda ada lokacin data Amince da aurensa ba'ayi da ita ze fara auren wata kafin itaba....


"Haba Alhj ka daina wannan mqganar" Baban Auta yafada' "yaushe zamu zauna yarinya 'karama kamar Zainab tana juyamu, "to kisani cewa aurenki da khaleed ba fashi, ke barima kiji in sanar dake, an sassauto da lokacin bikin yadawo lokaci daya da wanda za'a d'aura mashi nan da sati ukku, inshaAllah lokaci guda za'a kaima khaleed mata biyu, Alabashi kinga idan aka kaiki saiki kashe kanki saboda tsabar kishi, shashasha kawai wacce bata San ciwon kanta ba.


Cikin fushi yafita daga d'akin, daddyn khaleed yabi bayansa, Hajiya ma binsu tayi,
Harabar asibitin suka tsaya daddyn khaleed yana cigaba da ba d'an'uwansa hakuri " yana cew "Kabi kome a sannu Zainab d'in duka nawa take dazaka ri'ka yimata fad'a kamar kanayi da wata babbar mace, duka bana fa take cika shekara sha takwas, kaga kuwa akwai 'kuruciya tattare da ita.


Hajiya dake tsaye tana saurarensu, tace " haba Alhj ai halin Zainab dole sai da haka, idan ba'a tsawata mata haka zata ri'ka mana yawo da hankali, ni kaina naji dad'in haka, kuma 'kara da aka sassauto da bikin ayi a huta.


Daddy khaleed yace "Allah sa haka shine mafi Alkhairi, suduka suka Amsa da "Ameen.


Cikin d'akin kuwa khaleed na ganin fitar iayensu yafara rarrashin auta, yana nuna mata irin sonda yakemata,
Amma ko kallo be ishetaba,


Ahankali ya matso ya dur'kusa kusa da gadon datake kwance, ya marairaice, cikin sigar rarrashi yake magana.


"Haba Zainab ki yarda dani, ki yarda da son danike maki, duk duniya ba macen danikeso kamar ke,....


A fusace ta d'ago ta kalleshi cikin tsiwa tace "Akwai khaleed, na tabbata kafi son Fadila a kaina, khaleed ka ha'inceni, ban ta6a tinanin ko a mafarki zakayi mani haka ba.


Ya salam...ki fahimceni Zainab, Fadila fa bani nace ina sontaba, had'in iyaye ne,kuma ke....


"Dakata khaleed, bakada kalaman dazasuyi tasiri akaina, ka adana kalamanka, wata kila suyima amfani nan gaba....


_(Hmm zainabu kenan halinki sai ke)_








*Zee Elkaseem*
*Mnn Khady*
[02/08 6:26 pm] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_Page_ 56-60








โœ๐Ÿฝ Kwanan Autar Hajiya biyu aka sallamota daga asibiti, duk ta wani rame ta kod'e hancinnan ya'kara tsayi, ga wani haske data 'kara, idan ka ganta sai kayi tinanin tayi ciwon wata biyu ne, dan ba 'karamar rama tayiba, duk tsabar kishine kawai.


Ranar sukayi waya da 'kawarta sadiyya, tace dan Allah tazo yau tana son ganinta, sadiyya tace "lafiya dai? Auta tace "lafiya lao kizo mana akwai labari 'kawata wallahi ina cikin tsananin damuwa da ba'kin ciki, cikin rud'ewa sadiyya tace "Damuwa 'kawata?, wace irin damuwa kuma? Auta tace "kedai sai kinzo kome kenan kinji.




โ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ขโ€ข


Sanye take cikin doguwar riga ta atamfa kalar sararin samaniya, wacce tasha d'inkin zamani, dinkin ya matu'kar kar6ar jikinta, dan ba karamin kyau yayi mataba, bata d'aura d'an kwaliba, sai wani karamin gyale me sharara ta yafa akanta, amma hakan baze hana ka hango madaidaicin gashinta ba Wanda yasha 'kuna, tayi parking dinsa tsakiyar kanta.


Wankan tarwad'a ce, amma dayake tana amfani da cream da lotion masu tsadar gaske masu matu'kar gyara fata,hakan ya 'kara fito da hasken fatarta, tanada idanu madai-daita, da dogon hanci, Wanda yayi dai-dai da matsakaicin bakinta, Wanda yasha romantic red colour,
kallo d'aya zakayi mata ka tabbatar da boko ya zauna jikinta, da kwalwarta, *Fadila kenan*.


Da sallama ta shiga falon da akayi Mashi masauki, tafiya take cikin yanga da karairaya,
Lokacin khaleed ya d'ago ya kalleta tare da amsa sallamarta,
Yanda take tafiya baya birgesa ko Alama, dan tanada 'yar'kiba shiyasa tafiyar bata mata kyau, ga Allah ya hore mata manyan nonuwa kamar me shayarwa.


Sannu da zuwa angona, tafad'a tare da zama kan kujerar dake kusa dashi, hannu tasa ta d'auki sauran lemun dayasha cikin cup d'in glass ta kur6a sannan ta ajiye, ta maida kallonta gareshi, tare da tambayarshi, "ya hidima? Yace "Alhamdulillah,
My dear lefe yayi kyau amma ka manta, da sarkar gold d'in dana fad'ama ba irin wacce ka sako bace, inaso dan Allah ko zaka musanyo mani ne?.......


"Ke Fadila, cikin d'aga murya yafad'a, idan bazaki iya amfani da abinda kika gani acikiba, to ba'ayimaki dole ba, nidai namaki iya 'kok'arina.........


Daga mashi hannu tayi, cikin d'aga murya take magana, "Dakata khaleed, bazakaje wata ta 6ata maka raiba kazo ka huce kaina, ko kana tinanin banida labarin abinda ke faruwa, tsakaninka da wannna yarinyar, Auta take ko miye.....


A fusace ya mike tsaye, yace ni zan wuce, ba wannan ya kawoniba, zowa nayi inji idan kina bu'katar wani abu, kuma naji bakida bu'katar kome sai anjima,


Ya fita Daga falon yanufi harabr gidan inda ya ajiye motarsa, yana niyyar Shiga yaga mamar Fadila, direba ya sauketa, ta dawo daga Unguwa, nan ya gaisheta, ta tambayeshi momynsa, yace tana lafiya, sannan ya shiga motarsa ya wuce.










Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 7:55 PM] โ€ช+234 816 616 9254โ€ฌ: [03/08 10:20 am] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_Page_ 61-65




*_Bayan sati biyu_*โ€ข
โœ๐Ÿฝ Yau sauran sati d'aya bikin khaleed da Autar Hajiya da kuma Fadila, duka 6angarorin guda ukku shirye-shirye suke, ko'ina ka gani suna cikin farin ciki.


Amarya Fadila ansha gyara anyi fresh, dan tin ana saura sati biyu bikin take faman gyara kanta, duk wani Abu datasan yana da amfani a jikin mace tana amfani dashi, tin Daga kayan gyaran jiki zuwa kayan tsumi ba Wanda batayi.


6angaren Autar Hajiya kuwa kullum ba abinda take sai tinani, duk tabi ta rame ta kod'e tayi wani irin fari, idanunta sun kara fitowa, a haka dai aketa shirin biki, 6angaren Hajiya kuwa ba irin rarrashin da batayima Auta ba, haka babanta tin yana mata fad'a har ya dawo yana rarrashinta yana mata nasiha, da haka dai aka samu tad'an saki jikinta, aka cigaba da hidima.


A 6angaren khaleed kuwa shima hidima yake sosai shida abokaninsa, zuciyarshi fal da farin ciki, dan jiya yaje gurin Autar Hajiya ta saki jiki sunyi magana ta fahimta, wacce rabon daya samu haka tin ranar da tasan ze auri Fadila.








Ana saura kwana biyu d'aurin aure sadiyya tazo gidan su Auta, da sallama ta shigo, gidan cike yake da 'yan'uwa da abokan arzi'ki, bayan ta gaisheda mutanen dake tsakar gidan, sannan ta wuce kitchen inda ta hango Hajiya tana faman had'a wasu kaya, tace "Hajiya ina wuni, Hajiya ta amsa da "lafiya lao sadiyya, ya mamarki, tace "lafiya lao tace a gaiaheki, kuma tace abaki hakuri bazata samu zuwa yau ba sai zuwa gobe, saboda tayi ba'ki, cikin fara'a Hajiya tace "ba kome wallahi Allah kaimu goben, sadiyya ta amsa da Ameen, sannan ta tambaya, "ina Autar take? Tana d'aki ki isa, tana ciki.


Kwance take kan godo ta juya fuskarta ta kalli bango, tayi lamo kamar me bacci, muryar sadiyya taji tana cewa "Amarya bakya laifi koda kin kashe d'an masu gida......


Auta tayi kamar bata jita ba, dan ko motsi batayiba, daga inda take kwance, sadiyya ta matso kusa da ita ta zauna gefen gadon, takara magana karo na biyu, "Amarya......., nan ma shiru Auta tayi mata, sadiyya ta'kara magana karo na ukku cikin jin haushi ta kaimata duka, tare da fad'in Auta banison rainin wayo, ya inata maki magana zaki wani sahareni......


Da sauri Auta ta tashi zaune tana Sosa inda sadiyya ta doketa, tana murmushi, tace "ina jinki wallahi, abinne naki yabani haushi da kika kirani amarya, aini nafi 'karfin amarya sai uwar gida, sadiyya tayi dariya tace to ai kinsan dai Fadila ta girmeki saboda haka itace babba, kuma itace uwar gida kekuma amarya, Auta tace "tab wallahi bazan yardaba, badai ance d'akin wacce yafara kwana ba itace uwar gida, to wallahi d'akina ze fara kwana.


Sadiyya ta kyalkyale da dariya, dan ita yanzu rigimar Auta dariya take bata,tace "to yanzu ba wannan ba kitashi muje gurin gyaran jiki, Auta tace "ke nifa na gayamaki ba wani gyaran da zanyi, a kaini haka yanda nake, wallahi sadiyya konayi niyyar yin wani Abu da natuna ba nikad'ai za'a kai gidan khaleed a matsayin matar saba sai inji duk na sire,


Sadiyya tayi murmushi, tace "Hmm auta kenan, to ay yanzu yakamata ki gyara, dan na tabbata ita waccan bazata zauna hakaba, kema dagewa zakiyi, ki gyara kanki yanda koda kin jera da waccan aga kamar sarauniya da baiwarta.


Suduka suka kwashe da dariya, haka sadiyya ta rarrashi 'kawarta harta yadda sukaje gurin saloon, Daga nan suka wuce gurin 'kunshi,


Basu dawo gida ba sai gab da magrib, suna dawowa, sadiyya tayo Alwala ta kabbara sallah, ita kuma sadiyya wanka tashiga, bayan tafito Daga wankan ta haye gado tayi kwanciyarta, kasancewar tana fashin sallah, bayan sadiyya ta idar da sallar ne suka cigaba, da tattauna yanda party da za'ayi gobe ze kasance, dan kuwa partyn Baki d'aya za'a yishi da fadila da Auta, kuma kowace da 'kawayenta.














Zee Elkaseem
Mmn khady
[03/08 11:57 am] .: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




_*Page*_ 66-70






โœ๐Ÿฝwashe gari ana gobe d'aurin aure, yau ne aka shirya wani 'kawataccen party Wanda Za'ayi a liyafa parlance dake cikin garin katsina, duka a 6angarori guda ukku, kowane yana cikin shiri, khaleed da abokaninsa da 'yan'uwansa, Autar Hajiya ma da 'yan'uwanta da 'kawayenta, haka ma Fadila, tana cikin shiri itada 'kawayenta da 'yan'uwanta.


Da misalin karfe hud'u za'a fara aiwatar da partyn, sabida haka kafin lokacin Fadila ta gama shiryawa, wani tsadadden material ne red colour tasanya dinkin riga da siket, kayan sun matseta sosai, abinka game jiki, kirjinnan kamar ze fasa rigar, kanta kuma golden gwagwaro ta d'ora takalmanta masu masifar tsini, wanda suka taimaka gurin 'kara mata tsawo, suma golden colour, sai wata 'karamar jaka dake hannunta itama kalar golden, kallo d'aya zakama Fadila kasan amarya ce, fuskar nan tasha make-up, dan me kwalliya ta d'auko ta musamman ta gyara mata fuskarta, ta biyata kud'i me yawa.




A 6angaren Autar Hajiya kuwa zaune take itada 'kawayenta, anata labari anata shewa, ko kad'an Auta batada niyyar yin wanka barantana ta shirya, sadiyya ce ta duba agogon wayarta sannan ta kalli Auta tace, Auta kinsan kau 'karfe nawa yanzu? amma ko niyyar shiryawa bakiyiba, kafin tayi wata magana, taji 'karar wayarta, tana dubawa taga sunan Ahmad, wani abokin khaleed ne, hannu tasa ta d'auki wayar sannan ta dannan OK ta kara a kunne tare dayimashi sallama, a d'ayan 6angaren Ahmad yace Ku fito gamu kofar gida muna jiranku,
Tayi saurin tashi tsaye tare da dafe 'kirji tace kuna waje fa kace, yace "eh tace "gashi kuma bangama shiri ba, yace owk bari muje gidan su Fadila, idan kingama mundawo, bejira abunda zata fad'aba ya tsinke wayar.


Da sauri tashiga toilet tayi wanka, tana fitowa ta d'auko wani lotion me dad'in 'kamshi ta shafe jikinta dashi, sadiyya ce ta 6ata lokaci gurin yima Auta make-up, tin nan Auta tafara yin kyau, fuskar nan kamar wata balarabiya, ga kunshinta Wanda yayi masifar kyau, manyan Flowers ne yayi bakikirin sai Jan ranin daya 'kara 'kawata kunshin.




Wani tsadadden farin Swiss less ne, Wanda yasha ado da flowers silver colour ta sanya dinkin doguwar riga, rigar ta kar6i jikinta dan ba 'karamin kyau tayimata ba, sannan ta sanya, takalmi silver colour, sai yar post d'in hannunta itama silver colour,kanta kuwa gwahgwaro me ta d'ora shima kalar silver, tayi masifar kyau, sannan ta d'auko turarurruka masu dadin 'kamshi ta feshe jikinta dasu.


Sadiyya ta kalleta tace Amarya kinsha 'kamshi, Auta ta harareta, cikin wasa tace "kin manta, sadiyya tayi dariya tace "oh sorry tuba nike Amarya uwar gida, Auta tayi dariya tace "ki karani kirani Uwar gidana
Kawai,
Sadiyya tace "to uwar gida sarautar gida, suduka suka kyalkyale da dariya.


Suna cikin wannan sukaji tsayuwar motoci, Ahmad, yakirasu yace su fito gasu a waje, nan aka fafa d'ibar 'kawayen amarya ana kaisu.
Daga karshe kuma aka d'auki Auta da wasu sauran 'kawayenta dasuka rage.














Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 7:55 PM] โ€ช+234 816 616 9254โ€ฌ: [03/08 9:43 pm] Zee Elkaseem: ๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š


*AUTAR HAJIYA* ๐Ÿ’ƒ๐Ÿป


๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š๐Ÿ•Š




ยฎNWA




๐Ÿ‘‡๐Ÿป
_ZEE MMN KHADY_ ๐Ÿ˜˜




*_Page_* 71-75








โœ๐Ÿฝ Hall d'in cike yake ma'kil da 'yan'uwa da abokan arziki, tun daga kan 'yan'uwan khaleed da abokaninsa, har zuwa 'yan'uwan Autar Hajiya da kuma 'kawayen Fadila da kuma 'yan'uwanta, Kowa yayima kansa mazauni, ana jiran shigowar ango da Amarensa, Autar Hajiya da Fadila.


Bayan hall din yayi shiru, sakamakon Mr DJ daya fara magana cikin speaker's dinshi, Kowa ya maida hankali ga yanda yake jawabi.


Can na hango Ango khaleed da Amarensa sun jero, tsakiya suka sanyashi, Auta na gefen damarsa yayinda Fadila ke gefen hagu, suna tafiya ahankali cikin nutsuwa, kallo d'aya zakayima Auta ka fahimci tana cikin wani yanayi, dan yanda taga Fadila ta wani shishshigema khaleed ta kama hannunshi ta ri'ke abin ba 'karamin takaici yayi mata ba, tin nan tafara tinanin me zatayi ta ba'kantama fad'ila rai, kamar yanda ta ba'kanta mata.


Sun Isa high table inda nan ne yazama masaukin Ango da Amarenshi, tsayawa khaleed yayi yayima fad'ila nuni akan ta wuce tafara zama kujerar can, yayinda shi tashi kujerar take tsakiya,
Bayan Fadila ta wuce ta zauna kan kujerar ta, khaleed na niyyar zama kan tashi kujerar kawai sai

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment