Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bane a garin Mai ludaya ba. Shine aka ce mun wai Ram-santi sunansu."

Cike da mamaki Abuwa ta ce,
"Yo shi cikin Jinjin ai komai gani ake, Allah dai ya kai ni nima inga yarda take."
"Amin dai, inda kuna da dangi a can."

Kallon sama da k'asa gami da yatsina fusa ta bita da shi, "Mu a suwa da zamu yi dangi a birni? Ku da ke da dangi ai shiyasa naga kullum k'afarku na can, dad'in abun dai k'auye dai tushen birni ne, idan aka bi diddigi su Baffa a cikin k'auyen mai ludaya za a bankad'osu." Ta k'arashe maganar tana mai d'auke kanta daga kan Saratun.

"Ikon Allah! Daga magana kuma sai cibi ya zama k'ari? To, Allah ya baki hak'uri. Kinga tafiyata." Ta k'arashe maganar tana kunce mayafinta da ta d'aure a k'ugunta shirin fad'a.

"Sauk'a lafiya, agaida na gaba."

Sak'e-sak'e tashiga ya azuciyarta, na takoma gida ne? Ko tawuce dandali? Idan kuma ta je dandalin ba wani burgewa abun za ta gani ba.

Har ta juya zata yi gida, sai kuma ta sake juyowa ta nufi hanyar dandalin.

Tana gab da isa ne ta ji an k'wala mata k'ira, ko bata juyo ba ta shaida muryar mai k'iran nata.

Juyowa ta yi don ganin dalilin k'iran nata.

Hasken farin watan da ya haskaka duniya ne, ya hasko mata fuskar Muntari da yake ta zuba haki dalilin gudun da ya ci.

Tsaki ta ja kafin ta ce, "Lafiya ka ke k'wala min uwar k'ira a daren nan?"
"Inno ce ta ce in zo in k'iraki, na manta na tsaya yin Langa dasu Sabitu. Sai da naga wucewar Saratu na tuna Aradu."
"Jeka da Allah ina zuwa."
Ta juya zata tafi.
"Alk'ur an ta ce ki zo yanzu-yanzu."
Juyowa ta yi ta zabga mishi harara sannan ta d'au hanyar gida.


Indo da Karime da k'awayensu guda biyu da suka iso Dandalin tun da magribar fari suna jiran zuwan Abulle shiru ba labarinta, yasa suka fara taraddadin zuwan nata.

"Karime anya ko Abulle zata zo?"
"Tsaf zata zo in dai Abulle ce, kinsanta bata fashin zuwa dandali sai da dalili mai k'arfi, balle kuma yau a cike take, mu jira muga zuwanta."
"Ke nifa tunda kika zo gida ki ka gayan zancen nan nake tsuma, Allah-Allah nake ta iso. Aradu in sunkuya na kwashi k'afarta ku bita da duka."
"Ke, ni kayan tallana nake tunani a gidanku."
"Yanzu kika tuno da tallan naki?" Inji d'aya k'awar tasu.
"Lantana ai ina nan hankalina na can ne, tun fa rana dana fita ban koma gida ba."
"Ni fa kunga tafiyata ma zan yi."
"Ke Sahura ai dama ruwan ciki ne da ke."
"Hu umm! Ku ji Indon nan? Kuma dare ya yi sai in yi ta zaman jiran gawon shanu ko? To, ba da ni ba. Sai kun zo." Ta juya ta yi tafiyar ta.

Karime ta ce
"Kai, mu tafinku muna, gobe za ta fito ne, sai mun kwashi 'yan kallo."

Duk suka amsa da, "Mu je."



_Ummyn Yusrah_
[9/11, 9:31 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*


*© UMMYN YUSRAH*


*8*

Da dare, Abulle suna zaune a kan tabarmar da suka shimfiɗa a ƙarƙashin barandar ɗakin Inno, suna cikin tuwon dare.

Wani kafcecen loma Abullen ta yanko, ta iza shi cikin bakinta, ji ka ke ya ba da sautin "Muƙutt!" Sanadiyar haɗiyar da ta yi masa ba tare da ta tsaya taunawa ba.

Haka ta yi ta wurga lomomin nan, tana haɗiɗɗiyar su, ba tare da ta tsaya ɓata lokaci wajen taune su ba.

Ga zufar da ta gama wanke mata fuska, wanda har ɗiga ya ke a ƙasa.

Inno da ke can gefe kan kujerar tsuguno, ta ɗago fitilar ƙwan da ke gefen ta ta haska fuskar Abullen, a daidai lokacin da ta yanko wani tiƙeken loma ta zazzaro idanuwanta waje masu kama da ƙwan zabbi, tana shirin wurgashi baka, ganin hasken fitilar yasa ta tsagaitawa tana mai kallon Innon da ta saki baki tana binta da idanuwanta kafin ta ce.

"Ikon Allah! Wai ke a rayuwarki ba ki iya cin abinci cikin nutsuwa ba ne? Ki duba dai ki gani, ke ɗaya ke ci amma Allah-Allah ki ke ya ƙare, kamar wata mai warwaso kina tsoron kada a ƙwashe a barki hannu rabbana."

Turo baki ta yi gaba ta yi tana faɗin,
"Inno! Nifa a hankali na ke cikin abincina."

"Hoɗijam! A hakan?" Ta tambayeta.
"Eh." Ta bata amsa a taƙaice gami da wurga lomar da ta ke ta juya shi a  hannunta.
"Ummmhh! Lallai da aiki. Da alama gidan Sarkin noma za a wurgaki, domin wannan irin ci naki ba dai gidan rago ba."
Ta faɗa a lokacin da ta ke ajiye fitilar da ke hannunta a ƙasa.
"Shiyasa kullum ki ke ta hawa kamar farashi ai, daidai da sakan guda ba ki fatan bakin ki ya zauna shiru, ko da yaushe yana cikin motsi hayayam-hayayam. Ki sama ma kan ki lafiya tun wuri ina gaya miki, ba ko wani namiji ne zai iya da wannan cin naki ba ina gaya miki."
Ta ƙarashe maganar tana mai ci gaba da saƙar hular da ta ke yi da ƙwarashi.

"Inno! Shima fa cin nan lafiya ne aradu, idan mutum ba ya lafiya ina ya ga wani bakin cikin abinci, Allah duk randa aka kai ni gidan da ba abinci kullum gida zan riƙa turo da ƙwarya ta ana yi mun zubi, gara ma tun da wuri kada ku cire ƙwaryata ku barni a layi." Tana maganar ne tana lashe hannunta da ta gama damalmale shi da miya, tana gamawa ta kuma rarumo kwanon tuwon ta hau suɗewa.

Inno ta ce, "Wannan ai an yi, ba a yi ba kenan. An sai da akuya, ta dawo kuma tana ci mana danga."
Ba ta kula ta ba sai ma ci gaba da ta yi da suɗe kwanon, wanda baya buƙatar wani ruwa da omo wajen wanke shi, domin yawun Abullen ya wanke shi tas.

"Ko da yake shi gwanin naki ma Hamusu rago ne, tunda tun zamanin ƙuruciya da aka bashi gwaji a kan kaza ya gaza riƙe ta, duk da yake ita ɗin dabba ce, ina kuma ga an bashi ɗan mutum?"

"Taɓ! To ni me ruwana da wani Hamusu kuma? Can, su ƙarata da Indo ƴar gidan mai unguwa ni na wuce ajinsa"

"Iyee! Zamani. Kukam dai yaran yau sai dai abarku, kina gabana ko kunya ba ki ji."

"Yo, to Inno naga dai zancen nan ke ki ka fara yowa ita, ni ko na ɗora."

"Uhmmm! Haka ne."

"Inno shi kiwon kazar kuma ta me cece ne da na ji kin ce an ba shi Hamusun ya kasa riƙon ta?"

Kallon ta ta yi, kafin ta ce,  "Ita wannan kazar da ki ka ga ana ba duk wani ɗa namiji da ke wannan ƙauyen kiwo, ana bashi ne don gwajin yadda zai iya riƙe iyali. Idan aka ga yana kula da ita wannan kazar sosai, to a hankali za a bashi tunkiya, kinsan ita tunkiya uwar tamɓele ce, idan nan ma aka ga ba laifi, sai a yi mishi canji zuwa rago, da haka dai har zuwa kan saniya, idan aka ga ya iya kiwo to anan ne za a bashi mata. Idan kuma shiririta ya sa a gaba to sai dai a wurgashi gona kuma ya yi ta fama."

Baki ta saki tana jin jawabin Inno har ta dire, ita ma ta jefo mata tambaya da faɗin, " Kuma Inno shi wannan gwagwarmayar duk mutum ɗin na ƙarami ne zai yi shi? Kuma dama ba su noma ne sai sun gaza riƙon dabba?"



Ummyn yusrah
[9/13, 4:57 PM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*


*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*


_Ummyn Yusrah_


*9*

"Suna yi mana, idan yaro ya kai munzali kuma sai a yi mishi auren ladan noma." Cewar Inno.
Keɓe baki Abullen ta yi ta ce,
"Hu'umm! Sun ji daɗinsu."

Shigowa gidan ya yi, ba ko sallama sai ma bambamin faɗa da ya ke ta yi har ya iso inda suke zaune, ya ja ya tsaya.
Bayan shi ya yi ma masauƙi da garun ginin jar ƙasar da ke bayan shi, yana huci da huro iska daga cikin bakin shi, ya harɗe hannayeshi bisa ƙirjinshi yayin da ya ɗago ƙafarshi ɗaya ya dogare ta jikin garun, ɗayar kuma tana ajiye a ƙasa.

"Barka da shigowa Malam! Yanzu na ke neman Muntari ya kai muku abincinku waje, baya nan, ina ga ya fita dandali wasa ne."

Tsaki ya ja, ya ce, "Wa ke batun abinci kuma."
   "To, mai kuma ya faru? Na ji ka shigo kana ta bambamin faɗa."
   "Sarkin fada ne ya bi duk ya matsamin da zancen auren nan wallahi, ba dama ya ganni, duk  ya bi ya hanani sukuni."
  Jin an ambaci Sarkin fada yasa Abulle ta zaburo tana faɗin,  "Walle ɗazu ma ya aikoni, wai ko yana maka tuni ko me na dai manta."

Inno ta galla mata harara, "Ina kuka haɗu da shi? Ko binshi fadar ki ka yi?"
Zaro ido ta yi alamar tsoro, "Walle Inno a hanya muka haɗu, da na je sayo rama a kasuwa ina dawowa."

"To, dama da kin ganshi kafin ya hangoki, ki maza ki sake hanya, kin ji na faɗa miki."
   "Inno!"
      "Innon gidanku." Ta yi mata daƙuwa da yatsunta biyar.

"To, Malam yanzu meye abun yi?"
Ƙarasowa ya yi, ya zauna a gefen tabarmar da Abullen ke zaune.
  Da sauri ta tashi ta koma ƙasa ta zauna.

"Ni kaina na rasa ta cewa, da ina tunanin in ce mata cikin manemanta ta fidda gwani kawai, idan na je sai in sanar musu tana da gwaninta dama a hannu."
  Cewar Ilun mahaifin Abulle.

"Hakan ma ya yi, ke cikin maneman naki waye gwaninki?" Ta jefa ma Abulle tambayar.

    "Ni... Ni... Ba kowa."

"Ba kowa ki kace?"
    "Ba kowa Inno."
          "Umm! To kaji Malam. Da alama rabon mai unguwar ne."

"Ke Inno! Hauka nake zan ɗau Abulle in ba sa ar kakana?"
     "To Malam, idan rabon shi ce fa?"
           "Bama rabon shi ba ne."
      "U um fa Malam! Kasan fa rabo ajali ne, ba mu san me Allah ke nufi kan hakan ba. Idan dai ita Abullen tana so ai shikennan."

Jinjina kai ya yi, kafin ya ce,  "Kuma fa kin kashen jiki, kince Allah a lamarin dole in saduda tunda ita ɗin ma bata da wani tsayayye."

"Ke Abulle! Mai Unguwa ne ya turo Sarkin fada cewar yana son aurenki, me kika ce?"

Sai yanzu ta gane kan wa suke zancen su, domin da duk a baibai take fuskantar zancen nasu.

'Wai yau ni Mai Unguwa ke son aure? Lallai ina da sa a.'
    Zancen zuciyarta kenan, kafin ta sake dulmuya wata duniyar tunanin.

Hangota ta yi a gidan Mai Unguwa, an dire mata wani ƙaton kwanon kaya shaƙe da dafaffiyar shinkafa 'yar gwamnati mai santsi da miyar ja, ga kuma ƙatuwar kaza a kai, gefe kuma ga babban kwanon sha cike da sassanyar ruwan ranar ƙasa.
 
Sake kallon ƙeta ta yi ma hinkahwar a karo na ba adadi, tana kuma tuna irin cin walaƙancin da  za ta yi mishi.
  Sake ware ɗaurin zaninta ta yi don yayi sako-sako gudun kada cikin nata ya yi saurin cika, ta kalmashe ƙafafunta waje guda, ta zura hannunta ciki ta gauraya gefe guda, ta ciko hannunta ta kai shi zuwa bakinta.

"Kingani ko Inno! Na gaya miki yarinyar nan ba son auren nan za ta yi ba, gashi ko amsa bata bamu ba."

Maganar da mahaifinta ya yi, shi ya hanata jin ɗanɗanon hinkahwar da ta shaƙe hannunta da shi, maganar ce kuma ta yi silar dawo da ita daga duniyar tunanin da ta afka.
  Ta ji takaicin rashin ɗanɗana girkin, sai dai duk ranar da Allah ya kai damo ga harawa ba ƙaramin ɓarna za ta tafka ba, cin huce haushi za ta yi mishi.

Murmushi ta yi, wanda sautinshi ya fito,  "Kin gani ko Inno? Kuka fa ta ke yi, gara a janye maganar nan idan yaso a jira har ta samu gwani."
  Cewar Malam Ilu.

Salallami Inno ta sanya tare da tafa hannayenta, ta iza ɗaya a haɓarta ɗayan kuma ta ɗago fitilar dake ajiye ta haska fuskar Abullen da shi.
   Kallo suka bita da shi, fuskokinsu fal mamaki.

Madadin suga hawaye ya wanke fuskarta, murmushi ne ke ta bayyana a fuskarta, idanunta kuma a rufe.

"Ke Abulle! Lafiyar ki kuwa?"
Inno ta tambayeta.
Da sauri ta buɗe idon ta sunkuyar da kai alamar kunya ganin yadda iyayen nata suka tsatstsareta da ido.
A guje ta bar wajen ta nufi ɗakin kwananta, zuciyarta cike da farin cikin nesa ta kusan zuwa kusa.

"Shikennan ai Malam, abu ya zo gidan sauƙi, alamu sun nuna ta yi na am da zancen. Sai ka yi maza ka sanar da su kai ma ka sami lafiya."
  "Ai kamar yanzu ma kuwa ba sai an kai gobe ba."
  "Sai kuma mu toshe kunnuwanmu, don za mu sha surutu gurin jama ar garin nan."
  "Yo Inno! Idan sun yi ma ai za su bari, da yardar yarinya ai aka yi, ba dole aka yi mata ba."
  "Haka ne kam."

Ya miƙe yana faɗin, "Barin je in sanar ma Sarkin fadan."
   "To, a dawo lafiya."

Tunda aka sanar ma Sarkin fada bai yi wata-wata ba, a daren ya isar ma Mai Unguwa.
   Washegari Mai Unguwa ya turo wakilanshi neman auren Abulle, da sadakinta dubu ɗari. Take aka  sallama musu aka kuma sanya musu mako biyu mai zuwa aure.

Kafin kyaftu da Bismillah, zance ya karaɗe illahirin unguwar su Abulle, ya karaɗe garin mai ludaya da ƙauyukan dake maƙwaftaka da su.

  Tsegumi ne kawai ke yawo ta ko ina, ga uwar Indo ma ta ɗaga hankali a gidan Mai Unguwa.

"Kai  dai ba ka taɓa rabo da abun kunya, ka rasa wacce za ka aura sai ɗiyar cikinka. Allah wadai wallahi, girma dai ya faɗi."
Cewar Tabawa.

Kallo Mai Unguwa ya bita da shi, kafin ya ce  "Abun kunya? Ai mu gaba muka bashi ba baya ba, in dai ta nan hanyar ne. Yaya ina ƙoƙarin raya sunnar Ma aiki Rasulullahi, kuma ki ke neman jifata da wasu kalaman da basu dace ba?"

Harara ta zabga mishi,
"Wani raya sunnar? Ka rasa lokacin da zaka rayar sai da duk furfura ta gama baibaye ka, mutuwa  yau ko gobe, amma ka ke wani ƙiran raya sunna."

"Kai Tabawa! Ni da ke ba wanda ya san gawan fari, har yau ba za ki rage kishi ba. Yarinyar nan dai naga ƙarama ce, ba ruwanta, bata san komai ba. Don Allah ki sassauta kishin nan naki a kanta, kinga Lami kam ko a jikinta, bata wani nuna damuwar ta ba."
Gyara zama ta yi ta ce,  "Lami daban Tabawa daban. Yo ita dama ɗaga hankalin me za ta yi? Taga jiya taga yau, abu tun zamanin ƙuruciya kuke tare, tun auren saurayi da budurwa, ta riga ta ci lokacinta ai, tunda ko ni nan ma ta haifeni few da aniya, balle kuma wata can wai ita Abuwa. Har ka ke wani ƙirinta da yarinya, ƙarshen yarinta inga Inno ta sanya majanyi ta goyata a baya, ta kuma ɗauki bulumboti ta liƙa mata a baki sai in yarda."

Ganin da gaske take, zancen nata ba na ƙare ba, yasa ya miƙe yana gyara zaman rawaninshi ya saiti hanyar fita yana faɗin,
"Ni dai na faɗa miki, ki sa ma ranki salama ki yi fatan a zauna lafiya kawai don kin san bani son fitina a gidana."  Yana kaiwa nan yasa kai ya fice.

Tana huci tana faɗin,
"Za ma ka dawo ne ka samen, da rawani kamar an naɗa gammo."

Yana fita Indo ta faɗo ɗakin kamar wacce aka hankaɗo.

Gallamata harara Tabawa ta yi tana faɗin, "Ba ki iya tafiya a hankali ba ko? Kin wani faɗomin ɗaki kamar wacce kare ya biyo."
"Yi haƙuri Tabawa! Mutane ne suka ishen a gari, wai me yasa za a bar Baba ya auri waccar yarinyar? Wasu sunce don yana mai unguwa ne ya sa zai yi musu fin ƙarfi, wasu suce sayen ta yi yi, wasu ma cewa suke wa..."

Tsawa ta daka mata, "Koma me suka ce, ba ke kike jajiɓo ta ba? Inda ba ki talla mishi ita ba ina zai ganta? Na ji kuma ance saurayinta da suka daɗe tare ya yi ƙaura ya dawo wajenki, kinga da ta tashi huce haushin ta sai ta huce kan mahaifinki. Kinga nan da kwanaki goma ta zama kihiyar uwarki kenan. Sai ki shirya tarbar sabuwar uwa."
Ranta ɓace ta ce, "Allah ya satura! Ko rabin-rabin uwata ba ta kai ba, na san kuma kwaɗayin hinkahwa ne zai kawo ta Yasin za ta ga walaƙanci."

Masifa ta rufeta da shi har bakin da ya gama rinewa da goro yana fidda kumfa, inda ana bada aron baki, da ba abun da zai hana Tabawa ta yo aro yau.


Haushin kaza kenan.



Ummyn Yusrah
[9/22, 3:52 PM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA*

*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*
       *(HWA)*

_UMMYN YUSRAH_

_A ƙara haƙuri dai._

_10_

"Yi maza ki je gidan Goshi ta baki daddawar nan, kafin ki dawo na gama daka kukar sai a haɗa musu waje guda ki tafi, kinga rana na tafiya, kada dare ya riskeku, ga hanyar ba kyau ne da ita ba."  Cewar Inno da take ta tiƙar busheshshen ganyen kukan da ta zuba a turmi, babban burin ta ta mai dashi gari.

"To Inno!"
Ta fice daga gidan ta nufi gidan Goshi mai Daddawa.

"Abulle! Abulle!! Abulle!!!"

Tun daga nesa yake ta ƙwala mata ƙira, sosai ta jishi ta ƙi juyawa  Ganin ƙiran nashi ba na ƙare ba ne, yasa ta juyo a fusace tana hararar shi.

"Wai lafiya kake yi min irin wannan ƙira kamar wani tsohon makaho ko wacce ta sace maka ɗan taure?"

Ƙarasowa ya yi yana dariya ya ce,
"Yo Abulle don na ƙwala miƙi ƙira haka ai ba laifi ba ne, tun ranar nake so mu haɗu mu tattauna amma kin ƙi kulani."

Kallonshi take mai haɗe da harara,
"Kam me zan saurareka? Cemaka aka yi ina da lokacinka? Ka dai san ni ba sa arka ba ce ko?"

Cike da mamaki ya hangame baki kamar wani gaɓo yana kallonta kafin ya ce,
"Nine fa"
Ta yatsina fuska tana faɗin"Kaine wa?"

"Hamusu rabun ran Abulle."
Ya ƙarashe maganar cikin yanayin shauƙin so, har yana wani jijjiga jiki irin na jin daɗin nan.

"Hamusun Indo dai! Ai ni yanzu na wuci saninka."

"Ni ɗin?"

"Kai ɗin fa."

Ta juya ta fara tafiya, ko mai ta tuno sai kuma ta juyo ta yi mishi kallon sama da ƙasa.

"A je a bi wani sarkin, ba da ni ba, auren talaka."

Ta juya ta yi gaba.

"Dakata! Kada ki yi ƙoƙarin jifana da duwatsu, ina mai shawartarki da ki adanasu ki gina gida da su domin nasan duk daren daɗewa zai yi miki amfani. Sannan kada ki yi kuskuren ƙonani da wuta domin da shi muke kunna fitilun da ke haskaka duk wani gida da ke faɗin kyauyen nan. Duk ranar da ki ka kuskura ki ka yi wannan gangancin ina mai tabbatar miki da cewar za ki dawwama cikin duhu."

Yana kaiwa nan ya juya cikin ɓacin rai,
"Matsalar ka ce wannan kuma, mayaudari kawai."
Ta ja dogon tsaki ta wuce aikanta.

"Kinsan da tafiya a gabanki amma ki ka sami waje ki ka zauna ko Abulle?"

"Inno da na same ta a gida ai ba zan zauna ba, hegiyar yawo ne da Goshin nan kamar wacce ta ci ƙafar kare."

"Ni tafi ki je ki shirya, shegen iyayin tsiya, kin san hanyar Mai Rangwangwan ba kyau ne da shi ba. Idan ku ka yi dare ku kuka sani, don ma mai babur ɗin ɗan garin ne da ya sauƙeki gida zai wuce da sai dai ki zauna sai gobe kuma."

"Inno to a bari mana gobon na tafi."

"Ungo nan."

Ta watso mata yatsun hannunta biyar.
  "An ƙi a barwa goben. Dududu bikin saura kwana goma ne, idan kin je gidan Kawun naku Talle ki ka dawo Jinjin za mu tafi can gidan Kawun ku na burni, nan ma ki kwana biyu ki zo ki bi gidajen dangi na kurkusa suma ki musu sallama."

Murna ne ya rufeta da ta ji batun tafiya Jinjin, itama za ta je burni ta ga yadda yake.

Ruwa ta dauka a bokiti ta je ta watsa, tana fitowa ta sa kaya, yau ba batun kwalliya, kayanta kulle a cikin ɗankwali, sai wani ƙaramin buhu da aka sa mata dankalin hausa, kuka da daddawa.

Sallama ta yi ma Inno, bayan ta gargaɗeta ta kuma ja mata kunnen ta kula ta kuma dawo akan lokaci.

Muntari ya ɗaukar mata buhun kukan, suka nufi tasha wajen mai mashin ɗin da aka jima da yi mishi magana.

Tana isa ba ɓata lokaci ya suri Abulle da wata mata suka ɗau hanya.

Gam Abulle ta riƙe ƙarfen jikin mashin ɗin, domin idan ba haka ba a yadda suke cafke a kan hanyar nan za a iya tsintota a ƙasa idan aka daka wani tsallen.

Taimakon ta ɗaya a tsakiya take, ba don haka ba, abun ba dama ne.




_Ummyn Yusrah_

*ABULLE TA MAI UNGUWA*

     *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*

_Ummyn Yusrah_

_11_

Kwananta biyu a Mai Rangwangwan ta dawo, cike da ɗoki da murnar zuwa birni.  Har gida ta je ta sanar ma Sarai itama za ta birni gidan Baffanta Jafaru don haka gara a daina yi musu yanga, don ba a fi su tsumma ba, balle a baɗa musu ƙwarƙwata.

Kwananta ɗaya a Mai ludaya washe gari suka ɗau haramar barin gari zuwa babban birnin Jinjin.

Tsarabar 'yan Maraya daban da ta ƙauye, domin su ba daddawa ba kuka.
Kabeji ce da kayan miya, sai kuma manyan kaji guda biyu.

"Inno! Su mutanen Jinjin ɗin ba su cin kuka da daddawa ne? Naga nasu tsarabar daban da ta Mai Rangwangwan."
Abulle ta tambayi Inno, ganin yadda aka bambanta tsarabarsu

"Ke, tuwon girma ai miyarsa nama. Su can me za su yi da wani kuka da daddawa? Tuwon ma ai sai su shafe mako huɗu ma ko fiye da hakan ba su yi shi ba."

Cikin mamaki da sakin baki ta ce,
"To Inno me suke ci kuma?"

"Ohho! Idan mun je kya gani."

Tsuke bakinta ta yi har suka tattari shirginsu suka ɗau wanya.

Kalle-kalle kam Abulle ta yi shi, mussaman ma da suka fara shigowa cikin birnin, ga kwalta shimfiɗe kamar tabarma, ƙarafunan wutar layi a tsaye kan hanya, jere reras kamar an dasa bishiyoyi.

"Ikon Allah! Kayan burni daban da na ƙauye."
Abulle ta faɗa a bayyane.

Kallo wasu daga cikin mutanen cikin motan suka bita da shi, don daga dukkan alamu ita ɗin sabon shiga ce a zuwa Maraya.

Amai ko ta yi shi yafi sau biyar, tun tana wanke jikinta da shi har aka bata tallafin leda.

Har cikin tasha aka sauƙesu, anan ne fa taga tarin jama a, sai kaiwa da komowa a ke yi, kowa na sabgar gabanshi. Abulle kam banda kallo ba abun da ta sa a gaba.

Idan Inno ta yi gaba, sai ta sake dawowa baya ta jawo hannun Abulle idan ta ga wani abun. Wani lokacin ma tuntuɓe take yi ko ta yi karo da wani abun tsabar kallo. Haka dai har suka tsare adaidaita zuwa unguwar su Baffa Jafarun.

Nan ma dai mamakin ne cike da Abulle ganin mashin mai ƙafa uku, ga kuma gidaje harda masu hawa-hawa.
Wani akan wani.

'Ikon Allah! Na zaune bai ga gari ba.'

Zancen da Abulle ta yi a zuciyarta kenan.

Tafiya dai-tafiya dai, har suka iso inda za su, suka biya mai adaidaita, ya ƙara wuta.

Buga get ɗin ƙofar gidan suka yi, da sauri mai gadin ya zo ya buɗe musu ƙofar. Ganin Inno da ya yi ne yasa shi wangale baki yana faɗin,
"Maraba lale da mutanen Mai ludaya. Yau kune a garin namu?"

"Maraba dai Ɗayyabu! Gamu kamar an jefomu."

"Sannunku, ku shiga mana."

Ya faɗa yana ɗaukar wasu daga cikin kayan da suka zo da shi ya yi gaba.

"Inno kin san shi ne?"

"Farin sani ma kuwa, a Mai ludaya yake shima, ɗan gidan Malam Datta mai katako."

"Au! Na ɗauka ai tsabar zuwan da kike ne ya sanki."

"Yo ni yaushe ma nake zuwa? Rabon da garin nan tun ina goyon Muntari da muka zo yi ma Baffanku barka da dawowa daga Makka."

Haka suka ƙarasa har cikin gidan Inno na yi mata bayani, ita kam inda za a shaƙeta ma ba ta san ɓaɓatun da Inno take yi ba, don gaba ɗaya hankalinta ya tafi ga kallon tsari da haɗuwar da gidan ya yi.

Zuciyarta ke yi mata tambayar,
'Wai dama suna da dangi masu kuɗi kuma 'yan burni shine ba su taɓa zuwa ba?'

Ita dai a saninta da wayonta sau biyu ma ta taɓa ganin Baffan nata a ƙauyensu, sai dai Babanta ya zo ko kuma ya yi musu aike daga nan.

Suna ƙoƙarin shiga falon, Ɗayyabu kuma na fitowa. Ya ce,
"Inno wannan kamar Abuwa?"

"Ita ce."
"Ikon Allah! Girma dai ba wuya, ta girma abunta."
Ya faɗa yana riƙe haɓa.
"Girma kam ai

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment