Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://NovelsHQ.com to download more hausa novels visits our site at www.NovelsHQ.com For feedback and support Facebook : https://facebook.com/NovelsHQ Twitter : https://twitter.com/NovelsHQ Telegram : https://t.me/NovelsHQ Compiled By Umar Dalha Funtua. Copied By Ummee Yusuf. [8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAKE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_💃🏻NBA SONTA NAKE BA💃🏻 *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana gwiwa a wajen rubutu._ *BA SONTA NAKE BA* littafi ne daya kunshi darrusa na yau da kullum,ina rokon Allah kaman yanda na fara lafiya yasa na gama lafiya. Da fatan zaku bani hadin kai kaman yanda kuka saba. حَدَّثَنَا يَحْيَى بْنُ يَحْيَى التَّمِيمِىُّ وَأَبُو بَكْرِ بْنُ أَبِى شَيْبَةَ وَمُحَمَّدُ بْنُ الْعَلاَءِ الْهَمْدَانِىُّ جَمِيعًا عَنْ أَبِى مُعَاوِيَةَ - وَاللَّفْظُ لِيَحْيَى أَخْبَرَنَا أَبُو مُعَاوِيَةَ - عَنِ الأَعْمَشِ عَنْ إِبْرَاهِيمَ عَنْ عَلْقَمَةَ قَالَ كُنْتُ أَمْشِى مَعَ عَبْدِ اللَّهِ بِمِنًى فَلَقِيَهُ عُثْمَانُ فَقَامَ مَعَهُ يُحَدِّثُهُ فَقَالَ لَهُ عُثْمَانُ يَا أَبَا عَبْدِ الرَّحْمَنِ أَلاَ نُزَوِّجُكَ جَارِيَةً شَابَّةً لَعَلَّهَا تُذَكِّرُكَ بَعْضَ مَا مَضَى مِنْ زَمَانِكَ. قَالَ فَقَالَ عَبْدُ اللَّهِ لَئِنْ قُلْتَ ذَاكَ لَقَدْ قَالَ لَنَا رَسُولُ اللَّهِ -صلى الله عليه وسلم- « يَا مَعْشَرَ الشَّبَابِ مَنِ اسْتَطَاعَ مِنْكُمُ الْبَاءَةَ فَلْيَتَزَوَّجْ فَإِنَّهُ أَغَضُّ لِلْبَصَرِ وَأَحْصَنُ لِلْفَرْجِ وَمَنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَعَلَيْهِ بِالصَّوْمِ فَإِنَّهُ لَهُ وِجَاءٌ ». *It was narrated that `Alqamah said: "I was walking with Abdullah in Mina when he was met by Uthman. He stood and talked with him and Uthman said to him: `O Abu Abdur-ur-Rahman, shall we not marry you to a young girl who can remind you of the times past?` Abdullah said, `If that is what you are telling me, (let me tell you that) the Messenger of Allah (s.a.w) said to us: O young men, whoever among you can afford it, let him get married, for it is more effective in lowering the gaze and guarding one`s chastity. And whoever cannot afford it should fast, for it will be a shield for him."* Sahih Muslim *BISMILLAHI RAHMANIR RAHIM* ________Hmmmmm bansan ta ina zan fara baku labarin na da yake cukuikuiye ba *BA SON TA NAKE BA* wannan Kalmar da na saba ji kenan a gidan mu har zuwa gidan aure na, bari dai in fara muku daga d'an farko yanda zaku fi fahimta. Suna na Fatima. Amma Inna ta na kira na da Zareefa a halin yanzu shekaru na basu fi 10 zuwa 11 ba muna shirye-shiryen rubuta common entrance a makarantan mu na boko sai dai yau tunda na shigo kuka nake sosai saboda cin mutuncin da akayi min yau har yayi yawa duk da ba yau aka fara min ba sai dai na yau d'in ya tsaya min a rai. Uniforms aka zo dasu ana rabawa daga gwarzon Governor mu professor Babagana Umara Zullum, harda jaka wadda ya kunshi note books, tex books crayon pen da sauran tarkacen da d'alibi zai bukata gefe d'aya kuma ga sandal da socks amma aka tsallake ni wai dan ban biya 200 na PTA ba duk da kasancewar nafi kowa bukatan wa'yan nan kayan domin uniform d'ina ya gama yagalgalewa. Basa tab'a ganewa Inna ta ina zata samu gudan 200 ta bani in kawo musu Ita da kyar take samo 30 da safe ta bani 20 in sayi alale wajan Maman Dije dake gidan mu 10 kuma ta bani a matsayin kud'in tara, toh a wannan halin 200 ba karamin kud'i bane a wajan mu. Kudin taran ma in na zo dashi sai in rasa abun saya dashi, gashi kiri-kiri ana mana girki a makaranta a rabawa kowa banda ni da ban san me na tare musu ba, bakin jinin Malamai prefect harda monitor nake dashi akan wannan 200 da bana kawowa yasa duk suke jin haushi na, ina ji ina gani za'a tsallake ni a hanani abincin nan wanda nake masa kallon kaman naman kaza suke ci sai randa suka ga dama suke bani bani, duk ranan da na samu ci nake kaman in had'a da hannu na. Abinci ne da ake rabawa ko kwatankwacin sa babu a gidan mu, dan wata ran alale mai kwai da hanta ake rabawa wata ran kuma jallof d'in doya ko macroni ko kuma na shinkafa da wake yaji manja, toh ina mu ina cin wannan kayan dad'in a wannan gidan namu na yawa. Abban mu matan shi 3, dan haka in gari ya waye kowa shi zai nemawa cinsa da 'ya'yan sa abinda zai ci babu ruwan Baban mu da d'aukan nauyin ahalin da Allah ya bashi duk ranan da Allah ya bashi zai sayo masara ko dawa a nika dayawa a rinka tuwo da daddare da safe da rana kuma kowa yaji da kan shi dan haka duk yayuna da kanne na wanda muke uba d'aya da cousins d'ina duk tallah suke dan rufin asiri amma ni Inna ta bata yarda da tallah ba duk da ni kad'ai ce wajan ta tana iya kokarin ta wajan ganin ta sauke duk wani nauyi daya rataya akan ta dai-dai karfin ta shiyasa kaf gidan mu babu masu zuwa boko ko islamiya sai ni kad'ai wanda 'yan gidan mu sukewa lak'abi da iyayi ne sai dare kuma muke zuwa makarantan Allo gaba d'ayan mu amma banda 'yan matan da suke tsayawa zance abin su. Kona dawo makaranta wata rana babu abinda zanci in Inna bata samu wankau tayi ba sai dai ta tura ni gidan su da yake makotaka da namu inci duk abinda ya sauwaka a wajan kakata kasancewar suma kaman gidan namu suke babu wadata sai dai su basu da yawa kaman gidan mu,ranan da ta samu kud'in wankau kuma ta kan bani hamsin in sayi garau-garau nan wajan Gwaggo Aisha ta d'an yarfa min a roba dan mugunta ko mai da yajin kirki bata zuba min kuma in na fita waje na saya ya zama abin magana da habaice-habaice shiyasa ko zan fita saya a waje Inna ta ke hanani. *BA SON TA NAKE BA* shine kullum Kalmar da Baban mu yake fad'awa Inna ta in wani abu ya faru a cikin gida kuma kayan takaici a gaban kowa yake fad'a mata hakan sauran matan gida suyi ta shewa ana kara habaice-habaice tun bani da wayo har nayi wayo na gane me hakan ke nufi kuma a bakin matan gidan mu na tsinta wai Kakana Abban Inna ta tsohon soja ne in ba'a biya su fensho ba wajan Baban mu yake neman rance har kudin suka taru ya kai Kakana ba zai iya biya ba wanda yasa dole ya bashi Inna ta shiyasa ko kad'an bamu isa mu d'aga murya kaman kowa a gidan ba,Inna ta in ba wani abu take ba kullum tana cikin d'akin ta dan matan duk sun had'e mata kai har yaran su duk raini suke mata sai wajan matan kanin Baban mu Maman Dije take samun sauki dan babu ruwanta da hargitsin gidan mu sai kishiyarta itama tana shiga cikin sauran matan Baban mu tana taya su wulakanta Inna ta. Haka na fito daga cikin makarantan ina kukana na karin takaicin ma 'yar silifas da nake lallab'awa kuma nake shan bulalan rashin sandal akai ina zuwa bakin gate ya tsinke, ban tsaya neman leda dan gyarawa ba na rike a hannu na nufi titi ido rufe na manta da akwai motoci kan titin burina kawai in ganni a gida. Karan takawan brick ne ya dawo dani hayyaci na, ganin mota ya nufo ni gadan-gadan yasa na rasa yanda zanyi saboda firgita nan na durkushe ina jiran ta Allah ta kasance min. Motan daya ja brick Allah ya taimake ni bai kad'e ni ba amma motan bayan shi sai da ya fasa mishi danger, shima na bayan shi ya buga mishi a takaice dai motoci kusan 5 sukayi hatsari duk a dalilina, kuma duk abinda ake ina nan durkushen ban mike ba. Wani wanda motan shi yafi na sauran bugawa ya fito a zuciye ya janyo ni yana bala'i yana zagina ya d'aga hannu zai yarfa min mari, ihu na yi na rufe fuska ta da d'ayan hannuna ina jiran saukan marin amma na ji shiru ina bud'e idona naga ashe mutane ne suka rike shi suna bashi hakuri, ina jin ya sake min hannu na kama hanyan gida da gudu dama tsakanin makarantan mu da gidan babu wani nisa sosai. Ban iya tsayawa a ko ina ba saboda zafin rana da yake kona min kafa ina shigowa Hajara na fita da katon tire da aka jera mata robobi da aka zuba garau-garau hamsin hamsin a ciki, ni dai ban san ya akayi ba kawai sai gani nayi munyi karo kayan kan ta sun zube kamin kice kwabo almajirai sun fara wawaso nima ganin haka na wawasushi roba 2 na kama ci dama na kwaso yunwa ta na fitan hankali. Ihu Hajara ta fasa tana "Wayyoo Gwaggo zo ki gani zo kiga abinda Zareefa tayi min" jin an ambaci suna na yasa matan gidan da yaran su lekowa dukan su, ni kuwa ko a jikina ina gefe sai zabga loma nake yau na samu shinkafa da wake daya ji mai da yaji har roba 2. Salati manyan suka fara suna bina da kallo yanda baki na yayi nasha-nasha da mai,Gwaggo Aisha da fitowar ta kenan tace" kan uba ke Hajara meke faruwa ya akayi kika min b'arin abinci haka?" "Wallahi Gwaggo kin gan ta nan Zareefa ce ina fita ta shigo a guje ta ture ni har nayi barin, kuma tun kamin almajirai su zo ita ta fara wawason min abinci" Hajara ta karasa tana harara ta yanda nake ta sud'e roba dan ban san ma sunayi ba sam. Wani maka da Gwaggo ta kai min a gadon baya ban san lokacin da na saki roban na gatsare tare da fasa ihun azaba ba, wuyan matattacen uniform d'ina ta kama ta jani zuwa ciki tana" lalle na yarda wannan 'ya ta gado mugunta, hasada da tsiya yo banda tsiya yanda kuke ke da uwar ki baku da allura a cikin d'akin shine ta koya miki yanda zaki na yi min barna kina jawo min asara?? Ke Bintu koki fito wallahi kabo na ba zaiyi ciwon kai ba duk inda zaki shiga ki fita sai kin bani kudina yanzu kuma wallahi ba sai anjima ba, ki fito na ce ". Kallon yanda wuyan uniform d'ina yake kara yagewa yasa nace" Gwaggo ki sake min uniform d'ina kinga kina kara......" Ban samu karasawa ba sakamakon buge min baki da tayi tana huci tace" inifon din banza inifon din wofi ke iskanci uwar taki take koya miki ko boko shegiya yarinya duk wani gantali kin iya wai an likawa boko da baida baki" "Ni ai abin nasu dariya yake sakani haka masu bokon suke ko akan su aka fara oho, dubi kiga ko takarda d'aya bata dashi balle fensir,ko da uwar me take rubutun?" Cewar Inna Asabe. Inna ta duk tana jinsu amma ko lekowa bata yi ba balle ta tanka musu, hayaniya sosai ya kaure a gidan mu harda mokota masu zugi sai yi suke harda masu cewa a gaban su ma abin ya faru, dole yasa Inna ta fitowa daga d'aki jin abin yaki ci yaki cinyewa. "Yauwa daddawa uwar zaman d'aki dole ai yau ki fito azo a biyani kud'ina naira dubu daya da dari biyu ciff wallahi ko biyar d'ina ba zaiyi ciwo ba". Dariya suka fara suna " keko Aisha ina wannan taga har dubu da dari biyu sai dai in 'yar zata sai da ta biya ki" ko kuma kije wajan tsohon soja" wani tsohon soja sai dai ayi sata" ire-iren kalamai da suke jifan Inna ta dashi kenan. Kaman yanda ta saba bata kula kowa ba ta koma cikin d'akin ta sai gata ta fito da dubu d'aya da dari biyu ciff da Gwaggo Aisha ta ambata ta mika mata babu kunya ta sake min riga ta karb'e kudin tana lissafi tana mamakin ina Inna ta ta samu wannan kud'i ita da burin ta yau sai ta wulakan tamu yanda taga dama amma cikin ikon Allah ta biya. Duk watsewa suka yi cike da mamaki wasu ko cewa suke dama bar raina mutum baka san sirrin sa ba. Ana cika min rigata na shigo d'aki ina kallon wuyan rigata na ce, "Inna dubi fa yanda ta maida min wuyan rigata gobe ya zanyi in tafi makaranta?" Inna da ta had'a rai sosai ta ce, "ba wuyan riga ya kamata kiyiwa kuka ba, gobe kika ce za'a rufe karb'an kud'in common entrance ko?" Gyad'a mata kai nayi ina cire kayana. "Toh kud'in da nayi wata 3 da wani abu ina tara miki na common entrance d'in su na bada a maimakon abincin mutane da kika zubda, gobe ma in kin taso daga makaranta kada ki rinka kula da gaban ki". Yawan comments yawan typing. [8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` *_And now_* *_💃🏻UWANI💃🏻 *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'a Ga Wanda ka zage shi:* Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; اَللَّهُمَّ فَأَيـما مُؤْمِنٍ سَبَبْتُهُ فَاجْعَلْ ذَلِكَ لَهُ قُرْبَةً إِلَيْكَ يَوْمَ الْقِيَامَةِ. Allahumma fa'ayyuma mu'minin sababtuhu, faj'al zalika lahu kurbatan ilayka yawmal qiyamati. Ya Allah! Duk wnai mumini da na zage shi, to ka sanya wannan ya zamanto sababi gare shi na samun kusanci zuwa gare Ka ranar kiyama. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *2* Kasa cire rigan nayi na zaro ido waje ina kallon Innara na ce," Inna kud'in common entrance d'in kika basu?" "Ya kike son inyi? Kin san halin Aisha sarai a gidan in ta fara fitina zata kai awa goma tana yi ba tare da ta gaji ba,ni kuwa kin san ba iyawa zanyi ba gwara in bata a rabu lafiya gobe ma idan zaki shigo gida kada ki natsu " Inna kenan ta bani amsa. Zama nayi da rigan a wuyan na ina hawaye na ce," shikenan za'ayi banda ni kenan,ko yau ina kallo akayi ta rabon abubuwa a makaranta ni ban samu komai ba akan 200 balle 1500 nasan gobe ko class ba za'a barni in shiga ba". "Haka Allah ya kaddara ba zaki rubuta ba a wannan shekaran amma kiyi hakuri zuwa shekara mai zuwa ko kuma muyi addu'an Allah ya kawo wata hanyan,kinji ko?" Inna ta fad'a min cikin rarrashi. Goge hawayen fuskan ta nayi na tashi na cigaba da cire uniform d'in na ba tare da na kara cewa komai ba. "Ki d'auki hamsin cikin d'ari ukun daya rage kije ki sayi wani abin kici" cewar Inna. Dariya na fara kyakyalewa da shi harda rike ciki sai da nayi mai isa ta sannan na ce," ai inna ciki na kaman zai fashe saboda koshi, dan lokacin da Hajara tayi b'ari almajirai suka fara wawaso nima roba 2 na wawashe na cinye tas abina Gwaggo Aisha data ji haushi kinji yanda ta zuba min dundu a baya Wallahi ko jin zafi ma banyi ba". Cikin tsuke fuska Inna ta ce," wai ya akayi kika yi musu b'ari? Kullum inayi miki fad'an ki natsu amma ba kya ji ko?" Daina dariyan nayi sannan nayi kalan tausayi na fara bata labarin abinda ya faru a makaranta har zuwa yanda mukayi karo da Hajara,ajiyar zuciya Inna ta sauke tana mai jin tausayin na ta ce," hakuri zakiyi Zareefa insha Allah wata rana sai labari,karatu kuma da yardan Allah zakiyi shi". Gyad'a kai kawai nayi na fita yin alwala zahar a lokacin duk yaran gidan anyi musu abin sana'a duk sun fita talla,ina idar da sallah na fara shirin islamiya shi kam cikin dokin zuwa nake shirin na kasancewar a can bana takura kaman boko. Akwai wani Malamin mu da yake d'aukar mu Qur'an shi ya tsaya minsosai sabo kokarin na dan har kudin wata 500 shi yake biya min domin kullum dai-dai nake kawo hadda ta yanzu haka mun bawa izufi 30 baya. Ina gama shirin na nayiwa Innata sallama na tafi. Ina fita Inna ta kwaso uniform dana cire ta hau wanke min da sauran Omo da ta rage jiya,tanayi tana jin su suna ta haice-habaicen su ta gama ta shige d'aki ta rabu dasu. Mun taso a islamiya ni da kawayen na muka nufi gida muna d'an wasan su na yara,muna zuwa dai-dai gidan mu na fara jin muryan Baban mu yana ta masifa kaman zai ari baki. Dariya sauran yaran suka fara har suna lekowa ta rububben ginin daya zagaye gidan. Jiki a sanyaye na nufi cikin gidan namu dan nasan yanda Baba yake d'aga muryan nan nasan da inna ta yake,muryan Gwaggo Aisha naji tana kara zuga Baba da fad'in karya da gaskiya. "Toh ai Mallam dan ma baka ga irin rashin kunyan da yarinyan nan tayi min a waje ba,inda zaka san da gayya ta b'arar da kayan sana'a shine,itace farkon daka wawa sannan sauran almajirai suka bi bayanta. Koda yake b'ata baki na nake ina gaya maka abinda ya faru na san babu wani hukuncin da zaka d'auka tunda 'yar amayar ka ce abin sonka". A fusace Baba ya juyo kanta yana," wannan wani irin maganan banza kike min matar da *Ba sonta nake ba* aka lika min ita dole yasa na karb'a dan kar inyi asaran kud'i na,amma wallahi Aisha kin cuce ni".. Gwaggo Aisha ta saki shewa dama Kalmar da take son ji kenan. Baba ya cigaba da fad'an shi inda yake cewa," duk kin bi kin b'ata yarinya bata ganin kowa da darajan a gidan nan da anyi magana kice wai boko take sai kace ki d'in bokon kikayi aikin banza kawai zata zo ta same ni a gidan sai jikin ta ya gaya mata" Yana juyowa muka had'a ido ina can makure karshen bango ,aiko baiyi wata-wata ba ya nufo ni zai sake min wannan rankwashin sa nan da sai yasa kullum na saki fitsari a wando. A guje nayi d'akin mu na shige kamin ya kama ni sanin cewa in ba wani babban dalili ba baya shigowa,cikin sa'a kuwa bai shigon ba ya tsaya a tsakar gida yana cigaba da fad'an,sam na daina jin me yake cewa domin ganin Inna ta na kuka abinda ban tab'a gani ba kenan tun tasowa ta dan komai akayi mata a gidan ko Baban mu ko matan gidan sai dai tayi murmushin mai ciwo tace akwai Allah. Toh tana furta wannan kalman duk yanda za'ayi da ita ba zata kuma tankawa ba na sha tambayan ta me yasa itama ba zata ke rama cin fuska da ake mata ba sai dai tayi wannan murmushin nata mai ciwo ta ce," bakomai Zareefa akwai Allah" daga nan kuma ba zata kara cewa komai ba. Zuwa nayi har gaban ta na durkusa a gaban ta tare da d'aura hannu na kan guiwoyin ta na ce," Inna kuka kike,meya same ki?" Duk na jero mata wayan nan tambayoyi a lokaci guda. Murmushin nan nata mai ciwo tayi min kana ta ce," babu komai ba kuka nake ba wani abu ne ya shiga ido na". Ba dan na yarda ba nayi shiru nasan ko abinda ake mata a gidan nan dole tayi ta kuka kullum,komawa gefe nayi na zauna ina kallon ta tana dinke min wuyan uniform d'ina daya yage bata kuma yarda ta zubar da hawaye ba. Da washe gari da safe bayan na sayo alale na naci Inna ta bani 200 a cikin kudin daya saura ta ce in kai makarantan nima a bani bani sabon uniform d'in inya so ko shekara mai zuwa sai in zana jarrabawan. Cikin matukar farinciki na nufi makaranta yau nima za'a bani kyautan kayan makaranta kaman sauran d'alibai. Direct office d'in principal na wuce ina jin kaina yau kaman bani ba,bayan na gaishe shi na bashi kud'in na ce ni jiya ban samu daman zuwa ba shiyasa ban samu komai na rabo ba. Tambayan shekaru na yayi na fad'a mishi ya ko duba ya ciro uniform sabo dal ya miko min,murna fal jikina na karb'a amma sai na kasa tafiya ina jiran jaka da sauran tarkace. Ganin na ki tafiya ya ce," me kike jira kuma?" Kasa nayi da kaina na ce," Sir su jaka da takardu suma ban samu ba". "Okay toh sai gobe ko anjima dan suna store,ya suna ki kuma a wani class kike?" "Suna na Fatima Hassan,kuma ina class 6A" na bashi amsa. "Toh kije anjima zan sa akai miki" cike da farinciki na juya na koma ajin mu feeling proud. A wajan assembly akayi announcing cewa duk wanda bai biya kud'in common entrance ba ya koma gida dan zuwa nan da awa 2 za'a fara kuma ba barin mu za'ayi mu shiga ba,nan take murna ta ya koma ciki. Jiki a mace na kama hanyan gida dan nasan zaman nawa bashi da amfani,ina tafiya ina hawaye saboda na kwallafa rai na akan jarrabawan,shikenan inaji ina gani mates d'ina zasu wuce ni. Ina tafiya cikin tafiya naji horn a kusa dani ,matsawa gefe na karayi maimakon ya wuce sai naga ya tsaya kusa dani yana kallo na ya ce," kanwata meya same ki kike kuka akan titi?" Kallon shi na tsaya yi d'an kyakkyawa dashi duk da ba fari bane. "Kiyi magana mana kanwa ta?"ya katse ni. "Kud'in common entrance ake nema shine aka kore ni dan ban biya ba" na bashi amsa sabon hawaye na bin kunci na. "Oh stop crying,kiyi shiru muje makarantan naku in gani" yace yana fitowa daga cikin motan shi. Tsayawa nayi kallon shi ba tare da na motsa ba, murmushi shimfid'e a fuskar shi ya zagayo inda nake tsaye ya rankafo da kan sa kusa dani ya ce," me kike tunani ?" "Inna ta zata min fad'a ta hana ni magana da wanda ban sani ba" nace ina kara komawa baya. "Kada ki damu ni Yayan kine muje zan miki bayani kin ji?" Gyad'a mishi kai nayi muka koma makaranta dama banyi nisa ba. Office d'in principal muka tafi bayan sun gaisa ya mishi bayanin cewa shi Yaya nane yazo biya min kud'in common entrance,ni dai ban ce komai ba sai bin su da nake da ido,a take ya cire kud'i d'ari biyar- biyar sabbi fil ya biya muka fito ya ce," kije class kuma kiyi kokari sosai kinji kanwata?" Murmushi ne ya kwace min na gyad'a kai na tare da rugawa zuwa aji. [8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` *_And now_* *_💃🏻UBA SONTA NAKE BA💃🏻 *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Abin Da Musulmi Zai ce idan aka yabe Shi:* اَللَّهُمَّ لاَ تُؤَاخِذْنِي بِمَا يَقُولُونَ، وَاغْفِرْ لِي مَا لاَ يَعْلَمُونَ (وَاجْعَلْنِي خَيْرًا مِمَّا يَظُنُّونَ) Allahumma la tu'akhizni bima yakuluna waghfir lee ma la ya'alamun, (waj alne khayran mimma yazunnun). Ya Allah! Kar Ka rike ni da abin da suke fada, Ka gafarta mini abin dab a su sani ba, Ka sanya ni fiye da yadda suke zato. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *3* Koda na tafi class naga kowa harkan gaban shi yake kasancewar sai zuwa nan da awa 1 za'a fara jarrabawar, dan haka kawai sai na wuce bayan gida na canza sabon uniform nawa, na sanin cewar daga yau na gama amfani dashi dama Inna tasa na karb'a ne kan cewa zan ƙara wata shekarar amma Allah ya taimake ni ya kawo wannan mutumin da yake cewa shi Yaya nane. Kayan ba ƙaramin kyau suka yi ba, sun zauna sosai a jikina dama gani ba za'a kira ni mai jiki ba kuma ba za'a kira ni da sirirya ba,ga fata ta irin mai tsadan nan ce, wato chocolate colour wanda yayiwa round face na kyau,bani da dogon hanci can amma inada daidai gwargwado sannan manyan idanu na da d'an ƙaramin baki na su suke sa mutane suke min kallon wata kyakkyawa,wajan gashi ma dai babu laifi dan ina dashi ba laifi. A bola na watsar da tsohon uniform d'in nawa dan inada yakinin in aka bawa wani ko goge-goge ba zaiyi dasu ba,na kama hanyan class d'in mu sai na zama abin kallo ga sauran d'aliban wasu na min dariya wasun kuma na cewa sun min kyau,ni dai ban kula kowa ba nayi wucewa ta class d'in mu. Nan ma bata canza zani ba dan wasu har tsokana ta suke,kala bance musu ba sai harkan gaba na nake zuciya ta fari kal zan rubuta jarrabawa tare da 'yan uwana. Bayan wani lokaci malamai suka shigo raba mana paper, nan kowa ya natsu bayan sun gama raba mana kowa ya fara rubutu sai naga ashe abun ba wuya ba kaman yanda na tsorata da shi bane a farko,cikin kankanin lokaci na kammala na fito abu na ina mai jin farinciki a rai na. Da daddaya kowa ke fitowa bayan mun gama fitowa aka raba mana abinci mai d'an karan dad'i jallof na shinkafa harda naman kaza da bobo. Kin cin nawa nayi na kama hanyan gida da abinci na,ina tafiya ina ta dube-dube ko zan kara ganin bawan Allah nan amma ko mai kamanin sa ban gani ba har na iso gida. Duk 'yan matan gidan mu yau suna nan basu fita tallah dan azahar batayi ba sai dai kowacce suna bakin murhu da uwayen su suna aikin kayan sana'ar su sai yara mazan ne da suka fita sai da pure water. D'akin mu na wuce direct sanin cewa Inna ta tana ciki ko lura da kallon tsana da Gwaggo Aisha ke auna min banyi ba nayi sallama na shiga d'akin mu. Inna ta na zaune da sabuwar multi na hula a hannun ta tana tsakawa ,da sauri na ida shigowa ina cewa," laa Inna hula kika fara,yaushe kika koya ko dama can kin iya?" Na jero mata tambayoyin nan duk lokaci d'aya cikin zak'uwa. Murmushi shimfid'e a fuskar ta tace," kinga yanda sabuwar uniform d'in ya miki kyau kuwa,kinga har shekara mai zuwa zakiyi amfani da kayanki hankali kwance". Zama nayi ina ajiye takeaway da bobo na hannu na, nace mata," ai Inna bana bukatan uniform d'in hasalima daga yau amfanin shi ya kare domin dani aka zana jarrabawan". "Dake aka zana sun tausaya ne suka bar miki ko kuwa?"ta tambaya fuskarta d'auke da farinciki mai cakude da mamaki. "Ko kad'an basu ji tausayi na ba Inna,kora tama sukayi har na fito daga makaranta zan dawo gida...." Nan na bata labarin abinda ya faru tsakani na da wanda ya ce shi Yaya nane. Maimakon inga tana farinciki sai naga ta tsuke fuska ta fara min fad'an da kada in sake yarda da wani kan titi wanda ban sani ba ko ya bani abu in karb'a,a irin haka suke maida yara doya su tafi dasu suyi tsafi dasu ko kuma a yanke kan su. Tsoro sosai ya kama ni nayi ta zare ido ina ganin na tsallake rijiya da baya ashe,nan na bata hakuri tare da alkawarin bani ba wanda ban sani ba nan gaba. Daga nan hira muka zauna yi da Inna ta bayan na bud'e mana takeaway nace muci tare,kallon abincin tsaya yi kana tace,"yanzu dama irin wannan abincin ake raba muku harda naman kaza?" Dariya na kyakyale dashi sannan nace," Inna baki ga harda bobo na ba?" "Ikon Allah tunda nake ban tab'a jin labarin governor mai son talakawan shi haka ba sai akan bawan Allah nan,Allah ya kiyaye mana shi" cewar Inna . Da "Ameen na amsa sannan nace mata muci mana,amma taki ci d'an tab'awa kawai tayi ta bar min kaya na anan ne take gaya min ashe 'yar wata makociyar mu mai suna Ya'ana ita ta koya mata d'inkin hula,shikenan ta huta da zaman banza inta gama ance ana saya da kud'i da d'an yawa,murna nayi tayi muma mun samu sana'a da zamu rinka samun kud'i kaman sauran 'yan gidan mu. Tun daga wannan rana na mayar da hankali na kan makaranta islamiya da nake in kuma safiya ce Inna ta kan tura ni gidan kakanni na saboda gudun rigimar 'yan gidan mu sai lokacin islamiya yayi sai in dawo in shirya inyi wucewa ta domin Gwaggo Aisha tafi kowa iya tuggu kuma Baban mu sosai yake jin maganan ta in fact itace 'yar gaban goshin shi ba dan komai ba sai dan tafi sauran matan shi kud'i kuma tana bashi kud'i shiyasa yake ji da ita sosai. Maganan shiga secondary school mun ajiye ta a gefe kan cewa sai inna ta dinka hula 2 ko 3 sai ta had'a kud'in ayi min komai dashi. Cikin ikon Allah satin hulan 4 Inna ta kammala shi baiyi kyau irin na kwararre ba amma da yake cikin tsafta ta dinka shi babu datti ko kad'an a jiki sai ya zama abin sha'awa. Ya'ana wacce ta koya mata itama ta gama nata zata kai sayarwa Inna tace muje tare sai ta sayar a bani kud'in kasancewar ita zata wuce gidan kakanni ta daga can kuma zata kwana 2 kamin ta dawo. Bayan ta shirya ta biyo min muka tafi can London ciki wai can sun fi sayan hula da daraja, dubu da dari biyar aka sayi na inna ta ita kuma Ya'ana dubu tara aka sayi nata da saboda ita nata tangaran ne. A leda baki ya'ana ta kulle min kud'in ta saka ni a napep na zuwa anguwan mu ita kuma ta wuce,muna zuwa kusa da layin mu suka sauke ni suka wuce. Har nazo kusa da layin mu na had'u da wani mutum yace min," ke ana sadaka a wacan kwanan" kamin in bashi amsa wasu yaran su 4 suka zo wucewa ya fad'a musu ba musu suka bi hanyan daya nuna nuna musu,ganin sun bi hanyan yasa nima na bisu a guje muna shan kwanan ashe mutumin yana bin mu sai muryan shi muka ji yana cewa," kai ku tsaya in akwai abu a hannun ku,ku kawo in ajiye muku kar ya fad'i wajan karb'an sadakan". Gaba d'aya mu muka mika mishi duk kud'add'en hannun mu da alamu suma sauran yaran aiken su akayi,yana karb'a yace mana ga gidan can mu shiga shi yana jiran mu anan. Ga gudu muka shiga gidan da sunan karb'an sadaka amma me sai aka ce mana ai ba anan akeyi ba,wata da zata girme mu a ciki tana jin haka ta fita da gudu muka mara mata baya amma muna fita muka nemi mutumin nan sama ko kasa muka rasa shi,kuka ko wannen mu ya fara dan sai yanzu muka gane cewa ashe b'arawo ne yayi mana dabara ya sace mana kud'add'en mu. Gefen titi na samu nayi zama ta ina kuka na kasa komawa gida in naje me zan cewa Inna ta bayan kwanaki tayi min fad'a akan irin haka sai gashi na maimaita,bayan haka hulan nan yanda ta dage tayi ta d'inka shi ba dare ba rana dan ta samu saka ni a secondary school amma sai in koma ince mata wani ya min dabara ya kwace? gaskiya ba zan iya komawa ba. Ina zaune ina kuka na d'aya daga cikin yaran da shima an sace mishi kud'in yazo ya zauna kusa dani muka cigaba abin mu,kaman daga sama naji ance," kanwata yauma kukan kike?" Da sauri na d'aga kaina dan ganin waye sai naga wannan bawan Allah daya biya min kud'in jarrabawa ne hannun shi rike da bottle water inaga a shagon kusa damu ya saya ga mutane a wajan suna ta shiga da fita babu wanda ya kula mu sai shi da yazo yanzu. Kin kula shi nayi na d'auke kaina ina goge hawayen ido na. "Kai meya same ku kuka zauna anan kuke kuka?"ya tambayi yaron kusa dani. Shi kuwa kama jira yake ya fad'a mishi duk abinda ya faru nan ya tambayi shi nawa ne kud'in?. "Dari uku ne akace in sayo taliya da mai da maggi" ya bashi amsa. Dari biyar ya ciro a aljihu usual sabo dal ya bawa yaron,cike da murna yaron ya karb'a yana godiya ya ruga da gudu ya tafi shagon kusa damu ya sayi kayan yanda ya fad'a ya dawo mishi da canjin shi,amma sai yaki karb'a yace ya tafi ya bar mishi. Murna fal ranshi ya kama hanyan gida da gudu ya bar mu a wajan,ganin ban bi yaron ba yace min," ba tare kuke bane?" Jiki a mace na girgiza kaina saboda na zata yaron yana amsan kudin zai zama doya kaman yanda inna ta ta fad'a sai naga ba haka bane lafiya lau yayi sayayyar shi ya tafi gida. "Ke kuma nawa ya sace miki?" Muryan shi ya katse min tunanin da nake. "Kud'in hulan Inna ta ya karb'e gaba d'aya" na bashi amsa. "Stop crying kanwata kinji,gashi karb'i ki kai mata". Kallon kud'in na tsaya yi ina tunanin in karb'a ko a'a? "Karb'a mana ki goge hawayen ki" saka hannu 2 nayi na karb'a cikin sanyin murya nace," nagode!" Girgiza min kai yayi ya ce," kada ki damu tashi ki tafi gida". Da azama na tastashi nayi gidan mu ba tare da nasan nawa ya bani ba. A gida kuwa Inna duk ta damu tana tunanin me yasa na dad'e haka,tana ganina ta sauke ajiyan zuciya ta ce," zareefa me yasa kika dad'e haka?" Banyi kasa a guiwa ba na kwashe duk abinda ya faru na gaya mata,karban kud'in tayi ta kirga taga dubu uku ciff,fincikoni tayi da karfin tsiya na fad'i akan simintin d'akin na bud'i baki zanyi ihu ta ce kada na kuskura inyi mata ihu anan dole na had'iye kukana ina zaro ido saboda ganin Inna ta ta fusata yau sosai. " Wato ke ba kya jin magana ko zareefa duk abinda na gaya miki ta bayan kunnen ki suka wuce ko,baki san ki kama kan ki a matsayin ki na ya mace ba duk ko wani d'an iska ya baki kud'i karb'a kike yau kuma harda bin wani, Inna ilahi wa inna ilahi rajiun!!! Toh tunda kunnen kashi gare ki yau zanyi maganin ki wallahi" ta karasa tare da murd'e min kunne. Sosai ranan inna tayi min abinda tunda na san kaina bata tab'a yi min ba daga baya tayi min nasiha sosai mai ratsa jiki. Tun daga wannan rana nayi hankali ya kasance babu ruwana da duk abinda zai had'a ni da wanda ban sani ba sosai na kama kaina. Kullum Baba inya shigo gida Gwaggo Aisha itace zatayi ta dawainiya dashi dan ko Maman su Hafsa bata samu wannan matsayi a wajan shi ba,shi irin mazan nan ne da mace in zata rike shi tayi mai komai toh dad'i zaiji kwata-kwata bashi da zuciya d'aukan nauyin iyali da Allah ya d'aura mishi shiyasa gidan namu kullum sai kara hargitsewa yake. Maman su Hafsa abin na damun ta sai dai babu yanda ta iya tayi-tayi amma ta kasa kamo Gwaggo Aisha dan tafi ta samu nesa ba kusa ba. Ranan wani juma'a daya kasance girkin inna ta ne kuma a ranan munyi sa'a Baba ya kawo mana masara kusan kwano 10 ya ce a nik'a tunda babu garin tuwo. Maimakon manyan gidan su kai sai suka ce ba zasu kai ba tunda ba girkin iyayen su bane,shikenan sukayi zaman su babu wanda ya ce musu wani abu. Dole yasa wheelbarrow inna ta aro ta saka min a ciki ta ce in kai, ina turawa da kyar na kama hanya na fita a gida ga kuma inda zan kai nikan da d'an tazara da gidan mu. Inna ta ana cewa tana da girki a gidan ne amma baba baya shigowa d'akin ta kaman yanda yake shiga sauran d'akin matan shi kuma baya cin abincin ta,na sha jin yana cewa nima Allah ne ya kaddara sai na taka duniya amma har yau yana jin takaicin wannan abin. Na isa lafiya sannan nabi layi har aka zo kai na aka nik'a min mutumin shiya taimaka ya mayar min cikin wheelbarrown na kama hanyan dawowa gida. Ina cikin turawa jikina duk gumi ban san taya wannan yaron ya shiga gaba na ba da keken sa da alamu ma dan koyo ne dan da kyar ma in ya kaini shekaru,duk yanda naso kaucewa amma abin bai yiwu ba saboda nik'an da nauyi kamin kace me dani dashi duk muka zube a wajan tare da kurkurjewa buhun nik'a na kuma sai cikin kwata da yake kusa damu. Hannu 2 na d'aura a kai na rusa ihu ina gari na dan ko zafin kurjewan na daina ji saboda nasan in na koma gida babu garin nan wallahi Baban mu zai iya babbake ni da raina. Sosai nake kuka kaman raina ya fita mutane sun taru suna mana sannu ko jin su bana yi har yaron ya d'auki keken shi ya tafi babu wanda ya hana shi kasancewar karami ne babu abinda zai iya yi. "Oh not again yauma kuka take,meya same ta?"naji muryan shi kaman daga sama. "Karo sukayi da me keke nik'an ta ya fad'a kwata" wani yaro ya bashi amsa yana nuna mishi buhun da aka ciro a kwata wanda ko akuyoyi ba zasu iya cin garin da yake ciki balle mutum. Baice komai ba ya koma ya motan shi ya wuce,ajiyar zuciya nayi da Allah yasa bai ce zai ban wani abu ba yau,mutane suna bani bakin in tashi in tafi gida amma kirmitsitsi naki motsawa balle su saka ran zan tashi. Bayan kaman mint 5 na kara jin muryan shi yana cewa," ga wannan tashi in ajiye ki a gidan ku". Kallon inda yake nayi naga buhun shinkafa da wasu kwalaye harda jerrican mai ana saka mishi a boot din mota,kaman wanda aka jona da remote na tashi jiki na na b'ari na fara tura wheelbarrow na da gudu nayi hanyan gida na bar shi tsaye anan. Ana gama saka masa kayan ya tambaya ko akwai wanda ya san gidan mu anan? Wani yaro yayi caraf yace ya san gidan mu gashi can babu nisa sosai daga nan. Motan shi ya shiga tare da cewa yaron yazo ya raka shi,ba musu yaron ya shiga suka bi baya na. [8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *_4_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'ar Tsayuwa a Kan Dutsen Safa da Na Marwa* Jabir, Allah ya yarda da shi ya ce, yayin da yake siffanta hajjin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; yayin da ya kusanto dutsen Safa sai ya karanta: إِنَّ الصَّفَا وَالْمَرْوَةَ مِنْ شَعَائِرِ اللهِ. أَبْدَأُ بِمَا بَدَأَ اللهُ بِهِ. Bers Safa: Innas safa wal marwata min sha'a'irillah Abda'u bima bada'al lahu bihi. Hakika Dutdsen Safa da na Marwa suna daga cikin alamomin da Allah Ya sanya (na addininsa)". Ina farawa da abin da Allah ya fara da shi. Sannan ya fara da Dutsen Safa, ya hau shi har sai da ya hango dakin Allah, sai ya fuskanci alkibla, ya kadaita Allah, (ya yi hailala), ya girmama shi (ya yi kabbara) ya ce; اللهُ أَكْبرُ! اللهُ أَكْبرُ! اللهُ أَكْبرُ! Allahu akbar. Allahu akbar. Allahu akbar. Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma. لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ، اَللهُ أَكْبَرْ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ وَحْدَهُ أَنْجَزَ وَعْدَهُ، وَنَصَرَ عَبْدُهُ، وَهَزَمَ اْلأَحْزَابُ وَحْدَهُ. Bers la Ka'aba: La ilha illallahu, allahu akbar, La ilaha illal lahu wahdahu la sharika lahu, lahul mulku wa lahul hamdu, wa huwa ala kulli shay'in kadirun. La ilaha illal lahu wahdahu. Anjaza wa'adahu, wa nasara abdahu, wa hazamal ahzaba wahdahu. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Mulki ya tabbata a gare shi, kuma yabo ya tabbata a gare Shi; kuma Shi Mai iko ne a kan komai. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai. Allah ya gaskata alkawarinsa, Ya taimaki bawansa, Ya ruguza rundunonin kafirai Shi kadai. Ya karanta wannan zikiri sau uku, yana yin addu'a bayan kowace marra. Da ya hau Dutsen Marwa ma ya yi kamar yadda ya yi a kan Dutsen Safa. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *_4_* Ina isowa kofar gidan mu shima sun iso abinka da mota,ina ganin motan nayi jifa da wheelbarrow a nan bakin k'ofar gidan mu na shiga ciki da gudu ban tsaya a ko ina ba sai d'akin mu a d'akin ma a bayan k'ofa na b'uya ina lek'e. Inna da tun shigowa ta take kallo na fuska d'aure ta ce," wa kika tsokono a wajan da kika shigo min a guce haka?" Ban iya bata amsa ba sai zare ido da nake zuciya ta na cigaba da bugawa, Inna zata kara min magana muka ji muryan yaron daya rako mutumin nan ya ce,"wai ana neman zareefa". Wani kallo Inna tabi ni dashi sannan ta dubi yaron ta ce," yana ina?" Yana nan k'ofan gidan nan" yana gama bata amsa ya juya ya tafi abinsa. "Waye shi kuma me kika masa ya biyo ki har gida?" "Sh...shine wan...wanda ya biya min kud'in jarrabawa" na bata amsa. "Shine ya biyo ki har gida,ko dai da wani abu daban?" Shiru nayi na kasa bata amsa sai zare ido da nake saboda ban manta abinda tayi min akan shi ba. Hijabinta da yake gefenta ta saka ta fita dan taji me yake tafe dashi,a tsakar gida ta tarar da 'yan gidan mu kwan su da kwarkwatan su suna tsatsaye suna k'us-k'us. Suna ganin ta suka fara yi da karfi wasun su na cewa k'ila sata nayi mishi,wasu kuwa cewa suke asirin mu ne ya tonu k'ila yana cikin mazan da nake bi,tunda dama cewa suke karatun karuwanci nake. Inna ta bata kula kowa ba ta fito 'yar rub'abb'en zauren gidan mu da niyyan yi mishi iyaka dani domin ta gane fad'an da tayi min kwanaki shi ya firgita ni haka. Katuwar mota da ta gani ana sauke kayan abinci a ciki kaman za'a bud'e 'yar karamar shago yasa ta tsaya cak tana kallon d'an matashin saurayin da ba zai haura shekaru 21 zuwa 22 ba yana danna wata laftatiyiyar waya a hannun shi. Inna sai yayi mata kwarjini ta kasa karasa fitan balle tayi mishi magana,shine dai daya gaji da danne-danne shi ya d'ago da kai karaf suka had'a ido da Inna ta,asalin kamanin ta na d'auko shiyasa yana ganinta ya gane ta. Wayar nashi ya mayar aljihun rigan shaddar shi lafiyayya blue ya karaso gaban ta cikin sauri ya duka har k'asa ya fara gaishe ta,fuska a had'e ta amsa kana ta ce," lafiya kake neman zareefa,ko kuma akwai wani abinda kake nema daga gare ta,dan ta bani labarin duk abinda ta faru tsakanin ku kuma shine yau ka biyo ta har gida"? Girgiza mata kai ya fara wasu waye na taruwa a idon shi ya ce," ba haka bane Aunty kada ki min mummunan fahimta saboda ni ba nufi na kenan ba,domin duk had'uwa da muke da ita Allah ne yake had'a mu,lokacin da na gan ta a hanyan makaranta na fito zan tafi wajan aiki ne na gan ta tana kuka sai na biyu kuma na tsaya siyan ruwa a gefen hanya ne na ganta ita da wani yaro suna zaune a gefen titi suna kuka,and still yau shima gefen kwata na ganta zaune tana kukan garin ta ya fad'a kwata mutane duk sun zagaye ta ana taje gida ta fad'a amma taki tashi saboda wai Baban ta ba zai bar ta duk taji ciwo amma ko jin zafin bata yi. Ni suna na Abdulbasit kuma ni maraya ne da tunda na taso ban san kowa nawa ba,banida kowa akan titi nake rayuwata cikin yunwa,kunci da kuma kad'aici sai daga baya na samu wani bawan Allah ya tallafawa rayuwata har kika ganni haka sannan shiyasa na tsani inga karamin yaro yana kuka domin yana tuna min da lokacin kuruciya ta kuma duk yanda zanyi sai na san yanda zanyi in share mishi hawaye sannan hankali na zai kwanta. Ba ita kad'ai nakewa haka suna dayawa Aunty bana son kowa ya sha wahalan da nasha a baya amma in har hakan ya b'ata miki dan Allah ina neman alfarman ki yafe min". Inna da jikinta duk ya gama yin sanyi sai ta kasa furta komai saima jin ba dad'i da tayi kan yi mishi mummunan zato. "Ga wannan kayan abincin a saka su ciki Aunty sannan a bawa Baba hakuri kada ya dake ta tsautsayi ne " taji ya yanke mata tunani. Tulin kayan abincin ta kalla ido a waje ta girgiza mishi kai,"ta ce a'a ka tafi da kayan ka mun gode Baban ta kuwa zanyi mishi bayani zai fahimta kuma...." Katse ta yayi cikin sauri ya ce,"haba Aunty ba'a maida hannun kyauta baya,sannan ni ina farincikin na samu ahali da zan iya nunawa a ko ina amma kika ce haka? Sannan hakan na nunawa baki karb'e ni a matsayin d'an uwa ba,ina neman alfarman ki rike ni a wannan a matsayin inji ya ake ji in mutum yana da ahali". Wannan furucin da yayi saida yasa Inna hawaye,gyad'a mishi kai ta iya yi domin ta tabbata tana bud'e bakin ta kuka ne zai kufce mata saboda tsananin tausayi daya bata, shima cike da farinciki ya mike yana share hawayen idon shi ya ce,"nagode Aunty Allah ya saka da alkhairi zan tafi sai bayan kwana 2 zan rink'a zuwa mu gaisa". Bai jira cewar Inna ba ya fad'a motan shi sai da yayi ribas sannan ya kira wani yaro ya bashi kud'i masu yawa ya ce ya kaiwa Inna ta,yaja motan shi ya fita a layin namu. Inna tana tsaye ta rasa ta ina zata fara tab'a kayan sai ga yaron da aka bawa kud'in yazo gaban ta ya mik'a mata kud'in ya ce," wai gashi inji wancan mai motan ya ce in baki" Wani yawu ta had'iye da kyar hannun ta na rawa ta karb'i kud'in a ranta tana ayyana anya wannan bawan Allah abinda ya fad'a gaskiya ne kuwa? Nan wani sashi na zuciyar ta ya ce mata tunda take bata tab'a cutar da wani ko tabi wani da mugun kulli ba insha Allah in ma da wata manufar yazo Allah ba zai bashi sa'a ba. Da wannan kwarin guiwan ta samu ta kira wasu matasa da suke zaune gefe tace su taimaka mata su shigar mata da kayan abincin ciki,ba musu suka fara jidan kayan domin suna ganin girman ta sosai. Su Gwaggo Aisha baki da hanci suka bud'e suna kallon kayan da ake wucewa dashi d'akin mu,bakin ya mutu murus sun rasa abin fad'a,nima ina nan a bayan k'ofa duk na had'a zufa naga a nata shigowa da kayan suna jerawa a gefe har suka gama suka fita ban fito daga mab'uya na ba dan haka basu san da mutum a d'akin ba. Suna gama shigo da kayan Inna ta basu 500 cikin kud'in hannun ta tace su raba,cikin farinciki suka karb'a tare da yi mata godiya suka koma wajan zaman su,hannayyen ta cikin hijabi ta shigo dan haka babu wanda yaga abinda ke hannun ta. "Hmmmm kun ga ikon Allah ko 'yan gidan nan gaskiya ta fito fili ga ribar boko nan mun gani yarinya 'yar k'arama an koya mata bin maza har gida ake biyo ta,Allah yayi mana tsari ya kare mana 'ya'ya".cewar Gwaggo Aisha kenan cike da hasada. Suma sauran kaman jira suke suka fara nasu kowa na fad'an albarkacin bakin shi, Inna ko kallon inda suke ba tayi ba ta shigo d'aki ta cire hijabin jikin ta tare da zama dab'as kan simintin d'akin mu dako leda babu tana kallon kayan zuciyar ta na bugawa,kud'in hannun ta ta shiga kirgawa taga dubu goma ne cif ta ajiye a gefe. Hango ni tayi a bayan k'ofa ina lek'en ta tace," ba zaki fito bane ko sai nazo na same ki" cikin sauri na fito ina goge gumin jikina,kallon tausayi tabi ni dashi ta san Allah bai bata haihuwa dayawa ba amma alhamdullilahi tana alfahari dani domin jumm'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake gane ta. Na zata zatayi min fad'a ko ta ce wani abu akai amma naji tayi shiru bata ce komai ba sai tagumi data zuba tana yawan ajiyan zuciya,da taga zaman ba zaiyi mata ba ta mik'e ta saka hijabi tare da yi min gargad'in kada in fita koda k'ofar d'aki ne kuma kar in kula kowa duk abinda zasu ce min. Bata jira amsa ta ba ta fita daga gidan zuwa gidan su wato gidan kakanni na da muke makotaka dasu,da sallama ta shiga. Kakata Ya Jalo da suke kira da Maa tana soya gyad'a na sayarwa ta amsa tana mata sannu da zuwa,bata gama suyar ba ta sauke gyad'an ta taso sanin cewa in taga kafar Inna ta a gida da dalili ne ya kawo ta duk da kasancewar muna makota basu bata daman zuwa gida any how ba. "Bintu komai da kike gani na duniya mai wucewa ne sannan kowa yayi hakuri zai ga riba a gaba dan haka bana son kina sawa kan ki damuwa ko kad'an ki cigaba da hakuri wata rana sai labari" cewar kaka ta kenan ganin damuwa karara a fuskan Inna ta,dama haka take mata kullum koda tazo da damuwar ta bata bari ta fad'a sai dai tayi mata nasiha tare da kwantar mata da hankali ta koma gida. "Nagode Maa Allah ya kara girma amma ba matsalan gida ne ya kawo ni ba akan Zareefa ne...." nan ta kwashe labarin Abdulbasit tun farko har zuwa yau da yazo ya tafi. Shiru kaka tayi tana tunani kaman na second 20 can ta d'ago ta ce," a yanda na fahimci maganan nan yaron nan bashi da aibu da gasken sa taimakon yake yi in da bashi da gaskiya a yanda kika ce yana da kud'i nan ba zai tsaya yi miki wannan dogon bayanin ba balle ya gaya miki asalin sa,in kuma da yana da niyyan cutar da ita da tuni ya cutar da ita dan haka ki kwantar da hankalin ki Allah ne ya dubi zuciyar ki ya kawo wanda zai taimake ku ke da 'yar ki cikin ruwan sanyi". Cike da gamsuwa maganan mahaifiyarta ta ciro kud'in ta bawa Maa dubu uku a ciki amma taki karb'a ta ce," ki bar shi ki had'a dana wajan naki ki saka Zareefa makarantan gaba kaman yanda kika ce". "Maa akwai saura ai zasu isa ki karb'i wannan d'in ki saka albarka" cewar Inna kenan. Dubu 1 kawai ta zara a ciki ta mayar mata da sauran tare da cewa," Allah ya sanya albarka". Sun d'an tab'a hira kad'an sannan tayi mata sallama zuciyar ta fari kal ta dawo gida. D'ari biyar ta cire ta bani a cikin kud'in tace inje in sayo naman miya harda kayan miya,cike da murna na fita a guje yau za'a dafa shinkafa a gidan mu kuma harda nama abinda ada sai sallah yake faruwa. Ina dawowa Inna ta fito ta hura wuta ta fara girki nan da nan ko k'amshin miyan ta ya cika gidan, Inna Asabe ce ta fara mita," oh in da ranka zaka sha kallo yanzu fisabillilahi wannan abinci da aka samu ta haramtaccen hanya shi za'a girkawa 'ya'yan mu su shi?" Ta karasa maganan tana kallon gwaggo Aisha ko zata ce wani abu. "Hmmm ni yara na ba zasu ci ba dama kowa ya san ni ba irin ku bace ina da abinda zasu ci nan wata ko 3 ne koda ace bana sana'a dan haka ku kuka sani" Gwaggo Aisha ta fad'i haka tana yiwa karamar 'yar ta da muke sa'anni da juna kitso wato Jameela. "Ke kuwa daga magana sai ki wani dawo kaina kina wani cika baki,meye naki bamu sani ba wallahi mun san inda Hajara take zuwa tallah da abinda yake tafiya wallahi duk mun sani, a toh kada a cika mana baki kuma ba'a karya kusa da gida" Inna Asabe take mayarwa Gwaggo Aisha magana cikin fushi dan taji haushin maganan da ta yab'a mata. Nan fa fad'a ya kaure ba abinda kake ji sai ifacce-ifaccen su suna zagin juna tare da tonon asiri kala-kala, sai Maman Dije ce da ta gaji da hayaniyar tasu tazo ta shiga tsakanin su sukayi shiru. Inna ta dai tana gefe tana aikin ta ko inda suke bata kalla balle tayi gigin raba su domin ta sha gwadawa a baya sai fad'an ya dawo kan ta data fahimce su sai ta kama kanta ta koma gefe ta zama 'yar kallo. Ana kiran sallah magariba Inna ta gama girkin ta duk da taji sun ce ba zasu ci ba amma haka ta nemo kwanukan kowa ta zuzzuba musu ta bani na kaiwa ko wacce d'akin ta suka bini da zagi da tsinuwa kuma wai inzo in d'auke tsiyar mu amma nayi musu kunnen uwar shegu domin Inna taja kunne na kan ina ajiye musu in juya in basa ci su bawa almajirai amma ni kar in d'auko. Sai bayan sallah isha'i Baban mu ya shigo dama ko girkin Inna tane baya shigowa d'akin mu bare yaci abincin mu dan haka Inna tana jin muryan shi tace in d'auki abincin shi in kai mishi. "Na'am" na cewa Inna ba tare da na shirya ba jin tace wai in kaiwa Baba abinci,sai naji abin wani banbara kwai. "Ki kaiwa babanku abincin shi nace" ta kara maimaita min,amsawa nayi na d'auki tiren abincin da Inna ta d'aura kwanon tuwo daban miya ma daba sai kofin silver mai murfi da ta zuba ruwan randa mai sanyi. A tsorace na nufi d'akin nashi ina jan k'afa dan na san karamin aikin shine ya koro ni da abincin,ba yanda na iya haka na karasa bakin k'ofan d'akin cikin rawan murya nayi sallama,da yake tsanan da yake min bana wasa bane nan da nan ya gane murya ta cikin tsawa ya ce," uwar me kike nema a nan?" "Inna tace ta ce in kawo abinci" na bashi amsa cike da fargaba. "Ita Bintu dan yau ta haukace shine zata aiko ki kawo min jagwalgwalo,kafin in kirga uku ki bar nan ko kuma in na tashi wallahi...." Ai ban bari ya karasa ba na jiyo cikin sauri Allah ya taimake ni babu kowa a tsakar gidan dan haka babu wanda ya ganni na shige d'akin mu. Inna murmushi tayi ganin na dawo da abincin ta ce," koro ki yayi ko?" Gyad'a mata kai kawai nayi bata kara cewa komai ba ta sauke min tiren akaina ta zuba mana namu muka fara ci abin mu. Saida naji ciki na barazan fashewa sannan na hakura da tura shinkafa da jan miyan da nake na kwashe kwanukan na fitar sai ga sauran yaran ma suna fitowa da nasu kwanukan suna ta tsid'e hannu su da iyayen su suka ce ba zasu ci ba. Ina dariya na koma d'aki nake bawa Inna ta labari ta kwab'e ni kan bata son surutu in nemi waje in kwanta,ba musu kuwa na kwanta kan shimfid'a ta cikin abinda bai kai minti biyar ba bacci yayi gaba dani. Da washe gari da sassafe Innata da ta tashi hura wuta tayi ta d'aura abin karyawa duka gidan abinda tun tasowa ta ban tab'a ganin anayi ba, spaghetti ta dafa mana harda kifin gongoni da take d'ibawa su kakata kayan a nan data bud'e wani kwali taga duka shine a ciki. Kamshin girkin yauma ya cika ko Ina har ta gama, tana gamawa ta samu tire ta zuzzubawa yaran gidan ta ce duk su zauna su karya iyayen su kuma a kwano ta zuba na kai musu suna ta cika da batsewa bakinciki kaman su mutu. Baban mu yazo fita kaman yanda ya saba yaga yara suna ta kai loman taliya baji ba gani wasun su kuma suna kokawa akan kifin da yake ciki. "Kai uban wa ya baku abinci da sassafen nan kuke mana hayaniya a gida" Baba ya tambaya yana kara matsowa kusa dan tabbatar da abinda idon shi ya gani gaskiya ne ko akasinta . "Innar Zareefa ce ta bamu" cewar Ibrahim d'an gidan Inna Asabe. "Jiya ma shinkafa da miya ta zuba mana harda nama" shima musa d'an gidan Gwaggo Aisha ya kara akai. Cike da mamaki Baban mu ya ce," ita Bintun ce tayi girki harda nama?" Yana magana ne yana kallon k'ofar d'akin mu. Fasa fitan yayi ya koma d'akin shi yana tunanin ta ina zai fara rarrashin Inna ta zuba mishi wannan kayan dad'in shima. [8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* Yin Kabbara tare Da Kowace Tsakuwa Yayin Jifan Jamra. Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana yin kabbara tare da kowace tgsakuwa idan ya jefi jamrori uku. Sannan sai ya yi gaba kadan ya yi addu'a yana mai fuskantar alkibla, ya daga hannayensa biyu yayin addu'ar. Yana yin haka ne bayan jifan Jamra ta farko da ta biyu. Amma bayan jamratul Akaba (jamra ta karshe), sai ya yi jifan kawai, ya yi kabbara tare da kowace tsakuwa, sannan ya tafi; ba ya tsayawa ya yi addu'a a wajenta. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *5* Baba ya kasa zama yayi a d'aki sai safa da marwa yake,sai yayi kaman zai kira wani kuma sai ya fasa can dai yaja wani dogon tsaki shi kad'ai yana," in banda b'atawa kaina lokaci nake ba ita Bintun yaushe har tayi wani abin kanta zan tsinka kaina gaban yarinya k'arama" yana magana ne shi kad'ai tare da neman hanyan fita. Ta gefen ido yake kallon yaran da suke ta buduri da taliyarsu bakin nan duk mai yasa kai ya fice. Yana fita teburin mai shayi ya tafi kaman yanda ya saba ya bayar da naira d'ari yace a bashi shayi empty na naira ashirin da bredi na hamsin,ana bashi canji akwai mai kosai a gefen mai shayin itama ya sayi na talatin a wajan ta ya samu waje a rumfar mai shayin ya fara karyawa. A da in yana cin wannan had'in ji yake kaman mai cin kaza amma yau sai yaji babu taste sam sai tuno taliyan nan daya sha mai da kifin gongoni yake,kaman dole haka ya rinka cuccusawa har ya gama ya tashi ba dan dad'i ba. A gida kuwa muna gama karyawa da Inna ta tace mu shirya ta kaini makaranta kada wani abu yazo ya fad'awa kud'in, Muna gama shiryawa muka kama hanyan ainihin makarantan mu na da wato *YERWA PRACTICE* akwai jss a ciki daga 1 zuwa 3, cikin ikon Allah komai yazo mana da sauki ba kaman yanda Inna ta zata ba domin kud'in registration da kud'in PTA duka dubu biyu suka karb'a,daga nan uniform,takalmi,jaka,takardu duk kyauta aka bani kuma principal yace gobe in fara zuwa domin har an fara karatu. Cike da farinciki muka kama hanyan gida, a hanya sai da mukayi 'yan cefanen mu da kud'in hannun mu sai dubu uku ya rage muka dawo da kaya niki-niki a hannu. Gwaggo Aisha tana yiwa Hajara fad'a a tsakar gida kasancewar Inna Asabe ma ta fita,tana ganin mu tayi shiru sai rarraba ido take alaman basu da gaskiya,mu dai bamu bi ta kan su ba muka wuce d'aki suka bi ledojin hannun mu da kallo. Muryan Gwaggo Aisha ya cika gidan tana yiwa Hajara masifan me take bata fito ta tafi tallah ba gashi har azahar tayi,na fito da buta a hannu na dan zagawa makewayi muka had'a ido da Gwaggo Aisha ta gallah min wata muguwar harara,niko dan in cusa mata bakinciki sai nayi mata dariya dama in ina son kullar da ita haka nake yi. Ai kuwa ta hau yanda ya kamata ta hau zagina harda Inna ta da bata san wainar da ake toyawa ba,ni kuwa ko a jikina na shige bayan gidan na kama ruwa na fito tsakar gidan na fara alwala ita kuma bata fasa zagin nawa ba,dana lura bata da niyyan dainawa nayi mata gwalo amma sai na fake da cewa Jameela da take kusa da ita tayi min nima na rama. Ban gama wanke d'ayan kafa na ba naga ta rarumo murfin tukunya da yake kusa da ita ta jefi ni dashi, Allah ya taimake ni kamin ya karaso na gauce nayi d'akin mu da gudu ina dariya. Had'iye dariyan nawa nayi ganin fuskar Inna ta babu alaman wasa ta ce," wai ke wace irin yarinya ce Zareefa,ban hana ki kula su ba ko akwai sa'ar ki a ciki,bayan haka duk matan Baban kine saboda babu abokin wasan ki a cikin su tsakanin ki dasu shine girmamawa". Jiki a sanyaye na ce ," kiyi hakuri Inna ba zan sake ba dama ni bada ita nake ba nida Jameela ne" "Naji ki kiyaye bana son neman magana" ban kara cewa komai ba na fara sallah na a zuciya ta kuwa banga zan kyale ta ba in ta min wannan shegen kallon tunda ba wani laifi nayi mata ba. Da yamma Inna ta fito tayi tuwan ta na shinkafa da miyan yakuwa da yaji biscuit bone da wadacaccen gyad'an miya, jin yauma kamshi ya cika gidan yara suka fara tsallen murna suna," yauma Innar Zareefa zatayi mana kayan dad'i" iyayen su na hantaran su amma basu fasa ba. Yauma d'aki nabi su da abincin ba wanda ya kalle ni balle inji sun ce basa cin abincin da aka same ta ta haramtaccen hanya. Da wuri yau Baban mu ya dawo gida tare da tsammanin an girka kayan dad'i irin na d'azu,yana saka kafa a gidan kamshin abincin ya mishi maraba wanda sai da ya had'iye yawu yana bin tsakar gidan da kallo,yaji tsit kaman babu kowa a gidan saboda kowacce tana d'aki da yaran ta suna kwasan gara. Da gangan ya d'aga murya wai dan Inna taji ta aiko mishi nashi ya hau fad'an an watsar da kaya a hanya amma aka rasa wanda zai kula shi. Yana nan tsaye yanayi Ibrahim d'an gidan Inna Asabe ya fito da kwanukan da suka ci abinci yana kokuwa da kashi tare da tand'e yatsu. "Kai zo nan,zo ka kwashe kayan nan" ya yafito Ibrahim da hannu yazo yasa hannu ya kwashi kwanuka guda biyu da suke gefe har ya juya zai tafi ya rike shi murya kasa-kssa ya ce," kai yauma Bintun ce tayi girkin" gyad'a mishi kai Kai yayi dan santin kashin ya hana shi magana. Maida hankalin shi yayi kan d'akin mu da muka sauke d'an yalolon labulen mu, juyawa yayi ya shiga d'akin shi ya zauna jiran ko yauma za'a kawo mishi. Ya kai kusan rabin awa zaune yana kallon k'ofa amma ko motsin mutum bai jiba balle yaga mutum,tsaki yaja a karo na ba adadi ya mike ya fito tsakar gida tare da kama hanyan waje,bukutin roba na Maman Dije da yake ajiye a gefe akai ya sauke haushin sa sannan ya fita,ji kake kararass ya fashe sakamakon harbi daya kaiwa bucket din da k'afa. Fita yayi yana ta zage-zage shi kad'ai dole ne yasan yanda zaiyi ya shawo kan Inna ta kamin girkin ta ya zagayo. Da washe gari ba girkin Inna ta bane d'an haka indomine ta girka min na karya dashi ta bani talatin kud'in tara na fita makaranta cikin tsantsan farinciki domin haka naga sauran yara ake musu nima yau anyi min. Sosai a ranan na mayar da hankali na nayi karatu tsabani da,karfe d'aya dai-dai aka tashe mu na kama hanyan gida. Tun daga zaure na fara jin muryan Gwaggo Aisha tana zagina tare da aibata ni ga dukkan alamu kuma Baban mu take fad'awa,a jikin bango na makure naki karasowa sanin halin Baban mu ya kware a rankwashi. "Munafuka daina kallo na da shegun idanunki kaman na mujiya" cewar Gwaggo Aisha tare da aika min mugun kallo. "Ke Aisha ba kya kula da lokacin daya kamata ki tari mutum da magana,ni yanzu a gajiye na shigo hutu nake nema" yana gama fad'a kuwa yayi hanyan d'akin shi ya shige ya bar Gwaggo Aisha baki bud'e. Kuyi manage ba yawa *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 500 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'a Idan Mutum Ya ga wani abu mai ban Mamaki, ko na farin ciki* سُبْحَانَ اللهِ! Subhanal-lah!. Tsarki ya tabbata ga Allah. اللهُ أَكْبرُ! Allahu akbar Allah ne mafi girma. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *6* Yanda Gwaggo Aisha ta bud'e baki ta kasa rufewa saboda mamaki kowa a wajan sai da ya wangale baki muka bi Baba da kallo har ya shige d'akin shi abin sa ko waigowa baiyi ba. Wata wawiyar Ajiyar zuciya na sauke na samun tsira daga rankawshin Baba, kasancewar a tarihin rayuwa ta yau shine karo na farko da Gwaggo Aisha ta kawo kara ta yaki fad'a ko kuma duka na dan haka cikin jin dad'i fuska ta d'auke da murmushi na wuce d'akin mu. "Ni kikewa dariya dan uban ki,toh ba dani kike ba da lusarar uwar ki kike " cewar Gwaggo Aisha cikin matukar fushi. "Ni wallahi Inna banyi mata magana" na fad'awa Inna cikin marairaicewa saboda ganin irin kallon da take bi na dashi. Kwafa kawai tayi ta cigaba da d'inkin hular ta da take,cire uniform na nayi na saka kayana na gida har mukayi sallah Gwaggo Aisha nata bala'in ta babu wanda ya kula ta sai can Inna Asabe ta saka baki. "Kema dai Aisha akwai ki da son surutu,kullum Mallam yana biye miki ya zane 'yar nan amma dan yau kad'ai ya fad'i haka kika tashi hankalin ki,ya kamata ki mishi uzuri ki...." "Eh lallai Asabe kike kowa kin samu kaina har ni kika kalla kike cewa ina son surutu saboda wuyan ki yayi k'wari, ba surutu nayi ba uban surutu nayi sai inji bugu ga uwa ta nan" tana yi tana kara matsowa kusa da Inna Asabe wai tana jiran taji bugu. "Hmmm Allah ya tsari gatari da saran shuka kema kin san inda kika baro ta bani ba" cewar Inna Asabe tana kawar da kai gefe. Wannan kalaman sun fi k'ona mata rai akan na farkon nan da nan taci d'amara da d'an kwallin kanta suka fara zagin juna,har baka jin me suke cewa tsabar ihun da suke. Cikin tab'e baki na kai loman abinci na baki na kalli Inna da hankalin ta yake kan hular ta naja tsaki na ce," ni wallahi ihun nan ya ishe ni har ciwon kai na fara ji". "Ina ruwan ki da ihun su ko akan ki suke" da sauri na girgiza mata kai. "Toh kiyi abinda yake gaban ki" da kai na amsa ina jin haushin su suna da daman suyi ta zagin mu son ran su suyi mana abinda suka ga dama amma ko da wasa ita Inna ba zata bar mutum ko d'an gulman su yayi yaji dad'i ba. Basu fasa ba sai da suka tsinci muryan Baba yana magana," ni ban tab'a ganin fitina irin wannan ba,mutum ba shida daman hutawa a gidan shi saboda bala'in ku,mtswww sai ku cinye kan ku na bar muku gidan tunda zama nawa ne ba kwa so" yana gama maganan shi yasa kai ya fice. Duk takaici ya gama rufe shi dama ya dawo gida ne ko zai samu d'an abin sakawa a bakin salati amma hakan ya gagara saima kara mishi tension da sukayi. Majalisan nasu babu dad'i yau yana gani kowa ya sayi abu kiri-kiri suke hana shi dan yau ba shida ko ta sayan soyayyiyar gyad'a ne. Inna Asabe ita ta hakura taja tsaki ta shige d'akin ta ya bar Gwaggo Aisha na cewa taji tsoro da ta tsaya mana taga yanda zatayi da ita. ************ Haka rayuwar gidan mu ya cigaba da tafiya babu wani canji saima kullum kara gaba yake na yanda suke mana a gidan,shi kuwa Baba bayan wancan girkin Inna daya fita yanzu tayi kusan girki uku amma ya rasa taya zaiyi ya shawo kan ta a rinka cin dad'in nan dashi. Kullum in Inna tace da girki tun daga zaure zaka fara shak'an k'amshi mai saka yawu tsinkewa,haka Baban duk magariba zai dawo yayi ta b'uda hanci yana shak'an wannan kamshin yana," ikon Allah wai yau Bintu ce ke irin wannan girke-girke a gidan nan,da zan samu shawo kanta har na aljihu zan samu kashh Allah kawo hanya" haka zai zauna yayi ta sumbatu shi kad'ai kuma kullum cikin tsammanin zai ganni da tiren abinci yake. Kusan sati na 2 kenan a makaranta hankali na kwance nake zuwa, Alhamdullilahi karatun ma yana shiga k'wanya ta sosai tsab'anin da,ko assignment aka bamu da kaina nake yi in na dawo gida. Makaranta yayi min dad'i sosai dan yanzu har k'awaye gare ni,na murmure nayi kyau na k'ara haske abina yo kullum sai naci nayi nak abina,wani lokacin na saka Inna ta zubo min abinci na in tafi dashi makaranta kasancewar yanzu banda mu cikin way'an da ake rabawa abincin makaranta daga primary 6 ne zuwa kasa mu kuwa yanzu muna j.s.s1. Abdulbasit tun ranan daya tafi bai k'ara dawowa ba yau kusan sati uku kenan,kayan abincin mu sun fara d'an yi k'asa kad'an saboda yawanci Inna in tayi girki ko ba ranan girkin ta bane sai ta zubawa k'ananan yaran gidan sun ci,albarkacin wannan abincin da suke samu sun daina mata rashin kunya ko iyayen su sun nemi suyi kememe suke k'i. Ko aike zatayi in ni ina makaranta har rige-rigen karb'a suke suyi mata hankali kwance. Ranan wani asabar bayan sallah la'asar ina zaune a d'akin mu ina duba English textbook na kasancewar yau babu islamiya ana auren wani Malamin mu Inna kuma tana gefe tana ninke mana kayan mu data wanke muka ji sallaman wani yaro a k'ofar d'akin mu Inna ta amsa tana tambayan waye ne,ya amsa mata da shine Alai gana yaron Yakura dama wani ne a mota yake k'iran zareefa a waje. Kallon Inna nayi da sauri zuciya ta tana bugawa kaman ta fito ina jiran inji tayi min fad'a amma naji tace inje mu gaisa ince itama tana gaishe shi amma kada na dad'e. Ni dai mamaki ya hana ni tashi dan sam bata tab'a gaya min yanda sukayi dashi ba dan haka ban san komai akai ba. "Wai bada ke nake magana ba" ta fad'a a d'an tsawa ce tana ajiye kayan hannun ta, jiki a mace na tashi na saka hijabi na na fita, tsakar gidan mu babu kowa sai k'ananan yara da suke wasa iyayen su sun tafi biki can gaba da layin mu. K'ananan kaya ne a jikin shi yau wandon jeans baki da riga t shirt fari sol sai takalmin sa shima baki yana tsaye hannayen shi duka biyu cikin aljihun wandon shi. Ina fitowa muka had'a ido ya sake min murmushin sa mai kyau ni kuwa had'a rai nayi ina turo baki na tsaya d'an nesa dashi kad'an. "K'anwata babu gaisuwa ne?" Ya tambaya yana murmushin. Cikin turo baki na ce," ina wuni" bana buka rik'e kayan ki tunda sai da na rok'a". Yace Shiru nayi bance mishi komai ba. "Bud'e seat d'in baya yayi ya ciro wasu manyan shopping bags guda uku yace biyu nawa d'aya kuma in bawa Aunty wai yana sauri ne shiyasa ba zai samu su gaisa ba kuma in bata hakuri yayi tafiya ne shiyasa taji shi shiru. Ido na cike da hawaye na ce," in na karb'a fad'a Inna ta zata min kuma aini ban san Auntyn naka ba ta ina zan kai mata" na karasa hawaye na zubo min. Murmushi yayi yana ," cry cry Baby,ke sam ba kya gajiya da kuka ne?" Nan ma ban kula shi ba ya cigaba," ammm Innar ki babu abinda zata miki saboda last time da nazo ita ta yarda in dinga zuwa muna gaisawa nd Aunty na kuma ba kowa bace Innar kice". Sai a lokacin naji hankali na ya kwanta duk da dai ban yarda da abinda ya fad'a ba. "Ki shiga gida ina jiran ki anan in tayi miki fad'an sai ki dawo min da kayan,kin ji ko?" Yace min ganin har yanzu ban yarda da maganan shi ba.qa Da toh na amsa mishi na d'auki kayan da kyar saboda nauyin su na shiga gida zuciya ta cike da fargaban me Inna zata ce. Kayan na ajiye ina kallon idon ta bayan na shigo da sallama ta amsa min. "Har ya tafi?" Naji ta tambaye ni. Da eh na amsa sannan na fad'a mata abinda yace sai banga wani tashin hankali akan fuskar ta ba saima cewa da tayi tana amsa gaisuwan shi. Cire hijabin nayi na koma kan takardu na na cigaba da abinda nake ba tare da nabi ta kan kayan da na shigo dasu ba. Sai da Inna ta gama abinda takeyi sannan ta bud'e jakan daya ce nata ne, turmin zani masu kyau guda 2 da lace guda d'aya sai kuma dubu ashirin a k'asan kayan ta gani. Shiru Inna tayi tana kallon kayan cikin wani yanayi na damuwa da tsoro,ita in ba dan Maa tace mata bakomai ba data taka mishi brick. A hankali kuma ta jawo nawan ta bud'e shima 'yar kantuna ne masu tsananin kyau da d'aukan hankali kusan su biyar riga da skirt biyu sai dogagen riguna biyu da kuma riga da wando irin wanda rigan yake sauk'owa har guiwa shi kuma guda d'aya da katon baby na a k'asan. Shima ta dad'e shiru tana nazari sanna ta bud'e na karshen, roban ice cream manya biyu da sauran tarkacen su biscuit da chocolates sai kaji gassasu har biyu suma a kulle a ciki. Yanzu kam tagumi ta zuba tana tunani anya akwai wanda zaiyi maka haka saboda Allah babu komai a zuciyar sa, zamani ya lalace dole tayi shakkan wannan al'amari. Sanin gidan babu kowa yasa tace inje in kira mata Maman Dije ince tazo yanzu dan Allah. Matan k'anin Baban mu ne,tun fil azal a wajenta Inna ta ke samun sauki dan ita babu ruwata da haukan su sai kishiyarta ce bakin su d'aya dasu Inna Asabe. Batayi nawa ko gardama ba muka taho tare amma sai Inna ta ta dakatar dani shiga d'akin tace inje inyi wasa zasuyi magana. Ina jin haka ni kuwa na fice daga gidan zuwa gidan kakata nayi zama na acan. Inna tun daga farkon had'uwa ta da Abdulbasit har zuwa yau ta bata labari tare da fad'a mata abinda Maa tace da kuma yanda ita hankalin ta yaki kwanciya akan lamarin,dubu ashirin fa banda sauran sayayya da yayi gaskiya abin abun dubawa ne. Bayan d'an nazari itama exactly kusan abinda Maa ta fad'a shi ta fad'a mata tare da cewa ta rike Allah ta kuma rike addu'a insha Allah babu abinda zai faru. Godiya Inna tayi mata tare diban mata kayan makulashen tace ta bawa yara karb'a tayi tana godiya ta koma b'angaren su. Ban dawo gida ba sai da Inna tasa aka kira ni sannan na dawo nan ma kayan makulashen ta d'ibarwa Maa tare da dubu uku tace in kai mata ince Abdulbasit ne yazo yau. Karb'a nayi na fita ina maimaita sunan a raina wai Abdulbasit ni dai ban tab'a jin suna haka ba sai yau. Maa kin karb'an kud'in duka tayi dubu d'aya ta d'auka tayi godiya na komawa Inna da kud'in ta karb'a tana zata je anjima da daddare da kanta wajan ta. Kayan makulashen Inna ta bani, ice cream d'in nayi ta sharba dan ya min mugun dad'i sosai duk da rabi da kwata sun narke amma abinka da baka tab'a sha ba sai naji kaman madara empty nake sha,sai da ya kare muka ci kazar mu mukayi nak abin mu ranan ko girkin dare ba muyi ba. Sai bayan sallah magariba sannan Inna ta nuna min kayan da Abdulbasit ya kawo min, aiko kaman in haukace saboda murna kayakin da ban tab'a tsammanin zan mallaka sai gasu har kala biyar duka nawa ni kad'ai harda Baby na. Da kyar na samu nayi bacci a ranan saboda murna ina rungume da Babyn nawa nayi bacci a ranan. Da washe gari da safe na fito ina share kofar d'akin mu naga Jameela ta fito dasu ledan alale da sob'o ta ajiye a wajan wanke-wanke tana kallon ido na tana murmushi irin su jiya sun ci kayan dad'in biki. Ban kula ta ba sai da na kwashe sharan da nayi sannan na shiga d'aki nima na fito da robobin ice cream da kuma takardan naman kaza da muka ci harda warwarewa yanda za'a ga kasusuwan cikin sannan na ajiye a wajan wanke-wanke nima inayi mata murmushi na koma d'aki karb'o omo da zanyi mana wanke-wanken. Da na karb'o omo sai da na d'auko Baby na na fito ina danna madannin jikin ta fara wak'an larabci,ina fitowa na tarar da Gwaggo Aisha tana leken inda na ajiye kwanukan mu. Dariya nayi na ajiye Baby na a gefe na fara wanke-wanke na hankali kwance,ina jin Gwaggo Aisha tana jan tsaki tare da cewa," karyar banza bayan mun san komai me za'a nuna mana. Tana magana ne tare da shigewa d'akin ta sai dai tana shiga naji suna rigima da Jameela wai a saya mata irin Baby na,tun tana rarrashi naji an kai mata maka ta tsala ihu tayi waje da gudu. Ko a ido ka kalli babyn ka san mai tsada ce shiyasa tayi mata haka domin bata da kud'in sayan shi. Ranan muna zaune a d'aki bayan magariba ana gobe Inna zata karb'i girki muka ji muryan wani abokin Baban mu yazo yana ta masifa kan wai Baban ya ranci kud'in shi naira dubu biyu bai biya ba, ashe tun bayan la'asar Baba yake gida ya kasa fita majalisa saboda bashin da ake bin shi bamu sani ba. Abu kamar wasa fitinan yayi girma dan ana ta bashi hakuri yace babu inda zai je sai Baba ya biya shi kud'in sa yau kusan wata 2 kenan ana abu d'aya kuma shi ya gaji da yanda Baba ke cewa yau ko gobe. Jakar kayanta Inna ta bud'e ta ciro dubu biyun tace min in kaiwa Baban mu,karb'a nayi na fito kai mishi ba dan raina yaso ba saboda shima baya tausayin mu baya nuna kulawa gare mu sai sauran 'yan gidan shiyasa nima banga dalilin da yasa zamu tausaya mishi ba. Sai dai ina zuwa saida na tausaya mishi,yana rab'e jikin k'ofan shi yayi abin tausayi shi kuwa mai bashi sai ci mishi mutunci yake, ga kanin Baban mu da muke kira da baffa shima sai hakurin yake badawa amma a banza Ina zuwa kusa dashi na tab'a shi ya d'ago ya kalle ni da idon shi daya canza kala, mika mishi kud'in nayi na ce," gashi inji Inna tace ka biya su kud'in. Baba kasa karb'an kud'in yayi ya tsaya kallo na haka sauran matan ma suka tsaya kallon kallo. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/3, 9:06 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp حَدَّثَنَا سَعِيدُ بْنُ مَنْصُورٍ وَقُتَيْبَةُ بْنُ سَعِيدٍ وَأَبُو كَامِلٍ الْجَحْدَرِيُّ وَاللَّفْظُ لِسَعِيدٍ قَالُوا حَدَّثَنَا أَبُو عَوَانَةَ عَنْ سِمَاكِ بْنِ حَرْبٍ عَنْ مُصْعَبِ بْنِ سَعْدٍ قَالَ دَخَلَ عَبْدُ اللَّهِ بْنُ عُمَرَ عَلَى ابْنِ عَامِرٍ يَعُودُهُ وَهُوَ مَرِيضٌ فَقَالَ أَلَا تَدْعُو اللَّهَ لِي يَا ابْنَ عُمَرَ؟ قَالَ إِنِّي سَمِعْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ لَا تُقْبَلُ صَلَاةٌ بِغَيْرِ طُهُورٍ وَلَا صَدَقَةٌ مِنْ غُلُولٍ وَكُنْتَ عَلَى الْبَصْرَةِ. *It was narrated from Simak bin Harb, that Mus`ab bin Sa`d said: "`Abdullah bin `Umar came to visit Ibn `Amir when he was sick and he said: `Won`t you supplicate to Allah for me, O Ibn `Umar?` He said: `I heard the Messenger of Allah (s.a.w) say: "No Salat is accepted without Wudu` (purification), and no charity (is accepted) that comes from Ghulul," and you were the governor of Al-Basrah."`* [ Sahih Muslim ] *7* Baban mu jikin sane yayi sanyi sosai, wai Bintu ce ta biya mishi bashi. Bayan duk abubuwa da yayi mata basu da misali bayan wa'yan da ya fifita duk suna tsaye babu wanda yayi gigin biya mishi alhalin suna dashi, more especially 'yar gaban goshin sa wato Gwaggo Aisha, ga Baffan mu duk suna wajen taya zai iya kallon idon ta nan gaba?. "Amma Mallam Hassan ka cika mugu azzalumi,wato yanzu a baka kud'in da zaka biya ni shine ka rike ka maida ni d'an iska wato inyi in gama ko? Allah ma yasa a gaba na aka aiko da kud'in da shikenan sai ka cigaba da raina min hankali kana cewa babu" yana banbani ya matso kusa da Baban mu ya kwace kud'in a hannun sa ya fita yana," Allah ya so ka Mallam". Da ido kowa ya bi bayan shi har ya ida ficewa, bai san cewa mamaki ne daya cakud'u da mutuwar jiki su suka hana shi bayar da kudin ba, bai kara kallon kowa a wajan ba ya koma d'akin shi ya zauna a bakin gado tare da rafka uban tagumi yana tunanin ta yayane zai shawo kan Bintu yaci dad'i kuma ya samu na kashewa, dubu biyu fa?. Can shi kad'a ya saki murmushin jin dad'i alamun ya samu mafita kenan. A waje kuwa Baban mu yana shiga d'akin sa Baffan mu shima ya bar wajan yana tab'e baki dan bai ga dalilin da zai saka ya biya mishi bashi ba, da ace wannan kud'in yayi amfani dasu wajan ciyar da iyalin shine zai iya biya amma tunda kansa kad'ai ya sani bai san hakkin daya rataya akan sa ba shi ya sani yaje can ya karata. "Allah sarki Bintu Allah dai yasa ba mugun halin kema kika fara kaman sauran matan ba saboda mugun halin d'an uwana duk shi ya jefa iyalin shi cikin halaka" yana magana ne tare da shigewa b'angaren shi. Gwaggo Aisha da Inna Asabe duk sun kasa barin wajen suna tsaye a wajan kaman wanda aka dasa su kowacce da irin tunanin da take a zuciyar ta saboda Abin ya mugun daure musu kai sosai ita da duk gidan itace wacce bata dashi amma yanzu ta dara kowa a gidan. Gwaggo Aisha fargaban ta d'aya shine kada Inna tazo ta kwace mata matsayi a wajan Baban mu domin ta san halin shi tsab zai iya juya mata baya dama saboda tafi kowa kud'i a gidan yake fifita ta, kai dole ne tayi wani abu akai dan ba zata tab'a zuba ido Inna ta ta kwace mata ba. Da washe gari ina dawo daga makaranta a nesa na hango motan Abdulbasit a k'ofar gidan mu, aiko da gudu na karaso wajan motan cike da murna dan yanzu na daina tsoro tunda Innata da kanta take cewa inje mu gaisa bayan haka ga kayan dad'i da kullum in zai zo yake kawo min, yana zaune a ciki motan amma kafafun shi a waje hankalin shi yana kan wayar shi ban san me yake dan dannawa ba. "Sannu da zuwa Yaya na" na fad'a da d'an karfi bayan na karasa kusa dashi,a d'an razane ya d'ago sai kuma ya saki murmushin sa mai kyau da baya barin fuskan sa. "Har kin tsorata ni saura kad'an in ruga da gudu" ya ce yana dariya. Nima dariyan na kyakyale dashi sannan na ce," toh ya zakayi da motan ka in ka gudu ka barta?" "Sai in bar miki ita ki rink'a zuwa makaranta dashi" toh ai ban iya yanda ake tukawa ba" na fad'a a shagwab'e. "Kada ki damu zan koya miki, kije ki cewa Aunty zan shigo mu gaisa". Da toh na amsa sannan na juya na shige gida da sauri na, su Hajara duk sun tafi tallah iyayen nasu ma ban gan su ba da alamu duk sun fita. Inna tana k'ofar d'aki tana shara na shigo da sallama ta amsa tana yi min sannu da zuwa,ciki na shige na ajiye jaka ta sannan na kara fitowa na ce mata," Inna Yaya yazo yana waje yace zai shigo ku gaisa". "Ciki nan zai shigo yace?" Ta tambaya da alamun tsoro da damuwa akan fuskan ta, gyad'a mata kai nayi ina kallon duk yanda ta zama wani iri. "Toh ya shigo" ta ce tana komawa d'aki ni kuma na fita waje na sanar dashi kan ya shigo, a bakin k'ofan d'aki muka tadda Inna zaune cikin tagumi amma tana ganin mu ta saki ran ta tana mishi sannu da zuwa. Kallon gidan namu yake tare da nazarin sa,har k'asa ya duka suka gaisa da Inna a mutunce tare da bata hakurin rashin zuwan sa akai-akai kaman yanda yayi mata alkawari, nuna mishi tayi babu komai kana ta d'aura dayi mishi godiya tare da addu'oin gamawa da duniya lafiya. Cikin jin dad'i yake amsawa da Ameen sannan ya mike yace zai wuce dai-dai lokacin kuma iska mai karfi ya d'aga d'an yalolon labulen mu karaf idon sa sai a d'akin mu da ko arzikin leda babu sai siminti dasu ghana must gon mu a gefe. Tare muka fito dashi har zuwa wajan motan sa ya ciro manyan jakuna na shopping daya saba kawo mana ya mik'a min sannan ya kara da kud'i masu yawa yace in bawa Inna ince ta sayi carpet na tsakar d'aki dasu gado. Cikin tsananin murna na dawo cikin gida da kaya niki-niki sannan na nunawa Inna kud'in daya bata tare da fad'a mata abinda yace tayi dasu. Karb'a Inna tayi ta ajiye gefe ba tace komai ba dan yanzu zuciyar ta ta fara amincewa dashi sannan ta fara sabawa da lamarin sa. Ni kuwa duk na k'ogu ta bud'e kayan domin na san duk tsaraba nane a ciki, tana bud'ewa kuwa sune ice cream da sauran kayan dad'i sai kaza gasassu biyu,ice cream na na d'auka na koma gefe na fara sha domin ni yafi min kaza sau dubu. Da washe gari Inna ta sayo mana carpet d'in mu maroon mai d'an karan kyau harda katifan mu da sabon labule, murna a waje na ba'a magana muma munyi katifa kaman sauran 'yan gidan mu, a ranan da kyar Inna ta kirani waje domin tarewa nayi akan katifan. A wannan rana mun ga hasada kiri-kiri a wajan matan gidan mu, Gwaggo Aisha tafi kowa shiga tashin hankali sai zage-zage take babu wanda ya kula ta sai 'yan koron tane suke taya ta. Babu abinda zan cewa Allah sai Alhamdullilahi saboda rayuwar mu ta canza sosai yanzu muci mai kyau mu sha mai kyau mu kwanta a waje mai kyau hatta suturar da muke sakawa ya canza albarkacin Abdulbasit. Mu muna nan zaune zuciya d'aya ashe bamu sani ba Gwaggo Aisha ta saka ana tayi mata bincike ta ina muke samun kud'i har rayuwar mu ta canza muka zama zara a cikin su. Bata sha wahalan samun cewa wani saurayi mai kud'i ne yake taimaka mana ba, daga wannan rana ta saka ido sosai tana jiran zuwan shi,cikin ikon Allah duk lokacin da zai zo bata nan sai dai taji labarin yau yazo ya tafi. A wannan lokacin Gwaggo Aisha duk yawon ta daina fita muka ga tayi a gida take wuni haka Hajara ma ta daina zuwa tallah kullum suna gida,ni na d'auka cewa sun daina tallah ne ashe wai ta gaji da kullum sai ta dawo daga gantalin ta taji cewa yazo har ya tafi shiyasa suka daina fita kullum hanya suke kallo suna jiran zuwan shi. Sun kai kwana biyar da shiga kullen nasu Abdulbasit yazo yanzu mun saba sosai ni dashi dan har tambaya ta yake abubuwa da nake so, ni kuwa in kirgo mishi in zai dawo ya kawo min. Ranan ma haka ya kawo min sautu da nayi mishi na kayan kwalliya shi kuma ya sayo min masu tsadan gaske kaman wata budurwa da kuma kayan makulashe daya zame masa jiki kullum zai zo sai ya kawo min, bayan ya gama zolaya ta na gama kuka na muka shirya na kwashi kayana na zan shiga ciki bayan nima na saba kullum in yazo sai na zolaye shi da in d'an b'uda murya ince," sannu da zuwa Yaya naaa". Sai ya juyo a d'an razane yace," kin tsorata ni zaki sa in fita a guce" sai inyi ta kyalkyalan dariya. A zaure na tarar da Hajara tana tsaye sai lek'e take ta sha kwalliyan ta na 'yan tallah fuska ya sha make up har yayi over. Tana gani na ta had'a rai ta tsaya ni kuwa da hankali na na kuruciya ban kawo komai a raina ba nayi shigewa ta ciki, tana ganin na shiga ta fito da saurin ta zuwa wajan shi domin har ya shiga motan shi ya tayar saura yaja. "Assalamu alaikum barka da war haka ya kyakkyawan d'an saurayi". Fasa jan motan yayi ya tsaya kallon ta da wani irin fuska sannan ya ce," meke tafe dake?". Juya ido tayi mishi irin na jan hankalin nan sannan ta ce," haba yanzu har sai nayi maka bayanin abinda yake tafe dani,me budurwa zata nema a wajan saurayi? Koda yake bari in fito in fad'a maka yanda zaka gane. Naga kana wahalar da kanka akan wancan 'yar karamar yarinya, bayan gani na had'a duk abinda kake nema zan saka ka farinciki domin babu abinda zaka nema a waje na ka rasa" ta karasa tana kara matsowa jikin motan tana girgiza mishi kirji. Kallon takaici da kyama ya bita dashi sannan ya ce," pls matsa min ka jikin mota kada kisa min k'azanta a jiki". Kasa matsawa tayi ta tsaya da idanuwa a waje tana kallon shi dan tunda take ba'a tab'a ci mata mutunci haka ba duk yanda taci kwalliya nan yace wai zata shafawa motan shi k'azanta , a firgice ta koma baya jin ya fisgi motan da matukar gudu saura kad'an ya take mata k'afa ya tafi ya bar ta a wajan. Da hawaye shame-shame ta shigo gida tun daga bakin kofa ta fara ihu tana magana," ni Gwaggo wallahi baki ga wulakaci......" Da hannu Gwaggo Aisha tayi mata alama da tayi shiru, kama hannun ta tayi suka shige d'aki. A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu har munyi exam na third term muna hutu in mun koma kuma zamu shiga j.s.s 2. Ranan nan muna wasa a k'ofar gida da kawaye na 'yan mak'otan mu naga Baban mu yana dawo wa gida ban kula ba dan shima ba kulanin yake ba kuma ya tsani in kula shi dan ma yanzu da sauki naga ya rage tsana da yake nuna min. Bulala naga ya d'auka yayi kaina gadan-gadan zai zane ni bansan hawa ba ban san sauk'a ba, da gudu na kwasa nayi cikin gida ban tsaya a tsakar gidan ba na wuce d'akin mu sanin cewa baya tab'a biyo ni, Inna tana raba gasassun kaji da Abdulbasit ya kawo na fad'a d'akin ina haki. Inna barin abinda take tayi ta kama min fad'an waye na tsokono zan fad'o mata d'aki haka? "Inna wallahi ba tsokana nayi ba muna wasa ne sai naga Baban mu....." Had'iye sauran maganan nayi ganin Baban ya d'aga labule ya shigo, bani ba har Inna sai da ta zaro ido tana kallon shi da matukar mamaki. "Ke yanzu Bintu haka ake tarbiyan 'ya mace yarinya ta fara girma amma ki bar ta tana wasa a waje sai kace namiji" yana maganan ne idon shi na yawo a d'akin har ya sauk'a kan kajin da suke gaban inna, mukut ya had'iye yawu tare da tsura musu ido shiri. "Toh Mallam ayi hakuri insha Allah za'a kiyaye gaba" tana gama fad'an haka ta ture tiren da kajin suke ciki gefe tare da rufewa da wani tiren. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/8, 5:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Abin da ake fada idan za a yanka dabba, ko za a soke ta.* بِسْمِ اللهِ واللهُ أَكْبَرُ اللَّهُمَّ مِنْكَ ولَكَ اللَّهُمَّ تَقَبَّلْ مِنِّي. Bismil-lah wallahu akbar, allahumma minka walak, allahumma taqabbal minnee. Da sunan Allah, kuma Allah ne Mafi Girma. Ya Allah! (wannan dabba) daga gare Ka take, kuma mallakarka ce. Ya Allah! Ka karba daga gare ni. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *8* Karasa shigowa d'akin Baba yayi tare da yiwa kan shi masauki kan katifan mu yana kallon rufaffen tiren ya ce," haba Bintu yanzu iya abinda zaki ce kenan, Fateema ta fara girma sai da saka ido sosai fa". Cike da mamakin furucin sa ta ce," naji Mallam za'a kiyaye gaba insha Allah" a zuciyar ta kuwa bata daina mamakin wannan sabon al'amarin ba domin ita dai tunda take a gidan bata tab'a ganin ya damu da 'ya'yan matan shi da yake so ba balle 'yar ta da kullum sai ya tsaya a tsakar gida yace ba son su yake ba shiru ne ya biyo baya a d'akin,ni ina can bayan Inna ta saboda tsoron bulala duk da ya ajiye ta tuntuni naki fitowa, ita kuma Inna al'ajabin me ya zaunar dashi har yanzu a d'akin take gashi tana so ta gama rabon kazan in kaiwa wayan da take bawa kullum. Mun kai minti kusan ashirin muna zaune shiru babu mai magana shi ya gaji da zaman kurame da muke ya d'an gyara zama yana kallon tiren ta gefen ido ya ce," naga kaman aiki kike Bintu dana shigo ko, toh ki karasa abin ki mana, in ta nine babu matsala Wallahi". "Haba Mallam ba haka bane na riga da na gama ne shiyasa". Ta amsa mishi. "Kin gama, me kika gama?" Ya tambaya tare da kafe tiren da ido. "Rabo nake kuma na gama saura in bawa Zareefa ta kai" Inna ta amsa mishi cikin k'osawa da zaman nashi a d'akin. "Toh su waye kuma zaki aikawa?" "Maman Dije da Maa saboda sunyi yawa ga Zareefa ba ci take ba shiyasa nake aika musu". "Ikon Allah amma Bintu kina da abin mamaki, ya za'ayi ki aikawa wasu alhalin ga 'yan gida nan, ko kin manta da nine?" Cike da takaicin halin sa ta girgiza mishi kai sannan ta d'auko wani d'an gutsuri kad'an ta mika mishi jiki na rawa ya karb'a ya fara ci yana," kai amma Bintu baki da dama yanzu haka kike cin dad'i kuma ki manta uban 'yar ki?" Ita yanzu inna halin nashi tsoro ya fara bata ya za'ayi kana magidanci mai iyali baka damu da ka samu ka kawo musu ba sai dai in ka gani a wajan su jiki na rawa ka karb'a, dubi yanda yanzu jiki na rawa yake neman a bashi kaza bai damu da tambayan a ina kika samu ba, sata ko maita ko karuwanci duk kiyi in dai zaki bashi to kece ma 'yar gaban goshin sa. "Dama da yunwa na shigo kin ganni nan har wani juwa nake gani, Allah yasa da akwai abinci d'akin nan" yace yana faman tsid'e yatsu. Girgiza kai Inna tayi sannan ta ce," babu abinci Mallam ba muyi girki ba sai...." "Inna ki bashi nawa da kika ajiye min yaci dan ni nasha ice cream ba zan ci ba". Na katsewa Inna hanzari. "Yauwa 'yar albarka, Allah sarki yarinya mai tausayin Baban ta" Abba yace cikin jin dad'i yana washe baki. Inna tsuke fuska tayi tana jin kaman ta kamo ni tayi ta kirb'a sai yau ya san dasu a gidan a baya in ta aika mishi abinci kora ta yake hmmmm sai yau, ba dan taso ba ta tashi ta d'auko mishi hadaddiyar warmer sabuwa da ta sayo mana muke zuba abincin mu a ciki ta ajiye a gaban shi. Cikin sauri Baba ya bud'e warmer, ba shiri ya lumshe ido saboda kamshi mai dad'i daya bugi hancin sa, yana bud'e ido sai da ya had'iye wani yawu ganin shinkafa da miyar kaza , ko ruwan wanke hannu bai nema ba ya tsoma hannu ya fara aikawa cikin sa hannu baka hannu kwarya. Ni kuwa duk dad'i ya cika ni yau muma Baban mu ya shigo d'akin mu kaman sauran 'yan gida har yaci abincin mu tsab'anin Inna da duk zaman shi a d'akin namu ya takura ta saboda bata saba ba kuma ta san ba wai matsayin ta da yake kiran ta dashi a baya ba son ta yake bane ya canza a'a sai dan kwad'ayin abin hannun ta wanda ita kuwa ba zata so ya shiga jikin ta b sam.. Yana cikin cin abincin naje inda Inna take ajiye min juices da bobo na d'auko mishi orange juice na ajiye a gaban shi. "Ikon Allah shi kuma menene wannan 'yar albarka?" Ya tambaya cikin matukar farinciki. "Lemon kwali ne Baba" na bashi amsa nima cikin jin dad'in sabon sunan da yake kira na dashi. Balle murfin yayi ya kafa kai ya fara sha bai sauke ba sai da ya kusan shanyewa sannan ya ajiye yana tsid'e baki ya ce," wai..wai...wai.... Ikon Allah wai lemon kwali kika ce ko?" Ya kara tambaya bayan ya d'auko katon chicken breast a cikin abincin ya fara figa. Ina dariya na amsa mishi da " eh Baba" Inna dai ko kallon mu batayi ta cika tayi fam jira kawo take ya fita tayi magani na. Baba bai bar d'akin ba sai da ya gama cinye abincin harda lashe warmer sannan ya mike yana kallo na ya ce," 'yar albarka kada ki manta da Baban ki, ki rinka tunawa dani in kin samu kayan dad'i kinji ko?" Cikin jin dad'i na amsa mishi sannan yayiwa Inna sallama ya fita. Yana fita muka ji muryan Gwaggo Aisha tana shewa ta ce," ahaiyye nanaye yau me nake gani jama'a kuzo ku tayani duba ko dai ido na ne yake min gizo?" "Ba gizo idon ki yake miki ba nine nan Mallam Hassan kuma daga d'akin Bintu na fito ko kina da magana ne?" Baba ya b'ata amsa yana cire nama daya mak'ale mishi a hakori. A yanzu yana dai-dai daya b'ata da kowa a gidan in dai akan Bintu ne, haba yaushe rabon daya ci kaza ko shinkafa da miya ita in banda aukin shinkafa da wake me take bawa mutum ko naira d'ari ko d'ari biyu amma ga Bintu kwanaki bashin dubu biyu ta biya mishi a take,gaskiya dole ne ma ya mak'ale a wajan ta. Yana gama bata amsa yasa kai ya fice abinsa ya bar Gwaggo Aisha da ihu tana," aikin banza aikin wofi wato ta nan kika biyo dad'in abin kowa ya san dai sunan ki a gidan nan ba sonta nake ba, shine dai sunan ki". Inna tana jinta bata tanka ba saima kamo ni da tayi zata daka akan abinda nayi Allah ya taimake ni ya jefo Maman Dije ta kwace ni tare da nuna mata kada tayi haka saboda koma ya yake ba'a tab'a canzawa tuwo suna ba, duk abinda zasuyi suyi tsakanin su amma kada ta sakani a ciki. Da wannan nasihan Maman Dije na tsira ba'a jibge ni ba. Tun daga wannan rana Baba ya maida d'akin mu wajan hiran sa duk da yanda Inna take tsuke fuska baya damun sa in dai zai shigo ya samu abin tab'awa, ni kuwa duk dad'i ya cika ni yanzu Baba na shigo mana kuma ya daina hantara ta saima sabon suna daya lika min wai 'yar albarka. Inna kuwa duk rawan kafar da yake yi akan mu ba wani burge ta yake ba domin ta san dan abinda yake samu shiyasa har yake ihu da 'yar lelen shi wato Gwaggo Aisha, ta ina ma zata manta abubuwa da yayi mata na shekara da shekaru dad'in bakin sa na lokaci kad'an d'in nan ba zai tab'a goge tabo dake cikin zuciyar ta ba. Abin takaici ma har yau bai tab'a yunkurin tambayan ina Inna ta ya take samun kud'i da har take wayan nan abubuwan ba, kuma wani ikon Allah bai tab'a had'uwa da Abdulbasit ba dan haka bai san daga inda muke samun kud'i ba. Tsakani na da Abdulbasit kuwa wani shakuwa ne na ban mamaki ya shiga tsakanin mu ada yana kaiwa sati ko fiye kamin yazo gidan mu amma yanzu baya iyawa dan ana kwana 2 zai zo mu sha hiran mu yana sai dai mafi yawan hiran tsokana ta yake wai ya ganni da saurayi da sauran su ni kuwa insha kuka na in more daga baya kuma mu shirya abin mu ya tafi. Rayuwa yanzu tayi mana dad'i sosai dan bamu da maraba da masu kud'i tunda duk abinda masu kud'in suke ci suke sha suke sakawa muma haka ni da Inna ta duk mun murmure harda d'an kumatu mukayi. Gwaggo Aisha da Inna Asabe kuwa duk hankalin su a tashe yake ba ma kaman Gwaggo Aisha dan kiri-kiri ta rasa matsayin ta ya koma kan Inna tayi duk abubuwa da zatayi amma duk a banza dan gwara da yana d'an sauraron ta amma tunda ya shigo d'akin mu ranan ya tarar da Inna tana kirga kud'i sun kai kusan dubu hamsin a hannun ta tun daga wannan rana ya kara haukacewa kasancewar ko shi da yake d'a namiji bai tab'a rike irin wannan kud'i ba. Ganin duk ya rikice yasa Inna ta bashi dubu biyar a ciki a ranan kaman yayi mata sujada haka ya kwantar da murya yana mata godiya. Daga wannan ranan mulkin gidan ya koma hannun Inna ta dan Baban mu ya zama kaman wani bawan ta duk abinda tace baya musu balle ya karyata ta cin mutuncin kowa yake a gidan saboda mu. . Mun koma makaranta mun shiga jss 2 cikin farincikin sabon uniform da Abdulbasit ya d'inka min dasu sabon jaka da sauran kayan amfani na makaranta, tsab dani na koma kowa ma sai sha'awa ta yake masu tsokana ta da kuma yanzu sune suke bi na wai suna sona da k'awance. Na biye musu nima duk abinda na kai makaranta na kayan kwalama ina basu ko in sun ce in saya musu wani abu bana kyashin saya musu amma fa ba wai na manta abinda suka min bane sai dai na barwa Allah ne. A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu muna jss 3 komai na alamun girman 'ya mace duk sun bayyana a tare da ni kyawu na ya fito sosai, shakuwa da yake tsanani na da Yaya na ya rikid'e ya koma zallan soyayya, dan sosai yake nuna min abinda ke cikin zuciyar shi tun ina had'awa da kuruciya har ni da kaina na fahimci na fad'a son Yaya na sosai kullum zai zo mu sha hiran mu da kyar zai daure ya tafi, daya ga hakan ma ba zai wadatar dashi ba ya sayo min dankareriyar waya ta wanda kullum ya kasance muna cikin communicating. Wannan waya da Yaya na ya saya min gaba d'aya ya d'agawa Gwaggo Aisha da Hajara hankali harda Jameela wacce take ganin sa'anni muke da ita. Ban san ko ta yaya abin ya kasance ba sai dai gani nayi itama wani mai mota yana zuwa wajan ta hira, daga ranan da mai motan ya fara zuwa a ranan ta sallami duk sauran samarin ta dan dukan su babu mai mota a cikin su dama lallab'a su take. Tun daga wannan rana su Gwaggo Aisha suka fara d'aga murya a gidan komin kankantar abinda ya kawo mata sai an fito tsakar gida ana maimaitawa ana yi mana iyayi a gida, mu dai ko a jikin mu amma Inna Asabe duk ta damu dan tana da 'ya Hasiya kuma sa'ar Hajara ce, Allah ya jarabce ta da bakin jini babu wanda ya tab'a zuwa wajan ta . Yawanci Yaya na in zai zo wajena sai bayan la'asar yake zuwa kuma Baba baya zuwa gida a wannan lokacin amma a yau bayan azahar yazo saboda wai zaiyi tafiya amma ba dad'ewa zaiyi ba gobe zai dawo, muna cikin hira na hango Baba ya nufo gida sai gyara binjimar jikin sa yake, dum naji zuciya ta ta buga dan daga ni har Inna ta bama son Baba ya had'u da yaya na dan zai iya tafka abin kunya dan shi ba damuwar shi bane. Motan yabi da ido ya gan mu tsaye a gefe kaina a kasa dan bana son yayi min magana amma banyi nasara ba. Yana gani na ya nufo inda muke cikin sauri yana," a'a 'yar albarka kece anan?" Kamin in bashi amsa Yaya na ya durkusa har kasa ya fara gaishe shi, cikin washe baki yake amsawa yana bin katuwar motan shi da kallo . *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/17, 9:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'ar Wanda Ya ji Tsoron Faruwar Wani Abu Mummuna saboda Kambun Baka* Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Idan dayanku ya ga wani abu da ya kayatar da shi ga dan uwansa, ko ga kansa, ko ga dukiyarsa, to ya roki Allah ya sanya albarka gare shi; domin kambun baka gaskiya ne. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *Kuyi hakuri kunji ni shiru kwana biyu kun san jiki da jini sai a hankali amma yanzu Alhmdllh naji sauki, wayan da suka kira da wayan da suka turo sakonni duk ina godiya da kulawar ku Allah ya bar kauna. Nagode sosai*😘😘😘 *9* "Lafiya lau yaro.... lafiya lau" Baba ya amsa yana had'iyar yawu yana kara karewa motan kallo, ni dai sanin zai kwafsa min yasa ko d'ago kaina na kasa yi bare mu had'a ido da shi. Yayana kuwa yana gama gaishe shi bai d'ago daga tsugunen ba yayi kasa da kai yana jiran Baba ya bar wajan, Baba ba dan yaso ba yaja kafa zuwa cikin gida yaso ya samu wani abu wajan mai tsallen motan nan, amma ba komai bari yaje wajan Bintu zai ji ko wanene shi d'in. Wata b'oyayyen ajiyan zuciya na sauke ganin ya wuce gida salin-alin ba tare da yayi wani abu daya tsinka ni ba, nabi bayan shi da kallo kaman yanda shima Yaya na yabi sa da kallo sai faman gyara mayattacen binjimar sa ta tshohuwar shaddar sa fara ce amma saboda tsufa har ta koma ruwan toka . "Allah sarki Allah baiyi zamu had'u da Baba ba duk shekaru nan ba sai yau" naji Yaya na ya katse min tunanin da nake. Murmushi nayi ina gyada kaina. "Amma nima ban kyauta ba da ban tab'a tambayan shi ba all this while,wallahi yanzu dana gan shi sai naji ban kyauta ba sam" ya kara fad'a cikin damuwa sosai. "Laa! Kada ka damu Allah ne baiyi zaku had'u ba tun farkon amma yanzu daya so ba gashi kun had'u ba" na bashi amsa ina murmushi. Shiru kawai yayi dan shi a tunanin shi rashi da iyali ne yayiwa Baban yawa shiyasa ya zama haka bai san cewa duk wani yanayi da hali da mutum zai gan shi a ciki shi ya jefa kan sa ba. Har muka gama hiran mu a ranan yana cigaba da nuna min rashin jin dad'in sa ni kuma ina nuna masa ba komai da zai tafi dubu ashirin ya bani wai in bawa Inna ta ajiye min in case wai ko goben ba zai samu dawowa ba, na nuna mishi muna da komai ba sai ya bani kud'i ba amma yaki karb'a saima shopping bags daya maida farilla wajan kawo min su ya lodo min kusan su 3 yana complain wai dole ya nemawa inna fridge ko dan saboda rana irin ta yau, kasancewar na saba kullum sai ya kawo min ice cream na sha toh gashi gobe baya nan da Inna tana da fridge sai ya sayo dayawa a saka min a ciki ko na kwana nawa ne. Amma tunda ya bani 'yan canji a hannu in naga ba zan iya hakura ba sai inje today's ko sidis in sayo abina in sha tunda na saba sha. Ni dariya nayi ta masa ganin duk ya damu akan wai kawai ba zan sha ice cream gobe ba, in ba dan ba dan ba a da ina na san wani ice cream a rayuwa ta, dan gobe kad'ai ban sha ba me zai same ni, bai kyale ni.ba sai da nayi masa alkawarin zan je in sayo a today's d'in sannan ya hakura mukayi sallama ya tafi tare da bani hakurin inda zai tafi babu service dan haka ba zamu waya kaman yanda muka saba ba. Haka ya wuce duk sai naji na damu domin sosai na saba kullum sai naji muryan shi nake iya bacci yanzu haka muryan sa shi ke tada ni a bacci. A tsakar gida na tarar da Gwaggo Aisha da wata 'yar figaggiyar kaza guda d'aya ta saka a tire ta d'auko sharb'eb'iyar wuka sai faman kacan canawa take tana ta hura hanci,ni dariya ta bani ban ma kalli inda suke ba nayi shegewa ta d'akin mu anan na iske Baba yana zaune yana zaman jiran in shigo yaji karin bayani dan duk yanda yaso ji Inna kin bashi had'in kai tayi saboda ta san ba dan Allah yake neman sanin ba. "'Yar albarka har kin shigo kenan" "Eh Baba sannu da hutawa" na amsa ina ajiye kayan hannu na kusa da Inna amma kud'in yana hannu na cikin hijabina. Ko kallon kayan Inna taki yi ta cigaba da d'inkin hulan ta hankali kwance, gefe na samu na zauna shima Baba zama ya gyara yana jiran Inna ta bud'e yaga menene a ciki amma ta basar, can daya gaji da zama ya ce," 'yar albarka me kika shigo mana dashi ne?" "Kayan dad'i ne Baba na" na bashi da murmushi akan fuska ta ina kallon Inna ta gefen ido da take harara ta. "A'a toh...toh... Wato Bintu yau kuma rashin kirkin ne ya tashi muna ji muna gani zaki hana mu kayan dad'i?" Cewar Baba cikin raha, Inna dai bata ce k'ala ba ta cigaba da d'inkin hulan ta. "Mu kam bama zuciya kuma ba inda zamu je sai mun ci kayan dad'i ko 'yar albarka?" Dariya nayi ina kallon Inna da tayi kicin-kicin da fuska dan ita al'amarin Baban mu sosai yake bata takaici da haushi, ya za'ayi ace wai kana ganin 'yar da ka haifa ta shigo da kaya masu yawa haka kuma kasan daga hannun saurayi ta samu, baka damu da binciken waye shi ko kuma ya akayi ya bata ko meye tsakanin su ba, saima jiki na b'ari kake son handame abinda ta kawo koma menene kai ba damuwar ka bane. Cike da takaici halin sa da surutan sa daya ishe ta, ta bud'e d'ayan jakan da ta riga ta gane tambarin su kasancewar kullum ana kawowa, ba tare da ta lura da ko kaza nawa ne a ciki ba ta d'auko guda d'aya ta saka mishi a wata leda da babban roban juice d'aya duk ta had'a ta mik'a mishi . Ba batun fushi ko zuciya yasa hannu yana washe baki ya amsa har zai fita na tsaida shi nima na jawo d'ayan jakan sanin cewa nawa shi saboda kullum aka kawo Inna bata tab'awa tarkacen kayan zaki na ne a ciki, roban ice cream babba dasu chocolate dasu snacks ne a ciki nima na cika mishi leda na mika masa harda dubu biyar na saka masa a kasan ledan bayan na faki idon Inna. Ai Baba yanda kasan yayi hauka haka ya koma saboda murna dan akan idon shi na had'aa mishi kud'in yayin da Inna kuma hankalin ta yana kan hulan ta saboda dukkan mu haushi muke bata. Fita yayi yana baza babban rigan shi, zai wuce Gwaggo Aisha ta tare shi da cinyar kaza a hannu cike da jin kai ta ce," Mallam tsaya ka saka albarka kaga 'yar ka Hajara Allah yayi ta samu saurayi mai mota, shine daga zuwa zance ya kawo mata gashasshiyar kaza na rabawa yara shine nace bari kai ma in kawo maka ka saka albarka". "Amma Aisha kike kowa? Wallahi kin matukar raina ni, ni zaki tara ki tsamma wannan abu sai kace kin samu wani kwadayayye ko maye, toh tsaya kiji ni na fi karfin wannan abin naki mai kama da cinyar fara. Dubi kiga inda ake cin arziki da kaza kuma aka san darajan miji ba watsatsu irin ku ba" yana magana yana nad'e hannun babban rigan sa nan manyan ledojin suka bayyana. " Kinga wannan dakwaliyar kaza ce ta gidan gona da taji gashin inji ga lemon roba mai dad'in gaske, sannan kinga nan kuma kayan makulashe ne da sai in rantse da Allah ko wuka aka d'aura miki baki tab'a ganin irin su ba balle ki san sunan su, bayan nan kalli kasan kiga" yace yana nuna mata kud'in kasan ledan sannan ya mike tare da mai da komai cikin ledan ya cigaba da masifa," na dai gaya miki kada ki kara tare ni da maganan banza ko ranki yayi mugun b'aci ba abinda kika iya sai shegen surutu tsiya " nan ya shige d'akin shi ya bar Gwaggo Aisha da mataceccen jiki. Tabbas sai sun sake shiri babba ma kuwa dan bata tab'a sanin haka Bintu tayi nisa ba,gaskiya dole ne ta nemi shawaran aminiyar ta dan samun mafita ko kuma suna ji suna gani wankin hula zai kai su dare. Dariyan yaran gida ne ya dawo da ita hayyacin ta, sun had'a kai kusan su biyar suna mata dariyan yanda Baba ya bar ta da cinyar kaza a hannu, bata kula kowa a cikin su ba ta shige d'akin ta dan ji tayi gaba d'aya jikin ta ya mutu. A d'aki kuwa Baba yana fita Inna har ta juyo da niyyan yi min fad'a dramar su da Gwaggo Aisha ya dakatar da ita, bayan sun gama ya wuce ya bar ta na ce," haba Inna ta, me yasa kike fushi haka yanzu fa kin zama 'yar lele a gidan Mallam". Waje na fice da gudu da roban ice cream d'ina d'aya a hannu ina dariya ganin Inna ta shiga neman abinda zata buga min a kusa da ita bata samu ba. Ciki na shiga b'angaren su Dije muka zauna sha muna hiran Yaya ina bata labarin yanda yau muka rabu da juna dan kawai zaiyi tafiyan kwana d'aya. "Hmmmm gaskiya ke kam Zareefa Allah ya baki, ki ga yanda yake mutuwan son ki kuma yake nuna kulawa yake tarairayan ki, a gidan ku ma ya kula dake haka ina ga ya aure ki ya killa ce ki a gidan sa abin ba magana". Cewar Dije kenan. "Allah gaskiya soyayya akwai dad'i Dije, kin san yanda nake jin sa a cikin raina kuwa? Allah ya nuna min ranan auren mu" duka Dije ta kai min a gadon baya na tana dariya tace. "Shegiya Zareefa har nawa kike da zaki zauna kina maganan aure?" Murkud'a mata baki nayi ina ," eh d'in kema ai shirin yi miki ake nan da shekara d'aya idan munyi sauk'a, toh nima ina gama secondary shekaru biyu da rabi suka rage za'ayi mana ni da Yaya naaa" na karasa ina rungume hannye na biyu a kirji na tare da rufe ido nayi baya kaman zan fad'i Dije ta taro ni tana tafa hannu ta ce," ke yarinyan nan haka kika zama baki tafasa ba zaki kone mana mu shiga uku?" "Wai da kike fad'an haka shekaru nawa kika bani da kike ta cika baki tun d'azu , ina biyu ne kawai harda wani ........ zaki kone mu shiga uku" na fad'a cikin kwaikwayon muryan ta, ta kai min duka na goje haka muka cigaba da shan ice cream muna hiran mu cikin raha.. Dije itace babban 'ya a wajan Maman Dije ta bani kusan shekaru biyu amma hakan bai hana mu zama kawaye ba domin yaran gidan dukan su iyayen su sun hana su wasa dani tun muna yara dan haka babu wani shakuwa ta 'yan uwan taka tsakanin na dasu sai dai kallon kallo. Ba Yaya na kad'ai ba nima na shiga damuwa sosai na rashin sa a kusa da ni, cikin kwana biyu da yayi baya nan duk sai na zama kaman ba ni ba abinda yafi tayar mun da hankali rashin samun sa a waya, duk da ya gaya min inda zai tafi ba service amma hakan bai hana ni kwana da waya a hannu ina gwadawa ba, Inna tana ankare dani amma bata ce min cikan ki akai ba. A ranan da ya cika na uku ne kiran shi ya shigo min yana fara ringing na d'aga cikin d'auki na ce," wayyoo Yaya naaa" "Na'am k'anwa taaaa" shima yaja kaman yanda nake jan nashi. Dariya muka sanya dukkan mu sai da mukayi mai isar mu kaman sabobbin kamu sannan ya ce," na kusan shigowa gari k'anwa ta, insha Allah gobe war haka muna tare" Tsalle na daka da wayan a kunne na na ce," yessss Alhamdullilahi Allah ya shigo da ku lafiya Yaya na" da Ameen ya amsa sannan ya katse kiran. Dije da take gefe tana min dariya tare da min signal ga Maman su a kusa inyi a hankali ko kula ta banyi ba, ita kuma Maman Dije murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta shige kitchen d'in ta ta kyale mu tana mamakin wai yarinya kamata da iya soyayya, hmmm duniya kenan in da ran ka zaka sha kallo. Zama nayi tare da rafka tagumi ina tunanin ya kamata nima ko sau d'aya ne in kyautata mishi yanda yake kyautata min kullum ko ba komai shima zai ji na damu da shi. "Ke kuma lafiya, ba yanzu naga kina murnan masoyi zai dawo ba kuma inga kin zabga tagumi kina tunani kaman wacce akaiwa mutuwa?" Cewar Dije kenan. "Dije kawai so nake inyi wani abu da zai faranta ran Yaya na tunda bai tab'a tafiya ba shiyasa nake son inyi wani abu na tarban shi". "Gaskiya kinyi tunani mai kyau Zareefa in dai akwai kud'i a hannun ki ni zan taya ki ko abinci ne kiyi mishi". Cikin jin dad'i na amsa mata da akwai kud'i a waje na, nan da nan muka tsara yanda zamuyi da abinda zamu girka masa. Da washe gari tare muka je kasuwa muka sayo doya da nama sai kwai creast d'aya da mai muka dawo, gidan Maa muka kai kayan da muka sayo da taimakon Dije mukayi mishi yam balls da kwai cikin kwai da yake shine sana'an da suke ta kware sosai, Maa kuma tayi mana dambun nama mai dad'in gaske. 'Yan kulolli da Inna ta fara min tarun su nan gidan Maa na fito da set d'aya muka zuzzuba a ciki muka shirya a cikin tiren plastic mai kyau shima cikin kayan tarun muka d'auko. "Kinga yanda kayan nan sukayi kyau kuwa kuma sunyi dad'i da zamu had'a da kunun aya mai sanyi zai fi tafiya" Dije ta kawo sabon shawara nima ba b'ata lokaci na amince sanin yanda shima Dije ta kware da yin sa shima suna sayarwa amma a lokacin zafi. Da yake mu biyu ne bamu b'ata lokaci ba shima muka had'a ta muka zuba jug na glass haddade muka saka kankara, ni sai a ranan ma nasan na san cewa Inna tayi min taru dayawa haka, sai da muka gama tsab sannan muka wuce gida dan inyi wanka in shirya ita kuma Dije zata fita sana'a ta. Sai da na shigo Inna ta rutsa ni da tambayoyi ina naje tun dazu? Na amsa mata da ina gidan Maa tace karya nake bata yarda ba ta kira yaro ina gani ta tura gidan Maa dan a tambayo mata ni dai na shige wanka dan ina gudun kada Yaya na ya dawo ban shirya ba. Ko da na fito daga wankan bata kuma kula ni ba da alama an tambayo mata Maa,sai da nayi sallah naci ado na da riga da skirt na lace pure cotton dark blue ya sha adon flowers pink, sosai kayan suka min kyau domin Yaya na ya iya zab'en kayan da zasu yi min kyau. Inna duk tana kallon sabon falli da nake bata min magana ba sai da na gama sannan ta zaunar da ni ta fara min nasiha kan rike mutunci na na 'ya mace a duk inda nake, duk da ta amince da Abdulbasit amma tace kada in kuskura in bar shi ya rike min ko da hannu nane tunda shi ba muharrami na bane kuma ba aure na yayi ba, in ko na bari hakan ta kasance toh tabbas ciki ne zai bayyana a tare da ni wanda har jikokina zan barwa wannan bakin fenti. Sosai Inna tayi min nasiha daya kashe min jiki ba shiri na fad'a mata duk abinda mukayi a gidan Maa, nan tace ai ba wani abu bane kyautatawa wanda yake kyautata maka,kar inji komai in dan wannan ne ko yaushe na tashi yi inyi anan gida bai sai naje gidan Maa ba. Cikin jin dad'in fahimta da tayi muka zauna muna hira cikin dabara ta cigaba da wayar min kai akan zaman duniya da kalubalen da yawanci 'yan mata ke fuskan ta wajan kwad'ayi da bin maza kuma daki-daki suke shiga kaina, kiran wayan Yaya na ne ya katse mana hiran na saka hijabi na fito. Center kofan gidan mu yake kallo fuskar shi d'auke da murmushi na musamman, yana gani na ya kara fad'ad'a murmushi nasa cikin sabon takun da na koya saboda shi na karaso gaban shi sai dai ina zuwa na b'ata fuska ta. Cikin d'an damuwa yake tambaya ta me ya faru kuma nake b'ata fuska? "Ba kai bane yau baka kallon waya na fito balle in tsorata ka yanda na saba" na bashi amsa a shagwab'e. Dariya yayi yana shafa gashin kansa da hannun sa ya ce," ayi min afuwa k'anwa ta yau d'in ne nayi missing d'inki dayawa shiyasa na kasa hakuri har ki ban tsoro" "Nima nayi missing d'inka sosai Yaya naaa" "Ina son ki k'anwa ta" Rufe fuska ta nayi ina dariya kasa-kasa sannan na bashi amsa da ," nima ina son ka Yaya naaa". A take na bud'e fuska ta tunawa da nayi da abincin da na had'aa mishi a gidan Maa. "Dan Allah bani minti biyu ina zuwa" ban jira amsar shi ba nayi gaba na kira Bakura wani yaron makotan mu muka tafi tare na d'aura mishi tiren akai ni kuma na d'auko jug d'in muka dawo wajan shi. Tunda muka fito yake kallo na da mamaki har muka iso bai iya d'auke idan shi daga kaina ba, "Ban san a ina zan ajiye maka ka ci ba,ko zaure zan saka maka tabarma?" Girgiza kai yayi tare da nuna min motan shi, ban musa ba yayi gaba muka bi bayan shi ya bud'e seat na bayan motan ya karb'i tiren akan yaron ya saka a ciki sannan ya min nuni da in shiga ciki nima. Sororo nayi da jug a hannu na kasa shiga kasancewar ban tab'a shiga motan shi ba kuma ga nasiha da Inna ta min d'azu, sai da ya shiga ya zauna ya ganni nan tsaye banida niyyan shiga. Kara cewa in shiga yayi nayi shiru ni ban shiga ba kuma ban tafi ba sai raba ido nake nan ya fahimci cewa tsoro nake,sai da ya nuna min cewa tunda ban yarda da shi duk shekaru da muka d'auka tare in d'auke abinci na baya ci. Ganin kaman ran shi ya b'aci yasa na d'an dosana duwawu na kad'an na zauna, yana murmushi yace toh in bud'e yaga me na dafa mishi mai dad'i. Ina bubude mishi ya ce," iyye lalle k'anwa ta an girma,ke kika girka min ko Inna ce?" *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/23, 4:26 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *Addu'ar Cin Abinci* Idan mutum zai ci abinci sai ya ce; بِسْمِ اللهِ. Bismi l-lahi. Da sunan Allah Idan ya manta to sai ya ce (yayin da ya tuna) بِسْمِ اللهِ فِي أَوَّلِهِ وَآخِرِهِ. Bismi l-lahi fi awwalihi wa akhirihi. Da sunan Allah a farkonsa da karshensa. Wanda Allah ya azurta shi da abinci ya ci, to ya ce; اللّهُمَّ بارِكْ لَنَا فِيهِ وَأَطْعِمْنا خَيْراً مِنْهُ. Allahumma barik lana feehi wa-at'imna khayran minh. Ya Allah! Ka sanya mana albarka a cikinsa, kuma Ka ciyar da mu wanda ya fi shi alheri. Wanda kuma Allah ya azurta shi da madara ya sha, to ya ce; اللّهُمَّ بارِكْ لَنَا فِيهِ وَزِدْنا مِنْهُ. Allahumma barik lana feehi wazidna minh. Ya Allah! Ka sanya mana albarka a cikinta, kuma Ka kara mana ita (madarar) *10* Rufe fuska ta nayi da hijabi na ina dariya ba tare da nayi magana ba,shima dariyan yayi ya d'auki yam ball d'aya ya kai baki ya gutsura ya fara taunawa har da lumshe ido wai dad'i ya kawo sauran baki na cikin sauri na kawar da kai na duk kunya ya gama mamaye ni. Yaci ba laifi dambun naman da kunun ayan ne dai yace su kam gida zai tafi dasu sunyi dad'i sosai ya kara da cewa duk ranan da zai zo toh ya daina cin abinci anan zan rink'a mishi yana ci, koda ya gama muka sha hiran mu yauma kaman kada ya tafi haka nake ji amma haka muka hakura da zai tafi wani babban jaka ya bani yace in bawa Baban mu sannan muma ya bamu namu tsaraban mu nida Inna ya tafi. Sai da na nemi taimakon wasu yaran sannan muka shiga da kayan cikin gida Gwaggo Aisha da sauran 'yan koron ta suka bini da harara wanda ban san ma sunayi ba. "Ni ba wai bana son yayiwa Mallam alkhairi bane ba a'a yanzu Baban ku yazo yaga wannan tulin kayan da sunan nashi, gaba zai iya neman gidan yaron yace zai je maula ya zubar miki da mutunci gaba d'aya" Inna ke fad'an haka bayan na nuna mata jakan da Yaya na yace na Baban mu ne. Shiru nayi ina tunanin maganan dan na san gaskiya Inna ta fad'a, zuwa can na fara murmushi ni kad'ai saboda na samo mana mafita. "Inna in kin bashi kayan kice mishi a hukuma Yaya na yake aiki, kinsan yanda Baba yake tsoron hukuma na tabbata daga wannan rana ba zai yarda su had'a hanya ba balle har ya roke shi" na karasa ina dariya sosai dan na tuna yanda Baba yake bala'in tsoron su ban san kome yasa b ba. Dariya Inna kanta tayi bata kuma ce min komai ba nima ban kara magana ba na kwashi tulin kayan da Yaya na ya kawo min da sunan tsaraba na fara jerawa cikin babban trolleyn kaya na. Bayan sallah magariba Baba ya shigo d'akin mu ina gama mishi sannu da zuwa na wuce wajan Dije abina na basu waje wanda sam Inna bata san hakan domin ina barin wajan zai fara kokarin canza salon hiran nasu dan haka ba b'ata lokaci ta d'auko jakar kayan tsarabar shi ta ajiye a gaban shi ta koma can nesa dashi ta zauna. Fara bud'e jakan kayan yayi yana mitan wai Inna ta maida shi dodo da zaran sun kasance su 2 a waje d'aya sai ta koma can gefe......... Kasa magana Baba yayi saima jikin sa daya fara b'ari ya zaro ido yana kallon jakan in shock kawai, Inna da ta watsar da lamarin sa tana wasu sabgogin ta bata san halin daya shiga ba sai da ta juyo, a tsorace ta mike ta nufo shi tana," Mallam lafiya meya faru?" Bai motsa ba kuma bai bata amsa ba sai da ta saka hannun ta a kafadar shi ta jijigashi da karfi tana," Mallam.... Mallam..." Sai a wannan lokaci ya firgita yaja dogon numfashi ya d'ago da kai yana kallon ta ba tare da yace komai. "Kamin magana mana Mallam meya faru nace?" Ajiyar zuciya yaja ya sauke kusan sau uku sannan ya ce," Bintu wayan nan kayan masu tsada kuma masu yawan da nake gani duka nawa ne kika ce?" Ajiyan zuciyar itama Inna ta sauke jin cewa ashe wai kayan ne suka firgita shi ta koma wajan zaman ta ta zauna sannan ta amsa mishi da nashi d'in ne. Firfito da manyan shaddodi da suke ciki ya fara bakin sa kuwa kaman gonan auduga sai da ya fito da guda shida suka kare sai takalma suma masu kyau guda 2 da huluna mu had'u a banki guda 2 da kud'in d'inki a kasa dubu hamsin. Suma ne kawai Baban mu baiyi ba a wannan rana ya rasa ya zaiyi da rayuwar sa ya d'aga wannan kaya ya kalla sai ya d'aga wancan ga kud'in kuwa ya rike a hannu gam ya kasa ajiyewa kaman wani ne zai kwace mishi. "Bintu.... Bintu Allah yayi miki albarka yanzu wannan duka a dalilin 'yar albarka na samu dama ai wannan yaron kana ganin shi kaga dan albarka shima, ko ba shi bane na gan su tare kwanakin baya?" Ya tambaya yana ta washe baki. "Shine mana ma'aikacin hukuma ne ai, ni ko soja tace min ne ko d'an sanda, na manta dai" Inna ta bashi amsa ta kauda kai kada dariya ya sub'uce mata ganin yanda nan da nan Baba fuskar shi ta canza ya koma kalan fargaba da tsoro. "Oho ashe hukuma ne, toh yayi kyau madallah da har ina cewa in naga ya dawo zanje in mishi godiya kuma muna gaisawa ashe yafi karfina". Baba ya fad'a bakin shi na rawa. Inna had'iye dariyar ta tayi ta juyo tana kallon shi can ta ce," haba Mallam wani irin magana ne wannan, uhum sirikin naka shine yafi karfin ka?" "Kema dai Bintu da son jan zance kike kin san bana shan inuwa d'aya da hukuma, Allah yajikan Baban ki ai ta nan ya rinjaye ni nayi ta bashi kud'i mudin in ya tambaya ko a wani waje sai naje na ciwo bashi na kawo mishi duk da shi na san yayi ritaya amma nake tsoron sa balle wanda yake saurayi mai jini a jika? Hmmm ke dai kawai ki cewa 'yar albarka ta mik'a godiya ta a wajan sa". "Toh shikenan Mallam zan fad'a mata" Inna ta bashi amsa. Tun daga wannan rana Baban mu shima ya koma d'an gaye daga ya canza wannan sai ya cire wancan har a majalisan su yanzu shi yake mulki kowa so yake ya zama makusancin shi, maimakon kud'in nan daya samu ya juya su a kasuwanci suyi albarka ya rike gidan sa kaman kowani magidanci saima lalacin nasa ya karu d'an masarar da yake sayowa ma yanzu ya daina ba abinda ya shafe shi da lamarin cikin gida illa ya d'au wanka ya shigo d'akin mu yayi breakfast ya tura kud'i a aljihu yayi ficewar shi. Aike kuwa Yaya na bai daina yi mishi na kaya dana kud'in duk bayan kwana bibbiyu yake aikowa, ranan da ya rasa na kashewa kuwa ni yake tambaya in bashi dan ya san ko ya tambayi Inna ba bashi zatayi ba. Wahalar da muke ciki yanzu ya dawo kan Inna Asabe dan itace mai yara dayawa a gidan ga babu abinci babu jari balle ta daurawa yara sana'a, kananan yaran ta kullum a d'akin mu suke cin abinci. Rannan Gwaggo Aisha bata gida Inna ta fito ta kawo mata rabin bugu na shinkafa da kuma carton na taliya sannan ta bata dubu goma tace tayi jari ita mai yara kanana zama haka ba zai yiwu ba. Kuka wiwi ranan Inna Asabe tasa tana Inna ta yafe mata abubuwan da tayi mata a baya gashi wacce ta biyewa sukayi mata rashin mutunci yanzu babu ruwan ta da ita koda zasu wuni su kwana basu ci ba kuma basu sha ba ko a kwalar rigar ta sai wacce suka wulakanta itace yau ta mutumta ta haka? Inna Asabe tun daga wannan rana ta samu abinyi itama kuma tun daga wannan rana ta fita harkan gwaggo Aisha tsakanin ta da Inna ta kuma sai mutunta juna. ********************************** *Rubby private school* makaranta ce mai matukar tsada ta 'ya'yan masu kud'i ko manyan 'yan kasuwa, anan Yaya na ya nemo min gurbin karatu na fara fita ss1 abina kuma ya ajiye min mai napep da yake zuwa ya kaini kullum da safe kuma ya d'auko ni in an tashi, wata nayi kuma ya biya shi kud'in sa. Maryam Alhaji idris itace seat mate d'ina tun ranan mu na farko da had'uwa muka kulla k'awance da ita domin Allah ya had'a jini mu sosai. Kasancewar Maryam tana kusa dani yasa al'amarin makarantan yazo min da sauki, sosai take taimaka min kana ganin ta kaga wayayyiyar yarinya 'yar gayu tsabanin mu namu wayewar kauyenci ne a wajan su. Ba'a magana da hausa sai turanci a makarantan abinda ya fara bani matsala kenan sannan kuma in ana koyarwa shima sai turanci ko kad'an basa d'an sirka hausa yanda irin mu zamu fahimta sai dai in an gama koyarwa Maryam ta kara wayar min da kai. Term d'aya kawai mukayi na canza nayi wayewan 'yan gayu ga turanci ya fara zama a bakina domin makarantan ba wasa. A wannan lokaci ne kuma aka saka bikin Hajara da Alhaji data samu ,wata biyu kawai aka saka Gwaggo Aisha sai habaice-habaice take 'yar ta zata je gidan hutu gidan kud'in halal bana yankan kai ba, wai kud'in Yaya nane na yankan kai. Suna ta shirye-shiryen bikin su mu kuma muna shirye-shiryen walimar saukar mu a islamiya dan haka kona dawo daga makaranta banida lokacin zama sai na islamiya dan hadda muke kuma abinda ya rage mana bai fi izu biyar ba gashi har kuma date d'in da aka saka na saukan ya kusa shiyasa muka bada himma sosai, a yanda aka saka date d'in in anyi bikin Hajara da sati zamuyi walimar namu. A boye Gwaggo Aisha filin ta na gado ta sayar tayiwa Hajara kayan d'aki dashi wai 'yar ta zata shiga babban gida kada su raina ta, ba laifi kaya kam sunyi kyau dan a bakin Dije nake jin wai Italian bed 'yan dubu dari uku ta saya mata da kujeru dubu dari da hamsin, Allah ya sanya alkhairi nayi na shi a wajan toh me zance ? Nida anko ma sunce kada na kuskura inyi na bikin d'akin su. Ina gani su jamila suna ta rawan kai a shiga a fita sai shirye-shirye take itama wai zatayi nata shagalin daban dan haka ankon ma nata kala daban ne da k'awayen ta. Ana saura sati d'aya gidan mu ya fara cika da baki 'yan uwan Baban mu da nasu Gwaggo Aisha ga hayaniya ga rashin zaman lafiya saboda kullum sai an raba fad'a, ba shiri na tattara kaya na zuwa gidan Maa ko zan samu natsuwa in ida hadda ta kuma a zuciya ta na kuduri sai sun gama bikin su zan koma gida. Ana gobe daurin aure da yamma Yaya na yazo amma ya kasa parker motan shi inda ya saba saboda jama'a sunyi yawa anata shiga da fice sai gaba da gidan Maa yayi sannan ya kira ni a waya na fito wajan shi. "Meke faruwa a gidan naku ne naga jama'a haka?" Ya tambaya ko gaisuwan kirki ba muyi ba. Turo baki nayi ina mai jin haushi dan duk wanda zai min zancen auren nan haushi yake bani tayaya za'a ce wai ana biki a gidan ku amma ace wai an hana ka yin anko wani irin kiyayyane, me nayi musu da zafi haka?? Ina aiyana haka a raina naji hawaye ya zubo min wanda ya tayar da hankalin Yaya na ya shiga tambaya ta meya faru cikin damuwa. Maimakon in bashi amsa sai na fashe mishi da kuka tsakani da Allah, nan ya kara ricewa yana tambaya ta amma na kasa magana sai shassheka nake. Da kyar nayi shiru shima sai da naga hawaye a idon shi ba shiri na had'iye kukana na fara goge hawaye na da hijab. Sai da muka natsu sannan ya ce," in ba so kike zuciyata ta buga ba kanwa ta ki gaya min meya faru??" Cikin kara turo baki na ce," Auren Hajara za'ayi gobe" Wacece kuma Hajara?" "Yaya tace wacce a baya in kazo zaga ganta tana wucewa da abincin sayarwa" Nan da nan ko ya gane ta na cigaba," yar Gwaggo Aisha ce kuma itace babba a gidan mu dan ni ba yar d'akin su bace suka ce kada inyi ankon auren" na karasa wasu sabbin hawaye na bin kunci na dama abin yana cina a rai sai yau na samu daman amayarwa. Kallo na ya tsaya yi with expiration a fuskan shi, can ya girgiza kai ya ce," tunda can suke miki haka ko sai da auren yazo suka fara??" Ya tambaya fuskar sa na fallasa bacin rai da yake ciki. "Tun muna kanana na taso naga haka ware ni suke suna hana 'ya'yan su wasa dani, ni kad'ai nake al'amura na, nake wasa na kaman mayya in Dije bata nan. Shiru yayi na wasu dakiku sannan ya fara magana," dama bai kamata kiyi ankon su ba saboda kin fi su class shiyasa suke miki haka kuma ina so ki kwashe kayan ki zuwa gidan ku yanzu auren gidan ku ne dole dake za'ayi. Zan kawo miki kayan da zaki saka a bikin zuwa dare nd...." "Ba sai ka kawo min kaya ba ina da wayan da ban saka dayawa cikin wayan daka kawo min kuma ni ba zan je biki...." " I don't care about that zan kawo kayan anjima kuma dake za'ayi bikin" yana gama fad'an haka ya fad'a motan shi ya fita a guje. Da ido na bi shi ina jinjina girman irin son da yake min ko kad'an baya son gani na cikin damuwa. "Allah sarki Yaya na Allah ya bar mu tare" nace na juya zuwa gidan Maa raina fess dan aiwatar da abinda ya saka ni. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [9/30, 2:28 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'a Idan Mutum Ya yi fushi.* أَعُوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ. A'oothu billahi minash-shaytanir-rajeem. Ina neman tsarin Allah daga shaidan tsinanne. *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ Duk da kin ki fad'a min sunan ki hakan ba zai hana ni nuna miki farinciki tare da godiya ta a gare ki ba,naga kyauta na yaba nagode Allah ya bar kauna wallahi ina kaunar ku fiye da yanda kuke zato ina kuma alfahari daku. Lots of luv 😘😘😘😍😍😍 *11* Inna tana tsakar gida tana taya su aikace-aikace duk da habaice-habaice da suke bin ta dashi bai dame ta sai gani na tayi nazo na wuce ciki da jakan kaya na. Na shiga d'aki ban dad'e ba Inna ta biyo ni tana," har kin gama shanye yajin da kika daka ne? Ai na zata zaki yi wata kina sha kamin ya kare ki dawo sai kuma ya kare da wuri". Turo baki nayi tare da marairaice fuska na ce," Allah sarki Inna ni ina can ina ta kewar ki shiyasa na kasa zama na dawo amma ke ko kewa ta ba kiyi ba". "Wani abun dai ya dawo dake ba kewa ta " Inna ta fad'a tana shirin ficewa. "Shikenan tunda baki yarda ba amma a ina zan iya zaman sati ban gan ki ba inna taaaa" naja zancen ina murmushi,karasa ficewa tayi bata kuma kula ni ba. Kwanciya ta nayi nima a d'aki ina chatting da Maryam ban kuma lek'a waje ba, ina jin su a waje anata mayar da zance wai ashe yau akwai dinner da angon yace za'ayi da farko sai kuma wata 'yar uwar sa tazo da yamma tace an fasa dinnern saboda wata kanwar Maman su tayi hatsari a hanyan ta na zuwa bikin. Gyara kwanciya ta nayi ina ko akwai dinner ma wa zai je, can ta matse musu nace a zuciya ta tare da jan dogon tsaki ni kad'ai. Kusan isha'i sai ga wayan Yaya na yace yana waje, Inna har yanzu tana cikin mutane dan haka banyi mata magana ba na fita wajan sa, yana tsaye a inda ya saba tsayuwar yasha gayun sa kaman yanda ya saba sai zuba kamshi yake. "Naji dad'i da naga kin dawo gida kaman yanda na umarce ki" yace yana kallon karamin gyalen da nayi rolling dan kullum in zan fito wajan shi hijab nake sakawa sai yau nasa gyalen saboda dare ne kuma bai tab'a zuwa wajena da daddare ba sai yau. " Allah kada ya kawo ranan da zaka bani umarni in kasa bi, ka wuce duk wani matsayi na duniya da ka sani a waje na, u re my every thing". Na fad'a mishi cikin shaukin kaunar sa da yake d'iba ta. Murmushin nan nashi mai sanyi ya kara fad'ad'awa yana kallon na ya ce," nagode kanwata amma bake ya kamata ki fad'i wannan Kalmar ba sai ni domin na kasance maraya banida kowa kece kika zama dangina kika zama kanwata sannan above all kika zama masoyiya ta kin ga kuwa nine zance miki u re my everything". Kasa cewa komai nayi sai murmushi da nake saboda kalaman shi sun kara narkar min da zuciya ji nake ba zan iya rayuwa babu shi ba. "Wannan gyalen yayi matukar yi miki kyau amma ki daina saka shi in zaki fita ki cigaba da saka hijabi yanda kika saba " ya katse min tunani na. "Insha Allah Yaya na " na amsa mishi ina sunkuyar da kaina kasa. Wata katuwar jaka ya d'auko a seat d'in bayan motan shi ya mik'a min ya ce," ga kayan da nake son ki saka gobe ,zan zo kaman da karfe goma sha biyu dan kai ki beauty saloon make sure kin shirya before inzo" Na bud'i baki da niyyan godiya ya katse ni ki shiga gida sai nazo " gyad'a kai nayi ina murmushi na juya na shiga gida. Da ni da Inna ta duk saka kayan mukayi a gaba muna kallo cike da mamaki, wani haddaden gown ne light blue adon da akayi a jiki ma ya isa mutum kallo sannan ga wani karamin box da yake d'auke da wani tsiririn sarka mai d'an karan kyau da d'an kunnen shi wanda Inna tace tabbas gold ne sai kuma takalmi mai tudu da pos d'in sa suma ko makaho ya shafa su yasan naira tasha kashi wajan sayan ta. "Wannan hidima anya batayi yawa ba, yau kuma harda zinare?" Inna ke fad'in haka cike da jimami. " Yaya ne fa Inna meye abin damuwa saboda ya saya min kaya, ai ya riga ya saba yi " nace hankali na kwance kuma tsakani na da Allah na fad'a. Shiru kawai Inna tayi ba tare da ta kara cewa wani abu ba kasancewar ta gane in banda tarin kuruciya babu komai a cikin kaina, abu d'aya yake sanyaya mata zuciya shine yanda bata sakaci wajan tsayuwar dare kuma duk a kaina. A baya bata damu da lamarin Yaya na sosai ba kaman da yanzu na girma, duk da cikin hikima irin tasu ta manya tana jin yanda muke tsakani na da shi ko hannu na bai tab'a tab'awa ba. Addu'an Allah yayi jagora ya tsare daga duk abin ki tayi ta tashi a wajan ni kuwa cikin zak'uwa da zumud'i na jawo kayan na fara kallo saboda dazu idon Inna ya hana in sake in kalla da kyau har na kosa goben tayi in saka kaya na. Da washe gari da hayaniyan mutane muka tashi gidan mu ya cika ba masakar tsinke gaba d'aya sai naji na takura dan da naje da niyyan shiga bayan gida da gudu na dawo ina kakarin amai saboda yanda mutane suka b'ata shi, ba shiri na samu 'yar karamar jaka ta na had'a duk wasu abubuwa da zan bukata na zuba a ciki na wuce gidan Maa bayan na fad'awa Inna a can zan shirya sai in dawo. Ko da na je gidan Maa itama bata zauna ba gidan namu ta tafi aka bar ni kad'ai a nan Inna ta aiko min da abincin safe da akayi na d'aurin aure,da yake safe ne sai na kasa ci na fito na samu yaro a waje na aike shi wajan mai shayi ya had'o min breakfast na nayi na kwanta bacci ni ban tashi ba sai kusan sha d'aya . Ina shirin shiga wanka naga an ajiye min wani abincin bayan na safe, Allah sarki Inna ta na san wannan duk aikin ta ne, ban ci abincin ba sai bayan na fito daga wanka. Lotion kawai na shafa na saka kayan da Yaya na ya kawo min jiya da daddare, aiko ya zauna das a jikina kaman an gwada ni irin gown d'in nan da bayan yafi gaba tsayi wani sarka da d'an kunnen kira Dubai data sayo min a baya shi nayi amfani da shi dan gold din Inna b'oye shi tayi tace ba zanyi amfani da shi ba,ko minti goma banyi da gama shiryawa ba kiran Yaya na ya shigo waya ta hijabi na d'aura akan kayan na fito. Yau manyan kaya ne a jikin sa tsab'anin da ya murza hulan Ahaiyye a kan sa ya matukar kyau sai zuba kamshi yake. "Yaya naaa ka gan ka kuwa kayi kyau sosai sai kace kai ne angon" na ce mishi ina dariya. Murmushin sa mai sanyi ya yi min sannan ya ce" hmmm ke ba?" "Ni me?" Na tambaye shi ina turo baki. "Ke kanwa tace na ce". "Kanwa only?" Na kara tambaya ina fiddo da ido waje. "Baki kyauta min ba kin ki fad'a min auren nan in time balle in kawowa Baba wani abin kirki shiyasa na ki zuwa daurin auren,amma ki min magana da shi in bashi hakuri da gudumuwa na ko kad'an ne". Ya ce saboda kawar da wancan maganan da muka fara. Gyad'a kai kawai nayi na juya ina dan dariya tun kamin inga draman da zai faru tsakanin Baba da Yaya na. Allah yasa a hanya muka had'u da shi yana dawowa gida da yake ba a kofar gidan mu aka d'aura auren ba a can wani masallaci dake kan kwanan layin mu, yanzu haka suna tare da wasu 'yan uwan sa da sauran abokan shi ne a wajan bayan mutane sun watse. "A'a 'yar albarka ke ce, ina zuwa kuma?" "Baba dama wajan ka zan je, ummm...hmmmm wannan d'in nan da yake aiko maka da kaya shine ya zo yana so wai ku gaisa kuma ya baka hakuri da gudumuwan sa" na karasa kai na a kasa saboda kunya. "Wai wannan mai zuwa wajan ki nan?" Ya tambaya yana zaro ido. Danne dariyar daya taso min nayi ina gyad'a mishi kai. "Toh meye sai mun gaisa da shi,naga a baya ke yake bawa ki kawo min ba yau ma ya baki d'in mana". "Baba nima ban san dalilin da yake son ku gaisa ba yau amma tunda ya bukata kila yana da wani dalilin" na fad'a ina kallon yanda naga duk hankalin Baba ya tashi kaman ba yanzu na gan shi cikin annashuwa ba. "Ki ce ya zo nan ya same ni ina jiran sa a nan " . "Toh Baba" na ce tare da juyawa na koma wajan Yaya na sannan na fad'a mishi sakon Baba. Naso bin shi inga yanda zasu kare da Baba sai kuma naga rashin cancantan hakan na tsaya jiran shi. A nesa Baba ya hango shi yana zuwa yana saka wayar shi a aljihu wanda shi kuma Baba kallon bindinga sak ya yiwa wayan, nan da nan ko zuciyar Baba ta fara zillo kaman zata fito. Cikin matukar sauri ya juya ya fara tafiya kaman zai kifa ya nufi masallaci inda ya bar mutanen shi suna jiran shi, yana cikin tafiyan kuma wani tunani ya fad'o mishi ya canza hanya zuwa bayan layin mu. Yaya na yana zuwa wajan ya ga wayam bai ga kowa ba kaman zai koma kuma ya fasa ya karasa har bakin masallacin aka ce mishi baya nan, haka ya hakura ya dawo ya ce bai gan sa. A hanyan mu na zuwa saloon sai murmushi nake dokawa ina hana dariya ta fitowa na san Baba k'in tsayawa yayi saboda tsoro. Babban wani tsadadden saloon ya kai ni a west end wanda ba abinda basa yi na gyara da kamshi har da lalle, gefe naga Yaya na ya kira wata da alama ita ce babban su a wajan ban san me suka tattauna ba naga ya bata kud'i masu yawa ya fita, nan da nan suka shiga hidima da ni har da su drinks da snacks suka kawo min. Ba b'ata lokaci suka warware yalwantaccen gashi na suka wanke suka gyara shi nan da nan kuwa ya kara kyau sai d'aukan ido yake, wanke min kafa suka yi a wani abin wanke kafa ni dai ban tab'a gani ba sai ranan,fara ce na su ma sun gyara sannan suka yaryad'a min lalle mai ja da baki. Light makeup suka yiwa fuska ta daya kara fito da ainihin kyawu na, wani haddaden net mai kauri da yayi matching da kayan jiki na suka d'auko a shagon nasu suka nad'a min shi in a unique way. Fad'an irin kyan da nayi ma b'ata lokaci ne dan sai in rantse da Allah ban tab'a sanin ina da irin wannan kyau ba sai yau, sai kallon kai na nake a madubi, su ma 'yan wajan sai yaba kyau na suke. Da zan fita na fara kokarin saka hijabi na, 'yan wajan ne suka min caa wai kar in saka daurin net d'in zai lalace tun ban isa gidan auren ba,tunda a mota muka zo in tafi a haka. Ba dan naso ba na fito a cikin saloon d'in ina takawa a hankali kaman mai tausayin kasa saboda tudun takalmin kafa na har na iso bakin motan Yaya na bai sani ba kasancewar ya kwantar da seat ya kwanta da earpiece a kunnen shi ban san me yake saurara ba. Bud'e kofan motan nayi na shiga na zauna kamshin turare na shi ya isar da sakon isowa ta a gare shi ya bud'e ido ya sauke su a fuska ta da nima shi nake kallon, mun dad'e muna kallon juna daga baya nice na sauke nawa idon kasa ina d'an murmushi. Ina jiyo shi sai da ya sauke ajiyan zuciya har sau uku sannan ya tashi ya zauna tare da gyara kujeran, ya juyo ya kara kallo na kaman zai ce wani abu kuma ya fasa ya tada mota muka kama hanyan gida,har muka iso babu wanda ya yi magana. Yana yin parking na ce," nagode Yaya naaa zan shiga ciki sai anjima". Har na bud'e kofan na fita bai amsa min ba na fara tafiya, nayi kaman taku uku naji muryan shi ya ce," Zareefa...." Da matukar mamaki na juyo dan jin suna na a bakin shi yau. " Kinyi matukar kyau....,kyan da baki ba zai iya furawa ba, amma dan Allah in muna tare ki rinka saka hijabin ki" yana gama maganan shi yaja motan shi ya tafi. A hankali na juya zuwa cikin gida ina murmushi da mamakin me yasa yake yawan cewa in saka hijabi ba. Ina saka kafa gidan mu ido ya dawo kai na kowa ni yake kallo da gudu Dije ta zo ta rungume ni cikin ankon da suka hana ni yi sai naga ashe da a lokacin ma naga ankon ba sai sun hana ni ba da kaina zance ba nayi. Can b'angaren su taja ni muka tafi tana in bata labari meye sirrin? A nan muka zauna ina bata labarin saloon d'in da muka je na fara jin sautin kid'a daga waje. Da mamaki na ce", kaman kid'a nake ji?" "Eh dama naji Hajara da kawayen ta zasu kawo DJ tun shekaran jiya suke zancen Ina ga shi d'in ne suka kawo" Dije ta bani amsa. "Taso muje mu gani...taso muje" cewar Dije tana jan hannun na . Muna zuwa kofar gida muka ga Amarya da kawayen ta suna ta rawa, jan hannu na Dije ta fara wai muma mu shiga nace mata ta shiga ina zuwa. Ina daga gefe ina kallo kawai naga mutane sun rufu a kai na suna min liki, maza da mata amma mazan sun fi yawa na rasa ta ina ma suka zo dan ni dai ban san su ba. Neman shiga gida nake amma sun tare ko Ina ba hanyan wucewa daga cikin matan naji wata tana ", ke Hindu ki zo ga Amarya nan kiyi mata liki" Da mamaki na d'ago na kalle ta na ce", ni fa kanwar Amaryar ce ga Amaryan can" na karasa ina nuna musu inda Hajara da kawayen ta sukayi sororo suna kallon mu. "Eh ga Amaryar can wannan kanwar ta ce " wata kanwar Gwaggo Aisha ta fad'a tana harara ta. Jiki a tsabule suka juya ga Amaryan su suna kallon ta har taji ta muzan ta, ni dai ban san ya suka kare ba na shige cikin gida na bar su. Da daddare bayan an kai Amarya gidan ta Dije tazo d'akin mu a lokacin ina kwance ina chatting da Yaya na. "Zo...zo...zo muje ki sha labari zo muje" ta ce tana jan hannu na ina ta tsaya in ajiye waya amma ina haka taja ni muka tafi bangaren su. "Mijin Hajara da ake cewa mai kud'i ne ashe karya ne,kin ga gidan nata gidan yawa mutane sun fi shida a ciki ga d'akin nata ya yiwa kayan ta kad'an ke abun b dad'in gani wallahi. Ina matar da ta zo tace ita 'yar uwar sa ce tayi magana a kan an fasa dinner ashe gidan haya ce ta had'a su". *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku* [10/10, 7:42 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊 *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* _Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇 https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp _Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._ *12* Bangane ba Hajara me kike nufi wai?" Na tambayi Hajara cike da rud'u. Kamo hannu na tayi muka zauna a bakin k'ofar d'akin su sannan ta fara magana," hmmmm duk abinda Alhaji Khalid mai gidan gona ya fad'a a gidan nan ashe zuki ta malle ne sunan shi haladu kuma sana'ar sa kuma bawa dabbobi abinci a gidan gonan Alhaji Mukhtar dake Sabon layi". Samun kaina nayi da matukar jin haushin sa sannan ga tausayin 'yar uwata daya rufe ni lokaci guda,cikin wani irin yanayi nace", amma Allah ya isan Hajara makaryaci kawai in bashi da kud'in menene amfanin shirga mata wannan karyan? Allah sarki Hajara ko wani halin take ciki yanzu?" "Lalle Zareefa kin bani mamaki meye naki na wani zakewa haka, wallahi kada ma kiji tausayin ta ita ta jawowa kan ta ko ince su suka jawo dan harda uwar ta su ala dole dake zasu yi gasa, chab ni wallahi ko kad'an bata bani tausayi ba hasali ma dariya ta nayi ta sha, a mota ina ta tunanin yanda Gwaggo Aisha zatayi in taji wanga batu" ta karasa cikin shekiyanci tana dariya. Girgiza kai na nayi hawaye na taruwa a ido na, na ce mata," Dije kenan taya ba zan tausaya mata ba ko kin manta cewa 'yar uwata ce jini d'aya yake yawo a cikin jikin mu" "Na sani mana amma ba kya ganin yanda suka saka ki a gaba su da iyayen su sun hana ki sakat ke da mahaifiyar ki tun muna kanana har zuwa girman mu" "Koma menene Dije su d'in 'yan uwa na ne, jini d'aya yake yawo a jikin mu daurewa kawai nake ina share su amma ina kaunar su har cikin raina ina kuma sha'awa in ga mun had'a kan mu kaman sauran 'yan uwa" Hawayen da ya zubo min na share na mike na kama hanyan bangaren mu itama Dije ko motsi kasawa tayi dan maganganu na sun kashe mata jiki,ko da na shiga d'akin mu na samu Inna zaune gefen gado ta rafka tagumi da alamu itama taji zancen kenan. "Tun d'azu ake kiran wayan ki" ta ce min ba tare da ta sauke tagumin ba saboda wannan al'amari ya bata mamaki da tsoro samarin yanzu mayaudara ne kuma macuta ne, in banda cuta kazo da wata siffa da suna dan a baka mata me yasa ba zai zo a yanda yake ba? Ko da yake Maman Dije ta ce wai sun riga sun nunawa duniya cewa in ba mai kud'i ba akai kasuwa shine yasa shi zuwa da wannan siffa. Ajiyar zuciya ta sauke wanda sai da na juya na kalle ta dama rply na tex nake rubutawa 'yar ajin mu a islamiya ta kira bana kusa shine ta min tex tana min tuni kan abubuwa da muka shirya na walimar mu. "Inna lafiya kuwa na gan ki haka?" Na tambaya. "Hmmmm ba komai je ki wanke min hijabi na da da yake cikin bukiti a waje" da toh na amsa na fita wankin. Ina fara wankin naga Gwaggo Aisha sun shigo da kannen ta 2 duk sunyi wujiga-wujiga ko kallon inda nake ba suyi ba suka wuce, a zuciya ta na ce," chab Gwaggo Aisha ana cikin tashin hankali tunda bata harare ni ko ta tsaya ta zage ni ba, lalle yau tana cikin matsala, d'aki suka shige suna neman mafita. Har gari ya waye ba'a cimma abu d'aya ba sai shige da fice suke, sun samu Baban mu da maganan yace toh me zai mata, ta riga da ta fita a hannun sa lafiya dan haka sauran ya rage musu ita da mijin ta. Gwaggo Aisha takaici ya hana ta sauran sauran bayanin nashi tayi ficewar ta, ta rasa ina zata kai kukan ta a share mata hawaye, babban burin ta shine a raba auren domin jiya da daddare ita da kannen ta daga gidan Hajaran suke suka ja mata kunnen kada ta yarda ta bashi kan ta duk rintsi duk wuya dan gobe-goben za'a raba auren nasu sai gashi har sha biyu ta kusa babu alamun nasara ko kad'an. Gwaggo Aisha bata gama shiga tashin hankali ba sai da d'ayan kanwar ta da ta tura gidan Hajara dan a dubo mata lafiyr ta ta dawo da mummunan labarin cewa Haladu yayi nasaran kusantan Hajara jina-jina suka same ta abun babu kyan gani ko taimaka mata bai tsaya ba ya tsallake ta yayi tafiyar shi. "Yanzu fisabillilahi duk fad'an da muka yi mata sai da ta sakewa wannan mayaudarin jiki ya gama da ita?" Gwaggo Aisha ke tambaya tana goge hawaye da gefe zanin ta. "Ba laifin ta ba ne shi mijin ne tantiri, ta bamu labarin komai cewa da ta fara mishi taurin kai shine d'aure ta a jikin gado yayi abinda ya ga dama da ita wai bata isa ta hana shi more kud'in sa ba" 'yar uwar ta ta bata amsa. "Amma wannan yaro anyi tsinanne Allah ya isa tsakani da shi, ina zan shiga da wannan abin kunyan, kayyah " yanzu kam kuka Gwaggo Aisha take tsakani da Allah tana tunanin tayaya zata kalli idon 'yan gidan bayan duk abubuwa da tayi musu wai ita 'yar ta zata auri mai mota. "Mama kada ki tada hankalin ki domin nayi miki alkawarin saka ki farinciki, ba zan tab'a kula kowa ba kuma ba zan auri talaka ba sai mai kud'i" Jamila ke fad'an haka da take sauraron su tun d'azu ba tare da sun sani ba,d UK kallon juna suka tsaya yi babu wanda ya iya bata amsa sai dai ita Gwaggo Aisha ido ta zuba mata tana nazari tare da hasko yiwuwa da nasara a cikin abinda ta fad'a domin Jameela tafi Hajara kyau da tsarin jiki nesa ba kusa ba. Haka akayi wannan wunin a tsaye babu wanda ya lek'a gidan Amarya wasu ma saboda bakinciki a ranan suka koma inda suka fito shiyasa gidan namu ya zama shiru kaman ba biki ake ba. Bayan kwana 2 da bikin Hajara Yaya na yazo da rana bayan azahar cikin kananan kaya wandon kaman na sojoji sai bakin t shirt da bakin glass sosai yayi kyau, muna hira a kofar gidan mu yana tambaya ta me da me nake bukata a walimar saukar mu? Ni kuma ina ce mishi bana bukatan komai duk abinda ake bukata mun gama shirya su. A wannan lokacin ashe Baba yana gida ya dawo saboda wata bukatar shi lokacin da yazo Yaya na bai zo ba yana ciki ya zo dan haka bai san da zuwan shi ba,yana d'aki Gwaggo Aisha tabi shi tana magiya akan yayi wani abu akan al'amarin Hajara a raba auren domin muddin tana raye ba zata tab'a barin auran nan ya dad'e ba. Bata san duk haushi ya cika shi ba tazo ta ishe shi da surutu alhalin shi in ya tuna tsoro ya hana shi gaisawa da Yaya na da yanzu yana cikin kud'i yanzu gashi bashi da kud'i a hannu, tsaki yaja yana bin ta da mugun kallo ya ce," ke Aisha wai wace irin mace ce ke da zaran kin ga mutum ya shigo gida sai ki bi shi da korafin ki na banza da na wofi yarinya tana gidan mijin ta shine kike neman wai ni uban ta inje in fito da ita wannan wani irin rashin kan gado ne, toh ba dani ba wallahi kije can ki gama haukan ki kada ki kara tunkara ta da wannan iya shegen ko kuma ranki yayi mugun b'aci". Yana gama maganan shi ya mike a fusace zai fita ya juyo ya ce," ba sai kin kara gani na a gidan ba balle ki zo ki takura ni" Fita yayi rai a b'ace yana ta masifa shi yasa kai zai fita da sauri ya koma baya yana tunanin anya idon shi dai-dai ya nuna mishi kuwa? Kara lek'a kan shi waje yayi yaga dai da gaske ne Yaya na ya gani fuska a murtuke wai shi ala dole yayi fushi me yasa ban fad'a mishi maganan saukar namu ya d'auki nauyin komai na ba nayi da kai na. "Innalillahi wa inna ilahi rajiun wai shi wannan yaro banda bala'i irin nasu na sojoji meya kawo shi da rana tsaka yana muzurai sai kace anyi mishi dole" Baba ke fad'in haka bayan ya koma cikin zaure ya manne da bango wai duk dan kada Yaya na ya gan shi. Da kyar na shawo kan sa ya daina fushin muka ci gaba da hiran mu cikin annashuwa da shaukin soyayya, abinda bamu sani ba ashe Baba yana nan mak'ale a zaure yana jiran tafiyan Yaya na ya samu shima ya tafi majalisa, yaki komawa cikin gida kuma saboda rigimar su da Gwaggo Aisha kada taga ya koma ta mishi dariya. A takaice mun kai good 1 hour sannan mukayi sallama ya wuce ni kuma na shigo gida cikin farinciki hannu na d'auke da sayayyar da yayi min. Ina shigowa zaure saura kad'an in zubar da kayan hannu na saboda firgita ganin mutum manne a jikin bango yana goge zufa, sai da na tabbatar Baban mu ne sannan na samu natsuwa amma kuma mamaki da tambaya fal cikin zuciya ta me kuma yau Baba yake a nan ? Hanyan fita ya nufa yana masifa kallon inda nake bai yi ba hakan ko ya kara saka ni cikin konkonto, a yanda nasan Baba da son dad'i amma yau ko kulanin baiyi ba bayan ga shopping bags a hannu na, juyawa nayi da niyyan shiga gida naji muryan Baban mu yana," wallahi Allah yau yaron nan ya cuce ni, in banda ina gudun abin kunya cikin anguwa kada a ce ga Mallam Hassan can yana fad'a da sirikin sa ba Allah da na nuna mishi ko ni waye, Aikin banza wa zai yiwa barazana har kofar gida har da wani sako kayan sojoji toh sai me...?" Dariya na tintsire da shi har da dukawa sai yanzu na gane me Baba yake a zaure, da kyar na tashi na kwashi kayana zuwa cikin gida. Bayan kwana 2 akayi bikin saukar mu a islamiyar mu wanda ya tara duban jama'a ciki kuwa har da Yaya na sai dangin Inna a 'yan gidan mu Inna Asabe ce kad'ai ta tafi dan Gwaggo Aisha cewa tayi karatun karuwanci dama nake shine yau kuma za'a je party toh ba da ita ba. Bajintar da Yaya na yayi ba a cewa komai kayan rabo kala-kala ya kawo aka raba harda na malamai suma nasu daban ga gifts nima daya kwaso min ba zasu lissafi ba duk da haka cewa yake komai ya min gani yake bai yi ba saboda sauke Al' Qurani mai girma ba abin wasa bane. A islamiyar ma na samu kyauta daban-daban saboda hazaka ta daga karshe taro ya watse bayan mun sha pics saboda tarihi. ************************* Wato ka mai da ni mutuniyar banza a gidan nan saboda ban isa in fada kaji ba ko, fisabillilahi ka kyauwa kan ka kenan?"cewar wata 'yar dattijuwa mai kamala da kyau da haiba wacce ba zata haura shekaru hamsin ba. Wani kyakkyawan saurayi ne zaune a gaban ta shi take takewa fad'a amma shiru yayi kan shi a kasa yana kallon lallausan rug da yake malale a katafaren parlour nasu wanda kallo daya zaka mishi ka kira shi da aljannan duniya domin babu ne kawai babu a ciki, just ku hasaso shi a cikin zuciyar ku domin in nace zan tsaya zayyano muku tsari da kyan gidan sai mu kusan cika novel din bamu gama ba Duk da kan shi a kasa yake bai hana ni hango dogon hancin sa ba ga sajen sa baki wuluk na lallausan gashin sa sun kewaye fuskar shi, gashin kan sa kuwa kaman na larabawa saboda laushi da tsantsi sai dai yayi mata wani aski wanda an kwashe daga gefe-gefe da keya sai tsakiya da ta gaba ne da gashi kana ganin gashin ka san ya sha gyara da kulawa wajan mai shi. "Zafar... Wai ba da kai nake magana ba ka min shiru" wannan kyakkyawar dattijuwar ta fad'a cikin tsawa. Wanda ta kira da Zafar ya d'ago kai masha Allah ashe da kan sa yake kasa ban ga komai ba sai yanzu. Zafar fari tas irin farin nan mai yellow yana da dogon hanci wanda ya kawata kyakkyawan fuskan shi ga maidaicin bakin sa mai d'auke da jajayen lips sun kara fiddo ainihin kyan fuskar sa, idon sa kuma kaman mai jin bacci suke a takaice Zafar ya had'u iya had'uwa sai dai ya kasance d'an shan minti ne kasancewar shi d'a tilo ga multi millionaire. A shagwab'e ya d'ago da kai yana d'an tale baki kaman d'an karamin yaro alhalin ya kai shekaru ashirin da takwas yana kallon mahaifiyar tashi da lumsassun idon shi da baturai sukewa lak'abi da sexy eyes ya ce," wai ya kuke so inyi ne Mom for god sake ni komai nayi kice bai yi ba, look at dis " yace yana nuna mata gashin kan sa sannan ya cigaba. "Wats wrong with it nayi wancan kunce baiyi ba nayi wannan ma kice baiyi ba then which 1 do u want me to do?" Ya karasa yana watsa hannayen sa cikin iska. Wacce ya kira da Mom ido kawai ta zuba mishi ta kasa cewa komai domin lamarin tilon dan nata ya fara bata tsoro a ce d'an da ka haifa shi zai rink'a mayar maka da magana haka, babu wanda yake shaka a gidan sai Abban shi, sanin haka yasa ta cewa," ok haka kace ko? Kaje kayi duk abinda kake so amma kafin ka fita inayi maka albishir da gobe Abban ka zai taso daga Portugal zuwa gida sai ka tanadi bayanin da zakayi mishi in ya ga askin naka". A rikice ya dawo kusa da ita, da ya kai har tsakiyan parlour da niyyan komawa part d'in shi yana zuwa ya zauna a gaban ta tare da d'aura hannayen shi duka 2 kan guiwoyin ta ya ce," na san ko Abba ya dawo my sweet Mom zata kare ni kaman yanda ta saba ko Mommy naaaa just once daga wannan shikenan ba zan kara ba I promise shima wannan dan zamu yi bachelor's eve na Musaddiq ne shiyasa". Murmushi tayi tana shafa gashin kan nashi ta ce," promise.. promise dai wanda ban san sau nawa aka yi min su ba remember jiya me kace?" Dafe goshin sa yayi yana d'an tuno yanda yake mata in taki yi mishi abu, zai fara yi mata ta dakatar dashi tana," bana son wannan shagwab'an naka jeka let me think about it" "Yesss.... dats my sweet Mom" yace yana d'an tsalle a gaban ta sannan ya fita da gudu yana dariya, itama dariyan take a zuciyar ta kuwa tana blaming kan ta da duk abinda Zafar yake itace sila domin a koda yaushe itace mai kare shi wajan Abban sa in yayi wani laifi, ita da kan ta bata jin dad'in abinda take wasu lokutan amma ya zata yi shine fa kad'ai kwan ta a duniya dan ma Allah ya tsare baya wasu mugayen dabi'un na 'yan zamani shi dai bar shi da zuwa parties da kula 'yan mata sai kuma son swagger. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [1/26, 7:04 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *13* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *13* Yana fitowa daga parlourn Mommy shi fara'an fuskar sa ta d'auke lokaci daya dif kaman wutan NEPA sai ma wani shan kamshi da yake wanda ya kara fiddo da kyan sa, a nan na fahimci wato babu mai ganin wannan fara'ar tashi sai mahaifiyar sa. Wani haɗaɗɗen madaidaicin flat house ne dake gefensa na mahaifan sa, ya nufa ko kula masu aiki da suke gaida shi baiyi ba ya shige abin sa. "Dude ka san I have been waiting for you amma ka wani shanya ni, tun dazun su Sabeer suka dame ni da waya wai kowa ya hallara sai mu ake jira" cewar wani guy dake zaune kan sofa shima kana ganin shi kaga classic guy saidai ko rabin kyan Zafar bai kai ba. Ko inda yake Zafar bai kalla ba ya wuce bedroom d'in sa da yaji royal bed fari kal,komai na d'akin farare ne hatta da curtains tsab'a parlour kuma komai na ciki royal blue ne, bai tsaya cikin bedroom d'in ba ya fad'a bathroom domin yin wanka. Girgiza kai Sadiq yayi ganin Zafar yaki kula shi ya wuce ciki in da sabo yaci a ce ya saba kam duk da cikin abokan sa jinin su yafi had'uwa da Sadiq d'in kuma tare suka taso tun suna kanana har zuwa girman su babu abinda ya tab'a raba su ko a makaranta. Baban Sadiq yana da wadata shima amma ko rabin kudin su Zafar bashi dashi, saboda aminitar dake tsakanin su 2 yasa iyayen su maza da mata kulla zumunci sannan Baban Zafar shi yake biya Sadiq kud'in makaranta ganin cewa shine farincikin d'an su. Zafar yana da fara'a sosai da wasa da dariya amma fa sai ga Mommy sa dan ko shi Sadiq da suke tare shekara da shekaru bai cika ganin dariyar sa ba sai jifa-jifa wanda shima in mutum ya bibiya toh yaga abin mugunta ya sami shi Sadiq d'in anan zaki ga dariyar sa harda rike ciki. Zafar yana da wani hali ko kuma ince buri, ya raina 'yan matan mu na gida kwata-kwata basa burge shi a cewar sa bai ga abin so ba a tare dasu ba, 'ya'yan masu kud'i da masu fad'a aji na cikin kasar nan babu wacce bata kawo mishi kokon barar soyayyar ta ba duk yayi watsi dasu dan ko kallo basu ishe shi ba,sai dai in zasu tafi party wanda sai da chick ake zuwa toh shine zai kula ki shima da ya fito shikenan amfanin ki ya kare amma hakan ma farinciki wacce ta samu wannan daman take ko ba komai ta samu na canza status kenan tana sham kamshi cikin kawayen ta. Wannan halin nashi yasa mutane da yawa suke mishi kallon mai neman mata alhalin ba haka yake ba. Murya... Ya d'aga cikin k'osawa da zaman jira da yake ya ce " man wai me hakane, sai b'ata mana time kake pls ka fito mu tafi ba party zuwa da beb bane in dan wannan kake ja mana...…" Ganin ya fito yasa ya had'iye sauran maganan shi yana bin shi da kallo ko makiyin shi ne bai isa ya kushe shi ba, toh duk iya dai bin kwakwafin mutum babu abin kushewa a halittar sa dan ko dama aka bashi aka ce yayi kan sa iya kar sa kenan. Ya matukar had'u cikin dark blue polo shirt da wandon jeans baki sosai kayan sun matukar dacewa da farar fatar shi sai canvas dark blue dake kafar shi sai zuba kamshin tsadaddun perfumes din shi yake kasancewar sa mai son kamshi shiyasa baya amfani da turare daya kusan 4 ko 5 yake amfani dasu at a time dan haka ba zaka tab'a bambamce kamshin da yake ba. Yana gyara agogon Rolex dake hannun shi ba tare da ya kalli inda sadiq yake zaune ba yace,' muje" Girgiza kai kawai yayi ya mike yabi bayan shi dan har ya fita basu tsaya b'ata lokaci ba suka fad'a wata sport car d'in sa suka fice daga gidan. ******************** Gidan mu dai yana nan yanda kuka san shi babu abinda ya canza cikin zamtakewar da muke, cikin shekaru 2 da suka shud'e sai dan abinda ba za'a rasa ba, muna final year a makaranta sai shirye-shirye rubuta waec muke hankali kwance. In ka san ni a shekaru 2 da suka wuce ba lalle ne ka gane ni yanzu ba na canza matuka na kara wayewa ga girman jiki dana kara sosai ,kyau na kuwa ba'a magana duk inda na wuce sai an dad'e ana magana ta wasu ko cewa suke wai ni balarabiya ce,ko a makaranta na sha raba musu musu cewar ba abinda ya had'a ni da larabawa ni asalin hausa Fulani ce amma wasu basa yarda sai dai suce b'oyewa nake bana son asan gaskiya. Godiya sun tabbata ga Allah mahallacin komai da kowa sannan ga mutane 2 na cikin rayuwa ta wanda a dalilin su na zama abinda na zama wato Yaya na da besty na Maryam, dukan su 2 sun taka muhimmiyar rawa a rayuwa ta. Yaya na shine gata na shine abin alfahari na ba dan shi ba da ban kai wannan matsayin da nake ba, sai Maryam ita ta kasance kaman roll model na domin komai na 'yan gayu ita ta koya min na fito cikin 'yan mata masu aji, dalilin Maryam da ta nace muka shiga wani catering school da sai da muka shafe watan ni sannan aka yaye mu yanzu ba wani nau'in girki da ban iya ba da snacks da drinks kala-kala, mostly in Yaya na zai zo sai nayi mishi. Auren Yayan Maryam shi muka saka a gaba da za'ayi nan da wata 3 masu zuwa,sosai muke zuba tsare-tsaren mu dan so muke muke mu fita daban cikin 'yan biki. Soyayyar mu da Yaya na kuwa sai abinda ya karu domin a kullum kaman kara wutan son junan ake a cikin zukatan mu tun Inna tana d'ari-d'ari har ta saduda ta tabbatar son so yake min lokaci kawai ake jira da zaran na kammala secondary school na za'a saka mana rana, tsakani na dashi ban san wa yafi zumud'i ba kullum cikin kirga kwanaki muke na zuwan lokacin. Tsakanin su da Baba kuwa 😂😂 babu abinda ya canza dan Baba baya tab'a yarda su had'u duk yanda Yaya na ya kai ga son su gana amma yaki yarda kowani lokaci akwai excuse da zai nemo ya bada dan kaurace had'uwan nasu. Dije anyi auren ta kusan wata biyar da suka wuce ta auri mijin ta mai suna Bala ba mai arziki bane amma akwai wadatar zuci da rufin asiri, ko bikin ma kowa sai son barka yake kasancewar anyi komai cikin tsari. Hajara tana gida an kawo ta wanka satin da ya wuce bayan ta haifi d'a ba rai sakamakon yawan dukan da take sha wajan mijin nata ga yunwa da yake barin ta dashi sai dai Gwaggo Aisha tayi musu aike na kayan abincin domin yanzu tana samu ko sana'a ta daina yi duka bukatun ta Jameela ta d'auke mata su sakamakon samari masu kud'i da ta samu amma fa a cewar Gwaggo Aisha kenan dan ni dai ban tab'a ganin wani yazo kofar gidan mu neman ta da sunan zance ba sai dai inga taci kwalliya cikin matsattsun kaya ta fita kan zata je gidan kawaye in anyi sa'a ta dawo cikin dare ta kwana a gida wata rana kuma sai tayi kwana biyu bata dawo gidan ba, ta goge ta kara haske da kyau duk da hasken na shago ne. Dawainiya kula da Yayar ta ma itace ta d'auka babu abinda ta rage ta dashi shi kuwa mijin tunda aka kawo ta gida bai kara bi ta kansu ba balle yazo ya duba ta ko yayi musu aike, wannan dalilin yasa Gwaggo Aisha d'aukan alwashin 'yar ta ta gama auren shi ko uban wa yayi mishi tsaye ta gama auren shi kenan. Hura hanci da d'aukan kai da Gwaggo Aisha take a cikin gida sai wanda ya gani Inna Asabe take kula ta wani lokacin suyi tayi dan Inna ta kam ko iskar daya d'ebo ta bai ishe kallo ba. Sosai take kokari na son ta burge Baban mu dan ta dawo da matsayin ta na da amma hakan ta bai cimma ruwa ba kasancewar Baban mu gaba d'aya hankalin shi ya dawo kan Inna ta domin ita komai zata yi mishi ko ta bashi bata yi mishi gori tsabanin Gwaggo Aisha da sai ta tsaya a tsakar gida take mishi terere kowa yana ji yana gani hakan yasa Baban fifita Inna fiye da kowa a gidan ita kuma Gwaggo Aisha wannan dalilin yasa tace asiri Inna tayi mishi kuma ko zata tafi tsirara sai ta karya shi. *Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*. [1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ *14* _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Addu'ar Mash'arul Haram* Jabir, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hau taguwarsa mai suna Al-Kaswa har ya zo Mash'arul haram, sai ya fuskanci alkibla ya yi addu'a ga Allah, ya yi kabbara, ya yi hailala, ya kadaita Allah. Bai gushe ba a tsaye yana addu'a har sai da gari ya waye sosai, sannan ya dauki hanya kafin rana ta fito. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *14* Gwaggo Aisha tana riƙe da ƙudirinta a zuciyarta na sai ta warware asirin da Inna tayi wa Baba ta maida hankalin shi kanta tayi mulkin ta a gidan son ranta saidai rashin kud'i shi yake kawo mata cikas dan Jameela ta kwana 2 bata dawo gida ba amma ta kudirta tana dawowa zata karb'a a hannunta taje ta gabatar. Bayan kwana 2 Jameela ta dawo daga yawonta ba b'ata lokaci ta same ta da zancen ta bata dubu ashirin zata je gwaza wajan wani gawurtaccen boka da kawarta lantana ta bata labari dan yayi mata maganin Inna. Ba musu balle bata lokaci Jameela ta cake mata dubu ashirin da biyar tace tasha ruwa da dubu biyar d'in,in so samu ne zata so ta had'a da ni a shafa min bakin jini ko d'an yankan kai daya makale min zai guje ni su ga ta tsiya . (hmmm wai Yayana take nufi.) "Jameela wallahi kaman kin shiga zuciyata daman ita da kinibabbiyar uwarta duk shine takamarsu, kin ga in ya rabu da ita shikenan kowa ya huta tabbas hakan zamuyi zan fad'awa bokan ya shafa mata bakin jini da ko wani namiji sai ya guje ta muga ta tsiya". Dariya Jameela ta kwashe da shi har suna tafawa da uwarta kaman wasu kawayen juna sannan tace"shiyasa nake son ki ummata". Gwaggo Aisha ta bud'i baki zatayi magana suka ji muryan Hajara tana cewa "haba Umma wannan wani irin rayuwa ce,wayan nan bayin Allah babu ruwan su damu suna zaune da kowa agidan nan da zuciya d'aya amma ku burin ku shine ku cutar dasu ya kamata mu d'auki darasi ko akan abinda ya faru dani ga Jameela ta saka yawon karuwanci a gaba kina gan............" Buge mata baki da akayi shi ya hana ta karasa maganan da tayi niyyan fad'a musu,hannu tasa ta dafe bakin ta daya fara mata zugi tana bin binsu da kallo idon ta cike da hawaye su kuma suna aikin aika mata muguwar harara "Hajara ni kike gayawa magana akan wata banza can, ni mahaifiyar ki?" Gwaggo Aisha ke yiwa Hajara tsawa tana nuna kan ta da yatsa. Gyad'a kai tayi kana tace "Ko da yake ba laifin ki bane ina ganin harda ke suka had'a suka tsafe dole sai na tashi tsaye ko kuma Bintu ta kaini ta baro,in banda aikin asiri tayaya zaki kira 'yar uwar ki wacce ta d'auki nauyin kulawa dake da wannan suna,. Kai jama'a kaji tsoron mutum Allah ya isa Bintu ki jira kiga yanda Allah zai wulakanta ki". Ta karasa cikin wani irin d'acin rai da tsantsan tsana. Jameela da har ta fara jin haushin 'yar uwar ta amma jin abinda mahaifiyar su ta fad'a yasa taji ta huce ashe ba yin ta bane itama asirce ta sukayi, haba abin da mamaki a ce wai Hajara ke kare mu bayan a baya ta san yanda tafi kowa tsanan mu. Da washe gari da sassafe Gwaggo Aisha ta fita tasha dan tafiya Gwaza domin cika nufin su akan mu. ************************** A cikin wani tsadadden Hotel Zafar yayi parking motan na shi ba tare da ya cewa Sadiq ci kan ba ya kwashi wayoyin shi tare da bud'e murfin motan ya fita. Fitowa shima Sadiq d'in yayi suka nufi hall da ake partyn tun kamin ka shiga zaka ji cool music na tashi ga wajan ya matukar tsaruwa komai cikin tsari da aji akayi shi. Angon yana ganin su ya karaso da sauri ya tare su fuskar shi cike da farinciki, ricewa wajan yayi da hayaniyan zuwan nashi, ya d'an sake fuska kad'an yana amsa gaisuwan abokan shi bayan ya zauna a mazaunin shi. Hankali kwance aka fara party shima Zafar ya saki ran shi sosai akayi shagali dashi tsab'anin wasu parties da yake guduwa saboda 'yan mata masu takura mishi amma wannan har aka tashi yana nan dan babu mace ko d'aya . Yau tunda na tashi sai shirye-shiryen zuwan Yaya na nake saboda yau kwanan shi kusan 3 kenan baya gari yayi tafiyan nan nashi da na tsana dan yanzu sosai wannan tafiyan nashi yake bani haushi ko wani sati sai ya ciri tafiya har ta kai ina yawan fad'a mishi kan wallahi in munyi aure babu inda zai tafi ya barni kafa ta kafar shi ko kuma ya daina tafiyar gaba d'aya, dariya kawai zai min a duk lokacin da na fad'i haka baya ce min komai. Tun kamin sha biyu tayi na gama girkin da zanyi mishi harda su drinks na adana su na shiga wanka,ko da na fito azahar tayi,alwala nayi na tada sallah. Light makeup nayiwa fuska sannan na kama kalaba da Inna tayi min da ribon dan gashi na baya kitsuwa sam. Riga da skirt na wani material peach color na saka kayan sun zauna a jikina duk da ba wani matse ni suka yi ba,ban saka hijabi ba rolling kawai nayi da gyalen mai d'an fad'i sannan nabi jikina da turaruka kusan kala hud'u amma duk masu sanyi ne wanda sai ka zo kusa dani kamin kaji kamshin sa. Ina gama shiryawa kiran sa na shigowa cikin tsantsan farinciki da zumud'i na daga cikin tsigar shagwab'a da zallan so na ce" Yaya naaaaa" Ina jin shi ya sauke nannauyen ajiyan zuciya ya kasa magana sai can ya samu daman cewa " pls Baby ki fito mana in gan ki ko zan samu natsuwa I'm damn missing you " Dariya na kyakyale dashi tare da make kafad'a kaman yana gani na nace" ni fushi nake da kai dan haka ko gobe ba zaka ganni ba ina gama fad'a na kashe wayan gaba d'aya ina mishi dariyan muguta. Dariya shima yayi yana girgiza kai ya san fad'a kawai nayi ko baiga fuskata ba ya san na fishi zumud'i. Na share kusan minti 15 sannan na d'auki karamin basket dana shirya mishi abinci a ciki na fita, fuskata a d'aure tam na fito tsab'anin da, da nake fitowa daga gida kuma ko kad'an naki yarda mu had'a ido dashi. Ciki-ciki nayi mishi sallama ina kawar da kaina gefe ni a dole ina fushi, amsa sallaman yayi da murmushi akan fuskar shi yana leka fuskata, cikin tsigan tsokana yace"wannan duk fushin ni kad'ai akewa,ban san me zai biyo baya ba in nace miki gobe da safe zan koma wajan aiki." A wani dame na juyo ina kallon shi da ido duk a waje hannu na na dama kuma dafe da kirji na. Dariya ya kwashe da shi har yana rike ciki ganin yanda duk na rikice lokaci 1 yace "nima na rama munyi one-one kenan,ba ni kika shanya ba har na minti 15 ba". Kukan shagwaba na saka mishi har da bubbuga kafa a kasa rarrashi na ya fara tare da cewa inyi hakuri ya daina da kyar ya samu na daina kukan shagwaban na gabatar mishi da abincin da nayi mishi, asual yaci sosai har da santi kaman yanda ya saba yace yayi missing d'in abinci na. "Kaine kake ja mana lokaci da kaso da anyi komai ya wuce abinci kuma sai ka ture" nace ina hararrar shi ta kasan ido. Murmushi kawai yayi ba tare da ya tanka ba, ni dai kwana 2 nan wannan abin nashi yana damu na sai dai ban nuna mishi ba a duk lokacin da zanyi maganan auren mu ba zai tab'a ce min komai ba. Haka yau ma na daure zuciya ta mukayi hirar mu da zai tafi ya kwaso tsaraba ta harda na 1su Inna da Baban mu ya bani sannan mukayi sallama ya wuce. Karfe tara da kusan rabi sannan su Gwaggo Aisha suka d'auki hanyan Gwaza bayan sojoji sun tabbatar musu da hanya lafiya babu wani abin tsoro,shiru motan nasu kake ji tunda suka bar gari suka shigo cikin jeji kaman babu kowa a ciki sai karan engine motan, mafi yawan mutane dake ciki sai addu'an Allah ya sauke su lfy suke banda Gwaggo Aisha data rufe ido tana ayyana yanda zata taka kowa a gidan son ran ta sannan ta shimfid'a mulkin ta har yafi na baya. Kiiiiiiiii karan kama buriki da taji da karfin gaske shi yasa ta bud'e ido a firgice tana dube-dube, salati da taji 'yan motan suka fara yasa ta kalli gaban ta ba shiri. Kululuuuu taji cikin ta ya bada wani kara a take taji guduwa na son zubo mata hannaye duka 2 ta d'aura akai ta zunduma ihu tana " wayyoo Allah na shiga uku yau me zan gani haka ni shatu?" Mutane ne sun kai kusan su hamsin fuskar su a rufe kowanne d'auke da bindiga su tare gaban motan nasu sai muzurai suke. Kowa na cikin motan jikin shi sai karkarwa yake masu kuka nayi masu addu'a nayi Gwaggo Aisha kuwa sai ihu take zunduma musu iya karfin ta gaba d'aya ta fita hayyacin ta yau ga ita ga boko haram. A fusace wani daga cikin su ya d'aga AK47 din dake hannun shi ya fara harbin sama ba shiri kowa yayi tsit, Gwaggo Aisha ko harda sake fitsari saban rud'ewa da firgita da tayi. Su kaman 5 suka matso gaban motan suka bud'e kofan motan suka ce kowa ya fito kuma duk wanda ya musu wani rawan kai ko kuma taurin kai yanzu zasu aika shi barza'u. Tsimi-tsimi duk suka fito matan su da mazan su aka saka sukayi layi , su kuma sauka rabu kashi-kashi wasu suka tsaya nan dasu Gwaggo Aisha wasu kuma suka tafi taro sauran motoci masu wucewa. "Kowa ya kawo kudin da yake jikin shi da wayan ku gaba daya" cewar wani a cikin su gashi da babban murya kana jin hausan zaka san koya yayi. Layi sukayi suna jefa kud'add'e da wayoyin su a cikin wani katon kyale da suka shimfid'a a k'asa. Suna gama zuba duk abinda suka mallaka babban cikin su wato Amir din su yace musu saura suturan jikin su duk su ciro su kawo suma ba mata ba maza. Kallon kallo suka fara a tsakanin su dan basu fahimci me suke nufi ba. "Ku cire kayan ku duka ku zuba su anan nace" ya kara daka musu tsawa daya kara hargitsa su suka kama karkarwa amma babu wanda yayi yunkurin cirewa. Tau kake ji suka d'auke wani saurayi da bindiga babu wani nisa tsakanin shi da Gwaggo Aisha. Kaman kiftawan ido suka fara rige rigen cire kayan jikin su, aka kwashe duka aka zuba su cikin wani buhu sannan suka umarci driver da su shiga mota su koma cikin Maiduguri a haka. [1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ *15* _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *15* Shiru cikin motan kaman ba wani mai rai a ciki sai muryan mata da suke kuka kasa-kasa saboda kukanta su da akai babu mai kallon d'an uwan sa duk sun takure waje d'aya suna tunanin tayaya zasu shiga gari a haka? Ita kuma Gwaggo Aisha tana ganin kaman kaifin asirin Inna shi ya hana ta zuwa ga wannan mashahurin bokan har 'yan ta'addan suka samu daman yi mata aika-aika. A wani kauye driver ya tsaya Allah ya sa akwai wani tsumamun riga da ya maida duster yana goge-goge dashi a cikin motan, shi ya saka ya fita ya karasa cikin kauyen yayi musu bayanin halin da suke ciki, nan da nan mai garin yasa aka hado musu suturu na maza da mata ya kai musu dan ba karamin tausaya musu sukayi ba. Koda ya kai musu kayan kowa ya d'auka ya suturta jikin sa sannan suka mike hanya zuwa cikin gari. Azahar dai-dai suka shigo driver ya zubar da kowa nan cikin tasha ya kama gaban shi, Gwaggo Aisha da kyar taja kafafun ta da har yanzu rawa suke saboda firgita ta fito ta samu adaidaita sahu zuwa gida duk da ta san bata da ko sisi a hannu. A hanya ji take kaman kada taje gida ta wuce ko gidan 'yan uwan ta ko zata samu canza suturan dake jikin ta wai kada su Inna su raina ta, canza akalan tafiyan tayi daga gidan mu zuwa gidan kanwar ta. Da yake duk tafiyar su d'aya da kanwar nata da taji abinda ya faru da Gwaggo Aisha maimakon ta nutsar da ita ko ta d'aura ta kan hanya saima kara zuga ta da ta rinka yi harda cewa ta samu kudi ta kara komawa, kuma kar ta kuskura ta nuna gazawar ta har sai ta kawo karshen Inna ta. Da wayan nan kalaman nata ta kara karfafa mata guiwa, sai bayan sallahn magriba ta dawo gida hankalin ta kwance kaman babu abinda ya faru, anyi sa'a Jameela tana gida cikin murna ta tarbe ta kannuwan ta duk sun zaku da son jin daddadan labarin yanda sukayi da boka, Hajara tana yi mata sannu da zuwa ta fice ta bar musu d'akin tare da nema musu shiriya daga rabbi. "Umma wannan wani irin magana ne haka kike cewa ko kuma dai sabon rainin hankali da kika zo dashi kenan?" Muryan Jameela ke tashi daga cikin dakin nasu cikin tsawa kaman ba da mahaifiyar ta take magana ba. "Na lura tunda nace ki daina sana'a zanyi miki komai kika koyi wasa da kud'i saboda baki sha wahalan neman su ba, toh wallahi nima daga rana rin ta yau na daina baki kud'i na sai dai ki koma yin sanar ki dan ba zan iya ba" ta karashe tana harare-harare ita kad'ai. Gwaggo Aisha kin kula ta tayi ta shige can d'aki ta rabu da ita domin ta lura asirin ta take son tonawa gaban kishiyoyi wanda ba zata tab'a bata daman hakan ba duk da kwanan nan alamun karara sun fara bayyana cewa Jameela ta fara tab'a shaye-shaye. Hajara kam tana gefe tana sauraron su bata da daman saka. baki Gwaggo Aisha ta hau kan ta da bala'i, Jameela ta gama suratan ta tayi ficewar ta. Bata bawa kowa labarin abinda ya same su a hanya ba ta had'iye kayan ta amma ta kudiri aniyar neman kud'i tukuru domin ta samu tara kud'i ta koma wajan bokan ta. Ko sati bai kai ba muka ga ta fara sana'ar ta na abinci kaman yanda ta saba sai dai banbancin yanzu almajiri keyi mata tallah saboda bata da yara kanana yanzu. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya wata rana dad'i wata rana kuma akasin ta, sai dai mu kam babu abinda ya canza a soyayyar mu sai ma karuwa da yake a ko wani dakika cikin zukatan mu. Cikin ikon Allah yau muka gama waec d'in mu muka fito cikin farinciki muna taya juna murna tare da fatan Allah yasa mu fito da sakamako mai kyau, IV muka shiga rabawa kawayen mu na dinnern auren yayan Maryam Shamsuddeen wanda za'ayi sati mai zuwa. "Yaushe zaki zo gidan mu muje saloon tunda shine kad'ai ya rage mana cikin shirye-shiryen bikin?" Maryam ke tambaya ta bayan mun fito daga makaranta. "Toh uwar zumud'i in kin manta let me remind u auren fa saura sati". Nace ina aika mata da hararan wasa. Dariya tayi sosai sannan ta ce" nafi ki sanin cewa saura sati kuma ai ba cewa nayi muje yau ba ko?" "A toh ai na zata tsabar zumud'i yasa kin d'auka yau ne auren,ni ya kamata inyi wannan rawan kafar kin ga munyi waec d'in mu Allah yasa kada Baba yace sai anyi neco za'ayi bikin mu da Yaya na ayi mana yanzu wallahi in lokacin yin neco yayi sai ya rako ni muzo tare ina yi mishi 'yar...." Duka da Maryam ta d'ad'a min a baya shi ya hana ni karasa magana ta, ina sosa wajan nace" ke me yasa kin cika mugun ta ne?" "Ke ko kunya ba kya ji, bari in yi hanzarin zuwa gidan ku in fad'awa Inna tayi saurin aurar dake kada ....." "Da kin taimaka min kuwa dan Allah zo muje ki gaya mata yanzu " nace in riko hannun ta. Warce hannun ta tayi tana" Allah ya shirye ki Zareefa". Mukayi dariya dukan mu. A nan mukayi sallama ta shiga motan su da driver yake jiran ta nima na shiga a daidaita da yake zuwa d'auko kuma ya kawo ni makaranta kullum kaman yanda Yaya na ya tsara. Tun daga wannan rana bamu kara had'uwa da Maryam ba suna can hidima tayi musu yawa amma kowacce rana sai munyi waya kuma tana neman inje in taya ta wasu abubuwa sai dai kwata-kwata bana cikin natsuwa kasancewar Yaya na yau kusan kwanan shi 5 kenan da yin tafiya amma shiru bai dawo ba kuma wayar shi bata shiga balle inji lafiyar shi. Wannan dalilin yasa bani da kwanciyar hankali sam shiyasa na kasa zuwa gidan su Maryam d'in, haka kawai kuma nake jin yawan fad'uwar gaba har na kasa daurewa na fad'awa Inna tace min inyi ta addu'a ba abinda zai faru. A haka na daure nake dan al'amura na har ta kai gobe ne dinner gidan su Maryam kuma tun safe ta matsa min da waya kan yau bata son wani excuse lalle inzo da safe dan akwai abubuwan da zamuyi, ba dan ina so ba na amsa mata da toh kawai na katse waya ta dan rashin jin labarin Yaya na ya sanya bana jin dad'in duniya sam. Da washe gari ma Inna ce ta matsa min akan in tafi tun safen tunda haka ta bukata ko akwai ayyuka da zan kama musu itama tana zuwa anjima kad'an,dole na na shirya nayi mata sallama na fita. *********************** Tun jiya yaje tsadadden saloon da yake zuwa aka aske mishi gashin da ya tara kuma akayiwa askin zamani, sanin cewa in Abba shi ya gani ba zaiyi mishi da sauki ba , ko da yaji Abban nashi ya dawo duk daukin son ganin shi da yake sai da ya d'auko natsuwa da jarumta sannan ya nufi part din iyayen nasa cikin fargaban kada yayi mishi maganan aure. A parlour ya tadda su zaune suna hira Abba na shan fruit salad da Momy ta had'a mishi da kan ta. Kusa da kafafun shi ya karasa ya zauna tare da d'aura kan sa akan cinyan Abba ya kwantar, cikin tsantsan kaunar tilon d'an nashi ya hannu yana shafa kan a hankali fuskar shi d'auke da murmushi yana matukar son d'an nashi sai dai wasu halayan da ya kwaso marasa kyau ya d'aurawa kan shi yasa basa shiri, ganin sa cikin shigar kamala kad'ai yau yasa shi farinciki. Babban burin shi yanzu shine yaga d'an nashi yayi aure ko zai natsu ya daina abinda baya so sannan shima girma ya fara zuwa mishi yana bukatan hutu yana son d'aura shi kan d'inbin dukiyar shi da shi kan shi bai san iyakar su ba. Cikin girmamawa yayiwa Abban nashi barka da zuwa shima ya amsa cikin kulawa, zama ya gyara ya d'auki spoon d'in da Abba shi ke shan fruit shima ya fara sha yana kai na farko baki ya lumshe ido yace" Mom ji yanda wannan fruits din yayi dad'i amma ni in nace ki min ba yayin dad'i haka". Mom tana dariya tace" kayi aure matar ka zata yi maka wanda yafi wannan dad'i". Ras yaji gaban shi ya fad'i meya kai shi fad'in haka gashi har an tabo zancen da baya so ayi ta agaban Abba, shima dariyan yayi da son kawar da zancen yace" yauwa Mom abokinaboki na shamsuddeen nan da kike ta yabon shi kullum gobe ne fa auren shi anjima kad'an ma zan je dinnern kuma dasu Sadiq....." "Aikin kenan zuwa dinnern wasu amma kai baka tab'a tunanin kaima kayi settling down, ko har yanzu kana tsamanin yaro kake komawa?" Abba ya katse musu zancen cikin daure fuska da zaka san ran shi a bace yake. "Anyway duk ma laifi na ne da na zuba maka ido ina kallon ka da sunan ina jiran ka kawo min matar da kake so da kan ka,but tunda baka fahimta ba let me make my self clear, kwana 3..... Wallahi kwana 3 kacal na baka in baka fito da wacce kake so ba kauye zan je in samo maka mata cikin 'ya'yan dangi, in kuma ka d'auka wasa nake maka ka jira kwana 3 ka gani" Abba yana gama maganan shi ya mike fuuu ya bar musu parlon. Cikin wata irin murya mai cike da tashin hankali ya rarrafo gaban Mom ya fara magana" Mom pls ki bashi hakuri wallahi ni banida wacce nake so a yanzu dan Allah ya kara min lokaci wallahi zan kawo ta har nan ku gan ta". "Wannan karon nima babu hannu na a ciki saboda ka kai Abban ka makura sannan ni kaina ina son ganin auren ka ko dan jikoki su cika mana gida, so count me out of this" itama tana gamawa tabi bayan mijin ta suka bar Zafar cikin fargaba da tashin hankali. [1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *16* Zafar ya kai kusan 30 mins a zaune wajan sai share gumi yake duk da sanyin A.c dake parlor amma bai hana shi jikewa da gumi ba, ta ina ma shi zai nemo mata cikin kwana 3 kacal, shi fa ya raina 'yan mata 9ija kuma koda yayi karatu abroad bai samu wacce ta kwanta mishi a rai har yace zai iya auren ta ba. Ringing d'in waya ne ya dawo da shi hayyacin sa amma ya kasa d'aga hannu ya d'auki wayan balle ya amsa,sai da akayi mishi 2 missed calls a na 3 ne ya d'auki wayan ya kai kunne yayi shiru. "Zafar kana ina ne baka karaso ba, tun d'azu Shamsuddeen ya dame ni da na kira ka wai har an kusan tafiya hall" muryan Sadiq yaji cikin wayan yana magana, bai iya bashi amsa ba ya cire wayan daga kunnen shi ya mike a hankali ya fara tafiya cikin kasaita daya zame mishi jiki. Part d'in shi ya shiga bai tsaya a parlour ba ya wuce bedroom ya fad'a kan makeken gadon shi da a kalla zai lashe mutane 7 ba tare da wani takura ba, tunani kawai yake tayi dan komai na duniyan ya fice a ran sa bare zuwa bikin nan, bai dad'e da kwanciya ba d'ayan wayan shi ya fara ringing shima kaman ba zai d'aga amma ya daure ba tare da ya lura da sunan mai kiran ba ya amsa wayan, muryan ango Shamsuddeen yaji yana mishi magana. "Haba Zafar yanzu ka kyauta min kenan, har an fara shagalin biki na baka ciki?" "No Shams it's...., No just ba zan iya zuwa ba saboda wani dalili nd......" "Dan Allah mana kada kace haka please ko minti 2 ne Zafar we really need u here ,pls I'm begging..." "Stop that mana sai ka roke ni ne zan zo bikin ka, aiko saboda Sadiq zan zo ko yanzun ma wani issue ne yake son shige min gaba but gani ni nan zuwa tunda kace ko minti 2 then I will come sai dai ba zan dad'e ba" yana gama fad'in haka ya katse wayan tare da mikewa zuwa bathroom. Can b'angaren su Ango kuma sadiq yana kallon Shamsuddeen daya gama waya yace" ya zai zo d'in?" Gyad'a kai shamsuddeen yayi yana murmushi suka cigaba da shirin su. ******"""""******* Tunda nazo gidan bikin na daure zuciya ta ake ta hidima da ni sai kai komo muke, cikin wannan yanayin ban fasa trying number Yaya na ba sai dai amsar daya ce a kashe har a wayan Maryam na gwada wai ko daga layi na ne a natan ma switch off ake ta maimaita min, bayan munyi sallahn la'asar Maryam ta takura min muka tafi saloon inda akayi mana gyaran gashi lalle sannan aka mana kwalliyan mu. Muna dawowa daga saloon muka saka ankon mu na material Les dark blue da tie milk color sosai kayan suka zauna a jiki na, nayi wani kyau ina haske sai ka zata nice ma Amaryan , Maryam itama tayi kyau sosai abinta, Lokaci yanayi mutane suka fara tafiya ga motoci birjik sai wanda ka zaba zaka shiga wasu kuma a nasu suke tafiya, duk yanda Maryam tayi min nasiha kan in saki raina cikin jama'a in kwantar da hankalin na Yaya na yana lafiya amma na kasa. Ko da muka isa ma banyi wani abu ba na nemi waje na zauna kan wani table da babu kowa saboda ina bukatan kad'aici na fad'a duniyar tunani anya Yaya na lafiyan shi kuwa Allah yasa haka Allah ya kare min shi duk inda yake Ameen. Haka na cigaba da tunanin shi ina yi mishi addu'a Allah ya kare shi yasa yana cikin koshin lafiya tare da kokuwa da hawaye cikin ido na da suke ta bara zanan zasu fito ina maida su ciki. **************** A hankali yake takun sa cikin natsuwa da kasaita ya nufi wata bakar latest Honda wanda zai fita dashi, tsab yake kaman wani basarake yayi matukar kyau cikin half jamfa na wani arnanen voile milk color mai duhu wanda ya kara haska farar fatan sa, bai saka hula ba,gashin kan shi da sajen shi sun sha gyara sun kwanta lub sai sheki suke sai kamshin tsaddaun perfumes d'in shi yake, bai yiwa iyayen nashi sallama ba ya fad'a motan shi yaja ya tafi. Sowan abokan sa sosai ke tashi a lokacin da ya iso na murnan zuwan nashi dan wasu sun fidda ran cewa zai zo, bai biye musu ba hannu kawai ya d'aga musu ya wuce ya samu waje ya zauna yana auna maganan Abban shi wai shi zai had'a shi aure da 'yar kauye shida na birnin ma basa burge shi in aka aura mishi ita ko Ina zai kai ta, oho. Yana cikin zancen zuci yaji an dafa mishi kafad'a a dan razane ya d'ago yaga Sadiq ne tsaye a kan shi yana mishi murmushi yace " lafiya kake kuwa tun d'azu ina tsaye s kan ka ina maka magana baka ji ba har sai da na tab'a ka, kuma baka je kun gaisa da Shams din ba kazo ka zauna kai kad'ai". Zafar kallon shi kawai yayi ya d'auke kai ba tare da yace mishi ci kan ka ba kuma bashi da niyyan tankawan. A zuciye Sadiq ya mike zai bar wajan yana fad'in " d'an rainin hankali kada Allah yasa kayi maganan ai dama ka saba wulakanta mutane...". Caraf yaji Zafar ya riko hannun shi ta baya tare da dawo da shi baya fuska a had'e yace" seat" Ba musu Sadiq ya koma ya zauna yana mai nazarin yanayin Zafar d'in ,duk da bai cika faran-faram da mutane ba amma yaga tarin damuwa da tashin hankali a tare da shi kasancewar shine mafi kusanci dashi bayan iyayen shi. "Wats wrong u look so disturbed?" Sadiq ya tambaya cikin kulawa. Hannun shi duka 2 ya d'aura a goshi yana murzawa kaman ba zai amsa ba can kuma yace" ina cikin damuwa Sadiq kasan yau Abba ya dawo da naje...." "But naga kayi aski ai ko an bashi labarin kaje wani party ne?" Sadiq ya tambaya yana dariya. "Shut up just shut up it'ss not a joke ina gaya maka damuwa na nd u e making fun of me" Zafar ya katse shi a hasale. "I'm sorry sorry pls I don't mean it naga kawai shine matsalan ka da Abba most time" cikin rarrashi da kwanantar da murya Sadiq yake magana yaga da gaske abokin nashi ya fusata. "In wannan ne da sauki kaima kasan ba zai dame ni ba cos I'm used to it " sai da ya sarara yana had'iyen zuciya alaman abinda zai fad'a ya mishi zafi yace "can u imagine abba ya bani 3 days wai in kawo matar da zan aura ko ya had'a ni da 'yar kauye". Dariya Sadiq ya kwashe da shi harda rike ciki yace" kai nagodewa Abba yayi min maganin ka Wallahi ba ka raina 'yan matan Nigeria gaba d'aya ba, shikenan anyi maka mai kankat waya ga Zafar da village girl. Kasan me on ur wedding day ko kuma on ur dinner with d village girl nine zan....." A fusace Zafar ya mike ya koma wani table ya bar Sadiq na kwasan dariyan mugunta, yana zaune a wajan sai saka da warwara yake na yanda zai zillewa auren da Abba keso ya lik'a mishi idon shi ya sauk'a a kaina da nake zaune a gefe ni kad'ai kai na a sunkuye kan waya ta sai neman layin Yaya na nake da bata shiga. Ido ya zuba min ko kiftawa baya yi harda tagumi yayi kana ganin shi kasan yayi zurfi cikin nazari ni kuma ban san wainar da ake toyawa ba. Tab'a shi da akayi ya dawo dashi daga dogon tunani daya tafi ya juya yaga Sadiq ne, gira daya ya d'aga mishi yana murmushi yace " da alama dai Abba ba zai had'a ka da village girl ba". Cikin sauri shima ya amsa yana" yes I won't let dat happen Sadiq, look at dat girl Sadiq" yace tare da kallon inda nake zaune, bin wajan da kallo Sadiq yayi kamin yace" yes na ganta tun a can nake kallon yanda ka tsare 'yar mutane da ido, so finally Zafar got d love of his life,love at first sight huh" Buge mishi kafad'a Zafar yayi yana hararan shi yace " dallah can who told u I love her kaima ka san abinda ba zai tab'a yiyuwa bane *BA SONTA NAKE BA*. I just have plan on her dat will free me from Abba". Masu tambayan karshen Uwani ku kara hakuri shima zan cigaba nan bada dad'ewa ba. [1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *17* Komawa yayi ya zauna bayan ya tsurawa Zafar ido sannan yace" ban gane me kake nufi ba, *ba sonta kake ba* pls ka warware min ka saka ni a duhu" cewar Sadiq kenan. Ajiyan zuciya ya sauke mai nauyi irin ya samu relief d'in nan yace" well ba wani abu bane just zan kai ta a matsayin wacce zan aura wajan Abba in akayi auren shikenan I'm a free man ba mai takura min akan rashin aure in tayi 1 or 2 month sai in sallame ta, that's all". "What!! " Sadiq ya fad'a cikin zare ido sannan ya cigaba "Zafar me kake nufi da cewa zaka aure ta bayan wata d'aya ko biyu ka sallame ta, rayuwar 'yar mutane zaka lalata saboda cikan burin ka, haba my friend kada ka zama mai son kan ka mana wannan abinda kake yunkurin yi kuskure ne Babba". Wani kallo Zafar ya watsa mishi na irin ka raina ni nan ya kawar da kan shi gefe kaman ba zai tanka ba ya bud'i baki yace " did u expect har wani abu zai shiga tsakani na da ita ne? Zata amsa sunan mata tane a idon duniya but a zahiran ce ba haka bane kaima kasan irin wa'yan nan yaran ko kallo basu ishe ni ba balle ace zan so irin su ko kayi tunanin ni Zafar zan had'a shimfid'a da ita" ya fad'i hakan yana yatsina fuska kaman yaga kashi, shi dai Sadiq bai katse shi ba illa zuba mishi ido da yayi yana sauraron shi. "Zanyi hakan ne kawai dan samowa kai na mafita dan haka stop dreaming cos ni *Ba sonta nake ba* as I said earlier" ya karasa fuskar shi d'auke da sansayan murmushi. Har yanzu Sadiq ya kasa samun kalma ko d'aya da zaiyi amfani da shi ya gane abinda yake babban kuskure ne, shi kuwa hankali kwance ya zuba min ido yana kare min kallo a lokacin Maryam tana tsaye a kaina kan lalle sai mun shiga cikin masu rawa muyiwa Ya Shamsuddeen liki amma nace mata ba zan shiga zan koma gida saboda zazzab'i da naji yana son rufe ni. Bata yarda ba sai da ta d'aura hannun ta kan goshi na taji zafi rau, a take taja kujera dake opposite da nawa ta zauna fuskarta d'auke da dumbin damuwa ta kama hannu na tace" Zareefa pls ki kwantar da hankalin ki nasan damuwa da kika saka a ranki shi ya haifar miki da zazzab'in nan,addu'a ya kamata muyi tayi Allah ya dawo dashi lafiya" duk cikin sanyin murya da tsigan lallashi take maganan. Cikin son sakani dariya tace " ke nifa nafi ki damuwa Yayan mu ya dawo musha biki kin ga da bikin ku ne da muna can high table ba nan ba" Ta koyi nasara dan murmushin da ban shirya ba ya tsubuce min tare da hawayen da nake shanye su tun d'azu, Maryam ba zata tab'a ganewa ba ni kad'ai ce na san yanda nake ji a cikin zuciya ta. Rarrashi na Maryam ta fara da kyar ta samu nayi shiru ina ajiyan zuciya duk su Zafar suna kallon mu daga inda suke zaune, mikewa nayi ina gyara head tie dake kaina nace mata " zan tafi Maryam dan Allah kada ranki ya b'aci yanzu haka har na fara jin sanyi yana son rufe ni". "No babu komai muje in raka ki but tayaya zaki tafi bayan baki da lafiya?" Maryam ta tambaya cikin kulawa. Zan iya kada kiji komai" na bata amsa ina dafa kaina da nake jin kaman ya fashe. "Thats d right time " cewar Zafar tare da shuran car keys d'in shi akan table , ba tare da ya juyo ba ya cewa Sadiq" zo muje". Biyo shi Sadiq d'in yayi yana son yaga mai zai yi da yake cewa wannan shine right time, can gefen wasu flowers ya samu ya tsaya bayan ya fito daga cikin hall, Sadiq shima gefen shi ya samu ya tsaya. Ko minti 3 basu yi da tsayuwa ba muka fito muma daga cikin ina tafiya a hankali ,har muka iso inda suke ni ban san da mutane a wajan ba naji muryan Maryam tana " Ya Sadiq ina wuni ku" Sadiq d'in ne kad'ai ya amsa da " lafiya lau Maryam ya kuka fito lafiya kuwa?" "Wallahi k'awa tace bata da lafiya shine na rako ta zata tafi gida" "Subhallah Allah ya bata lafiya, amma ba zata iya driving a wannan yanayin ba ko da driver tazo?" Sadiq ya kara tambaya. "No zan rakata bakin hanya ta hau napep ne". "Allah ya bata lafiya" yace tare da kallon Zafar daya d'auke kan shi kaman baya jin me suke cewa alhalin duk hankalin shi yana kan mu. Zungurin Sadiq yayi tare da yi mishi magana da ido, cikin sauri Sadiq yabi bayan mu ya tsaida mu yace " nan anguwan abin hawa yana wahala bari mu sauke ta tunda muma fita zamuyi" Cikin farinciki Maryam ta fara musu godiya tare da jan hannu na zuwa wajan wata mota daya bud'e mana, da ido nakewa Maryam nuni da ba zan shiga motan su ba ita kuma ta min nuni da babu komai 'yan gida ne, rashin karfin jiki da hajijiya da nake ji ya bata daman tusa ni a bayan motan ta rufe tana d'aga mana hannu. Kwantar da kaina nayi a jikin seat d'in tare da lumshe ido na fara shak'an wani fitinannen kamshi da ban tab'a ji ba a rayuwa ta, ina ji motan ya fara tafiya amma na kasa bud'e ido na can naji Sadiq d'in yana tambaya ta wani anguwan zasu sauke ni? Sai da naji a jiki na alaman ana kallo na ban damu da in bud'e ba saboda nasan sunan anguwan mu da na fad'a ne ya bashi mamaki kasancewar duka gidajen talakawa ne a anguwan. "Sai ki nuna mana inda zamu bi mun shigo anguwan naku" muryan Sadiq ya katse min tunani, a hankali na bud'e ido sannan na nuna mishi hanya da zamu bi can nesa da gidan mu nace ya sauke ni anan. Parking yayi daga gefe na bude kofan na sauka sauka a hankali cikin muryana mai sanyi da baya fita sosai nace " nagode jazakallahu khairan" na kama hanyan gida ina layi,da ido Sadiq ya rakani har na shige ciki. Gyaran murya Zafar yayi wanda ya dawo da hankalin Sadiq ya juyo yana kallon shi yace" sai ka gaya min ma'anan kawo ta gida sannan dan wulakaci kaja baki kayi shiru na tabbata bata san mu 2 muka kawo ta ba. "Mu tafi Mallam ba wai ka kama min tambayoyi ba" Zafar yace hankalin sa na kan wayan shi, girgiza kai kawai Sadiq yayi yaja motan suka fita daga layin dan wannan halin abokin nashi ya ci ace ya saba. Da kyar na kai kaina d'akin mu na zube a gefen Inna da take kwance a kan gado,a firgice ta tashi zaune saboda ta fara bacci kuma bata ji shigowa ta ba. "Wani irin rashin hankali ne wannan zaki shigo min d'aki ba sallama sannan kuma ki fad'o min a ka sai kace wata 'yar maye, ko daga wajan bikin kika koyo ne..." Shasshekan kuka na da taji shiya dakatar da ita daga fad'an da take min cikin fargaba ta d'ago ni ta fara dudduba jikin na tana tambaya ta meya faru??? "Inna Yaya na yau kusan sati da yin tafiya amma har yanzu babu labarin shi ga wayar shi bata shiga, Inna tsoro nake ji anya yana lafiya kuwa? Yaya na ba zai tab'a mantawa dani ba har na tsawon sati ba tare da yaji lafiya ta ba Inna kin..." Rufe min baki da Inna tayi da hannun ta yasa nayi shiru ina kallon ta hawaye na bin fuska ta. "Babu abinda ya same shi insha Allah yana cikin koshin lafiya,bana son kina sawa kanki damuwa dayawa ki bari zuwa gobe da safe sai mu san yanda zamu bullowa lamarin" duk cikin rarrashi take min magana hannun ta kuma na kaina tana shafa gashina daya sha gyara ya kwanta yayi lub. Jin ina sauke ajiyan zuciya kuma numfashi na fita d'aya-daya yasa ta gane nayi bacci, gyara min kwanciya tayi tare da zuba tagumi ta zauna tunani yanda zata bullowa wannan al'amarin domin babu abinda yake d'aga mata hankali kaman ganin tilon 'yar ta cikin tashin hankali, balle ma wannan na soyayya. Kusan raba dare Inna tayi kan sallaya tana nafilfilu tare da kai kukan ta wajan Rabbi izzatti ya shiga lamuran 'yar ta ya zaba min abinda yafi alkhairi. Koda gari ya waye da kyar na tashi daga kan gado nayi sallah na kara komawa na kudundune cikin bargo ina rawan dari saboda sabon zazzab'i da ciwon kai daya tsanan ta min, cikin matukar damuwa Inna ta had'a min tea mai kauri ta lallab'a ni na sha kad'an sannan ta b'allo paracetamol 2 ta bani tace in sha zuwa azahar in babu sauki sai mu tafi asibiti. Cikin ikon Allah ina kwanciya bacci mai nauyi yayi gaba dani sakamakon jiya ban samu ishasshen bacci ba, gaba d'aya fita daga d'akin Inna tayi wai kada tayi wani babban motsi ta katse min bacci anan ta cigaba da ayyukan ta cikin dauriya. Kaman a cikin mafarki naji waya ta tana ringing, da kyar na bud'e ido na da suka min matukar nauyi. A zabure na tashi na zauna ganin sunan da na gani yana yawo kan screen d'ina, a hanzarce na d'aga kiran na kai kunne na kamin ya min magana na fashe mishi da matukar kuka kaman zan shid'e. "Ki fito ina waje" yace min cikin wata murya da ban san shi da ita ba, amma duk da haka ban tsaya b'ata lokaci ba na diro daga kan gado dama da hijabin da nayi sallah asuba a jikina na kwanta dan haka takalmi kawai na zura na fito kofar gida ko lura da Inna dake tsakar gida banyi ba burina shine inje in saka shi a idanu na ko zanji sanyi a cikin raina. Inda ya saba parking anan na gan shi tsaye ya juyawa kofar gidan mu baya haka kawai sai naji jikina yayi sanyi sosai a haka naja kafa na isa inda yake cikin murya na daya dashe saboda kuka da nasha nayi mishi sallama. Amsawa yayi yana juyowa muka fuskanci juna, kasa tsaida hawayen ido na nayi ina kallon fuskar shi mai sanyaya min rai nace" barka da zuwa Yaya na aikin ne ya rike haka, wannan karon ka dad'e sosai har ya saka ni cikin matukar damuwa ga number ka bata shiga". "Lafiya lau mana, hmmm kema dai Zareefa meye abin damuwa anan kin san in nayi tafiya bana saka miki ranan dawowa balle kice har kwanakin sun wuce ban dawo ba sannan tun a baya na gaya miki wajan babu network shiyasa bana iya kira ko a kira ni". Ya bani amsa hankali kwance. Amsar yasa duk naji wani iri amma na daure tare da share hawayen fuska ta da gefen hijabi na ina sakin mishi murmushin da nasan yana saka shi farinciki nace" hmm ka gama komai ka yanzu dan wallahi in akayi mana aure ba zan yarda kana tafiya kana bari na ba kafar ka kafata". Sun glasses na fuskan shi ya gyara yana kallo na ta ciki yace" Zareefa kenan kin ga matsalar ki kenan wanda yasa nake ganin ba zamu iya zama inuwa d'aya ba". Rass-rass naji zuciyata ta wani irin bugawa da har sai da na kai hannu na kan tsaitin wajan ido a waje nake kallon shi dan na rasa bakin magana, can dai nayi dariya kad'an ganin bai kara ce min komai ba nace " Allah Yaya na ka bar min irin wannan wasan zaka saka zuciya ta bugawa wallahi". "Wasa!! Wasa fa kika ce, u see kina da matsaloli dayawa a rayuwar ki da in mutum ya duba koya auna ba zai fara ma kusantar inda kike balle maganan aure ya shiga tsakani, ke ko irin kunyan nan da aka san mace dashi baki da ita kullum maganan ki d'aya aure-aure mtsw..." Yaja dogon tsaki yana kawar da kai gefe kaman yaga abin kyama. Ko kifta idona na kasa yi balle in iya cewa wani abu kawai ji nake wasa yake min jira nake in ga ya juyo yace min wasa yake amma ko kallon inda nake bai kara yiba. Murya na rawa da son kara tabbatarwa kai na ba mafarki nake ba nace" Yaya na kaine kuwa ,nice fa kanwar ka Zareefa". "Zareefa my foot me mutum zaiyi da macen da bata kamun kai, tunda can daure zuciya ta nake tare da saka ran zaki canza wata rana sai dai da alamu nayi kuskure dan abin naki kara gaba yake. Pls ki bar nan in daina ganin ki ko zuciya ta zatayi sanyi saboda yanzu ko ganin ki nayi zuciya tafasa yake, dama abinda ya kawo ni kofar gidan ku kenan kada ki kara kira na a waya cos I don't have time for cheap girls like u". Yace yana min wani kallon tsana. Wani irin kuka na fashe da shi na juya zuwa cikin gida da gudun tsiya har bana iya ganin gaba na, saura kad'an in mangaje Baban mu da yazo fita yayi sauri ya bani hanya na wuce shi zuwa cikin gida ko waiwayowa banyi ba duk da kira na da yake ta faman yi. A masifance yace" wani d'an kwal uban ne ya tab'a ki a anguwan nan, bari inje in gani duk wanda na gani mai raba ni dashi sai Allah" ya faman gyara babban rigan shi ya nufi hanyan fita. Da sauri ya dawo da baya yana zare ido tare da dafa kirji yace" wai-wai dama da wannan hukuman ne????? [1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *19* "Masha Allah an gode ranka ya dad'e har zaku tafi kenan?" Su Zafar suka tsinkayi muryan Baban mu a bayan su, wani malalacin murmushi yayi sannan ya juyo yana yiwa Sadiq signal da ido. "Eh Baba zamu wuce tunda jikin nata da sauki sai mun kara dawowa" Sadiq ya bashi amsa ya juya zuwa ga motan nasu. Zafar gaban Baban mu ya dawo ya tsugunna yana wani sunkuyar da kai kaman mutumin Kwarai yace" nagodewa Allah daya had'a ni da kai Baba, dama na dad'e ina son muyi magana amma ta ki hadani da kai". "A'a ranka ya dad'e ni kuma gani na abu ne mai sauki me kake bukata?" Baba ya amsa jiki na rawa. Sai da ya d'an sosa keya alamun yana jin nauyin abinda zai ce yace" Abba ne yake son su zo ayi maganan aure na da ita, shine nace bari in fara fad'a maka in ka amince sai su zo" wannan karan Baba rasa inda zai saka ran sa yaji dad'i yayi ji yake kaman ya kurma ihun murna sai dai ba hali cikin sauri har muryan shi na rawa yace" kai amma yaro yaro ne meye na wani sai an tambaye ni, bayan babu inda zan je kullum ina gida. Ko yau suke so su zo ina jiran su kaji?". "Toh Baba nagode, mu zamu tafi" yace tare da mikewa ya kara ciro wasu bundles d'in ya zubar da su a gaban Baba sannan ya mike har suka fita daga compound d'in Baba bai dawo daga suman ganin makudan kud'ad'e daya tafi ba. Sun hau kan hanya ba tare da Sadiq ya kalle shi ba yace " Zafar it's wrong, it's totally wrong". "And who are you to say so?" Zafar ya tambaye sh yana kara cin magani, Sadiq bai kara ce mishi uffan ba sai ma kara maida hankalin shi da yayi kan tukin da yake. A nan asibiti kuwa Gwaggo Aisha kasa zaune ta kasa tsaye sai jujjuya ido take wai me yake shirin faruwa ne, bata gama da wancan ba kuma ace ga wani ya bullo? Ita abinda yafi d'aga mata hankali shine ita 'yan matan ta basa samun masu kud'i sai ni, shi wannan kam bayan mai kud'in ne kuma gashi balarabe. "Wallahi ba zata tsabu ba wai bindiga a ruwa wannan karan sai ta raba ni da komai na jin dad'in rayuwa ko da duk abinda ta mallaka zasu kare ba zata tab'a zuba ido Bintu da 'yar ta su kasance fiye da ita da yaran ta ba. Kaman wacce aka tsikare ta da allura muka ga zuruf ta mike fuuu tayi waje kaman wata kububuwa,da ido kowa ya bi ta dan tunda su Zafar suka fita babu wanda yayi magana cikin d'akin kowa da kalan tunanin da yake a cikin zuciyar shi. Tashin hankali da Gwaggo Aisha ta tarar a waje yasa taji kaman ta kurma ihu dan bakinciki, akan idon ta Zafar ya yiwa Baba kyautan makudan kud'ad'e suka shiga mota su dashi kad'ai ta kalla ta san cewa kud'in sa ya wuce duka tunanin ta. Ganin Baban mu ya hangame baki ya kasa dawowa hayyacin sa tunda yaga ruwan kud'i ya kara tunzura ta, ta taho a fusace ta cikin d'aga murya tace "kai Mallam meye haka?" sai a sannan yaja doguwar ajiyan zuciya ya juyo ya kalle ta,ba tare da yace mata ci kanki ba ya kwashi kud'add'en sa yayi gaba abin shi. Sosai Gwaggo Aisha ta shak'a wato ya mai da ita mahaukaciya ko? Zasu gani zata nuna musu ainihin true colors d'in ta zasu san da ita suke zancen, sai matsayin ta na da ya dawo ta cigaba da mulkan gidan baki d'aya. Bayan fitan Gwaggo Aisha Inna abu da Hajara suka mike sukayi mana sallama tare da yi min Allah kara sauki suka fita, cikin sauri Inna tabi bayan su dan basu kud'in mota d'akin ya kasance daga ni sai Maryam da Maa da ta juya mana baya ta kwanta da alamu dai tayi bacci. "Ni fa na kasa yarda Yaya na zai min haka, saboda yana matukar so na Maryam wallahi yana so na" na karasa ina fashewa da sabon kuka. Gyad'a kai kawai Maryam ta iya yi min tana share hawaye itama saboda ta shiga duhu sosai a yanda muke matukar son junan mu ace ya juya min baya lokaci d'aya, tabbas babban al'amari ne zai iya raba mu , addu'an ta Allah ya daidaita tsakanin mu. "Kiyi hakuri Zareefa ko wani tsanani yana tare da sauki, mu cigaba da addu'a insha Allah komai zai daidaita" ban iya bata amsa ba sai kuka da nake ina jin zuciya ta na min wani irin suya. "Hmmm ni ban san su Ya Sadiq me ya kawo su nan ba abin ya daure min kai" cikin sauri na d'ago da kaina ina duban ta dama tambayoyin dake cin raina kenan su waye su, kuma menene dalilin zuwan su har asibiti duba ni ba dan ni dai ban san su ba. "Ai na zata wajan ki suka zo " na fad'a da dashassiyar murya ta. Girgiza kai ta shiga yi kana tace " ko d'aya, na shirya ina shirin zuwa duba ki kiran Ya Sadiq ya shigo bayan na d'aga mun gaisa yake tambaya ta labarin ki shine fa nace mishi nima yanzu zan zo duba ki anyi admitting d'in ki a Kanem Hospital, sai naji yace suma gasu nan zuwa in sun iso zai kira waya ta in shigo da su. Ni dai da toh na bi shi ina mamakin ya akayi ya samu number ta". Ido kawai na zuba mata ina sauraron ta itama tace haka toh ni kuma in ce me kenan. "D'ayan kuma shine Zafar Baban shi multi millionaire ne maybe ma zaki san shi sunan shi....." Saurin katse ta nayi nace" bana bukatan ji koma shi d'an wanene wannan damuwar shi ce nima ki bar ni inji da nawa damuwar". Shigowan Inna yasa muka bar zancen ta cigaba da bani baki, cikin dabara ta zubo min pepper soup na kayan cikin rago da ta kawo min naci ba laifi da yake tana ta Jana da hiran Yaya na sai gashi na d'an ware muna hira. Sai kusan azahar sannan Maryam tayi mana sallama ta tafi, a takaice sai da nayi kwana 2 a asibiti sannan aka sallame mu. Cikin kwanaki 3 nan da nayi a asibiti kullum ido na yana kan hanya wai ko zanga Yaya na yazo duba ni yace min wasa yake amma shiru kuma kullum cikin gwada layi shi nake amma ko sau d'aya bai tab'a shiga ba. Cikin kwanaki 3 nan da mukayi a asibiti abubuwa da yawa sun faru cikin su kuwa yanda Zafar ya bi ya shiga jikin Baban mu yayi amfani da son abin duniya na Baban mu ya saye shi tsaf har yayi mishi alkawarin bani da wani miji a duniya sai shi, hakan kuwa ba karamin dad'i yayi mishi ba dan ya san yanzu bashi da matsala ta ko Ina . Da yamma muka dawo gida nan da nan gidan ya cika da makota da basu samu daman zuwa asibiti duba ni ba suka shigo suna min ya jiki, har mutanen suka watse Gwaggo Aisha bata shigo ba dama rabon ta da asibitin tun ranan da suka je duba ni dukkan su daga nan bamu kara ganin ta ba sai Inna Asabe ce mai zuwa ita da Hajara, Jameela kam tunda aka kwa tar dani bamu ga keyar ta ba balle kuma yanzu kila ma bata gidan ta fita wannan gantalin nata. Zafar da Sadiq sai da suka kusan samun tsab'ani a kaina wai lalle sai Sadiq yazo ya same ni ya min bayanin auren shi kuma yace ba da shi ba wannan dan wallahi in ya kuskura ya turo shi wajena ce mishi zaiyi sona yake kaman rayuwar shi shiyasa ya turo shi in taimaka inji tausayin shi in aure shi. Wannan magana da Sadiq yayi ba karamin tunzura Zafar yayi ba wai kaman shi za'a ce wai k'aramar yarinya mara class mara kyau wacce yake ganin in ba dan takurar Abban shi ba ko a mai wanke-wanke gidan shi ba zai d'auke ni ba balle ace wai sona yake Allah ya kiyaye. Cikin fushi yaja motan shi yayi hanyan gidan mu dan dole ayi ta ta kare saboda yau ne deadline da Abban shi ya bashi, shi kuma Sadiq yayi hakane dan yaje da kan shi saboda gaba yake jiye mishi amma shi sam baya gani. Ina zaune kan sallaya dana idar da sallah isha'i nayi zuru ina tunanin ta yaya zan iya rayuwa ba tare da Yaya na ba, shine komai nawa na taso da soyayyar sa cikin jinin jikina duk wata rayuwa da shi na tsara yanzu rana tsaka ace ya rabu dani, to ya zanyi da rayuwata? Muryan kani na Ibrahim naji yana cewa Inna ta daya tarar a waje wai ana sallama da Zareefa. Ban tsaya jin me Inna tace mishi ba na fita da sauri kaman zan had'a da gudu, a zuciya ta ina haba na sani mana shima ba zai iya rayuwa babu ni ba na san dama wasa yake min. Murmushin dana fito da shi a fuska tace ta b'ace bat ganin wanda ban tab'a zato ba tsaye a kofar gidan mu. [1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *19 & 20* Ina fitowa na ga ya ajiye motan sa a inda ya saba ajiyewa yana sanye da kaftani na farar shadda ya d'aura waya a kunne yana magana, farinciki naji kamar ya kashe ni Yayana ya dawo gare ni wayyoo ni. Da gudu na ƙarasa ta bayan shi saboda farinciki ya rufe min ido nayi abinda ban tab'a yi ba wato ina zuwa banyi wata-wata ba na rungume shi ta baya ina sauke tagwayen ajiyan zuciya cikin muryan kuka na fara magana ; " Yaya naaaaa ni na san ba zaka iya ba dole zaka dawo gare ni i know u truly love me idon ka kad'ai nake kallo in gane hakan"". Cak ya tsaya ya kasa juyowa kuma ya daina wayan mun kusan minti 1 a haka ya juyo tare da banbare ni a jikin shi ya watsar a gefe yace; "Yuck how disgusting baki da hankali ne daga gani na zaki wani zo kiyi huging na haka ko ance miki irin samarin nan naki ne marasa kan gado?" Yanayi yana watsa min wani kallon kaskanci, muryan da naji kad'ai yasa gaba na fad'uwa dan wannan dai ba muryan Yaya na bane amma kuma na san mai muryan sai dai a sani na da tunani na babu abinda zai kawo shi gidan mu. Cikin fargaba na d'aga ido na dan tabbatarwa kai na cewa bashi bane, amma me ina dagowa idona sai cikin nashi da yake aiko min da munanan sakonni. D'auke nawa idon nayi cikin second d'aya ganin wanda ban tab'a zato balle tsamani ba a kofar gidan mu, na had'iye wani bushashan yawu da ya tsaya min a makoshi sai yanzu na lura da yanayin shigar sa tsayin sa fatan jikin sa komai daban dana Yaya na. Kara d'agowa nayi naga yana min wani kallo kaman yaga kashi , cike da jin haushin kaina kama hanya zan shiga gida garin murnanan zuwan Yaya bada kaina. Gaba na yasha yana wani kumbura fuska kaman ni na jawo shi gidan namu yace; "Nasan yanzu gurgun tunanin ki ya baki cewa wajan ki nazo ko? well I don't have much time but to say I have a contract with you" "Contract!?" Naji baki na ya furta cikin mamaki ba tare da na shirya ba, shi kuwa murmushin gefen baki yayi yana like father like daughter" shi a zaton sa duk son abin duniya yasa na amsa mishi lokaci d'aya bai san cewa mamaki ne ya kama ni ba. "Yeah contract marriage kuma if possible ba zai wuce 1 to 2 months ba zakiyi tafiyan ki nd zan iya baki daga 100 millions zuwa sama kuma kada ki d'auka wai zaman ma'auran gaske zamuyi, no zanyi haka ne kawai dan in fita daga mess d'in da Abba na yake son jefa ni ciki" a garance ya cigaba da tambaya ta nawa zai bani. Juyowa nayi ina fuskar shi da kyau duk da ina jin yanda zuciya ta take bugawa kaman ya fito saboda tsaban kwarjini da yayi min dan sosai yake cika min ido amma dole ne in nuna mishi mu mata daraja ne damu kud'i bai isa ya saye mu ba. "Hmmm ikon Allah , naji ni mai gurguwar tunani ce, kai kuma wannan tunanin naka me zan kira ta dashi miskini ko nakashasshe? "Anyway bari in fada maka ko duniya da abinda yake ciki zaka mallaka min toh ni Zareefa na fi karfin wannan kazami ko haramtaccen rayuwa da kazo min dashi sai dai ka kara gaba kila ka samu wata gantalalliya da zata amince maka amma ba ni ba" Ina gama maganata na rab'a ta gefen shi zan wuce zuwa cikin gida naji an finciko ni ta baya tare da d'aga hannu zai yarfa min mari kuma ya fasa ya dungule hannun ya kaiwa iska naushi yace; Damn u ! Who do u think u re ? Da har zaki bud'i baki ki fad'a min magana son ranki, I don't blame you baki san wanene ni ba da ko wuka aka d'aura miki a wuya u will not have d guts to do it. Kada gani na a kofar gidan ku yasa ki d'auki kan ki kaman wata mace u re nothing yes I mean nothing, ba duniya da abinda suke ciki zan bayar ba amma Baban ki yace min ko gobe inzo zai d'aura min aure dake nazo nan na fad'a miki ne cus na san ba lalle bane su fad'a miki irin auren da zakiyi but for now at least kin san irin auren da zakiyi, as for me I don't have time for cheap girls like u". Yana gama maganan shi fad'a motan shi yaja shi a d'ari ya fita daga layin mu tare da bad'e ni da kurar motan ya tafi abin shi. Ni kuwa ko kafata na kasa d'agawa a wajan ba wai maganganun shi ne suka b'ata min rai ba illa sunan Baban mu daya ambata a cikin maganan shi ya jefa ni cikin tashin hankali mara misaltuwa. Na san Baban mu tun ina k'arama akan kud'in Baban mu ba abinda ba zai aikata ba koda akan dubu d'ari ne zai amince balle yaji million d'ari, " Na shiga uku" nace hawaye na ambaliya a fuskata. Nafi minti 5 tsaye a wajan ina hawaye sannan na goge fuska ta da hijabi na,naja kafafu na da sukayi min nauyi zuwa cikin gida. Allah ya so ni babu kowa a tsakar gidan duk suna d'akunan su sai hayaniyar su daya cika ko Ina kai tsaye na wuce d'akin mu, da sallama na shiga d'akin ban tadda Inna ba ina zaton ta zaga bayi ne. Ban tsaya bata lokaci ba na haye gado na kwanta ko hijabin dake jikina ban cire ba gudun kada Inna tazo ta same ni cikin sabon tashin hankali dan ban san wani bayani zanyi mata ba. Tunani na zurfafa a ciki na yanda rayuwa take neman juya min baya ina 'yar k'arama ta koda yake Allah ba bawan sa da baya jarabta babba ko karami mace ko namiji, ni na san ina cikin jarrabawan ubangiji nane, yau na dawo daga asibiti wanda tashin hankali yaja min kwanciya can kuma gashi yanzu ga wata fitinan da kwanciya asibitin ma ba zai min maganin ta ba. Ina ji Inna ta shigo tana min magana nayi likimo kaman mai bacci saboda bana son ta tambaye ni waye yazo, jin wanene ko meya zo dashi babu abinda zai kara mata illah tashin hankali. Addu'oin bacci tayi ta shafa nima ta shafa min ta kwanta a gefe na taja mana bargo ba tafi 15 mins da kwanciya ba naji tayi bacci, a zuciya ta nace Allah sarki Inna ta dana fad'a miki halin da nake ciki yanzu na tabbata da baki samu daman runtsawa ba. Har karfe d'ayan dare tayi ido na babu alamun bacci, cikin tsand'a na sauka daga kan gadon na fita na d'auro alwala na fara kai kuka na ga Rabbil Izzatti shine kad'ai madogara na. **************** Zafar har ya isa gida zuciyar shi bai bar tafasa ba har kaman shi wannan yarinyan zata dubi cikin idon shi ta fad'a mishi abinda taga dama " bull shit" yace yana dukan stairin shi da karfi kaman shi ya mishi lafin. Yana zuwa gida kai tsaye part d'in iyayen shi ya wuce, a kofan parlour ya tsaya ya gyara fuskan shi kaman he is in good mood saboda baya so su fahimci halin da yake ciki. Da sallama ya shiga parlour suna zaune suna kallon wa'azi a Sunna TV da Sheikh Aminu Daurawa da yake , amsa mishi sukayi duka ya karaso ya zauna kan lallausan rug dake parlour ya gaishe su suka amsa mishi cikin kulawa daga nan yaja bakin shi yayi shiru shima ya maida hankalin shi kan wa'azin. Kusan mint 10 wa'azin ya kare dama yazo karshe , remote Abban shi ya d'auka ya rage volume d'in TV sannan ya kalli inda Zafar yake zaune yace; "Ina ta zuba ido ka kawo min wacce kake so kaman yanda mukayi magana tun kwanaki 3 da suka wuce amma na jika shiru, so yau ne deadline d'in kuma dole ne in cika alkawari na dana d'auka na samo maka mata a cikin 'ya'yan dangi". "Kayi min afuwa Abba yanzu haka abinda nazo fad'a maka kenan na tarar kuna kallon wa'azi shiyasa na jira ku gama sai muyi magana" ya amsa yana wani sussunne kai. "Okay sai yau kaga dama kazo min da zancen?? Hmm toh bakin alkalami ya bushe gobe zanje duk wacce tayi min itace matar ka insha Allah" Abba ya karasa hankalin sa kwance. A rikice Zafar ya d'ago da kai ya rarrafo gaban Abba ya fara magana duk a rikice" Abba wallahi ba wai nayi biris da maganan ka bane na zata kace in kawo ta yau ne shiyasa nayi shiru, please Mom kisa baki wallahi maganan da nazo dashi yanzu kenan please Abba". "Alhaji kayi mishi afuwa tunda bai fahimci abinda kake nufi ba sai yanzu ". Cewar Mom kenan da duk har yanayin ta ya canza. "Hum kuma daina b'ata bakin ku kema kin san in nayi magana d'aya bana canza ta". "Abba na sani wallahi na sani amma dan Allah kayi hakuri ba dan hali na ba" ya cigaba da magiya shida Mom Abba yana jin su bai kula su har sai da ya wana su son ran shi sannan ya ce; "Ya isa haka naji sai ka kiyaye next time 'yar waye ne ka samo mana??" Harshan sa har hard'ewa yake wajan bada amsa " sunan ta Zareefa a garin nan take 'yar Mallam....." "Mallam kuma Zafar ?" Mom ta katse shi fuskar ta d'auke da matsanacin damuwa. Kamin ya bata amsa Abba ya karb'e da cewa" ke yakewa bayani da zaki katse shi? Meye laifi a auren 'yar Mallam, so kike kiji yace 'yar Alhaji ko 'yar governor or what?" Ya karasa fuskar shi na nuna bacin rai. Cikin kwantar da murya Mom ta shiga bashi bashi hakuri bai amsa ba illa mikewa da yayi ya wuce sama tare da cewa Zafar ya biyo shi. *********** Gwaggo Aisha da kawar ta Lantana suna tattaunawa cikin farinciki a cikin motar haya suna dawowa daga kauyen Manguno inda aka kai ta wajan wani boka. Cikin annashuwa ta ce" gaskiya Lantana na jinjina miki dama kin san irin wajan nan.amma kika barni ina ta shan wahala kan kananan kwarin nan?" Cikin fariya Lantana tayi wani dariya ta amsa da " A'i kenan ai ba nan kad'ai na sani ba wajaje dayawa na sani kin san duniyan nan sai da dan shige-shigen nan zaki kwacin kanki kuma ki wuce rainin miji ko kishiya. Kin gan ni nan wallahi Mallam Ado sai abinda nace a gidan sa yake babu wanda ya isa ya tsallake magana ta har matan shi da yaran su". "Kai kawata kina wuta ina bin ki da fetir har kinsa na fara hangowa ina juya Bintu da wannan fitsararriyar 'yar ta" cewar Gwaggo Aisha cikin jin dad'i. "Ke dai kibi duk sharud'a daya kindaya miki kiga aiki da cikawa kasancewar aikin shi kaman yankan wuka yake. "Ai dole ne in bi sharud'an nashi" da wannan tattaunawan har suka iso gida. Sai bayan karfe 3 bacci yayi nasaran sace ni nan kan sallayan, kiran sallah farko Inna ta farka ta ganni kwance kan sallaya bata tashe ni ba tayi alwala ta fara nata nafilfilu kasan zuciyar ta kuwa tana mamakin kwanciya ta a nan. Sai da aka fara sallah a sauran masallatai sannan ta tashe ni na fita nayi alwala nazo na kabbara sallah, ko azkar kasawa nayi saboda baccin dake cin ido na kara bingirewa nayi na cigaba abina anan Inna ta fahimci bacci bai ishe ni ba jiya cikin tausaya min ta kama 'yan aiyukan ta nan cikin d'akin ba tare da ta fita ba, bata kawo komai a zuciyan ta ba duk a zaton ta ban dawo dai-dai daga shock na rabuwa da Yaya na ba. A wannan Gwaggo Aisha tayi bine-binne ta a mashigar kitchen d'in mu ta saka kujera a k'ofar d'akin ta tana jira mu fito mu tsallaka kaman yanda bokan ta yace. Cikin ikon Allah Inna itama baccin ta koma tunda babu wani abu na azo a gani da zatayi, cikin bacci muka ji kaman ana tonon abu cikin k'asa, ko motsi banyi ba amma na farka sai Inna tace tayi karfin halin fitowa jin muryan maza kuma bakin murya ya cika gidan. Maza tayani sun kai su biyar kowanne da abu a hannun shi yana tono Baban mu na tsaye daga gefe , kamin Inna ta bud'i baki tayi tambayi me yake faruwa suka ji muryan Gwaggo Aisha tana" kai! Kai!! Ku dakata me kukeyi haka?" Duk suka juyo suna kallon ta duk ta had'a zufa sai wurwurga ido take, Baba ne ya bata amsa da " meye naki na ihu haka sai kace gidan ki ake tono, Toh gini zanyi zan canza ginin gidan nan ya zama na zamani"..... [1/26, 7:12 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *21&22* "Haba Mallam ba zaka bari mu d'an kimtsa ba gyara da sassafe haka?" Gwaggo Aisha ke fad'an haka cikin matukar tashin hankalin gani za'a saka ta wahalan banza. "Wani irin kimtsawa sai kace daga kofar ki aka fara, ki bari in aka zo kofar ki sai ki kawo korafin naki" Baban mu ya amsa a dakile. "Ni ba wani abu nake nufi ba naga safiya ce kuma ai ko ita Bintun zata so a bar ta ta d'aura abin karyawa ita da 'yar ta, ko ba haka ba Bintu?" A zuciyar ta kuwa tana ta addu'an Allah yasa Inna ta amince da abinda ta fad'a a fasa tonon sai bayan mun shiga kitchen d'in mu munyi girki, kamin nan mun sallake abubuwan da ta binne shiyasa dama ta zab'i binnewa a kofar kitchen d'in mu sanin ba wanda zai taka wajan sai mu. "A'a in ta nine bakomai suyi aikin su, ba zamu rasa yanda zamuyi ba, wannan ai abin farinciki ne kuma cigaba ne muma zamu zama 'yan gayu" Inna ta amsa tana dariya sauran mutane da suke wajan suma dariyan sukayi suka cigaba da aikin su ba tare da sun lura da halin da sun lura da halin da Gwaggo Aisha ta shiga ba. Afujajjan ta shiga d'akinta sai safa da marwa take duk ta had'a zufa ta kasa zama sai neman hanyar da zata dakatar dasu take amma kasan zuciyar ta kuwa gargad'i take mata na kar ta tsauwala har ta tonawa kanta asiri cikin mutane, da wannan shawaran ta nemi waje ta zauna sai karkad'a kafa take tana sharce gumi,Hajara tana ankare da ita amma taki tanka mata. Ni kuwa tunda naji Baba yace ginin zamani za'a yiwa gidan mu na kasa ko daga yatsa na sannan kuma na tabbatar da zancen bawan Allah nan na jiya gaskiya ne kenan in ba haka ba ina Baba yaga kud'in ginin zamani, "Ya Allah ka dube ni ka fidda ni cikin wannan fitinan" nace cikin raina. Basuyi wani nisa ba suka fara tono tsirkullen Gwaggo Aisha, cikin mamaki suka tsaya cirko-cirko suna kare musu kallo an rasa mai magana cikin su. "Mu cigaba da aikin mu mana" cewar d'aya daga cikin su. "Kaman yaya mu cigaba bayan wannan abubuwa da muka tono,kamata yayi a sanarwa mai gidan sai ya san matakin da zai d'auka" nan duk sukayi na'am da shawaran nan suka tura karamin cikin su kiran Baba. "Innalillahi wa inna ilahi rajiun" shine Kalmar da Inna ta samu daman maimaitawa fitowar ta kenan daga bayan gida taga sun tara tsirkullen a gefe suna ta tattaunawa akai. Kasa wucewa tayi tana mamakin me ya kawo layu da guraye kofan kitchen d'in ta, fargaba fal a zuciyar ta na kada ace itace ta binne su,har Baba iso wajan tana tsaye sai ambaton sunan Allah take. "Wannan ai ba wani abin tada hankali bane, ta yiwu tun na kakanin mune sune zasu iya ajiye irin wayan nan abubuwan su jima haka kasa haka" cewar Baba kenan cikin rashin d'aukan abin da muhimanci. "A'a wayanan tsurkullen basu dad'e a kasa ba ta, da gani kwananan aka binne su" cewar d'aya daga cikin su. "Matsalaha daya ne shine a k'ona su kurmus in ma mai shi da wata manufa ya binne toh zai zo da sauki" Inna da jikin ta yayi sanyi sosai barin ma irin kallon tuhuma da taga Baba na aiko mata da shi yasa duk taji ba dad'i, tana jin anyi maganan konawa yasa cikin sauri ta wuce d'aki ta d'auko ashana a cikin drowern d'aki inda take ajiyewa in ta sayo kwali. Kamin ta fito har sun tara su a gefe sun zuba kalanzir suna neman ashana, Baban mu ta mikawa ta koma gefe ta tsaya babu b'ata lokaci wanda ya karba ya ketta ashana bayan yayi addu'oi nan da nan kuwa wuta ya kama ya fara ci bakin hayaki na tashi a jiki kaman ana kona taya. A d'akin Gwaggo Aisha kuwa tunda aka cinnawa layun nata wuta ta fara ganin d'akin na juya mata ga wani zafi-zafi da take ji a jikin ta kaman ana hura mata wuta, tun tana iya daurewa har abin yafi karfin ta ta fara ihu tana birgima a tsakiyar d'aki. Sharewa nayi kaman banji ba dan nima ina fama da nawa matsololin inda zan samu daman ihun nima da nayi ko zanji sauki cikin raina. Tsaki naja ina mikewa tsaye da d'an sauran kuzarin daya rage min na fita saboda yanda naji ihun yaki tsayawa kuma kana ji kasan wanda yake yana cikin mamuyacin hali. Kus-kus na tarar masu aikin nayi ban kula su ba nayi wucewa ta zuwa d'akin Gwaggo Aisha da zan iya kirga shiga ta ciki tunda aka haife ni. Da gudu na karasa nima ina kokarin rike ta kaman yanda naga Inna da Hajara sukayi Inna sai tofa mata addu'oi take, ban tsaya b'ata lokaci ba nima na fara taya ta muka cigaba da tofa mata har ta daina birgima sai jikin ta da yake rawa sosai, tuni Baban mu ya fice abin shi zuwa d'akin shi ya bar mu da ita. Mun Kai good 30 mins muna yi mata sannan ta dawo hayyacin ta sai ajiyan zuciya take a kai- akai hawaye na bin gefen fuskan ta amma koda wasa bata bud'e ido ba, ganin taji sauki yasa Inna mikewa tacewa Hajara ta lullub'a mata abin rufuwa da alamu ta samu bacci, amsawa tayi da toh tare da mana godiya muka fito zuwa d'akin mu Inna bata zauna ba ta d'auki dubu d'aya ta bawa Ibrahim kan ya sayo mana abin karyawa a waje. Tunda ta bada sakon ta dawo d'aki ta zauna shiru na san shirun nata baya rasa nasaba da abinda ya faru a safiyar yau, ba Inna da take shekaru ba ko ni nan na fahimci abinda ya faru da Kuma musababbin ta. Allah sarki Inna ta kamin ka samu mai irin zuciyar ta a wannan zamnin sai an tona, tsab ta gane komai amma taje tayi mata addu'a, da wata ce sai dai ta mutu ko nice nan Yasin ko kurar da ya debo ki ba zan kallah balle har in nema miki waraka barin ki zanyi ki girbi abinda kika shuka. Shi kuwa Baban mu akwai shi da kyaluwa ba kasafai kake gane mishi ba in ba harkan kud'i bane, ko ya fahinmci abinda ya faru ko bai fahimta ba oho. ************* A b'angaren Zafar kuma yau cikin farinciki ya tashi ko ba komai ya ragewa kan shi tention da kuma fad'an Abban shi, ba komai yake kara mishi nishad'i ba kaman in ya tuno da hiran shi da Abban shi jiya a kaina. Murmushi ya kara saki lokacin da ya tuna Abba shi yace" ina matukar alfahari da kai ka birge ni sosai da ka tashi neman aure baka nema cikin 'ya'yan masu kud'i ba ka nema a irin gidan da nake son in samu sirka, Naji dad'i da baka bi halin mahaifiyar ka ba na wajan kin talaka, da mai kud'i da talaka duka Allah ne yayi mu saboda hikimomin shi ba yayi hakan bane dan baya son su ba. Ina son ka auna da kanka ka gani a nan ne zaka gane hikiman ubangiji da nake fad'a maka, misali ace duniyan gaba d'aya babu talaka ya kake ganin zai kasance ko kuma ace duka talakawa ne babu mai kud'i, ka fahimta?" Ya tambaya yana kallon yanda ya natsu yana sauraron shi. Gyad'a kai Zafar yayi a hankali kan shi a kasa da sai yanzu da Abba ya fad'a mishi ya gane dole talaka yana bukatan mai kud'i haka Kuma mai kud'i yana bukatan talaka a rayuwar shi. Muryan Abba yaji ya cigaba da magana " babu wanda yafi wani sai wanda ya mutu ya samu aljanna, kana nan duniya kana taka mutum saboda kai kana da shi shi kuma talaka baka sani ba kila a wajan Allah yafi ka daraja, dan haka ka cigaba da rike mutane da kyakkyawan zuciya zaka ga amfanin haka duniya da kiyama". Shi dai Zafar duk mamaki ya hana shi sakat yaushe rabon da su zauna da Abban shi har suyi magana mai tsayi cikin lumana haka, tun kafin zuwan sa abroad karatu, tunda ya dawo da sabbin halayen sa na shan minti kuwa suka daina shan inuwa d'aya tare. "Kana da kud'i a account d'inka?" Ya karajin muryan Abba ya katse mishi zancen zuci yake. "Eh akwai Abba ba za'a rasa ba" ya amsa a sanyaye kaman mutumin kirki. "Ok bari zuwa anjima ko gobe zanyi maka transfer ko kad'an ne kada sirkata ta nemi wani abu kace mata babu" yace yana dariya. Shima dariyan yayi yana kara sadda Kai kasa. Cikin wani irin kwarin guiwa ya nufi part d'in iyayen nashi bayan yayi wanka ya sha gayun shi kaman kullum sai kamshin tsadaddaun turaruka yake, tsab'anin da in Abba yana gari da kyar yake iya zuwa saboda ya san in yaje ma ba zasu kwashe da dad'i ba. Da sallama ya shiga parlour amma babu kowa sai masu aiki da suke kai kawo, kowa na aikin da yake gaban shi, zama yayi kan d'aya daga cikin royal cussion d'in da suka lamushe kusan set 2 ya d'auki remote yana canza channel zuwa aljazeera sports yaji motsin saukowan su. Ajiye remote d'in yayi ya mike tsaye ya tarbe su basu tsaya anan ba direct dinning suka wuce kowa yaja kujera ya zauna banda Mom da sai da tayi serving din su sannan ta zauna suka fara cin abinci Basu dad'e da farawa ba Zafar yaga alert na zunzurutun kud'i har 10 million cikin tsananin murna bai san lokacin daya durkusa jiki na rawa har kasa ya fara godiya yana" Abba naga sako nagode Allah ya kara girma da nisan kwana" ba dan komai ba Abba yafi shekara rabon shi daya bashi kud'i sai dai Mom ce ke bashi a cewar shi ba zai bashi kudin shi yaje yana shashanci dasu ba. Abba kuma ya kalli Mom da take bin tilon d'an nata da kallon mamaki yace" da fatan kin fahimci abinda nake nuna miki kika kasa fahimta kinga tun kamin ayi auren ta fara canza mana shi ina ga Kuma anyi auren?" "Oh yanzu duk sun d'auka wannan village girl d'in ce ta canza ni..." Muryan Mom yaji tana cewa" na fahimta Alhaji ya tabbatar da alkhairi" "Ameen Ameen addu'an ki yake bukata dama, Kai kuma a yau d'in nan ka cewa 'yar Mallam gobe zamu je mu tsaida magana da Baban ta" Murmushi da bai shirya bane ya kwace mishi jin sunan da Abba ya kira ni dashi wai 'yar Mallam. "Ja'iri ji duk wannan washe bakin dan nace gobe zamu je ne, ina ga inda aka daura auren Kuma ya zakayi?" Dariya yayi kawai yana ficewa ya nufi part d'in shi yana kara dariyan sunan da kuma na Abban shi da yake ganin auren soyayya zaiyi bai san auren contract zaiyi ba. Direct bedroom d'in shi ya wuce yana cigaba da dariyan shi yayi dialing no Sadiq , saida ya gama ringing kamn zai katse sannan ya daga yana cewa " meye ya faru??" " Hey Ni ba fad'a yasa na kira ka ba, I just called dan in fad'a maka gobe Abba zai je nema min auren 'Yar Mallam" ya karasa yana dariyan da sai da yasa Sadiq ya cire wayan a kunnen shi ya kalli screen d'in ya kara tabbatarwa eh zafard'in ne sannan ya mayar kunnen shi. "Wacece da wannan sunan ko cikin relatives d'in ka na kauyen ne aka samo maka wata". Sadiq ya tambaya. "God for bid, bakin ka ya sari d'anyan kashi mugu kawai meya had'a ni da 'yar kauye, wannan village girl da kuka had'a ni da ita mana Abba ne ya saka mata wannan funny name d'in koda yake it suits her" ya karasa yana kara saka dariya dan d more zai fad'i sunan d more yake saka shi dariya. "Ikon Allah, amma ban san Kai cikakken d'an rainin wayo bane sai yau, yarinyan da ta sace maka zuciya at first sight shine zaka ce mu muka nemo maka ita?" "Damn it wai har sai yaushe zaka fahimta ni *BA SONTA NAKE BA* kuma kafi kowa sanin why I will marry her amma ba zaka daina fad'a min rubbish ba, anyway phone no ta nake nema in fad'a mata sakon Abba" yana kawo nan a zancen shi katse kiran yayi jifa da wayan kan gadon shima yabi shi ya kwanta ringine yana huci shi ala dole an b'ata mishi rai. Ko minti 5 baiyi da kwanciyar ba yaji karan shigowan sako wayan shi, sai da yaja tsaki sannan ya bude sakon ba dan komai ba sai dan yaga daga Sadiq ne. Number kad'ai ya gani babu rubutu hakan ya tabbatar mishi da number na daya nema ne ya turo mishi, sai da ya fara saving sannan ya kira ni lokacin muna zaune da Inna tana had'a min tea dan tace inzo mu karya nace bana jin yunwa, shine ta shiga had'a min wai ko shi kad'ai in sha. Inaji har tagama ringing ban d'auka ba ganin sabon no ce, kara kira yayi Inna ta dakata da had'a shayin tace min " Wai ke ba wayar ki ake kira bane?" "Inna sabon number ce babu suna" na amsa mata a sanyaye. "Ko ba suna ai zaki daga kiji ko waye ko?" Inna ta sake fad'a min. Koda na juya da niyan daukawa naji ya katse dan haka banyi magana ba nayi shiru Inna ma bata kara cewa komai ba ta cigaba da had'a min. Miko min tayi bayan ta gama harda 🍞 tace in gusura ko kad'an amma na ce mata sai anjima, sama-sama itama ta karya bata ci wani abu dayawa ba ta ture gefe duk gani na cikin rashin walwala yana hana ta sukuni itama. Gwaggo Aisha sai bayan fitan mu da kusan minti goma ta tashi ta zauna tana goge fuskan ta da hijabin da Hajara ta lullub'a mata ba hawayen amma duk ta jike da zufa. Harara ta zabgawa Hajara da take ta jera mata sannu tayi kana tace" ke dai Allah yayi magulmaciya da kinibibi in banda gulma waye yace ki gaiyato min wacan manufukar matan can da 'yarta fitinanniyan nan?" Baki a hangame hajara take kallon ta tace " haba Umma in baki gode musu ba ba zaki tsine musu ba, ihu fa kike tayi kina birgima kan an k'ona abinda kika binne dan su cutu ita da yarta amma matan nan ta zauna tana tofa miki addu'oi ita da yarta har kika samu lafiya, mutane nawa ne a gidan nan babu Wanda yazo kan ki sai su hatta Baba ma tafiyan shi yayi ya bar ki....." "Ki min shiru wawuya kawai mai fifita uwar wasu kan uwar ta koda yake ba laifin ki bane duk asirce ku tayi Kuma wallahi ba zan saduda ba sai na warware duka mugun kulli da tayi a cikin gidan harda Baban naku..." Shiru tayi tana wur-wurga ido kaman me neman wani abu, a zabure ta mike tana " kan bala'i in na yarda shigiya nake" tana gama magana ta fice fuuu zuwa tsakar gida. Cikin daga murya ta fara magana" ina kake ka fito shanyayye kawai wallahi na gaji da rashin adalci da kake nuna min a cikin gidan dole ne ayi abu d'aya ehe" "Ke Wai wace irin dakikiya ce mara hankali meya faru da zaki zo tsakar gida kinawa mutane ihu" cewar Abba kenan daya tsaya daga nesa yana kallon ta. "Eh dole ka kira ni da sunaye da kaga dama Amma kada ka manta ko rigar sakawa na kirki baka da ita lokacin da na aure ka sai yau dan ka samu abu zaka wukanta ni, ace Wai gini zakayi a gidan baka fara ta kaina ba nida nake uwargidan ka sai wancan jamammiyar matar taka". "Kinga dakikancin ki da nake fad'a ko, in kika ga abu tambaya ya kama kiyi ba Wai kiyi tayiwa mutane ihu ba, toh kudin daga hannun mijin da zai auri yar albarka ya fito kinga kuwa dole afara gyara mata b'angaren ta tunda auren ma ba zai fi wata d'aya ba". Ras-rass naji zuciyata ya tsinke duk da na san da zancen amma jinta a bakin Baban mu yafi daga min hankali, a zabure Inna ta mike tana girgiza kai tana magana " ba zai yiwu ba wa zai aurawa 'yata ba tare dasani na ba,ba zan yarda da wannan cin fuskan ba zan iya jure ko wani irin cin mutunci amma banda kan 'yata ba" [1/26, 7:12 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *23&24* "Na sha had'iye wulaƙanci da cin fuska daga wajan sa da matan shi, amma wallahi kada wani yace zai tab'a min ke anan ne zasu ga fushi na". Tana magana ne a wannan lokacin tare da saka hijabinta ta kama hanyan waje. Da gudu nima na miƙe ina kwala mata kira akan kada ta fita wajan nasu amma ina har ta fice daga d'akin, bakin gado na koma na zauna dabas ina jin zuciya ta na suya tsanar bawan Allah nan na ninkuwa a cikin ta ba dan komai ba sai dan yanda naga tashin hankali da bacin rai shimfud'e akan fuskan ta wanda zan iya cewa tunda aka haife ni ban tab'a ganin koda kwatancin shi a tare da ita ba. Gata kuma ta fita sa-in-sa da Baban mu da Gwaggo Aisha shima wannan ban tab'a ganin Inna ta kula kowa ba a gidan,koda kuwa me zasu ce mata ko suyi mata bata tankawa kowa sai dai ta shige d'aki tayi zaman ta,nice dai a baya nake dan kula su kasancewa ta bana iya wuce tayi in dai na fad'a ne sannan kuma na tsani wulakanci da raini wanda duk Gwaggo Aisha tayi degree akan su. Sosai take min fad'a kaman ta doke ni akan kula su da nayi amma yau itace dakanta ta fita yau; " Innalillahi wa inna ilahi raji'un" na zauna maimaitawa ina kuka, wannan wani irin mutum ne shi tunda ya shigo rayuwa ta komai kara cakub'ewa suke " I hate that ugly creature" nace ina Kara fashewa da sabon kuka. Naci kuka na na more sai dai ga mamaki na banji motsin Inna ta a tsakar gidan ba balle inji muryan ta, Baban mu ma na daina jin muryar sa sai Gwaggo Aisha da take ta ihun ta ita kad'ai. Shirun da naji yayi yawa ne yasa na mike a hankali na l'eka waje bayan na yaye labule kad'an, tsakar gidan babu kowa da alamu Gwaggo Aisha tayi ta gaji ta koma ciki sai masu aiki da suke ta aikin su sai kanne na da suke wasa a gefe,toh ina Inna ta ta tafi??? Ras-ras naji zuciyata ta harba da karfi kar dai yaji Inna tayi, abinda tunda akayi mata aure bata tab'a yi ba. Cikin mutuwar jiki na koma d'aki na zauna ina tsiyayan hawaye masu zafin gaske, ban jima da zama ba naji waya ta ta fara ringing ko juyowa banyi ba balle in sa ran zanyi answering, haka ya gama ihun sa ya daina. Kwanciya ta nayi akan gado ina rokon Allah yasa ba yajin tayi ba cos I can't imagine myself in dis house without my inna, wayance ta fara ringing Kuma cikin gajiyawa na d'auka ina kallon no data kasance special in ban manta ba kaman d'azu dashi aka jera min 2 missed calls. Saura kad'an ya katse na daga kai kunne na nayi shiru ba tare da nayi magana ba, shiru naji shi wanda ya Kiran ma yayi bashida niyyan magana,mun kusan minti 2 a haka ina shirin cire wayan a kunne na kaman yana kallo na yace; "Who do you think you are? Da har zaki dinga ignoring calls na, be very careful with whom you are dealing with or akwai lokacin da yana zuwa da zakiyi regretting duk abubuwa da kike". Yawu mai d'aci na had'iye da ya makale min a makokoro ina sauraran bakaken kalaman sa da suka fi wuta zafi, sarai na gane muryan nashi wanda kullum in yana magana zaki jita cike da isa da kasaita. Bai san cewe nima a wuya nake ba tunda har ya zama shine silan fara fitan Inna a gidan auren ta da sunan yaji, tsab zan juya mishi duk rashin mutunci da nake dauke dashhi dama nima ba tayar baya bace. Muryan shi ce ta maido ni hankali na naji yana cewa; " 'yar Mallam kada kice wai saboda na damu da kene nake ta jera miki kira haka, nooo ko daya I just want you to tell Mallam Abbana zasu zo anjima". Kit naji ya katse kiran ba tare da ya jira yaji me zance ba. " 'yar Mallam!! " Na maimaita sunan a fili "kunbu in na yarda shegiya nake nice 'yar Mallam din, wallahi sai na koyawa dan raini nan hankali ni har akwai wanda zai takale ni in kyale shi never". Tsakani da Allah na zage ina masifata ni kad'ai kaman yana gaba na, danna mishi kira nayi ina jiran ya daga nima in rama amma har ya katse bai daga ba, ban hakura ba sai da na jera mishi missed calls 5 bai daga ba, cillar da wayan nayi na fashe da kuka sosai dan jin zuciya ta nake kaman ta fashe da ban samu na rama ba dama can ina da wannan halin tun ina karama na taso da abuna, cikin 'yan gidan mu babba ko karami ya tab'a ni sai na rama hankali na yake kwanciya, har duka Inna ta sha yi min akan in daina amma na kasa saboda a jini na yake. Wannan dalilin yana daya daga cikin dalilan da Gwaggo Aisha take min zazzafan tsana. Inna kuwa tana fita a d'aki bata ko kalli inda Baba da Gwaggo Aisha suke ba ta fice zuwa gidan su, suma dai basu lura da ita ba duk hankalin su yana kan fad'an da suke. A tsakar gida ta samu Maa da kanwar ta wacce suke kira da Ya ma'aji suna hiran su na 'yan uwan taka gwanin sha'awa, da sallama ta shiga sai dai bata tsaya taji amsawar sun ba ta shige d'akin Maa. Da ido duk suka bita har ta shige cikin d'aki ba tare da ta tsaya wajan su ba kaman yanda ta saba ba ko kuma ince yanda ya kamata ba, Ya ma'aji ta dubi yayar ta tace" Yaya da alamau yarinyan nan tana cikin damuwa,dubi yanda ta shigo gidan nan hankali tashe, ni wallahi wannan kaddararren auren nata da kina jin shawara ta da tuni ta rabu da shi haba yarinya tana 'yar karamar ta amma kullum cikin tashi hankali take dubi yanda duk ta motsare,ga fitinan miji gana kishiyoyi da wanne zata ji" ta karasa da matukar fushi a fuskarta domin ita halin ta daban dasu Maa fad'a ne da ita sosai ga rashin hakuri. Murmushi mai sanyi Maa tayi mata tana girgiza kai tace "kai ma'aji akwai ki da daukan abu da zafi baki san halin yaran yanzu ba abu bai kai ya kawo ba zasu d'auke shi da zafi........". "A'a Yaya kada ki raina hankalin ta na tabbata ko ke da kika fimu sanyin hali aka ki gidan nan nata zasu kure ki,bari inje inji meya faru" tace tana mikewa tare da nufan d'akin da Inna take ciki. A kan carpet da yake shimfid'e a tsakar dakin ta samu Inna ta had'a kai da giwa tana kuka kasa kasa. Dafa ta Ya ma'aji tayi yasa ta d'ago da kai suka had'a ido tayi mata murmushi ita kuma kukan ta kara fashewa da shi cikin muryan kuka ta fara magana"Ya ma'aji ku ceci Zareefa dan Allah ku cece ta ni na yarda suyi min duk abinda suke so amma dan Allah su kyale ta tayi rayuwa mai yanci da farin ciki, yarinya ce k'arama bata san rayuwa ba dan Allah kada su jefa rayuwar ta cikin.........." "Ya isa haka ya isa, ki natsu ba abinda zai faru da Zareefa muna tare da ke kuma Allah yana tare da mu dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki min bayanin me yake faruwa?. Ya ma'aji ta katse Inna da take magana cikin fitan hankali. "Wai aure zaiyi mata kuma ni baiyi shawara dani ba ban san waye zai bawa ba,kawai yau da safe ya shigo da masu gini wai zai canza ginin gidan zuwa na zamani kuma yana so ayi da wuri kuma a bangare na aka fara saboda auren wai ba zai wuce wata d'aya ba. ni abinda yake bani tsoro na san halin shi in game da kud'i ne komai zai iya yi......." "Ba 'yar sa bace ko saida ta zaiyi ina ruwanki " suka ji muryan Maa a bakin k'ofa wacce da alamu ta dad'e tsaye a wajan,duk kallon ta suka tsaya yi har ta shigo ta samu waje ta zauna tana fuskantar Inna. "Kin bani mamaki Bintu da har zaki tada hanklin ki kiyi abinda baki tab'a yi ba wato kawo karan miji, yanzu da kika kwashi kafa kika zo min gida menene a zuciyar ki ko so kike ni in kira shi ince bashi da daman zabawa 'yarsa mijin aurex ko kin manta addinin musulunci ne ya koyar da hakan...." "Maa na sani wallahi na sani amma kema kin san halin shi zai iya yin komai akan kud'i, sannan ya kamata ya shawarce ni ya fad'a min abinda yake faruwa ba wai inji maganan ta sama ba" Inna ke fad'an haka cikin wani irin murya mai nuna tsananin halin da take ciki. "Menene halin sa Bint? koma wani irin hali ne dashi ba zai tab'a cutar da Yar cikin sa kuma maganan shawara da kike so yayi dake, wani shawarwan zaiyi bayan ke kan ki a karkashin sa kike. Tashi ki koma d'akin ki ki cigaba da ibadan ki cikin kwanciyar hankali kaman yanda kika saba sannan kija yarinyan nan a jikin ki,ki kwantar mata da hankali kiyi mata tuni da duk wanda yayiwa iyayen sa biyayya to tabbas zai ga alkhairi a cikin rayuwar sa, kada ki kuma yin abinda zai tashi hankalin ta, duk halin da zata shiga in fana ganin ki a kusa da ita zata ji sanyi, Sannan ke kuma ki bita da addu'oin zaman lafiya da farinciki Mai daurewa ya tabbata a gidan ta, insha Allah sai ts samu fiye da yanda muke hasashe". Inna share hawayen ta take wasu na zubowa bata son musu da mahaifiyar ta amma ta san halin Baban mu sai shi, mikewa tayi da niyyan komawa Ya Maaji da bata da hakuri ga zafin zuciya ta bud'i baki da nufin zatace wani abu Maa tayi saurin dakatar da ita ta hanyan daga mata hannnu, kawar da kai gefe tayi tana cize lebe na haushin an hana ta magana. "Ya Maaji na tafi ki gaida su Bayuram,Maa na gode Allah ya saka da alkhairi ya baki nisan kwana insha Allah zanyi kaman yanda kika ce" Inna ke fad'an haka tana gyara hijhabi dake jikinta. Ya Maaji da duk takaici ya hana ta saka baki cikin maganan nasu da taga Inna ta juya zata tafi tayi yunkurin magana nan ma Maa bata bata dama ba ta kara daga mata hannu alaman tayi shiru. Shirun tayi tana kallon Inna har ta fice sannan ta dawo da hankalin ta kan 'yar uwar ta tace " haba yaya yanzu sanyin halin naki ya kai kija baki kiyi shiru a cuci 'yar jikar ki guda d'aya tilo, ni dai wallahi tafiya ta zanyi ba zan zauna bakinciki ya kashe ni ba" Hijabinta ta shura tayi hanyan waje, Maa tana ta kwala mata kira bata yarda ta juyo ba balle ta amsa, Dan murmushi Maa tayi tana girgiza kai tare da mata addu'a Allah ya rage mata wannan zafin zuciyan. Lokacin da ta dawo bacci ya d'an sace ni ban san ma ta dawo ba sai cikin bacci naji kaman kuka harda shashheka, a hankali na bud'e ido na dan tabbatarwa, bayan ta na gani tana ta kuka tsakanin da Allah wanda tun tasowa ta banga ko kwatanci sa tayi ba. Tausayi da kaunar tane naji yana bin ko ina a cikin jinin jikina saboda na san duk a kaina ta tada hanklin ta kan auren da taji Baba yace zai min, banida zab'i dole in kwantar da hankali in nuna mata babu komai ta wajena ko zata samu natsuwa, wannan dalilin yasa naki fad'a mata tun farko kenan amma ba yanda zanyi dole ne ta sani. D'an motsi nayi yanda zata ji, aiko nan da nan ta shiga share hawayen sannan ta d'an juyo sai taga ido na a rufe, bakin gado tazo ta zauna tana shafa min gashin kaina, jin ta daina kuka yasa na bud'e ido na kaman yanzu ne na tashi daga baccin. Murmushi ta sakar min tace " bacci kika koma kenan?" Gyad'a kai na nayi nima ina maida mata martanin murmushin. Ina ta jira inji ko zata min maganan auren amma naji tayi shiru sai jana take da hira tana bani labaran ban dariya, nima dan in kwantar mata da hankali yasa na saki raina nayi ta dariya amma can kasan raina cike ya tab da damuwa. Bayan sallah magarib sai ga Abban Zafar da tawagar sa a kofar gidan mu Kuma sun taki sa'a Baba yana nan bai tafi ko ina ba, Baba duk ya rikice ya susuce ganin manyan masu kud'in garin maiduguri a kofar gidan sa kuma da sunan sun zo had'a zuri'a dashi. Makotan mu biyu ya kira sannan ya kira Baban Dije wanda zance shi ya jagoranci komai ya hana Baban mu gudun kada ya kwafsa ko ya saki layi, hakan da yayi ya taimaka kuwa dan shi Abban Zafar tunda yaji ance Mallam ya zata Baban Mallamin ne da gaske. Wata 2 ciff aka saka na biki mu aka rabu cikin mutunci bayan sun sauke carton carton na minti da chewing gum da goro na rabawa yan uwa, Abba yaja Baba gefe ya bashi check na wasu kud'ad'e kan yayi hidimar biki da gida sannan ya d'aura da basa bukatan a kaini koda cokali guda d'aya su zasu tanada min komai su kawai surka suke bukata. Murna da Baba yake ji kaman ya daka tsalle amma ganin yanda Baban Dije ya kama kai yake musu magana shima hakan ya kwaikwaya har yayi mishi sallama ya shiga mota driver yaja suka tafi. Muna zaune sai gani mukayi anata shigowa da kwalaye kaman za'a bud'e shago, kowa kallon kayan yake tare da neman karin bayani sai dai babu mai bamu, sai da aka gama shigowa da kayan tass sannan Baba ya shigo yana jan banban rigan shi a kasa cikin d'aga murya ya fara magana yanda kowa na gidan zai ji. "Allahu yayi Allahu yayi!!! Ina kuke mutanen gidan nan kowa ya fito yaga abin arziki daya same mu, kayan saka rana ne na 'yar albarka, wata 2 kacal iyayen ango suka ce a saka dan suna bukatan ayi auren da wuri. Ba wayan nan kayan kawai ba har takardan karb'an kud'i na banki sirikin nata ya bani sannan yace basa bukatan mu kai ta koda cokali su zasuyi mata komai...." "Aaaaaaayyyyyyiiirrrrrrrr!!! Inna Asabe ce ta rangad'a wannan gud'a cikin farinciki tace" Masha Allah 'ya tayi goshi duk abubuwa daka lissafo duk na saka rana ne ina ga Allah ya nuna mana ranan auren ba magana....." "Aikin banza aikin wofi kowa yaga dama zaiyi ai tunda abin shige-shige ne" Gwaggo Aisha ta katse ta, Inna Asabe dai bata kula ta sai shewa suke da Allah ya sanya albarka suke da Mama Dije. Tashin hankali sosai na shiga da ganin kayan da muka maganan Baba duk da na san da zancen, kokarin dannewa nake saboda kada in karawa Inna tashin hankali amma na kasa daurewa,kuka na fashe dashi sosai har jikina yana rawa na shiga d'aki da gudu na fad'a kan gado ina mai cigaba da kuka mai tsuma zuciyan mai sauraro. . Jiki a sanyaye Inna ta biyo baya na ta zauna a gefena ta kura min ido itama idon ta na cikowa da hawaye amma ta hana su zubowa, tana rayawa a ranta inama zata iya dakatar da wannan auren da tuni ta dakatar da wanne zan ji cikin lokaci d'aya na had'u da jarrabawan rayuwa ga rad'ad'in rabuwa da Yaya na bai bar ni ba ace kuma ga auren da bamu san daga ina ya fito ba. Sai dai bata da zab'i dole ne ta karfafa min guiwa inyiwa mahaifina biyayya kaman yanda itama tayiwa nata mahaifin, gyara zama tayi tana gyaran murya sannan ta fara magana cikin rarrashi" wani lokacin kuka bashi ne waraka ba ga matsaloli na rayuwar mu ba,sai dai mu kanji sauki da rad'ad'in da zuciyoyin mu suka tsinci kan su a ciki dan haka ba zan hana ki kuka ba kiyi Zareefa kema ko zaki ji sauki. A al'adance da kuma addinin musulunci ya bawa mahaifi daman zab'awa 'yar shi miji daya ga ya dace da ita bi ma'ana ya yarda da addinin shi da kuma tarbiyan shi dan haka kada kiyiwa mahaifin ki mummunan fahimta domin ba zai tab'a Kai ki inda zaki wulakan ta ba kuma albarkacin biyayya da kikayi mana Allah zai saka miki da mafi alkhairi ko kuma da abinda baki tab'a zato ba balle tsammani. Abu d'aya da nake son ki tuna wannan auren ko dan Abdulbasit ya kamata ki rike shi da hannu bibbiyu saboda na san duk inda yake zai ji cewa za'a miki aure,kn ga kuwa kin nuna mishi zaki iha rayuwa ko babu shi sannan zai fahimci cewa kina da masoya ba shi kad'ai ne gare ki ba". Tun ina kuka kasa-kasa har na daina nayi shiru ina sauraron kalaman Inna, ya zanyi dole ne inyi biyayya in aure shi tunda ya biyo ta hannun Baba, baya ga haka in nace bana son shi waye nake dashi a yanzu, wanda na taso da son shi tun ban san kaina ba ya guje ni ya watsa min kasa a ido I don't have choice rather than accept this man domin na gama soyayya a rayuwata zuciya ta ta rufe kofa tayi ban kwana da soyayya harb abada. Sanyi sosai Inna taji a ranta na ganin kalamanta sunyi tasiri a kaina har na daina kukan sai ajiyan zuciya da nake akai-akai, matsowa nayi jikin ta sosai tare da d'aura kaina a kan cinyar ta na saka hannaye na duka biyu na rungumo kwankwason ta, itama tasa hannu ta dama tana shafa min gashin kaina na fara magana a hankali kaman mai rad'a. " Inna ku iyaye nane biyayya a gare ku ya zama wajibi a gare ni, kukan da kika ga inayi ba dan auren da Baba yace zai min bane kawai na tuna da Yaya nane" na karasa wasu sabbin hawayen na zubo min na tausayin kai na, na fad'i haka ne dan in kwantarwa Inna hankali ba wai da gaske ba. Cikin jin dad'in kalamai na Inna ta kara rungumo ni jikin ta tana shafa kaina tare saka min albarka da addu'oin gamawa da duniya lafiya. ****************** A kwana a tashi babu wuya a wajan Rabbi Izzati, mun cinye wata d'aya cikin watanni 2 da aka saka na bikina kuma gini da Baban mu yake yayi nisa sa dan har an gamawa Inna bangaren ta,2 bedroom da babban parlour sai kitchen da store sosai ginin yayi kyau, yanzu bangaren Inna Asabe da Gwaggo Aisha ake yi. Maryam ta dage sai rawan kai take akan bikin ni bata san haushi ma take bani ba, duk wasu frnds d'in mu na makaranta ta sanar dasu sai shirye-shiryen su suke ni dai na kawao na mujiya na zuba musu. A bangaren Zafar ma hakan take dan shi cewa yayi babu wani biki da zaayi sai ranan da zai auri love of his life sannan zasu sha bukukuwa ba biki bama. Sadiq ne yace bai isa ba dole ne su sha biki in ya tashi yin wancan yayi abinda ya ga dama, yaso yayi jayayya amma ganin yanda Abba da Mom suka dage suna shirye-shiryen auren yasa yaja bakin shi yayyi shiru tare da zuba musu ido ya san in har zai cigaba da nuna halin ko in kula asirin shi zai iya tonuwa. Akwai wata mata daga sudan take ta kware wajan gyaran amare Inna ta nemo kuma wai dole sai kaje gidan ta da farko ta ganki sannan zata duba gyaran daya dace da fatar ki,sun gama magana da Inna saura wai ta tura ni ta ganni, ba dan naso ba Inna tasa na kira Maryam a waya kan tazo ta rakani. Da washe gari kuwa tazo muka tafi gidan nata da yake can Shokari, koda muka je gidan ta cike yake da matan aure harda sabin amare ana tayi musu aiki dan harda 'yan mata masu taya ta tana biyan su. Tarba na musamman akay mana a babban parlour ta inda take sauke bakin ta na musamman,bamu dad'e da zama ba tazo wajan mu bayan mun gaishe ta cikin girmamawa itama ta amsa mana cikin kulawa sannan ta fara aikin ta wato rubuta duk kayakin da zasu dace da fatana da kuma gashi na sannan ta sallame kan cewa sai next week zan fara zuwa, godiya mukayi mata muka fito zuwa gida. A gajiye tibis muka dawo kasancewar Anguwan nata da nisa sosai da namu, mun shigo layin mu kenan wata had'add'iyar mota baka wuluk tazo zata fita mu Kuma muna shiga kaman ance min dago kanki ina d'agawa na tsaya cak tare da dafe kirji na da hannu biyu ina zaro ido waje duk at da same time bakina na rawa nace " YAYA NAAA..." [1/26, 7:14 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *25&26* Yanda ka san statue haka na tsaya ko motsi na kasa yi sai motan nabi da kallo da idanuwana kaman zasu zazzago kasa ga kuma zuciya ta na ta lugude kaman zai faso kirji na ya fito. " What's wrong with you Zareefa daga ganin mota sai kice ga Yayan ki, ke duk wulakanci da mutumin nan yayi miki ashe baki cire shi a ranki ba har kina tunanin zai dawo gare ki Kuma ga dukkan alamu zaki karb'e shi da hannu bibbiyu kenan...." "Maryam shi na gani fa ba imagination bane" na katse ta da muryar tausayi. "What ever, zo muje ga Inna can da kaya a hannu zata shiga gida muje mu taimaka mata ba wannan surutu mara kan gado ba" tana magana ne tare da jan hannu na muka fara tafiya ina waiwayen baya ko zan ga motan zai dawo amma har muka shiga gida banga ko kalar motan ba, kamin mu karasa Inna har ta riga mu shiga gida. A parlour muka iske ta zaune tana kallo babu lodin kaya da muka ga ta shigo dasu, zama mukayi muma anan Maryam tana yi mata bayqni akan zuwan mu gidan mai gyaran amma hankalin ta yana kai na ganin nayi shiru na zama wani iri ba kaman yanda muka fita ba. "Ke kuma lafiyan ki kuwa ana magana kinyi wani zuru dake?" Kaina na mayar kasa ina kokuwa da hawayen da naji suna son zubowa, harara Maryam ta b'alla min tana muskudawa sannan ta bawa Inna amsa. "Kyale ta Inna ni takaici ma ya hanani kula ta, muna shigowa layin nan wai kawai dan taga mota ya wuce kin ga yanda ta daskare waje d'aya wai taga wannan mayaudarin da kyar fa naja ta muka biyo bayan ki lokacin kina shiga gida ga kaya a hannun ki nace muzo mu taya ki". "Ban san meyasa taki sakawa ranta dangana ba ko kin manta aure zakiyi, haka zaki je gida wani kina wanna shirmen da shashanci? Ki kama kanki daga irin haka na gaya miki" Inna take dad'in haka cikin fushi ba tare da ta bawa Maryam amsar tambayar ta ba, nima hakuri na shiga bata ina cewa na daina ba zan sake ba Maryam tana taya ni sai da muka ga ta sauko sannan muka bari. Bayan mun huta mun ci abincin da Inna ta ajiye mana sannan Maryam ta wuce gida tare da cewa sai munyi waya. Tun daga wannan rana suka kara kaimin shirye-shirye da suke Inna ta ta zama busy sosai these days sai fita sayayya suke da Maman Dije wata rana Kuma da Inna Asabe, Gwaggo Aisha ce dai ko kallo basu ishe ta saima yad'a habaice-habaice da take. A haka satin da matan tace zan fara zuwa gyara ya zagayo na fara zuwa wajan gyaran a motan su Maryam wanda Mamanta ce ta d'auki nauyin hakan kullum driver zai zo ya d'auke ni in mun gama zuwa yamma kuma waya kawai zanyi yaje ya maido ni gida kasancewar tace ba'a son ina shiga rana saboda zai maida aikin baya. *************** A gidan su Zafar suma ba karamin shiri suke ba abinka da masu kud'i an gyara mana gidan da zamu zauna duk da sabon gini ne sai da suka Kara da d'an gyare gyare,kayan da za'a saka na cikin wannan gida Abban Zafar ne yayi order su daga kasar waje haka ma kayan lefe na suma duk a kasar waje suka had'o su, shi dai yana gefe yana kallon su yana jin ina zai iya hana su ko kuma inama zai iya fad'a musu gaskiya cewa auren da zaiyi temporary ce ba permanent ba su daina kashe kud'in su amma hakan ba mai yiwuwa bane dan yayi Imani Abban shi yaji abinda ya shirya suna iya batawa na har abada. Sadiq kuwa in ka ganshi zaka zata shine angon kan yanda ya kasa ya tsare komai yana tafiya daidai, baya ko neman shawaran Zafar yake abinsa shi kad'ai ko Kuma suyi da sauran friends d'in su saboda ko ya nema baram-baram suke rabuwa dan haka suma suka ajiye shi a gefe suke abinda ya dace. Ana saura kwana goma bikin duk an gama komai a gidan nasu had'a dasu cards da kayan da zamu saka na duk event d'in sun kammala sai bikin kawai suke jira. Da yamma Mom ta kira shi a waya kan ya same ta a part d'in su, amsawa yayi da toh dama ba wani abu yake ba dan haka ya mike ya fita zuwa amsa kiran nata. A parlour ya iske su kusan su biyar da Aunty's d'insa wasu ta bangaren Mom wasu kuma ta bangaren Abba sun baza uban kaya a gaban su suna ta kallo. Gaishe su yayi ya koma gefe ya zauna yana yan dane-dane da wayar shi. "Ya kuma zaka zauna a nesa, oya come closer kayan amaryar ka ne zo ka duba in akwai abinda baiyi ba sai a canza ko" Mom tace mishi hakan. " No Mom ba sai na duba ba duk abinda kukayi daidai ne" yace yana kara gyara zama alamun bashida niyyan motsawa bare tashi. "Kema dai Yaya da son jan magana kike, wannan lefen nayi Imani ko gidan governor zamu iya kaiwa without fargaba balle Kuma wannan 'yar talakawan" cewar wata kanwar Mom da suke kira da Aunty Hauwa dama tana takaicin Zafar daya tashi aure bai nema a cikin 'yan uwa ba yaje ya jajib'o musu 'yar talakawa. "Hmmmmm" Mom tace tana tabe baki alamun maganan yayi mata dad'i. "Ai babu zancen duk abinda akayi dadidai ne kai kafi mu sanin matar ka da abinda take so da Kuma abinda zaiyi mata kyau dan haka kazo ka duba nace maka" Aunty Falmata ke fad'in haka babu alamun wasa kan fuskar ta. Da yake ya san halin ta bata da sauki sam kusan halin su d'aya da Abban shi shiyasa yake matukar shakkar ta, ba musu ya taso yazo ya tsugunna gaban kayan ya fara dubawa kaman da gaske bayan kawai d'agawa yake yana ajiyewa ,su Kuma kannen Mom da ita kanta sai tab'e baki suke na jin takaicin wai sai ya duba. Yana yi yana kallon ta ta gefen ido ganin hankalin ta baya kan shi ya mike ya dawo gabanta ya zauna cikin natsuwa yace " na duba su duk sunyi kyau sosai Baawa". Murmushin jin dad'i tayi tana ajiye wayar ta a gefe sannan ta maido da hankalin ta gare shi ta fara magana tace" yanzu abinda ya rage ga kayan da zatayi amfani dasu a events na bikin ku naka da nata duk suna wajan mahaifiyar ka it's a small gift from me". Mom da taji kaman tayi kuka dan haushi dama niyyan ta in har ba tayi magana ba ta tafi ba zata aika min su ba, cikin dauriya tace" eh gasu nan Son, zoka duba Baawar ka ta sayo muku latest designs na birgewa". Karasawa yayi zuwa inda Mom take nuna mishi ya zauna ya bud'e had'add'un trollys d'in da wani cool suits mai d'an karan kyau ya fara arba wanda kana gani ba sai an fad'a maka kasan mai tsada ne, cikin farinciki ya cigaba da duba su d'aya bayan d'aya ko wani event da kayan da zai saka har zuwa ranar daurin aure kuma kowanne da takalmi da wrist watch d'in shi, godiya ya fara yi mata cikin jin dad'i dan kayan sun burge shi sosai. "I'm glad u like it, sai dai ka manta baka duba na amarya ba" ta amsa mishi itama cikin farinciki, sai da ta fad'a ya tuna da wata amarya, bashi da wani zab'in illa kirkiro murmushi tare da bud'e first 1 dake kusa shi. Sai da yaji numfashin shi ya d'an d'auke na second biyar da yayi arba da wata gown na Indian material sai walwali da d'aukan ido yake ya had'u har ya gaji da had'uwan, daurewa yayi ya cigaba da duba kayan Wanda gaba d'aya anko ne da nashi sai dai a tunanin shi wayan nan zasu fi nashi tsada tunda su kowanne ga jewelry da takalmi da jakan shi. Tun yana kirkiro murmushi na kar a gane halin da yake ciki har zuciyar shi ta rinjaye shi fuskar shi ya nuna abinda ke cikin zuciyar shi, Baawa da hankalin ta yana kan shi tana jiran taga yayi ta murnan ganin irin kayan da ta hadawa amaryan shi sai taga tsab'anin haka fuskan duk a murtuke yake duba su. Cikin sanyin jiki ta fara mishi magana" da alamu dai Zafar kayan amaryar nan basuyi maka ba ko?" " Haba Baawa wad'an nan kayan ko makaho ya shafa su ya san sunyi matukar kyau, abinda yasa kika gan ni haka jikina ne yayi sanyi ban san wani kalamai zanyi amfani dasu ba wajan gode miki domin kayan sun burge ni sosai" yabata amsa yana gyara mood da kawata fuskar shi da yalwataccen murmushi. "Menene a nan da har kake fad'in haka Son, ko ka manta kai d'in gudan jini nane?" Girgiza mata kan sa da yake kasa yayi ya cigaba da murmushin dole. "Good yanzu abinda nake so da ksi shine kada ka bar kayan anan ka kai su can bangaren ka ko zuwa dare sai ka kai mata ko?" "Toh Aunty mun gode Allah ya saka da alkhairi" yace mata. "Ameen my son Allah ya nuna mana ranan lafiya mu sha biki" tace tana d'an dariya 'yar uwar ta Hadiza na taya ta dan su Mom sun bar musu parlorn tuntuni. Maida boxes d'in yayi ya rufe ya kira masu aiki suka taya shi d'auka yayi musu sallama ya fita, a parlour shi suka ajiye suka fita shi kuma ya nemi waje ya zauna yana ta jan tsaki dan shi raini ne baya so da girman shi da komai wai shi za'a aika wajan 'yar yarinyan ga Sadeeq ma jiya yazo mishi da rainin hankali wai shi zai kai mata invitation cards shi kuma yace in ba zai Kai da kan shi ba ya zubar dasu a bola shi Kuma ya watsar mishi akan gado yace ga bolan nan, da gudu ya bi shi ya fita yana mishi dariyan mugunta. "D'an iska zamu had'u ai sai na koya mishi hankali" yace shi kad'ai kaman wani sabon kamu. Ni kuma gyaran nan da akayi min na kwana 2 ya karamin masifan kyau kaman an canza min fata ta saboda yanda ya kara laushi da tsantsi ga kamshi na musamman da yake tashi jikina. Da daddare bayan mun idar da sallah isha'i Inna ta kawo min wani had'i da akayi na madara tace in shanye in bata kofin ta, karb'a nayi na shanye na saboda ta zata auren gaskiya zanyi take b'ata kud'in ta bata san auren wata 2 ko uku bane. Lafiyayyan abinci ta zubo min shima tace in cinye dan kwanakin nan abinci masu gina jiki take bani Kuma shine ya bada gudumuwar hana rama ta bayyana a idon mutane, ina cikin tsakurar abincin ina sauraron wa'azi da sheikh Aminu daurawa da yake akan rayuwa a tashan sunna tv,o sosai wa'azin ya saukar min da natsuwa domin kaman dani yake yi. Sallaman yaron makocin mu da yayi yasa na dago da kai na tare da amsa mishi kasancewar ni. kad'ai ce a parlour Inna tana kitchen. "Wai ana kiran ki inji wani mai mota a waje". Rasss shine sautin da naji zuciyata ya bada, na kasa bashi amsa saima zuciya ta daya tafi tunani waye zai kasance kenan,Yaya na ko d'an rainin hankali nan ne? Koma wanene ina daidai da shi, kamin in samu amsan da zan bashi naji muryan Inna a kaina tana " baki ji bane ana kiran ki kikayiwa mutane shiru ko duk salon wulakanci ne haka, wato duk maganganun dana gaya miki ta bayan kunne suke wucewa ko?" Kamin in bata amsa ta cewa yaron yaje yace tana zuwa, shi kuwa ya amsa da toh ya fita abinsa. Itama kitchen ta koma ba tare da ta kara kallon inda nake ba, hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min sannnan na mike na d'auki hijabi na dake kan kujera na saka na kama hanyan fita nima. Har na kai hannu zan bud'e kofa naji muryan Inna a bayana tace" ki tabbatar kin shigo dashi parlour baki na Baban ku kada ki bar shi a waje kuma in kun shigo ki zo ki kai mishi ruwa". Da toh na amsa na fita, ina jan kafa har na fita waje na tsaya a kofar gidan mu da yanzu ya koma gate, na kusan minti uku tsaye a wajan ina kallon motan banida niyyan karasawa, shima kuma ko fitowa bai da niyyan yi balle in saka ran zai fito. Tunawa da yanda naga Inna ta b'ata ran ta d'azu yasa na fara takawa a hankali kaman mai tsoron kasan har na isa jikin motan na tsaya. Sauke glass d'in motan yayi yana min kallon up nd down fuskar shi d'auke da wannan shu'umin murmushin sa na gefen baki " 'yar Mallam Ni kike jira in je in same ki kenan, baki san cewa duk zuwan da zaki ga nayi nan dalili yake kawo Ni ba wai dan kin isa ba...." "Kaman yanda nima dalili ne yake sakani fitowa ba dan kana gaba na" na katse shi nima ba tare da na bari ya gama ba. "Really!!! I like ur courage, ki cigaba but ki rike a ran ki cewa zaki gane kuskuren ki when we are together under the same roof" yace har yana wani cize lebe. Kaina na kawar gefe ina son bashi amsa amma abinda nake hangowa a nesa damu kuma cikin d'an duhu shiya d'auke min hankali har na kasa kula shi, shima ganin hankalin na baya tare dani yasa ya fito tare da sauke kayan da ya kawo ya kira yara da suke wasan su a gefe yace su shigar min dashi cikin gida. Shiga motan shi yayi ya tayar yayi revise, karan motan shi da naji shiya da na mayar da hankali na kan motan ba tare da ya kara ko kallon inda nake ba yaja motan shi ya tafi na raka shi da ido, sai da ya kusan b'ace min sannan na dawo da ido na wajan dana d'auke sai dai Kuma yanzun naga wayam babu kowa a wajan sai duhu da ya kara mamaye wajan. Dafe Kai na nayi da naji yana juya min saboda tsananin ciwo da yake min , da kyar naja kafafu na da suka min nauyi na nufi gida ina mai mamakin ya akayi Inga mutum kuma lokaci d'aya kuma ya b'ace, ko dan na kasa cire shi a raina shiyasa yake min gizo. [6/16, 9:15 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *26&27* Haka na shigo ciki hannuna dafe da kaina, ragwajab na zube akan kujera ina lumshe ido ba tare da na lura da kayan da aka shigo da su ba Inna ta saka su a gaba tana aikin kallo. "Ban san yaushe kika samo wannan halin na rashin ji ba Zareefa, yanzu duk maganan da na gaya miki amma babu wanda kika d'auka kika bar bawan Allah nan a waje ko balle ki kai mishi ruwan sha?" Ban iya bata amsa ba sai goge hawaye da suka ki tsayawa nake dan na san ba lalle ne ta amince da abin da zan fad'a ba kasancewar bata san komai akai ba, nima kallon kayan da ban san daga ina suka zo ba nake domin ko za'a yanka ni ba zan iya cewa shi ne ya kawo su ba. "Kai jama'a wannan lodin kaya daya kawo su kuma na menene, uhum harda su gwalagwalai kuma da alamu na fitan biki ne ko?" Na tsinkayi muryar Inna ta katse min zancen zucin da nake. Bani da mafitar da ta wuce na amsa mata da " eh " tunda yanzu na fahimci daga ina kayan suka fito. "Toh Masha Allah amma hidiman nasu yayi yawa bana so gaskiya ki gaya mishi su rage hakan nan kinji?" Nan ma dai gyad'a mata kan nayi ina mamakin dukiya da aka narkar wajan sayan kayan nan. Nan na kwanta kan kujera duk abin duniya ya ishe ni na rasa ya zanyi da rayuwata, ban tab'a kawowa a raina zan shiga cikin irin tashin hankalin makamancin wannan ba A kwana a tashi babu wuya wajan Allah dan yau shine karshen gyaran fata da ake min sai lalle da aka shiga yarfa min na jan lalle gwanin sha'awa taso a yi min kitso nace mata bana so ta bar min gashi na haka, ba dan taso ba ta kyale ni suka maida hankali kan lallen. Sai bayan sallah isha'i muka samu daman komawa gida ta d'eba min wasu kayan gyaran tace in rinka yi a gida tunda auren saura kwana 3, karb'a kawai nayi na amsa mata da toh amma ba dan ina da niyyan yi ba. A kofar gida suka sauke ni Maryam bata shiga ba saboda dare yayi suka wuce tana ta santin lallen da akayi mata wai yayi kyau, ni dai ban iya biye mata na juya zuwa gida abina kasancewar na kwaso gajiya. Mutane na gani cike a cikin gidan mu ana ta cece kuce kuma kana jin maganan kasan kaman fad'a ake , d'an d'aga kai na nayi naga matan gidan mu ne harda makota, ban kara gigin d'aga kai na ba na wuce b'angaren mu tunda banga Inna ta a wajan ba. A parlour na samu Inna da 'yan uwan ta zaune sun saka kaya a gaba suna maida abinda ya faru duk fuskan su babu dad'i sai ita Inna ce ba zaka gane mataa ba. Zama nayi a kasa kan carpet na fara gaishe su d'aya bayan d'aya duk suka amsa min fuska sake, muna gama gaisawa na wuce kitchen neman ruwan sha anan ma wasu kayan abinci na gani gari guda. Ina cikin shan ruwa ne naji Ya Maaji tana magana cikin b'acin rai wanda ya sani maida hankali kan zancen nasu I really want to know what happened. "Ni dai idan kun san ba zaku canza halin ku ba wallahi karshen ta ba dani za'a yi bikin nan ba, haba wannan wacce irin rayuwa ce ayi ta cutan ka ana kunsa maka bakinciki amma ka kasa ramawa, wa za'a nunawa hakurin muma ai muna da itan matsalsr idan yayi yawa sai a maida ki kwandon shara yanda kowa ya kwaso nashi kan ki zai juye". "Gaskiya ne hakurin Bintu yayi yawa sosai har ta doke Yaya wajan sanyin hali, amma wannan zalincin ne dai ba zamu bari ba dole ne a d'auki mataki saboda gaba" cewar Aunty Batool. "Kina ji fa ita Bintun da bakin ta yanzu take cewa ba yau ta fara yi ba wai ranan da aka fara musu gini an ga wasu layu wanda aka kona ita kuma a take ta fara iface-iface wani babban abin takaici wai ita da Zareefa su sukayi mata addu'a har ta samu lafiya...." "Har ta samu kafan komawa wajan bokan ta zaki ce Batool, in ba dan Allah ya takaita wannan yaro Ibrahim ya ganta yazo ya fad'a ba, da shikenan auren nan ya fasu amma da yake bata da kunya bakin ta bai mutu ba ana magana tana mayarwa" fad'in Ya Maaji. "Ban ki ta naku ba nima ba wai kuma fad'an ne ban iya ba, amma abinda nake son in tuna muku duk wanda ya rike Allah in ba wani ikon sa ba babu abinda zai same ka, ku duba mana sau 2 tayi yunkurin cutar da mu Allah yana mayar mata da abin ta. Ban so kuka kula ta ba, jibi yanda asirin ta ya tonu cikin bainar jama'a wannan ma ya ishe ta ishara, mu kuma bama gajiya da d'aga hannayen mu sama insha Allah, Allah zai kare mu" Inna ta basu amsa cikin sanyin murya babu wacce ta kara cewa kala da alamu maganganun ta ya kashe musu jiki. "Innalillahi wa Inna ilahi raji'un" shi kawai nake ta maimaitawa tare da sulalewa na zauna dabas kan tiles na kitchen d'in, cikin tashin hankali amma ni kam Ibrahim bai kyauta min ba da yazo ya fad'a har aka dakatar da ita, ina ma tayi nasaran sake binnewa da shikenan na fita daga wannan cakwakiyar matsalan. "Gata da hassada da ya gama bin jinin jikin ta dubi yanda ta fito wai tana nuna adawar ta a zahiri kan kayan cin-cin da aka kawo" naji muryan Aunty Fatima tana magana cikin d'acin rai. Sai ana na fahimci ashe kayan da na gani kayan cin-cin ne kenan, shikenan yanzu da gaske ake aure za'a yi min, auren ma da wanda bai san daraja ta ba? Hawaye sai rige-rigen saukowa suke banyi yunkurin hana su ba na bar su suna kwarara domin yana rage min rad'ad'in dake cikin zuciya ta. Muryan Inna naji tana kwala min kira ba shiri na mike daga zaunen da nayi ina share hawaye na na fito duk suka bini da kallon tausayi . "Me kike yi a kitchen d'in tun d'azu" ta jeho min tambaya, "Ruwa na sha " na amsa mata cikin murya kuka, kan kace me kuma hawaye suka fara kwaranya. "Daga tambayan ki shine zaki fara min kuka? Bari in tashi inyi miki abinda zakiyi kukan da hujja" Inna ke fad'an haka tana shirin mikewa, da gudu nayi d'aki na maida kofa na rufe ina jin su Ya Maaji suna mata fad'an kada ta kuskura ta tab'a ni ta bar ni inyi kuka na, ban ji karshen maganan su nayi shirin kwanciya na kwanta abina. Da washe gari ga mamakina ashe duk basu tafi ba anan suka kwana sai ya Maaji da ta kwana gidan Maa, da rana ya fara yi sai ga gidan mu ya fara cika da 'yan uwa ashe wai yau ake cin-cin ni dai ganin sun fara yawa na wuce bangaren su Maman Dije saboda kowacce ta ganni sai ta kira ni da sunan amarya basu san hakan kona min rai yake ba shiyasa na gwammace in tattara in bar musu gidan su kara ta. Kamin in wuce naji sun fara sa-in-sa da 'yan uwan Baba da suka zo cewar su zasuyi, su Aunty Batool kuma suka ce anyi magana da professional bakers su zasuyi kasancewar komai ya zama na zamani ita kuma Gwaggo Hinde ta fara masifa wai ai zagin su akayi a fakaice meye basu iya ba da za'a ce zasu kira wasu suyi dama sun raina su. Wucewa ta nayi abina ban san ya suka kare ba, ina can b'angaren su Dije Ni kad'ai duk abin duniya ya ishe ni zuwan su Maryam da sauran 'yan class d'in mu yasa naji d'an dama-dama. Kusan azahar Dije ma ta iso da yaron ta da yayi wayo gidan ya gama kacamewa saboda surutun ta, hatta Hajara nan tazo tana d'an kqma jiki tana baya-baya saboda abinda ya faru jiya, sai da naja ta da wasa sannan ta saki jiki suka cigaba hayaniyar su Jameela ce dai ban san ina take ba domin yanzu abin nata kullum kara muni yake dan sai tafi sati bata gida kuma koda ta dawo to a buge take dawowa ta zama cikakkiyar 'yar kwaya. Muna nan a b'angaren Maman Dije Har dare a lokacin mafi yawancin 'yan matan sun wuce Dije ma ta tafi sai Maryam da Hajara ne kad'ai suke tare da ni amma itama Maryam d'in shirin tafiyan take wai sai gobe zata taho gaba d'aya ba zata koma ba sai an gama bikin. Har bakin gate muka raka ta nida Hajara inda driver gidan su yake jiran ta, ta shiga yaja suka tafi mu Kuma muka koma cikin gida, Hajara har tana shirin shiga kofan su na tsaida ta nace " Dan Allah Hajara muje mu kwana tare a d'aki na kin ga har yanzu da sauran mutane a b'angaren mu". "Kina ganin babu matsala?" Tambayan da ta jeho min kenan idon ta na cikowa da kwalla. "Wani matsala kuma ko kin manta ke'yar uwa tace" na bata amsa tare da jan hannun ta muka wuce, a parlorn muka tadda su Ya Maaji sun baje suna rarraba snacks da akayi da wayan da aka bayar akayi cikin different containers wai suna rarraba su. Za'a cire na gidan su Ango da wanda za'a rabawa baki sai kuma w so hg6xhanda za'a rage min "wai" atoh dole ince wai dan ni har yanzu na kasa gaskata aure na ake. Hajara duk ta kasa sakin jikin ta akan abinda ya faru jiya ga ya ma'aji sai binta da kallon banza take,ganin haka yasa na jata zuwa d'aki da yake mallaki na a yanzu, tunda muka shiga naga jikin ta ya kara sanyi sai bin d'akin da ido take alaman d'akin yayi mata kyau dan sai ince zan iya kira shigowan ta d'akin mu tun kamin ayi mana wannan ginin. A bakin gado nace ta zauna ni kuma ina shiga bayi nayi wanka tare da dauro alwala na fito na fara shirin bacci,duk tana zaune a inda na bar ta"tashi kema ki watsa ruwa zaki fi jin dad'in baccin" nace mata ina saka kayan bacci na ba musu ta mike ta shiga kamin ta fito na fitar mata da rigan bacci sannan na haye gado na kwanta,ko da ta fito ta mayar da kayan jikin ta nace ta canza tare da nuna mata kayan da na fitar mata. Ba zan iya cewa nayi bacci ko banyi ba a wannan daren saboda zanyi kaman bacci ya fige ni kuma duk juyi da Hajara tayi ina ji,ni dai gani nan har aka kira sallahn farko na tashi nayi alwala na fara nafila har aka kira na sallahn asuba mukayi tun da sanyin safiya mutane suka fara hidiman gaban su gidan ya d'auki hayaniya na ana shirin biki a gidan da gaske. Breakfast da aka kawo mana ban iya cin komai illah tea dana sha kawai nayi wanka muka koma can b'angaren Maman Dije a lokacin 'yan uwan sun fara cika gidan na kusa da nesa 'Yan mata da muke mates duk wajan mu suka zo suka dasa sabon hira sunayi suna ta tsokananta amma na kasa kula kowa cikin su sai yake da nake binsu dashi. Kusan 12 rana sai ga masu decor sun zo wai daga gidan su Ango aka turo su suyi decoration na wajan da za'ayi wushe-wushe. Duk yanda nayi gudun kitso bai yiwu ba dan Maa ce da kanta ta turo wata mata tace in zauna a min kitso,dole na na zauna aka yaryad'a min kitson KELEYASKU. Ba karamin kara fito dani kitson yayi ba, da yake step 2 akayi min wasu ta baya wasu Kuma ta gaba,na gaban nan ya sauk'o min har kan kirjina na baya kuma har gadon bayana kowa na wajan sai santi kitson suke,bayan sallah la'asar wasu masu make-up kusan su 4 wai suma daga can aka turo su harda photographer da masu video coverage kan kace kabo duk sun fara abinda ya kawo su,kamin ayi sallahn magriba naga 'yan mata sunyi wanka kowacce ta fito cikin ankon ta na atamfa mai tabarma da Maryam ta jagoranta sukayi. Nima ina yin sallah aka tilasta ni nayi wanka ina fitowa masu make-up din suka rufu kaina kowacce tana baza fasaharta,cikin lokaci kankani na fito kaman wata tauraruwa ni kaina kasa daina kallon kaina nayi ta cikin mirror. Maryam ce ta d'auko min akwati da kayan da zan saka suke ciki,ashe kowanne sun manna sunan event din da zan saka a jiki,ban tab'a gani ba duk da boxes d'ina a d'akina suke ko dan basa gaba nane oho. Wani atampa ce da ban san sunan ta ba amma kana gani kasan kud'in ta ba na wasa bane anyi mishi d'inkin GUMJE KANURI daya sha aikin stones kaman ba gobe sai Kuma laffaya wacce zata shiga da kayan shima duk ya Sha adon stones sai Kuma jewelry na d'anyen gold. Ba zan iya misalta muku irin kyan da nayi ba ku dai kawai ku hasaso da kan ku. Fito dani waje akayi nan bakin gate din mu inda yasha decorations dada fararen fitulu kaman rana, su Maryam na min jagora Aunty Fatima na bin mu da turarrn wuta har zuwa inda aka tanada wai wajan zaman mu ni da shi suka zaunar dani wai ana jiran zuwan ango. Ni dariyar suma nake a zuciya ta da suke saka ran wannan d'an rainin hankalin ne zai zo nan lalle suna da babban aiki. Kaman daga sama naji gud'a da kid'an GANGA KURA ana shelan isowan ango da jama'arsa, tun daga nesa na hango shi cikin wasu dankareriyar shadda wanda yayi shige da kayan jikina wato sky blue. Tun kamin ya karaso naji zuciya ta nata bugawa kaman ya fito Dan na San halin shi ban san yau Kuma da me yazo ba. [6/16, 9:16 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *28&29* Duk kamshin turaren wuta da yake wajan dana sauran mutane sai da wannan mayen kamshin nashi ya cika wajan,Kara sadda kaina kasa nayi ban kara gigin d'agawa ba tunda na d'aga na farko zuciya ta kuwa kaman zai faso kirji na ya fito haka nake ji tsabar bugu da yake. Ba komai ya saka ni shiga wannan halin ba sai dan sanin halin sa na wulakanci da disgi, ina gudun kada ya gwada su a nan a gaban kowa ba abinda na tsana a rayuwata kaman mutum ya wulakanta ni ko ya disgani a bayyanar jama'a. Ina cikin zancen zuci naji alamun mutum a kaina d'aga ido da zanyi na ga shine ya rankwafo da kan sa daidai fuska na yana sake min wannan shu'umin murmushi nasa yana kallon na, ni d'in ma shi nake kallo ya bala'in kara had'uwa cikin light blue shadda shi ga hula da ya saka itama light blue ce ba zan iya kwatanta muku yanda yayi kyau ba just imagined him. Na shagala da kallon shi naji yana dariya kasa-kasa yace " please da baki wahalar da kan ki wajan wannan abubuwa da kika shafa ba domin kara miki muni sukayi" ya karasa da kara sautin dariyar shi sannan ya zauna a gefe na inda aka tanada domin zaman shi. Hawaye naji sun cika min ido amma ban bar su sun zubo ba, I knew it na san dole ne ya shimfid'a min wulakanci son ran shi wai kara min muni sukayi ko ina ruwan shi da kwalliya ta. Kuma abin takaicin salon da yayi amfani dashi ya min maganan zaka d'auka hiran soyayya muke sai wani narke ido yake dan haka abin ya birge mutane sukayi ta mana hoto a wannan yanayin . Kawar da kai na nayi gefe ina jin kaman in tashi in gaggaura mishi maruka amma na danne zuciya ta ina hasaso yanda zaman namu zaya kaya nida shi. Ina cikin zancen zuci naji wannan mayen kamshin nashi ya kara cika min hanci wanda yake kara tabbbar min da kusancin namu ya karu, ban juyo ba balle inga wace irin zama mukayi da shi. A zabure na juyo ina kallon shi da ido na duk a waje sakamakon jin hannun shi a cikin nawa, muna had'a ido ya sake min wannan killer smile d'in nan nashi da in yayi babu alkhairi a cikin ta Aiko kamin in tantance me yake faruwa naji ya fara murza min hannu cikin kwarewa da cin zali da mugunta, a take naji kaman in saki fitsari a wajan amma da yake nima ba baya ba wajan iya basar da abu dan haka na basar kaman ba ni yakewa wannan muguntan ba. Cikin abokan shi wasu suka zo suna mu fito muyi rawa amma kememe yaki ko matsawa balle ya tashi , da suka ga bashi da niyyan tashi duk suka rufu kan mu tare da fara mana barin kud'i kaman basu san zafin su harda wasu cousins d'in shi 'yan mata da naga suna yi min wani kallon kasa-kasa ko me suke nufi oho dan ni Yayan nasu ma bai ishe ni kallo ba balle su. A cikin gida kuma iyaye na sun yiwa nashi tarba na mutunci sannan aka fara wasu events na al'ada game da wushe-wushen, dama wushe means welcome da yaren kanuri so they are welcoming them to our family wato an zama family d'aya kenan suma sun bada kayyaki na al'ada da ake bayarwa sannan su Inna ma sun mayar musu da wasu kayan suma. Sun d'auki lokaci mai tsawo sannan suka gama nasu a cikin gida suka fito gaba d'ayan su harda nawa iyayen, wata mata ce cikin 'yan uwan sa naga ta nufo mu kai tsaye tana murmushi tace " wannan wani irin Ango ne da ba zai cashe ba a ranar bikini sa?" Turo baki yayi kaman wani karamin yaro sannan ya bata amsa " Baawa ni ban iya rawa ba Kuma..." Mugun kallo da yaga ta watsa mishi yasa ya mike babu shiri da hannu na a cikin nasa wanda yanzu nake ji kaman ba a jiki na yake ba tsaban mugunta da yasha. A yanda ya mike ya tabbatar min da yana matukar shakkan matar nan jibi yanda ya mike babu shiri, a raina ina ashe duk wannan muzuran nashi na banza ne tunda da wanda yake. tsoro har haka. Yanda kika san statues haka muka tsaya musu kikam ba wanda yake da yunkurin yin motsi balle a je ga zancen rawa, iyaye na da nashi suka fure ruf sai barin naira suke mana. Ni dai duk mamaki ya ishe ni a raina yanda suke zubar da kud'i kaman basu san zafin su ba, a zuciya ta nace ina Gwaggo Aisha Mai cewa Yaya na d'an yankan kai ne tazo taga wayanan da ko ni kaina zan iya kiran su da hakan dan barnan kud'in yayi yawa. Ana cikin filin Sadeeq yazo ya fara mishi magana a kunne wanda yaja hankali shi ya saki hannu na ba tare da ya sani ba, ban san me suka tattauna ba sai dai naga yana murmushi ya juyo zai kara rike min hannu kan zamu koma mazaunin mu nayi azamar janyewa nayi gaba yabi baya na har muka zauna basu daina mana liki ba. Sai wajan sha d'ayan dare sannan taron ya tashi suka shiga motocin su suka tafi mu kuma muka koma cikin gida muka bar masu decor da tattare wajan. Muna shiga ban tsaya a ko ina ba sai bathroom na samu ruwa mai d'umi sosai nayi wanka tare da gasa hannu na da nake jin sa kaman ba a jiki na yake ba dan tsabar jin zali daya sha. Ina fitowa a wanka naji su Maryam da sauran cousins d'ina da muke mates sun zo taya ni kwana suna ta yaba mugun da basu san halin shi ba. "Wow kai Zareefa tayi babban sa'an samun hadadden miji mai iya love ga kyau ga naira ohh so romantic" cewar Zainab tana zama kusa da Maryam. "Allah ya samu a danshin ta abun yana bala'in burge ni samun classic miji haka" inji Hanan. "Ni abinda yafi birge tunda ya iso yake makale da hannun ta kaman za'a kwace mishi ita" Hauwa ta katse ta. Kallon hannun nawa nayi wanda ya koma jajawur saboda azaba su kuma a haukan su suna yabawa sun zata zallar soyayya ce, cike da jin haushin su na juya musu baya tare da jan duvet na rufe har kaina, ina jin su suka cigaba da suratan su daga baya suka hakura suka kwanta bacci. Basu dad'e da kwanciya ba duk sukayi baccin su hankali kwance, tashi nayi na zauna ina kallon su cikin sha'awa ni da nake jin ido na a bushe babu alaman d'igon bacci, ba yau kad'ai ba tunda maganan auren nan ya tabbata na rabu da bacci mai dad'i dan sai in d'auki lokaci Mai tsawo ban runtsa ba, ko kuma na samu baccin ya kwashe ni daren yana rabawa rabi sai in farka kuma wani lokacin ya tafi kenan wani lokacin kuma sai kusan asuba zai kara sace ni. Yanzu ma da naji kwanciyar ya ishe ni na shiga bayi nayi alwala nazo na tada sallah tare da neman agaji wajan ubangiji na. A b'angaren su Zafar kuwa yan uwan Abba cikin farinciki da Kuma yaba yanda iyaye na suka karrama su suka isa gida yayin da yan uwan Mom sai tab'e baki suke wai ya rasa inda zai nemo aure sai a wannan gida kaman akurkin kaji. Shi kuwa Zafar ko bai kula kowa ba ya shige part din shi ya kulle kan shi a ciki dan kowa ma haushi yake bashi, duk yanda abokanen shi suka so su gan shi bai yiwu suka wuce. ******************** Hausawa sun ce rana bata karya sai dai uwar d'iya taji kunya, toh hakane ya kasance a yau asabar itace ranar daurin auren kaman yanda naji suke fad'a kuma nake gani a yanzu duka gidan ya kaceme da hayaniya kowa sai hidiman gaban shi yake, masu gyaran gida nayi masu girke-girke nayi masu wanka ma nayi. Ni kuwa ina can kuryan d'aki abin duniya duk ya ishe ni ganin cewa fa da gaske ne auren nawa za'a daura maimakon na tsinci kaina cikin farinciki kaman kowace amarya sai dai ni a bakinciki na tsinci kai na dumu-dumu ga kewan Yaya na da ya dawo min sabo fil, na san da aure na da shine da nafi kowa farinciki a rayuwa amma sai gashi yau da wanda bai sona bai san daraja ta ba za'a had'i ni aure.dashi wace irin rayuwa zan shiga??? Kuka naji mai tsanani ya taho min na tausayin kai na, mikewa nayi ba tare da na kula 'yan mata da suke ta hayaniyar su ba na shiga bathroom dan in samu sukunin yin kuka na ko zan ji saukin rad'ad'in da zuciya ke min. Zama nayi dirshan a ciki na kama kuka kaman rai na zai fita ji nake kaman rayuwa ta tazo karshe ji nake shikenan nayi ban kwana da farinciki a rayuwa ta ji nake kaman na yanki ticket na shiga kunci na har abada. Ban san iya adadin lokaci da na d'auka a bathroom d'in ba sai knocking da naji ana yi a kofan yasa na d'an tsagaita kukan tare da maida hankali na kan mai bugawan. "Zo ki bud'e kofan nan Zareefa" naji muryan Inna daga waje, goge hawaye na na shiga na nufi kofan na bud'e tare da komawa gefe kai na a kasa naki yarda mu had'a ido da ita, shigowa tayi ciki tana bin fuska ta da kallo. "Rufe kan ki kikayi kina kuka ko?" Ta tambaye ni still tana karantar yanayi na ta maida kofan ta rufe, maimakon in bata amsa fad'awa nayi jikinta ina mai kara rushewa da kuka mai tsuma zuciyan mai sauraro balle ita da take mahaifiya a gare ni. Rungume tayi itama tana kokuwa da nata hawayen dan kada su zubo da kyar tayi nasaran maida su sannan ta dago ni tana share min hawayen fuska ta tanayi wasu na kara zubowa. Murmushi d'auke a fuskata ta take kallo na sannan ta fara magana " toh menene abin kuka anan kuma uhum? Yakin matan kenan muma haka aka rabo mu da gidajen zuwa inda bamu saba kuma muka d'auki hakuri da juriya muka saba kema hakuri zaki yi wata rana sai labari. Aure bautan ubangiji ne a gare mu mata shine kuma mafi saukin hanyan shiga aljanna in min bi Allah kuma kika yiwa mijin ki biyayya kaman yanda Allah ya umarce da muyi toh tabbas zaki rabauta, miji a duk yanda kike tunani a musulunci ya wuce nan miji babban jigo ne a rayuwar 'ya mace tunda da zaran an kai mace d'akin mijin ta shikenan komai nata ya koma hannun shi ko iyayen ta basu da iko a kanta ko kad'an misali koda mutuwa akace nayi in yace ba zaki zo jana'iza ta ba dole ne kiyi hakuri ki zauna kiyiwa mijin ki biyayya...." A razane na dago jajayen ido na da kuka ya rina ina kallon ta ina son yin magana amma na kasa sai baki na da yake ta karkarwa. Gyad'a min Kai tayi tana mai cigaba da murmushin " irin wannan biyayyan ake son mace tayi a gidan mijin ta, nasan yanda kike ji na san abinda kike tunani amma ina mai baki shawara a matsayi na na mahaifiyar ki, ki cigaba da hakuri kiyiwa mahaifin ki biyayya insha Allah gaba ba mu ba ke da kan ki sai kinfi mu alfahari da wannan aure zan cigaba da yi muku addu'a insha Allah komai zai dai-dai ta . Yanzu kiyi wanka ki fito ga masu miki kwalliya suna jiran ki a d'aki" tana fad'an haka ta wuce ta fita ta ja min kofa bata tsaya a ko ina ba sai bathroom din ta,ta fashe da kukan da take ta dannewa tun d'azu " ya Allah ka taimake ta ka kare ta kada ta fuskaci irin rayuwar da nayi a cikin gida na ya Allah ka sanyawa rayuwar auren ta albarka". Haka ta cigaba da kukan ta tana sumbatu domin a kullum daurewa kawai take ace a aurar da 'yarka ga wanda baka san daga inda yake ba balle ayi bincike a san halin shi babban tashin hankalin ta shine bata da daman cewa komai akai saboda mahaifiyarta ta gargad'e ta tun farko, amma ba zata daina fad'awa Allah ba ya bani ribar biyayyan da nayi musu. Da kyar ta rarrashi kan ta ta daina kukan ta fito jin hayaniya na kara yawa alamun mutane suna karuwa kenan. Ko da ta fito sai ta aro jarumta ta daurawa wanda take dashi a baya ta cigaba gaggaisawa da yan uwa da abokan arziki amma taki yarda ta kalli gefen da Maa take balle su had'a ido ta fahinmci tayi kuka, sai dai bata sani ba ta makaro domin Maa ta riga da ta gane halin da take ciki, murmushi kawai tayi tana yaba jarumtar 'yar tata. Bayan fitan Inna daga bayin sabon babin kuka na bud'e inayi ina mai tausayin kaina ta yaya zan iya yin biyyan nan da Inna take Fadi ga wannan azzalumin? Da kyar na rarrashi kaina na daina kukan na fara wankan sanadiyan takura ni dasu Maryam suka yi. Koda na fito na kasa kallon kowa a d'akin sai kan stool na gaban mirror naja na zauna kai na a kasa ba dan komai ba sai dan bana son yawan magana, su kuma masu make-up suna ganin na fito suka iso dan yin aikin su, ban hana su ba kuma banyi musu gardama ba suka fara min sai dai yau light make up sukayi min amma duk da haka ba karamin kyau nayi ba, Maryam da jikin ta duk yayi sanyi ganin yanayi na ta d'auko musu trolley da aka saka kayan da zan saka yau da safe ta kawo musu. Su suka taimaka min na shirya cinkin wata expensive lace fari sol dashi yasha diamond stones, ni dai tunda nake a rayuwata ko labarin irin lace din ban tab'a ji ba balle gani, headtie na wani yadi mai sheki suka nad'a min shima fari ne sai set na dan kunne da sarka harda zoben shi na pure diamond suka saka min. Ba zan iya kwatanta muku yanda ni Zareefa nayi kyau a wannan rana ba just imagine it urself sai dai ko kad'an babu abinda ya burge ni a ciki in na tuna sabon rayuwan kunci da zan shiga ma sai inji kuka na neman kwace min. Kawaye na suma sun fito cikin wani hadadden atamfa da sukayi anko kowacce sai zuba kamshi da haske suke zubawa ana jiran su angwaye su karaso dan karfe goma sha d'aya ne daurin auren. A can gidan su Zafar suma haka suka tashi da shirye-shiryen gaske ba irin na jiya ba dan Baawa jiya bayan dawowar su daga gidan mu ta kai karan su Mom akan yaja musu kunne kada su zubar mishi da kima gidan surukai, aiko bata ji da dad'i ba wajan Abba dan sosai ya nuna mata b'acin ran shi sannan yaja mata kunne tayiwa 'yan uwanta magana kowacce ta kama kanta in ko ba zasu kama ba kofa a bud'e take duk su watse bayan son harkan k'ananan mutane, dole ta nuna tayi nadama a gaban shi da alkawarin babu wata b'araka da zata taso daga gare su sannan ya kyale ta ta koma ciki cike da tsana ta. Sadeeq shine yazo ya tada Zafar daga bacci dan har tara saura yana kwance yana bacci cikin kwanciyar hankali abin shi, ya shirya tsaf cikin hadaddiyar shaddar shi ash color sai kamshi yake zubawa kaman shine angon,Koda ya farkan ma fad'a sukayi tayi shida Sadeeq din kan me yasa zai tashe shi yana cikin baccin shi mai dad'i. Ganin yana son yaja hankali sauran abokanen su da suke parlour yasa shi yayi shiru yace toh yayi laifi kuma ya amsa ya tashi yayi wanka ya shirya ga Abba da sauran abokan su suna jiran shi su tafi wajan daurin auren. Jin ya ambaci sunan Abba yasa ya mike Yana kumbure-kumbure kaman karamin yaro ya shige bathroom d'in shi dan yin wankan, dariya Sadeeq yayi sai da yayi Mai isar sa sannan ya ciro mishi kayan da aka tanada mishi domin d'aurin auren. Sadeeq shiya taya shi shiryawa sunayi suna fad'a shi dai Sadeeq dariya yake ta mishi ganin yanda yake turo baki kaman wani karamin karamin yaro mai shagwab'a. Farar dok ce mai matukar tsada yasa mai d'aukan ido yasha aikin hannu wato (gatau) hula takalmi duk farare ne wrist watch na hannun shi shima na pure diamond ne sai kamshi na musamman yake kana ganin shi kaga haddaen ango, suna gamawa suka fito parlour inda abokan sa suke jiran sa. Yana fitowa ihu suka fara suna mishi kirari saura na tsokanan shi dan sake fuska yayi ya dan biye musu suka tab'a wasa sannan suka raka shi wajan Mom. Tsakar gidan babu mutane sosai dan haka basu sha wahalan karasawa cikin ba , parlour Mom a cike yake ana ta hidima suna ganin shi wata mai murya ta saki wani irin gud'a da ya cika gidan nan da nan sukayi kan shi ana ta wasa da dariya da kyar ya samu ya karasa sama d'akin Mom, tana zaune cikin kawayen ta da 'yan uwan ta suna hira. Ido ta zuba mishi har ya karaso ciki zuciyar ta kuwa kaman farar takarda yau Allah ya nuna mata auren tilon d'an ta. Albarka suka yi ta saka mishi bayan ya suguna har kasa ya gaida su, Mom harda hawayen farinciki dan yau babbar rana ce mai babban tarihi a rayuwata. Kiran da Abba yayi mishi ne yasa shi mikewa ya fita ya tarar da tawagar Abba har sun fara tafiya, ba b'ata lokaci shima ya shiga cikin abokan sa suka kama hanya. Akwai wani babban masallacin juma'a a bakin layin mu kuma a nan ne za'a d'aura auren, so duk a can wajan layin sukayi parking wasu ma ko wajan parking din basu samu ba saboda yawan motocin dan haka wasu suka fara shigowa cikin layin namu Dan samun wajan parking. Masallacin kan shi ma har yayiwa mutane kad'an wasu basu samu shiga ba ko ina ka duba taron al'umma ne, in wanda bai sani ba yazo yaga taron zai zata auren 'yar babban mai kud'i ake ba ko dan siyasa ba 'yar Mallam Hassan ba. Baba yau in ka ganshi kaman yayi hauka saboda farinciki harda su governor a daurin auren 'yar shi harda manyan kusoshi na gomnati ,ba'a tsaya b'ata lokaci ba aka daura aure na da Zafar kan sadaki naira million 2. Muryan maroki da ya fara shelan d'aurin auren har cikin gudan mu a lokacin ina tsakar gida cikin mutane dan Inna ta saka ni fitowa waje gaida 'yan uwan Baban mu, a take wajen ya kacame masu farinciki suka fara masu bakinciki ma nayi, ni kuwa ji nayi kaman an saka ni a cikin kankara haka naji jiki na yayi wani bala'in sanyi tare da zazzab'i mai zafin gaske ba shiri na nufi bangaren mu kamin na karasa d'aki na har na fara rawan sanyi ina shiga na kwanta na lullub'a da bargo ina hawaye a haka Aunty Batool tazo ta same ni cikin rarrashi tayi min nasiyan yadda da kaddara sannan ta bani magani na sha bata bar d'akin ba sai da taga bacci mai nauyi ya d'auke ni sannan taja min kofa ta fita. Anan d'aura aure su Abban Zafar gaba daya suka wuce reception da Abba ya had'a a nan cikin gidan shi, su Zafar ma bayan shi suka bi duk yanda Sadeeq yayi dashi akan su tsaya ya d'anyi pics tare dani saboda tarihi yaki ya shiga mota suma suka rufa mishi baya. Sai yamma naji d'an karfin jiki na aka kara canza min kwalliya zuwa walima cikin abaya da Inna ta siya min saboda walimar ba'a dad'e da farwa ba yan gidan su Zafar suka kawo lefe na da ya kusan haukata mutanen gidan mu dana anguwan baki d'aya, nima a yanda naji Maryam tana lissafowa ban tab'a jin labarin irin su ba. Bayan an gama cece-kucen ganin lefen suma suka shiga cikin mu akayi walimar dasu inda Mallama Falmata Zanna ta wa'azantar kan biyayyan aure ko Inna ce tace tayi hakan oho, sai kusan magariba taro ya watse bayan anyi rabon manyan jakkuna masu d'auke da Al'quran ma daidaici sai sallaya da hijabi,nayi mamakin yaushe Inna ta shirya haka ko dan ban maida hankali ga bikin bane ban sani ba. Basu bar ni nayi alwalan magriba sai da nayi wanka da ruwan turare sannan nayi alwala na fito nayi sallah ina kuka ganin cewa dai da gaske suke dan sai shirye-shiryen kai ni suke shirya ni sukayi cikin atampa super mai ratstsin silver a jiki , d'an kunne da sarka da suka saka min suma duk silver ne sannan suka nad'a min laffaya mai masifan kyau shima silver color aka fito dani wajan su Inna da yan uwan ta. Nasiha suka fara min kan hakuri d'aya bayan d'aya Inna ta dai tana gefe tana kallon yanda nake kuka kaman raina ya fita, Maa ce ta katse ta tace itama tace wani abu mana. Murmushi mai ciwo tayi muryar ta na rawa tace" me zancen Maa da ku baku fad'a ba, ni sai dai inyi mata addu'a Allah yaa...." Kukan da take rikewa ne ya kwace mata ta tashi cikin sauri tayi d'akin ta, kara kuka na nayi na mike zan bita suka rike ni ina musu magiya da roko amma basu saurare ni suka sada ni da d'akin Abba yana zaune shi kad'ai sai washe baki yake. "Sai ku fita ku d'an bamu guri ni da 'yata ko" yace musu bayan sun zaunar dani a tsakiyar parlour shi, Aunty Batool har ta tsaya da nufin gasa mishi magana Aunty Fatima ta mata alama da ido da tayi shiru kawai su fita, ba dan ta so ba suka fita tana mitan wai dama ya san ni 'yar sace? Suna fita ya juyo gaba daya gare ni yana kara washe baki yace " ke kuma in banda kuruciya menene abin kuka anan, Allah ya azurta ki da samun irin wannan mijin da babu kamar sa duk maiduguri yaushe kuka hadu dashi amma ga yanda ya sauya mana rayuwa baki d'ayan mu, Wannan ai abin alfahari ne a gare mu ba ki saki baki kina kuka ba d'aurin auren ki har da gomna fa suka zo" ya karasa feeling very proud Yana gyara Zama. "Abinda nake so dake shine kada kice zaki manta da gida dan kin samu daula ya kamata ki san yanda zaki rinka tatso wasu abubuwa daga gare shi kina aiko mana ai kin gane abinda nake nufi" ya karasa tare da zuba min ido gyad'a mishi kai nayi hawayen takaici na zubo min dan ni da yace su Aunty's dina su fita na zata zai min nasiya ko kuma ya rarrashe ni kan auren da ya d'aura min ashe shi tunanin shi daban, wai yaushe ne Baban mu zai canza?? Na jehowa kai na tambayan da babu mai bani amsa. D'aga murya yayi ya kira su Aunty Fatima suka zo suka fita dani direct sai mota suka sakani suna ta zabga guda Aunty Fatima da Aunty Batool su suka sakani a tsakiya suna hirar su anan naji cewa wai Gwaggo Aisha da taji labarin taron d'aurin auren ta yanki jiki ta fad'i yanzu haka tana asbiti ba lafiya. Har muka karasa gidan Zafar da ya amsa sunan shi gida ko ince Aljannar duniya dake can bolori lay out hawaye bai kara zubo min saboda mamakin halin Baban mu dana Gwaggo Aisha. A maidaicin compound din gidan da fitilu da flowers suka ma ado drivern yayi parking ,Aunty Fatima dake zaune a gefe na dama ita ta fara fita sannan ta kama hannu na tace in fito da kafar dama, hakan kuwa nayi na fito kaina a kasa dan rabin fuskata a rufe yake tana rike da hannu na har entrance din parlour nan ma cewa tayi inyi Bismillah sannan in shiga da kafar dama. Ni dai tafiya kawai nake ban san inda nake jefa kafa ta ba har naji mun shigo wani d'aki kuma naji an zaunar dani akan wani tattausan gado, sai a lokacin naji sabon kuka ya zo min na fara ina rike a jikin Aunty na, sauran yan rakiyan kuwa suka bazama duba gidan suna ta santi tare da yaba kayan d'aki da Inna ta min wanda ni ban san ma yaushe akayi su ba kasancewar naji Baba na cewa ba za'a min komai ba dan sun ce basa bukata komai daga gare mu. Allah sarki Inna ta na san tayi hakan ne dan samo min martaba da Kuma daga gare su, bamu fi minti talatin da zuwa ba naga sun fara shirin tafiya dinner nima kara shirya ni sukayi cikin wani Indian material mai dan karan tsada da kyau, net suka saka min a tsakiyan kai suka kama da pin ana ganin kitson da aka min na gaba sai suka saka min sarkan kai wanda yazo min har goshi sarkan set ne da dan kunne da sarkan wuya da warwaro masu bada sauti mai dad'i. Kamin su gama min duk sun tafi sai Maryam da wasu cousins dina 2 su suka tsaya Jira na da kuma Aunty Fatima har bakin wata arniyar mota da ko sunan ta ban sani ba suka rako ni tare da bud'e min kofa na shiga, ina jira inga ta shigo kaman dazu sai naga ta mayar da kofan ta rufe suka nufi wasu motoci guda 2 daya a gaban mu yake daya kuma a baya ya kasance sun saka mu a tsakiya. Har motan ya fara tafiya naji motsi a gefe na a firgice na juya dan a zato na Ni kad'ai ce a cikin motan sai ganin mutum nayi a kishind'e kaman wani basarake yana latsa waya ko kallon inda nake baiyi ba, ni kuwa kasa d'auke ido nayi a kansa ganin sa cikin arniyar suit ko dan ban tab'a ganin ya saka bane sai naga ya masifan yi mishi kyau, "Bana son kauyanci ki daina kallo na da wayan nan idanun naki" naji muryan shi ya katse ni. Cike da jin haushin kaina na murkud'a mishi baki nace " da wani idon kasan ana kallon ka..." Ko rufe baki na banyi ba naji ya dalle min baki da yatsan shi a take naji hawaye sun cika min ido dan ba karya naji zafi sosai, a zuciya ta naja masa Allah ya isa cikin kwando na cigaba da murza lebe na can dai na kasa hakura dan abin na cizo na a rai ace kullum shi yake ha'in ta na ni bana ramawa. Cike da tsiwa nima na bud'i baki zan rama naji mutumin da yake gaban motan yana ce mishi mun iso, bari yayiwa sauran magana su zo yace, kamin ma ya rufe baki su Sadeeq suka zagaye motan tare da bud'e mana, shi ya fara fitowa sannan ya zagaya ta bangare na ya kama hannu na ya fito dani yana wani murmushi kaman ba shine ya gama cin zalina yanzu ba. "Come on wifey walk gently" yace min cikin wani murya da ban san shi da ita ba, a zuciya ta nace lalle wannan ya cika dan drama toh bai sani ba gidan ta yazo. Cike da yanga da fari nima na amsa mishi da " yes husby". A dan zabure ya juya ya kalle ni na second 5 ya d'auke kai yana murmushi, tafiya cikin hall din muka fara su Maryam suna watsa mana wasu abubuwa masu kyalli gefe daya kuma turaren wuta Hamra take bin mu da shi a baya. Hannun mu sakale dana juna kaman masoyan gaske har muka karasa wajan zaman mu, tunda muka shigo mc ya saki wakan bikin da Ali jita ya rera mana mai taken Zareefa ta Zafar. Sai da kowa ya zauna aka natsu sannan Mc ya fara gabatar da event cikin burgewa da wayewa, da aka nemi abokin ango ya bada tarihin ango Sadeeq ne ya fito ya bayar sannan Maryam ta bada nawa,daga nan aka bukaci mu fito mu yanka 🍰 kaman ince ba zan fito ba amma sanin duk abinda ya wakana anan zai je kunnen Inna yasa na fito muka tsaya a gaban tangamamen cake wanda ya kusan tsayin mu after d count of 3 muka yanka a tare, cikin wani salo ya gutsuro cake din ya saka min a baki da gangan na had'a da yatsun shi 2 na dalla mishi cizo wanda har ya saka shi saurin janye hannun shi yana yarfewa. Dariya na tintsere dashi cikin tsananin farincikin nima na rama muguntan da yayi min, suma yan hall din dariya suke su a tunanin su wata salon soyayya ce haka. Ina kallon shi sai harara ta yake ta kasan ido yana jiran in bashi shima ya rama bai san cewa na gama gano shi ba. Maimakon in gutsuro cake din in bashi a baki sai lakato shi nayi a yatsana na shafa mishi a hanci nan ma dariyan yan hall din suka kwashe da shi ni kuwa ganin ya harzuka kaman ya shake ni yasa na juya da sauri zan bar wajan, har nayi step 2 naji anyi sama dani. Tafi da ihu sosai ne ya cika hall din wanda ya ankarar da Zafar inda muke yayi saurin ajiye ni dan idon shi ya rufe burin shi ya min muguntan da nan gaba in muka had'a hanya da kaina zan gudu, lakace min hanci yayi yana yaken da yafi kuka ciwo, ni kuwa harda yi mishi gwalo muka koma wajan zaman mu raina fari tass yayin da shi kuma yake jin kaman ya had'iye zuciya ta mutu saboda haushi. Ali jita shi ya baza basirar sa a wajan anyi rawa an cashe anyi barin nairori harda daloli , anci an sha sannan mun samu gift ba adadi zuwa 10 aka tashi kowa yayi inda ya fito, a mota daya muka dawo da kawaye na nayi musu karyan zai sallami abokan sa basu san guduwa nayi ba dan in na shiga mota daya dashi ban san kalan muguntan da zai min ba. Muna zuwa gidan Aunty Batool ta had'a min ruwan turare ta sani a gaba nayi wanka ta shirya ni cikin wani dogon riga na material pink ta min light make-up ta zaunar da ni akan gado bayan ta min barin humra kala kala a jikina ta lulluba min katon gyale sannan ta zauna a gefe na ta kama hannu na duka 2 cikin nata tace; "Toh Zareefa ni zan tafi sai gobe zamu dawo zan kara maimaita miki kiyi hakuri kiyi hakuri sannan...." Aunty dan Allah kadaki tafi ki bar ni mu kwana tare dan Allah Aunty" nace ina kokrin rushewa da sabon kuka. "Kada ki kuskura hawayen nan su zubo shikenan naji zan kwana anan bari inje in rufo mana kofa sai mu kwanta ko" ta karasa cikin rarrashi. Ajiyan zuciya mai nauyi na sauke ina gyad'a mata kai ta mike ta fita tare da bar min jakar ta a d'akin. Toh fans yanzu aka fara wasan koyaya zaman ma'auratan nan zai kasance ?? Sai ku biyo ni a next page, sai kuna hakuri kwananan I'm so busy . [6/16, 9:18 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *30&31* Ina zaune da jakan Aunty sai baza ido nake in ga ta dawo amma shiru ko alaman motsi bana ji balle muryan mutum, gidan yayi wani irin shiru na ban mamaki, cike matsanacin tsoro da ya kamani lokaci guda na mike jiki na tsuma na nufi bakin kofa na bud'e na l'eko ina kyautata zaton parlour ne nan amma tashin hankali da nake ciki bai bar ni na tantance ba. Muryata na rawa alaman kuka na iya kufce min a ko wani lokaci na bud'i baki na kwala mata, shiru kake ji babu wanda ya amsa ga dukkan yanayin gidan ma ni kad'ai ce a ciki, da gudu na koma d'akin da na fito na maida kofa na rufe harda murza key da na gani a jiki na haye gado da kayan jikina ko mayafi ban cire ba naja bargo na gudundune har Kai na saboda tsoro na fashe da kuka yanzu shikenan ya tabbata an min aure kuma da wannan mugun sannan gida d'aya zamu zauna, shikenan na shiga uku na sai yanda rayuwa tayi dani. Tun ina kuka ina sake-sake har baccin wahala ya d'auke ni ba tare da na sani ba dama ga gajiyar biki ga rashin bacci su suka had'e min waje guda sai ajiyan zuciya nake a cikin baccin alamun na ci kuka na koshi. Zafar kuwa tunda taro ya tashi duk hankalin sa yana kai na burin shi d'aya ne shine mu keben ce ya ci mutunci na sai zuba sauri yake mu shiga mota wani abokin shi da yazo bikin tun daga turkey ya tsaida shi yana mishi jawabin gobe jirgin karfe shida zasu bi su koma so ba lalle ne su had'u ba dan sun san a wannan lokaci yana can rungume da amarya ana shan soyayya, nan suka shiga yi mishi tsiya irin ta abokanen ango ya biye su ba dan yana so ba sai dan kawai kada su zargi wani abu yasa ya d'an b'ata lokaci har muka wuce bai sani ba. Ya sha takaici kaman ba gobe da ya neme ni ya rasa, a bakin sauran mutane da basu gama wucewa yaji cewa mun wuce da 'yan uwana, minti biyu bai kara ba yace shima ya kamata ya tafi yayiwa wayan da zasu bi flight d'in safe Allah ya kiyaye hanya ya juya ko kula masu tsokanan shi wai zai gudu gida wajan amaryan shi,ko waiwayowa bai yi ba balle ya tanka shi dai burin shi ya same ni a wannan gida da babu kowa ya rama abinda nayi mishi. Da kyar ya yarda Sadiq da wani abokin su mai suna Shu'aib suka mishi rakiya, a cikin motan ma bai tsira ba Shu'aib sai takalan sa yake Sadeeq na musu dariya. A suya spot dake baga road Sadeeq ya tsaya ya saya musu manyan kaji 2 da drinks suka kama hanya, shi dai Zafar sai tab'e baki yake yana mamakin Sadeeq daya dage har da sayan kajin Amarci ko uban wa yace mishi wani abu zai shiga tsakin mu oho. A bakin gate ya sauka yace musu ya gode ba sai sun bishi ciki ba "Dama ni na san ksud'in banza ake mana gashi dai idon mu ya gane mana" cewar Sadeeq kenan yana bud'e murya dan Zafar da ya kusa shiga ciki yaji hannun sa d'auke da ledodin da sukayi shopping d'in. Mai gadi na zaune har ya fara gyanyadi yaji tura karamin kofa na jikin gate d'in, cikin sauri ya mike yana yi mishi barka da zuwa. Tsayawa yayi suka gaisa cikin mutunci sannan ya wuce ciki shi kuma ya kulle gate d'in tare da shigewa makwancin sa, murya can ciki yayi sallama ya shigo parlour ba shiri ya lumshe ido yana shakan daddadan kamshin turaren wuta da Aunty ta saka kamin ta tafi, ya kai good 5 seconds yana shakan kamshin sannan ya bud'e ido yana bin ko ina da kallo yanda aka jera komai cikin tsari gwanin burgewa. Tab'e baki yayi ya kama tafiya ciki yana da shi Abba ya bawa kud'in nan yaki ya bada order furnitures masu tsadan nan dan da farko shi aka ce ya zab'a min da gangan ya zab'i wasu bakake wai tunda painting gidan masu haske ne wayan nan sune zasu haska. Abba bai kara kula shi ba ya zab'o wayan nan da aka jera a parlorn, Kai tsaye inda ya san nan ne b'angare na ya nufa ya bud'e kofa kamshi days tarar a nan yafi na farkon, madaidaicin parlour nawa yabi da ido yanda komai aka shirya shi cikin kwarewa da wayewa babu tarkace dayawa amma komai ka gani a ciki classic nd expensive ne. Sosai parlour ya tafi da imanin shi yana tunanin yaushe Abba ya sayo wayan nan dan shi dai a gaban shi akayi ordern komai, toh meye ma damuwar shi da zai damu kqn shi sai ya san ta ina suka zo kayan. Cikin sauri ya karasa kofar bedroom da nake ciki ya murd'a handle d'in yaji ta a garkame gam kara murd'awa yayi yana jijjiga kofar wai ko zan zo in bud'e ni kuwa Ina can ina ta sharar bacci na ban san ma yana yi ba. Tsaki yayi tayi yana cizon yatsa da takaicin kulle kofa da nayi,nan da nan wani tunani ya fad'o mishi ai ba za'a rasa spare keys na ko wani kofa ba, cikin sauri ya juya da nufin zuwa d'akin shi ya duba har yayi steps 2 zuwa 3 ya tsaya cak sakamakon wani abu daya fad'o mishi a rai. Kar dai ace na rufe d'aki nane saboda ina tunain zai shigo min as ango?? Hmmm inko haka ne ba zai bud'e ba balle in saka ran cewa wani abu ya kawo shi, God forbid ba zai tab'a abinda wannan kucakar zata raina shi ba, dangwaran da ledan hannun shi yayi a bakin kofan ya juya ya nufi nashi d'akin . Tun a parlour shi ya fara kunce necktie dake wuyan shi da maballan suit din shi a haka ya karasa cikin bedroom ya gama cire kayan ya shiga bathroom, wanka yayi da expensive liquid soaps da kamshin su ya cika gidan gaba d'aya bai dad'e ba ya fito sama-sama ya shafa d'an 🧴 a jikin shi ya saka white pyjamas d'in shi masu taushin gaske ya bi lafiyar gado. Tsaki yaja shi kad'ai yana kara Jan bargo ya lullub'e jikin shi da kyau yana mai jin haushin kan shi na kawo irin wannan tunanin a ran shi,wai da auren gaske yayi da yana can tare da amaryan shi " Allah ya sauwake 'yar Mallam ce fa Kuma ka aure ta ne dan gujewa Abba ko ba haka ba?" Ya tambayi kan shi yana lumshe ido saboda ya fara jin bacci " Anya zan iya bari tayi min wata 2 a gida? she have to leave within a month kamin nan na samu d love of my life". Tun yana suratai wa kan shi har bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi. Hankali kwance na sha bacci na ban tashi ba har sai da naji ana kiraye-kirayen sallah duk da naji na kwanta shiru ina jiran inji Inna ta leko ta tashe ni amma shiru, ganin kila zamu makara yasa na tashi a raina ina mamakin lafiya kuwa yau Inna bata tashi ba. Da Addu'an tashi daga bacci na tashi zaune ina murza ido, a firgice na mike tsaye ganin Ashe ba a d'aki na da na sani na kwana ba domin Ina kallon komai tar dan ban kashe wutan d'akin ba na kwanta haka saboda tsoro. A hankali na fara bin d'akin da akace nawa ne da kallo tare da mamakin irin dukiyar da aka narkar a ciki, ba komai ya saka ni mamaki ba sai dan jiya naji suna ambatar cewa Inna ce tayi min kayan d'aki. Kara kallon wannan Royal set maroon da sirkin baki nayi sai sheki suke kaman an shafa musu mai ko kuma ince kaman da glass akayi su yanda suke walwali da d'aukan ido, ko turaren wuta,humra,kulacham da sauran su da aka jera min a cikin tangamemen show glass abin kallo ne dan kwalaben kad'ai sunyi jarin wani. Jiki a mace naja kafafu na cikin bathroom nan d'in ma tsayawa nayi ina kare mishi kallo yanda komai na ciki fari ne kal kuma duk na zamani da kyar na gane wasu abubuwan na had'a ruwan zafi nayi wanka dan jiya tsoro ya hana ni yi, alwala ta na d'auro bayan na gama wankan na fito. Aunty Fatima duk ta nuna min yanda suka ajiye min kaya na duk da ba'a kawo min lefen ba na gidan mu ne da Inna tayi min, wata atamfa doguwar riga na saka wanda ya sha dinki mai kyau kuma cif na cika shi, abin sallah na shimfid'a na saka hijabi na kabbara sallah. Ban tashi a kan abin sallah ba sai kusan 6:40 domin sai da nayi azkar na safe na d'an yi karatun Qur'an sannan na mike na cire hijab na ninke su da sallaya na ajiye gefe, shafa shaffafen tommy na da yake kaman babu hanji nayi jin yana kukan yunwa dan ni kaina na manta yaushe rabo na da abinci, da fa auren gaske nayi ko kuma da Yaya na na aura I know he will pampered me yana rarrashi yana bani a baki ba zai tab'a bari in kwanta da yunwa ba, but dubi wannan mugun ko irin Kazan amarci da naji ana bada labari bai kawo ba. A take Kuma wani sashin zuciya ta ya kwab'e ni da cewa ta ina zan sammaci wani kazan amarci daga gare shi bayan ya jadda min dalilin aure na da yayi kuma baya gajiya da nanata min ba so na yake ba. "Hmmm" kawai nace a raina tare da niyyan neman abinda zan ci, kaman mai tsoron kada wani abu ya kamata na bud'e kofa na leka naga wata fitinanniyar parlour na da ya kusan saka numfashi na barin jikina. "Masha Allah " nake ta maimaitawa da jinjinawa Inna, yanda parlour nan ya tsaru koma wanene kai dole ne ya burge ka ba'a cika mashi tarkace dayawa ba but yanda aka jera komai a position din shi sai ya fito da kyan parlorn cushions labulaye duk kalan su daya wato peach nd milk color ne sai tangamemen plasma da sauran abubuwan kallo suma wajan su d'aya, abinda da yafi birge ni wasu manyan flower vase da aka ajiye a kowani angle shima ya bada ma'ana. Tafiya na farayi zuciya ta na dukan 3-3 dan ina tsoron had'uwa da wannan dodon, ina bud'e kofa wani parlour na kara gani har yafi nawa komai I mean girma da dukiya da aka zuba a ciki baya lissafuwa shi kuma nan komai na cikin sa brown nd white ne. Nan ma da naga kallon ba zai fishe ni ba na fara duba kofofi da na gani a cikin parlour dan neman kitchen na san anyi min gara ba na wasa ba so ko indomie ne in samu in dafa in sakawa cikin nan nawa da nake ji sai kara ya mutsewa yake. Babu tunanin komai kai tsaye na nufi wata kofa da hankali na ya kwanta dashi na bud'e, wani sanyi da wannan sassayan kamshin sa suka min maraba da sauri na waro ido ganin inda na kawo kaina, a can tsakiyan tanfatsetsen gadon shi na hango shi kwance yana baccin sa cikin kwanciyar hankali dan bai san ma na shigo ba a hankali na mayar da kofan na rufe kaman yanda na samu na juya cikin sauri na koma inda na fito domin har naji na daina jin yunwan. In ba dan Allah ya taimake ni yana bacci ba wani bayani zanyi mishi na kare kaina, da shikenan sai yace biyo shi nayi. Ido na rufe sai sauri nake buri na in shige d'aki na naji nayi tuntube da abu a gefen kofata, tsayawa nayi Ina kallo tambarin jikin ledan ba sai an fad'a min ba na gane kajin amarcin ya kawo min amma banida darajan da za'a miko min hannu da hannu shine ya dangwarar min ita anan? A zuciye nayi ciki tare da banko kofa Ina huci ni kad'ai lalle ya cika d'an rainin hankali, nima ban d'auka kaman yanda ya ajiye abin shi haka zai dawo ya d'auka sai dai yunwar ta kashe ni. Na kusan minti 30 zaune sai tsaki nake ta jerawa saboda takaicin da ciki na ke bani na kasa hakurin yunwan ni kuwa nace sai dai in mutu ban cin kazar da aka dangwar min. Jiki na rawa ya fara na kai last stage da ba zan iya jurewa ba kuma,tashi na kara yi ina tafiya da kyar tare da addu'an Allah yasa bai fito ya d'auke ba dan na lura in na zauna yunwar ta kashe ni ba matsalar shi bace Inna ta akayiwa asara. Ina bud'ewa kuwa naga tana nan ajiye kaman yanda na barta, wawurar ta nayi na koma ciki da sauri bayan na maida kofa na rufe, ban iya karasawa cikin bedroom din ba a nan parlorn na zauna jiki na rawa na dauki goran yogurt na kafa kai ban sauke ba sai da na shanye tas sannan na ajiye roban Ina ajiyan zuciya. Kullin kajin na warware shima na fara ci hannu baka hannu kwarya, ban sarara ba sai da naji nayi kat sannan na ture su gefe na jingina da jikin kujera sai sakin ajiyan zuciya nake amma kuma can kasan zuciya ta kuma haushin kaina nake ji da na kasa hakuri na ci wannan kayan shikenan ya samu hanyan cewa ni kwad'ayayyiya ce na san kad'an daga cikin halin sa kenan. Tashi nayi na tattara su na kai su cikin frdge da na gani cikin parlour na saka duk wai dan Kar ya shigo ya gani na ci, hmmm in banda abu na a Ina ma zai ganni ai duk hanyan da zan kaucewa had'uwa ta da shi zanyi har lokaci da ya d'iba yayi ya sallame ni in kama gaba na. Da wannan kwarin guiwan na shiga bathroom na wanko hannyaye na yafa veil karami a kaina na fito parlour na zauna akan sofa tare da cigaba da nazarin rayuwata tun daga kuruciya zuwa yau. Tun yanzu na kogu lokacin da ya d'iba yayi ya sallame ni makaranta zan shiga abuna inyi karatu mai zurfi in cika buri na, na zamewa Inna farinciki kuma abin alfahari. Ban san lokaci ya tafi sosai ba nayi zurfi cikin tunani naji muryan mace na sallama. Firgigit na dawo hayyaci na tare da tashi zaune na amsa sallaman tare da aro 'yar fara'a na yafawa fuska ta Ina kallon kyakkyawan yarinya da ba zata wuce age mate na ba hannun ta rike da wani hadadden basket mai dan girma da warmers masu kyau a ciki, nuni nayi mata da wajan zama nace ta zauna. Ba musu ta zauna ta fara gaishe ni jin abun nayi bambara kwai wai ni za'a gaisar, amsawa nayi Ina tambayan ta mutanen gida tace min suna lafiya. Miko min basket din hannun ta tayi tare da cewa " suna na Yasmin ni cousin sister ce ga Ya Zafar, mama na da Abban shi 'yan d'aki d'aya ne yanzu ma ita tace in kawo muku wannan breakfast din sannan akwai sakon da tace a bashi". D'an murmushi nayi nace " Allah sarki yayi kyau". D'aukan basket nayi na kai kan dinning table na jajjera warmers din na dawo na zauna kusa da ita da ko motsawa bata yi ba a inda na bar ta ba, I'm feeling nervous dan ban san wani irin hira zamuyi ba. "Pls kiyi mishi magana zan tafi dan ance kada in dad'e" naji muryan ta ya katse ni. "Toh" kawai na iya ce mata na mike Ina d'aga kafa da kyar zuciya ta kuwa kaman ya fasa kirjina ya fito, me zan ce mishi tayaya ma zan iya shiga d'akin wannan masifaffen?. Na fi minti biyar tsaye a bakin kofan amma na rasa tayaya zanyi sallama ko kwankwasawa ba mamaki ma in ya ganni kofan d'akin shi yayi min wata fassarar, ganin babu sarki sai Allah yasa na daure na kwankwasa kofan amma a hankali kaman mai tsoron kada a jita. Nayi knocking kusan sau 3 amma banji alamun motsin mutum ba, hakan yasa na bud'e a hankali na leka naga babu kowa sai sanyin ac daya had'u da kamshin sa ya bada wani yanayi mai ni'imar gaske, lumshe ido na nayi Ina kara bud'e kofofin hanci na Ina shakan kamshin naji bud'e kofa wanda ya haddasa min bud'e ido ba shiri. Shine ya fito daga bathoom d'in shi daure da towel alamun daga wanka yake ya rike waya da hannu daya d'ayan kuma rike da karamin towel yana goge kirjin shi da ya wadatu da yalwataccen gashi mai taushi da d'aukan ido. Zafar da sai yanzu ya lura da mutum a d'akin shi ya bini da kallon mamaki yana watsa min harara , ganin nayi nisa hankali na baya tare da shi ,tsawa ya daka min yana tambaya ta uban me na shigo yi a d'akin shi? . A zabure na d'auke ido na akan shi tare da sauke kaina kasa ina mai jin haushin Kai na, how comes har nayi haka na tambayi kaina, shikenan ya gama raina ni na gama zubar da aji na a gaban shi dama ba wani girma na yake gani ba. Ban iya yi mishi magana ba Kuma na kasa juyawa in koma inda na fito, kaman daga sama naji hannun shi mai d'an danshi ruwa akan hannu na, cikin kid'ima na d'aga kai na ina kallon shi da idanuwa na da suka fiffito kaman zasu fad'o kasa. Murmushin gefen baki ya min yana kashe min ido daya yace " irin wannan kallon haka 'yar Mallam kaman zaki cinye ni , wato kin ga well builded body ko baki san cewa kwalele kike kallo ba" "But let me help you ki d'an rage zafi na San abinda ya shigo dake kenan" yana gama fad'an haka naji ya d'aura hannu na kan lallausan gashin kirjin shi yana bina da naughty look harda karkata kai gefe d'aya. Yanda kika san an d'aura min hannu kan wayan wuta tsirara haka naji wani irin shocking tun daga tsakiyar kai na zuwa tafin kafa ta, ba shiri na janye hannu na da karfin gaske jiki na rawa na fice a d'akin da gudu Ina jin dariyan mugunta da yake min. [6/16, 9:18 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *32&33* Zama nayi a inda na tashi ina daidaita natsuwata tare da kakolo murmushi dole na yabawa fuskata amma kuma sai na gaza furta mata komai,toh mema zance mata dan haka shiru nayi na cigaba da wasa 'yan yatsun hannuna. " Yana zuwa ne?naji muryar ta ya katse mana zaman kurame da muke duk da ita naga alamun irin mai surutu ce sai dai rashin samun fuskata yasa tayi shiru itama". "Eh......yana....yana shiryawa ne?na amsa mata a rarrabe. Shi kuma ina barin d'akin shi sai da yaci dariya ya more sannan ya juya ya cigaba da shirin shi yana aiyana yanda zaiyi magani na inji tsoron shi sosai dan jiya a wajan dinner nan yaga rashin tsoro a idona. Munfi minti 20 a zaune da yasmeen shiru sai dai itace mai kokarin kawo hira wanda ni amsa ta baya wuce ehh ko a'a. Cikin wata maroon danyan shadda ya fito hatta da hular kan shi maroon ce kayan san matukar fito da shi ya haska farar fatan sa yana gyara agogo hannun sa ya fito bai ko kalli inda muke ba yayi hanyan fita koda yake na lura bai san muna parlour ba, yasmeen ce tayi saurin dakatar da shi ta hanyan gaishe shi. Fara'a kwance saman fuskan shi ya dawo baya tare da amsawa a yana tambayan ta ya Baawa take?. "Tana lafiya ita ta aiko ni in kawo muku breakfast kuma tace in fad'a maka tana son ganin ka a gidan mu yau d'in nan kuma da wuri". "Allah sarki Ba'awa muna godiya baby ki tayani godiya mana" yace yana min wani kallo da yasa naji zuciya ta harba da karfin gaske cikin in ina na amsa da "ai tun dazu nayi sai dai in kara". "Toh ni zan tafi sai ka shigo,amaryan yayan mu na tafi sai na juyo" tace tana mikewa da fuskar ta cike da fara'a ,mik'ewa nima nayi Ina amsa mata na biyo su da niyyan d'an taka mata nace " toh sai na ganta ta gaida mutanen gida,muna cikin magana da ita naji kaman daga sama anyi kissing d'in goshina,ba shiri na tsaya cak na kasa d'aga kafa balle inci faba da tafiyan saboda wani irin kasala daya sauko min lokaci d'aya na juya ina kallon shi cikin tsananin mamaki. "Babyna sai na dawo ki kulan mun da kan ki kinji?"yana magana ne yana satan kallon yasmeen ta gefen ido yaga ta d'auke kai tana murmushi kasa-kasa,shima murmushin yayi, yayi gaba abin shi ko ba komai ya cire mata tantama daya gani d'azu shimfid'e a fuskar ta ko dan yanayin da da taga yazo fita bai nema ni bane oho. Har suka fita ina nan tsaye kaman an dasa ni,da kyar na koma kan kujera na zauna ina kara mamakin halaiyan wannan mutumin mai halin hawainiya yana iya canzawa a duk lokacin da yayi niyya. Misalin eleven kawaye na da sauran 'yan uwa suka fara zuwa nan da nan gidan ya cika da hayaniya 'yan mata baka jin na wani,nima ganin su yasa na wassake tare da rage damuwa mukayi ta hiran mu. A can gidan mu kuwa da gaske Gwaggo Aisha ta kwana a asibiti amma da sauki ta tashi sai dai jin labarin irin gidan da aka kai ni da kuma labarin lefe na da Hajara ta kai mata ya kara birkita yanayin ta mata da suka zo da washe gari saboda yini yawancin sunje duba jikin nata dan babu wanda yasan takamaiman dalilin ciwon nata. A gidan mu aka kawo mana abincin rana da akayi na yini kuma aka kai gidan su Zafar kaman yanda al'adar Maiduguri yake,daga baya kuma su aunties na da sauran jama'a sukayi ta zuwa ganin gida suna saka albarka,sai yamma likis suka fara watsewa. Bayan magariba gidan yayi tsit duk sun watse sai na jiki da suka tsaya dan kimtsa gidan, bayan sun gama da gidan nima shirya ni sukayi cikin wani haddaden less pink mai adon stones sannan suma sukayi haraman tafiya,sabon babu kuka na bud'e inayi musu magiya ko mutum d'aya ne ya tsaya tare da ni mu kwana. Dabara suka min suka tafi suka bar ni kaman wata mayya,tsoro duk ya cika ni na rasa me yake min dad'i komawa d'aki nayi na murza key kaman jiya nayi kwanciya ta nayi shiru ina jin matsaneciyar kewar Inna ta ji nake kaman na kai shekara ban saka ta a idona ba,wani b'angare na zuciya ta yana raya min in tashi in gudu in bar gidan in koma gidan mu. Wasi- wasin da yayin yawa yasa na d'auko wayata da su Maryam suka zo min da shi na fara kallon pics da videos na biki da suka turo min, ai kuwa duk sai ya d'auke min hankali na shagala nayi ina ta kallo ina murmushi wani wajan inyi dariya saboda babu wanda zai kalle mu ba zaice masoyan gaske bane,tun ina kallo har bacci yayi gaba da ni ban sani ba. Zafar bai dawo gidan ba sai past eleven saboda wai baya son ya shigo da wuri mu had'u dan ya lura da cewa kai na yana hayaki so gwara ya rabu da ni in lokacin da ya d'iba yayi mu rabu. Kwana na 3 a wannan gida ban kara saka shi a ido ba in fact bana jin motsin mutum ma ni kad'ai nake rayuwa ta, tun ina d'ari-da'ri har na saki jikina ina sha'ani na,bana fitowa babban parlour a cikin b'angare na nake rayuwa ta bana fita ko Ina babu ruwa na da ya gidan yake yana bukatan shara ko goge-goge. Yau da rana ina kwance a parlour na ina kallo naji ina kwad'ayin cin wani abu daffafe dan tunda aka yi yini rabon da inci abinci sai snacks da aka yi min nake ci in hada tea in sha ko in kora da juice. Tight legins ne a jikina da rigan shi har iya guiwa amma bashi da hannu,rigan yellow ne da adon baki a jikin sai wandon shima baki ne ribbon yellow nayi amfani dashi na tufke gashina da ya zubo min har baya. Ina sauraron favorite track a waya na , yanzu da nayi shirin shiga kitchen sai na saka earpiece a kunne na na fito abina ina mai bin wakan ina d'an rausayawa . A wannan lokaci Zafar na zaune a parlour Abba ya bashi wani aiki yana taya shi yi a cewar sa ya fara da kad'an kad'an a gidan kamin ya fara fita office completely. Ni kuma ban san da wani a cikin parlour ba na fito abina ina rausayawa nayi hanyan kitchen,da ido ya bini har na kulle zuciyar shi na ingiza shi cewar lalle wuyana ya isa yanka in shigo in same shi a zaune amma ko arzikin kallo bai samu ba balle in gaishe shi,ya lura kyale nin nan da yayi ya kara fand'arar dani dubi parlourn nan kaman ba mutum a cikin gidan. A fusace ya mike yabi bayana zuwa cikin kitchen d'in ya same ni ina wanke set d'in tukane dana fito dasu zanyi amfani dasu. "Keh" yace a d'an tsawa ce amma da yake earpiece ne a kunne na ban ji komai ba saima kara bin wakan nake ina rausayawa shi kuma ya zata duk salon raini ne wannan yasa bai tsaya tunanin komai ya shigo a fusace ya janyo ni ta baya. Ni kuma da ban san da mutum a gidan ba balle in san da shigowar shi yasa na firgita sosai na rufe ido na na fara ihu iya karfina ina jero duk addu'a da yazo bakina "keep ur mouth shout my friend"naji muryan shi yana daka min tsawa da karfin gaske da yake earpiece din ya fita a kunne tar naji muryan nashi,a take na waro ido na waje ina kallon shi da fuska ta duk hawaye. "Stop staring at me,da idon ki kaman na mayya.wato ke wuyan ki yayi kwarin har zaki taka ki wuce ni ba tare da kin gaishe ni ba"da sauri na girgiza kai na hawaye na zab'o min,sannan ya kara da cewa"and look at this house for god sake ace wai da mace a ciki ko'ina dirt ko kina jira inzo in share miki ne?"nan ma cikin sauri na girgiza kai na. Kasa nayi da kai na tare da dana sanin fitowa da nayi da ban fito ba da ban hadu da wannan mugun ba. "Baki iya gaisun ba ko?" Naji muryan shi cikin kunne na, murya ta na rawa na gai da shi ba tare da na dago Kai na ba. Maimakon ya amsa sai yace " haka ake gaida na gaba, ina tsaye kina tsaye common kneel down and greet my friend". Kuka na Kara fashewa da shi na takaici na durkusa nace " Ina kwana" still bai amsa min ba ya gyara tsayuwar shi da kyau yana wannan murmushin sa da na tsana dan duk lokacin da yayi shi babu alkhairi sai zallar mugunta. "Zan kindaya miki sharud'a wanda dole ne ki bisu kamin lokacin ki yayi in sallame ki, na farko ya zama miki dole ko wani wani safiya kizo ki gaida ni, na 2 kuma kada ki kuskura ki bar gidan nan da datti dole ne ki rinka sharewa kina mopping din ko ina nd last thing kina girki kuma duk abinda na lissafo su make sure kinyi su before 8 am in ko kika tsab'a ko daya daga cikin su hmmmm" yace yana taune leb'en shi na kasa. Ban iya bashi amsan komai ba kaina dai yana kasa har yanzu hawaye basu dai na zubo min, murmushi yake ran shi fari kal yana jin wani irin nishad'i ganin ina hawaye duk ya wanke mishi takaicin sa na daren dinner. "Tashi ki gyara gidan yanzu ki tabbatar kin share kinyi mopping na ko ina kuma in har kikayi su any how zaki Kara repeating ne so its left for u" yana gama fad'a yayi gaba yana dariya cikin ranshi tare da kisisima yanda zai ci uba na cikin ruwan sanyi. Tashi nayi daga tsugunen dana gaji da yin ta dan kasa tashi nayi daga farko ina tunanin ta ina zan fara, ganin dai babu mafita yasa na fito da vacuum cleaner da na gani a cikin kwalin sa na daidaita shi na fito dashi parlour dan in jona in fara sharan kaman yanda ya umarta. Tun kamin in karasa wajan socket din ya daga min tsawa daya firgita ni na tsaya sororo Ina kallon shi " samun waje kenan wato baki da hannu kenan ko a gidan ku da wannan kike shara ?" Ya fad'a yana nuna min vacuum din da hannu. Shiru nayi ban amsa ba kuma ban juya ba sai zuciya ta dake min zafi wai a gidan mu dashi nake amfani? "Ki maida shi ki d'auko tsintiya ki share dashi right now" kala ban ce mishi ba na juya zuwa kitchen din na ajiye shi na d'auko tsintiya na fito na fara sharan bana ko kallon inda yake. Ajiye pen din hannun shi yayi ya kwanta yana kallo na yana Kara jin nishad'i gani na cikin hawaye, da gangan ya kirkiro atishawa yayi kusan guda 3 sannan yace wai da gangan nake sharo mishi da kura har ya saka shi yin atishawa. "Kina sharewa a hankali in kika sa na kara yi zan nuna miki true colour na" kaman in kurma ihu nake ji saboda takaici wani kura ne a parlour nan da za'a ce har ya saka mutum atishawa kawai dai salon wulakancin sa ne wannan na sani. Ban kula shi na gama sharan ko Ina da mopping duk yana zaune ko motsawa baiyi ba, baya na duk ciwo yake min da yake ban saba aiki haka ba har zan wuce d'aki yace in dawo in d'aura girkin yanzu. Cikin gunguni na wuce kitchen ina shiga na fara ja mishi Allah ya isa " wannan ai zallinci ne haka kawai ya sani sharan da tunda aka haife ni ban tab'a yin irin shi ba tunda gidan mu dai kowa b'angare shi yake sharewa amma dan mugunta yasa inyi wannan uban aikin, dani yake wallahi sai na rama" duk ni kad'ai nake ta masifa ta ina fere dankalin turawa dana gani an zuba su a cikin store. Patatos omllet nayi na zubo mishi a plate na d'aura a kan tray na plastic mai dan Karan kyau na saka mishi spoon na fito dashi zuwa inda yake zaune kaman wani sarki na duka har kasa na ajiye mishi, wani abin takaici da wannan bawan Allah ya min yanda kika san kashi na ajiye mishi haka ya tsaya kallon abincin. A kyamace ya d'auki spoon din ya sakuro kaman mai tsakuran kashi ya kai bakin shi, dama ina kallon shi ta gefen ido saboda inga wani reaction zaiyi domin na san karyan mutum ya kushe girki na koda banyi catering school ba Inna ta ba baya bace wajan girki, alaman mamaki na gani karara akan fuskar shi lokacin da abincin ya shiga bakin shi amma tsaban iyayi furzar da abincin yayi yana yamutsa fuska yace " meye wannan, tambayan ki nake meye wannan is this what u called food , muguwa wato so kike inci in mutu Allah kad'ai ya san abinda kika zuba a cik tsaban muguntai, common kwashe kayan ki nd leave my sight" Duk a masifance yake min maganan , rai na kara baki yayi na rasa me zancen ko inyi mishi da zan huce nayi, kawai tattara kayana nayi na koma kitchen ban kula shi ba. "What a mess" ina cikin had'a nawa abincin naji ihun shi daya kara firgita ni kamin in san me yake faruwa na gan shi a fusace a bakin kofan yace; " lalle kin cika Yar rainin hankali ki gyara ko ina amma ki kasa gyara min d'aki?" Ya karasa yana zubo min ido tare da tare kofan kitchen din. "Baka ce min harda d'akin ka ba shiyasa ban shiga ba". "Oh sai na gaya miki sannan zaki gyara ko d'akin nawa ba acikin gidan yake ba?" Kamin in samu amsan bashi ya cigaba "wuce ki gyara min yanzu plus my bathroom" Rufe plate din nayi nazo zan wuce na zata zai bar min kofan in fita ne sai naga matsawa kad'an yayi yace in wuce,ban san lokacin da na daga kai na kalle shi ba naga ya wqni kankantar da Lulu eyes din shi yana kallo na. " Toh... Z...an ...wuce" nace mishi murya ta na rawa. Na hana ki wucewa ne?" Ya tambaya Yana kara gyara tsayuwar shi, girgiza kai na kawai nayi ina maida shi kasa, da hannu ya min alama da inzo in wuce. Tafiya na fara yi kaman wacce take tsoron taka kqsa ba dan komai ba sai dan sanin in zan wuce sai jikina ya gogi nashi, karkata jiki na nayi sosai yanda ba zai hadu da nashi ba, na ko yi sa'a dan ko bai hadun ba har na kusa fita naga ya saka hannuwan shi duka 2 ya tare kofan ya zama banida daman fita Kuma banida daman komawa ciki. "Ni kike guduwa da wani kazamin jikin ki, ni banyi kyaman zaki had'a jikina da naki ba sai kece zakiyi?" Jikin na karkarwa kawai yake tsaban tsoro ban tab'a samun kusanci da d'a namiji kaman haka ba sai yau so ban san ya zan kwatanta muku halin da na shiga ba a wannan likacin. Sai da yaga ya gama tsoratani sannan ya bani hanya, haba kaman in kifa haka na fara sauri na shiga d'akin na maida kofa na rufe na jingina a jikin kofan ina maida numfashi, sai da na dawo hayyaci na sannan na tsaya kallon d'akin ko ina fes yake a gyara kaman d'akin mace sai kamshi ke tashi, ajiyar zuciya nayi na wuce bathroom din shima dai fes yake. Haka dai na had'a ruwan omo da hypo na goge ko ina na bayin nan ya kara kyalli da walwali, sai da na tabbatar komai yayi na bude kofa na fito. A razane na koma baya ganin shi tsaye a bakin kofan daga shi sai dogon wando ya cire rigan jikin shi, rab'awa nayi na wuce shi Kuma ya shigah har zai rufe kofa naji shi yana cewa in tabbatar na gama gyaran d'akin ya fito. Da toh na amsa mishi yana shiga na fara gyara mishi gado da jera pillows sannan na fara mopping din d'akin inda babu carpet, har na gama zan fita wata zuciyar ta zuga ni da yanzu shikenan ba abinda zanyi in rama yaci bulus kenan?? Bakin kofan bathroom din na dawo hankali na zubar da ruwan omo kad'an yanda ba zai iya ganewa ba na fita da sauri ina addu'an Allah yasa ya taka wajan da na huta takaici da ya guma min yau. Jikin kofan na d'aura kunne na na tsaya jiran fitowan shi, aiko ban dad'e da tsayuwa ba naji karan fad'uwa muryan shi da karfi yace " ouch my back" haba da gudu na koma daki Ina dariyan mugunta raina fari kal. [6/16, 9:19 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *35&36* Zaune take kan sallaya da carbi a hannunta tana ja a hankali tare da kurawa waje d'aya ido,kallo d'aya zaka mata ka gane tana cikin damuwa kullum cikin wannan yanayi take tunda aka fitar dani daga gidan sai dai in damuwar yayi mata yawa,sai tayi nafila tana kai kukanta wajan mai kowa mai komai kan Allah ya bamu zaman lafiya mai d'aurewa. 'Yan biki duk sun watse tun ranan yini saboda an riga da an daina zaman bakwai sai dai gobe ne satin auran kuma a goben uwa take zuwa ganin d'akin 'yar ta amma ita tana ganin ba zata je ba hakan zai fi mata kwanciya hankali bata son taje ta ganni cikin wani yanayi ko kuma cikin tashin hankali hakan zai tsaya mata a rai ya hana ta sukuni, ta yanke shawaran zamanta a gida ta bini da addu'oi samun zaman lafiya. Tana cikin zancen zuci baba yayi sallama ya shigo,sallamar nashi ne ya katse ta ta juyo tana kallon shi tare da amsawa a hankali tana bin shi da kallo yanda ya sauya zaka ce wani hamshakin mai kud'i ne,duk mamaki ya cika ta dan zata iya cewa tunda bikin nan yazo sai yau ta saka shi a ido saboda taga bashi da niyyan yin komai ya zauna akan abinda Abban Zafar yace na cewa kada suyi min komai su zasu yin min. A lokacin ta nemi su zauna suyi magana ta fahimta bai kamata su sake musu komai ba kaman wacce bata da gata koda kayan d'aki daya ne ya kamata suyi min gudun gori watarana amma yaki sauraronta sam,wai tunda sunce abari a bari kawai itama tunda ta lura da takun shi ta fita harkan shi tayi duk abinda Allah ya hore mata dana 'yan uwa da abokan arziki cikin ikon Allah kuma asiri ya rufu. Zama yayi a kan kujera ya d'auki remote ya kara volume na TV data rage,kaman ta share shi sai kuma taga koma yaya ne shine gaba da ita,tashi tayi ta kowa mishi ruwan sanyi da snacks na biki ta ajiye a gaban shi ta gaida shi tana zama a gefen shi. Amsawa yayi sannan ya d'an sha ruwan da ta kawo mishi yana kare mata kallo yana murmushi yace"kinga yanda kika dawo kaman kece Amaryar gaya min menene sirrin?" murmushi kad'an tayi bata ce komai ba wai yau ita yake fad'awa haka ya manta duk munanan kalamai da yake furta mata da kuma aurar dani ga wanda ba son sa nake ba.......... "Tunanin 'yar albarka kike ne ,nima nan kullum sai nayi tunanin ta a raina toh ya za'ayi dole ne kiyi hakuri kuma kiyi murna tunda tana gidan hutu" yace yana gyara zama "Yauwa ni abinda ya kawo ni daban, kin gan ni nan wallahi bikin nan ya cinye min duka kud'ad'en hannu na shine nace bari inzo ki bani wani abu na san 'yar ki na aiko miki tunda maganan da nayi ta jaddada mata kenan daren da za'a Kai ta gidan ta cewa kada ta kuskura ta zauna shiru duk dabarun da zatayi tayi ta rinka turo mana gida mu rinka shan maikon tare, in ma bata turo ba na san tana kan tarawa ne kema na san ki adana balle kuma kin samu makudan kud'i a bikin nan d'an gutsoro min rabo kamin 'yar albarka ta aiko mana" ya karasa yana washe baki. Takaici ne ya kawowa Inna har wuya ya hana ta magana tir da mai irin halin sa irin nasihar da yayiwa 'yarsa da zata shiga gidan miji kenan, wai har sai yaushe zai canza sai yaushe ne zai gane gaskiya? " Abin haushi ma kin ga banida number sirkin nawa ai da kai tsaye zan Kira shi muyi magana ta fah....." Cikin sauri Inna ta katse shi tana " haba Mallam yin hakan ba girman mu bane zai iya raina mu ka bari tunda dai ka fad'awa ita Zareefan zata aiko su ne da zaran ta samu" "Ji wani zance wai ba girman mu bane, yo wani girma talaka yake da ita in banda abinki menene a ciki dan Mai kud'i ya raina talaka." " Babu komai ba komai bane Amma ka bari in an kwana 2 da kaina zan karb'o maka numbern nashi a wajan ta kaga daga nan zaka iya magana dashi kai tsaye a duk lokacin da kake so" tana gama dad'in haka ta mike zuwa cikin bedroom dinta ta d'auko mishi bunch na dubu daya wato dubu dari kenan ta kawo mishi. "Ka rike wannan zuwa wani lokacin ko?" " Ai shiyasa nake son ki ke d'in ta daban ce" yace yana ta washe baki ya mike ya fice daga parlour ba tare da ya jira amsar ta ba. Dabas Inna ta koma ta zauna tana nazari inko hakane tana da aiki babba a gaban ta ba zata tab'a bari ya zubar min da kima a gidan miji ba dole ta mike tsaye akan shi sannan ta dage da addu'a Allah ya shirye shi ya gane gaskiya. *********************** Tundaga wannan rana ban kara ganin kowa a gidan da sunan ziyara ba daga ni sai shi, duk aikin da yace inyi kullum da sassafe nake yi kamin ya fito na tsabtace ko ina na saka turaren wuta abincin sa kuwa bana fashi ina ajiye mishi a kan table in koma d'aki in kulle kaina duk da akwai lokacin da ya same ni yace in daina ajiye mishi wannan jagwalgwalo na dan yafi karfin ci kullum masu aiki yake bawa, ban kula shi ba na cigaba da ajiyewa dan jiki na ya bani shi yake cinyewa ya fake da masu aiki, d'akin shi ne dai ban kara gigin lekawa ba balle ince zan share. Duk wannan kokarin da nake bai hanawa in 'yan rashin mutuncin nashi suka motsa ya sauke su a kaina, ina dai daurewa bana nuna mishi rauni na sai na koma daki nake cin kuka na in more duk rayuwar gidan ya ishe ni. Yau tunda na farka nake ta murna saboda a yau za'ayi yinin bakwai kuma a gidan nan za'a yi shi kaman yanda al'ada yake, babban farinciki na harda Inna za'a zo shima iyayen shi zasu zo a hadu gaba daya asan juna a kara karfafa zumunci. Irin gyaran da nayiwa gidan yau na musamman ne tun 7:30 na shirya cikin wata hadaddiyar shadda ta blue dinkin doguwar riga yasha zubi har kasa, duk da ban iya wani d'aurin kirki ba na kokarta nayi yanda zan iya kuma cikin ikon Allah yayi kyau sosai sai na kara zama Amarya sak, duk d'auki ya hana ni sukuni sai kallon time nake ina jin lokaci baya tafiya, ina zaune ina ta kallon agogo naji an murd'a handle din kofan parlour cike da murna da d'auki na mike na tafi da gudu dan in rungume duk wacce ta fara zuwa, da gudu na kwasa nayi kofan sai dai kamin in karasa naja wani wawan briki na tsaya a tsoroce tare da mayar da kai na kasa. Shiru banji yayi min magana ba Kuma banji alamun ya tafi ba, ina ta ayyanawa a rai na kila ya tafi ne in ba tafiya yayi ba me zai tsayar dashi anan? Hakan da na saka a raina yasa na dago da kaina karaf ido na a cikin nashi yana min wani kallo da ni dai ban san fassaran shi ba, mayar da kai nayi na shiga gulman shi a zuciya ta mutum sai shegen fadin ran tsiya da iyayi.... "Meye na gaya miki last time akan gidan nan?" Muryan shi ya katse min gulman shi da nake. "Kace in rika share gidan nan kullum...." "And then?" Ya katse ni tun kamin in karasa. "Ina yi kuma harda girki" daki na fa?" Ya kara katse ni. Harga Allah bai zata da gangan na zubar da ruwa ya fad'i ba a wancan ranan Kuma yaji dad'in gyaran da nayi mishi shiyasa ya biyo ni, ni kuma a tunani na ya sani shiyasa naki shiga d'akin kada ya kama ni na San halin shi na cin zali. "Kayi hakuri zan rinka gyarawa " na bashi amsa cikin sanyin murya. "Better " yace tare da juyawa ya fita nabi shi da ido har ya b'ace min dan yayi min masifan kyau cikin riga armless da wando 3 quater duka farare ne tass anr rubuta Gucci da manyan harufa da bakin fenti a gaban rigan mutum yana ganin well builded body shi a zahiri ga gashi kwance luf a fatan jikin shi kaman wani balarabe. Kofan na rufe na dawo na zauna jiki na duk a mace me yasa kwanan man nake jin wannan yanayin in muna zaune waje daya kuma duk abinda yake yanzu birge ni yake ba kaman da danake jin haushin shi ba. 9:00 am dot Yasmeen da kannen ta 2 suka zo cikin farinciki na taro su bamu zauna a babban parlour ba naja zuwa nawa muka zauna naja karamin kanin ta da ba zai wuce 7 years ba ina tambayan shi ya sunan shi? Dan Allah ya daura min son k'ananan yara ko dan babu a d'akin mu ne oho. "Muhsin " ya amsa min da karamin muryan shi mai dad'i, murmushi nayi nace " sunan ka mai dad'i". "Aunty Amarya kin gan mu da sassafe ko, wlh muhsin ne ya takura mana tunda ya farka daga bacci yana ta kuka shi lalle sai an kawo shi nan shine fa da ya ishi Momy da fitina tace muzo kamin ta karaso" Yasmeen ta katse ni da murmushi a fuskar ta.. "Ni ai Muhsin ya burge ni ina zaune ni kad'ai kaman mayya gashi na samu abokanen hira, kema kince zaki dawo ban Kara ganin kafar ki ba tun ranan da kika fice daga gidan nan" na bata amsa ina dan dariya. "Cab ai Momy ce ta hani ni zuwa wai zan zo in takura ku" ta karasa itama tana dariyan. Kawar da wannan maganan nayi na kawo wata hirar daban nake tambayar ta ya matakin karatun ta yake, ta amsa min da zata rubuta jamb tayi joining next year, naga ashe matakin mu daya da ita a karatu. ***************** Tun goma da rabi na safe gidan mu ya fara tara mutane amma na jiki sun zo ne dan raka Inna taga gida na, su Aunty's dina sune farko-farkon zuwa amma Inna tace musu babu inda zata je bata shirya zuwa a yau ba sai wani lokacin. Ba yanda ba suyi da ita ba tace su suje kawai ta riga ta shirya duk kayayyakin da zasu kai min kaman su kayen lefe na da sauran kayan da ba'a samu kaiwa a ranan bikin ba, Aunty Batul cewa tayi shikenan tayi zaman ta tunda hankalin ta yaki kwanciya da zuwan nata. Ita kuma Aunty Fatima bata yiwa kowa magana cikin su ba ta fita a gidan zuwa gidan Yar uwar su wato Maa ta same ta zaune cikin shirin tafiya su kawai take jira, tana ganin Aunty Fatima ta mike tana nad'a latfayan ta tace " aini tun d'azu ku nake jira sai yanzu Bintun ta gama ne?" "Bintu fa cewa tayi babu inda zata je wai sai dai mu muje..." Ban gane babu inda zata je ba, zuwan uwa taga gidan 'yar ta ranan bakwai ai al'ada ce da ta kafu tuntuni balle tace akan ta za'a fara, maza wuce kice mata ta fito yanzu kuzo mu tafi".Maa ta katse ta a zafafe. Ba musu Aunty Fatima ta juya zuwa gidan mu dama zuwa tayi ta fad'awa Maa ta san ita kad'ai ce zata iya saka ta zuwa ko bata so. Masu rakiya duk sunyi jigum jin cewa uwar Amarya ba zata je ba Aunty Fatima ta shigo taja ta gefe tace mata maza ta shirya inji Maa su tafi, ba yanda ta iya haka ta shirya suka kama hanya a motoci kusan 3 da aka aiko musu daga gidan su Zafar. Ni kuwa hira sosai muka Sha da yasmeen Wanda yawanci labarin Yayan ta take bani kan yanda yake tsoron Abban shi Kuma hakan baya hana shi tsula tsiyar shi Mom tana rufa mishi asiri, sosai nake ta shan dariya harda rike ciki bamu tsagaita ba saida su Maryam suka zo sannan ta bar labarin nashi muka shiga wata daban. Sai bayan azahar su Inna suka iso baki na ya kasa rufuwa da gudu na fad'a jikin ta na kenkeme ta ina hawayen farinciki, ajiyar zuciya Inna take ta saukewa akai akai na kwanciyar hankali dan bata ga alamun tashin hankali a tare da ni ba. Sai a lokacin ta samu kwanciyar hankali ganin gida tana ta jero min addu'oi a zuciya na samun farinciki mai daurewa a gidan mijina, duk wani abu na tarban baki maman Yasmeen ta aiko mana har manyan kuloli na abinci dan haka bamu nemi komai ba aka shiga serving din baki mu dai muna can ciki muna ta hayaniyar mu. A daidai wannan lokacin Momyn Zafar da gayyar ta suka iso ,sai huhhura hanci suke suna kallon mutane a d'age su Inna basu kula su suka karbe su da hannu 2 har ana ce musu ga wajan Zama budan bakin wata daga cikin su tace; "Yau naga ikon Allah mu da gidan dan mu wasu bare ke kokarin nuna mana iko" ta karasa harda rike haba irin abin ya bata mamakin nan, Aunty Batul da bata da hakuri kaman gudawa ta yunkura zata basu amsa Inna da take kusa da ita tayi saurin rike hannun ta Maa da suke zaune opposite da ita ta girgiza mata kai alaman kada tayi magana. Haka ta koma ta zauna tana ta girgiza kafa bala'i na cinta, su Kuma sai da suka gama dariyar su na wulakanci sannan suka nemi waje suka zauna suna zama cikin ikon Allah ko sai ga Maman Yasmeen da wasu mata 3sunyi sallama sun shigo da fara'ar su a take fuskar Momyn Zafar da mutanen ta ya kuntata dan basuyi tsammanin zuwan ta a wannan lokacin ba sun so su gama tsula tsiyar su kamin ta iso ba dan wai suna tsoron ta ba sai dan sun san duk abinda da sukayi zaije kunnen Abba kuma bata manta warning din da yayi mata ba akan bikin ba. A mutunce suka gaggaisa dasu Maman Yasmeen har suna tambayan ina 'yar su take basu ganta ba , Aunty Fatima ce ta shiga ta fito dani bayan ta nada min laffaya ta kara bulbule ni da humra. A kunyace Kuma kaina a kasa na gaishe su suka amsa da kulawa banda su Momyn Zafar da suke amsawa kaman anyi musu dole ko masu ciwon baki, ina gama gaishe su ko minti 1 ban kara ba na koma ciki daman gaba daya a takure nake jina a wajan. Zuwan Baawa duk ya rusawa Momy badget kuma zaman su a inuwa daya babu riba dan haka suka mike da niyyan tafiya Baawan taso tsaida su amma suka ki tsayawa suka Kara wuta, suma ba wani jimawa sukayi ba suka ce zasu tafi aka rabu cikin mutunci. Karfe 3 su Inna suma sukayi haraman tafiya suka saka ni a gaba da nasihu sosai masu ratsa jiki sannan suka tafi suka bar ni ina ta kuka, su Maryam dasu Yasmeen suna ta bani baki suka taya ni gyara gidan sannan suma suka wuce suka bar ni. [6/16, 9:20 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *37&38* A hanyar su ta komawa gida sauran mata suna ta hira da santin gida na amma banda Inna da tayi jigum duk abin duniya ya ishe ta dama shiyasa bata son zuwa Maa ta tilasta mata dole tazo gashi ta ga abinda ya tayar mata da hankalin, alamu ya nuna cewa ni da Zafar babu matsala a zamanta kewar mu amma mahaifiyar shi itace babbar kalubele a cikin rayuwar aure na. Duk yanda miji ya Kai ga son matar shi in har dangin shi basa kaunar ta toh fa babu zaman lafiya balle ace mahaifiyar shi ce sukutum bata son ta ai babu kwanciyar hankali, ajiyan zuciya ta sauke mai nauyi har Maa da take kusa da ita ta dago suka had'a ido, alama tayi mata da ido cewa kada ta tada hankalin ta sai sunje gida zasu nemi mafita. Wani ajiyan zuciyan ta sauke tana mai lumshe idanun ta alamun ta fahimta, a bakin kasuwa mafi yawancin matan suka sauka kowacce zata nemi motan da zai Kai ta Anguwan ta sai su Inna, Maa, Maman Dije dasu Inna Asabe sune kad'ai aka karasa dasu kofar gida. Maa bata shiga gidan mu ba ta wuce gidan ta su kuma suka shigo gida, a tsakar gida suka iske Gwaggo Aisha tana wanke wani abinta cikin bucket, sallama kawai sukayi kowacce ta wuce bangaren ta ba tare da sun tanka mata ba domin habaice-habaice take tana bin su da harara wai kwadayi yasa suka bi Inna, ita kuwa har duniya ta nad'e bata ga abinda zai sa tabi ta ba dan har abada a matar cushe matar biyan bashin take kallon ta. Wankin ta bari tana cizon yatsa dan ba haka taso ba taso koda Maman Dije ce ta tsaya acikin su ta tanka mata sanin halin ta na bata barin ta kwana sai dai yau harda itan suka ki kulatan. "Ai duk hanyan da zan bi sai nabi naga bayan ki Bintu baki isa kiyi walwala ba muddin ina numfashi a doron kasa sai nabi na kuntata rayuwar ku keda wancan kod'add'iyar 'yar taki" tana magana ne da dukan karsashi dake zuciyar ta fuskarta kuwa na nuna zata iya aikata koda kisa ne dan cimma burin ta. Hajara da shigowar ta kenan gidan tana tsaye a bakin gate kuma tana jin duk kalaman da mahaifiyar ta take furtawa akan mu, hawaye take na tausayi mahaifiyar tasu kan rayuwar da ta zabarwa kanta kullum cikin addu'an neman shiriya take mata amma da alamu tayi nisa sai a hankali, hawayen fuskarta ta goge tsab tana ayyanawa dole ne tayi wani abu na dakatar da duka Shirin ta in ba haka ba ta san halin mahaifiyar ta zata iya aikata komai da ta fada koma fima. Bayan ta tabi zuwa cikin parlour su da ko carpet din arziki babu, da tsaki ta shigo maimakon sallama ta zauna a kasa tana kara jan tsakin da karfi yanda zata ji tayi magana. " Ke kuma lafiya zaki zo ki saka mutane a gaba kina ta jan tsaki kaman wata tsaka?" Gwaggo Aisaha ta tambaya tana mata wani mugun kallo dan harda ita cikin wayan da take jin haushin su kan ko kad'an bata son taji anyi maganan mu balle a fad'i laifin mu. "Umma ki taimake ni zuciya ta zata buga, wannan kyakkyawan mijin da gida kaman aljannar duniya dani ya dace ba wannan kod'add'iyar yariyan ba" ta karasa tana kara b'ata fuska kaman zata fashe da kuka. A mamakince Gwaggo ta juyo tana kallon ta fuskarta d'auke da alamun tambaya tace " wai maganan wa kike min kuma wwni gida?" Sai da Hajara ta tab'e baki kaman abinda zata fad'a har cikin ran ta ne tace " hmmm maganan wannan kod'add'iyar yariyan mana 'yar gidan Bintu". Cikin wani irin sauri tazo gaban Hajaran ta zauna tare da kamo hannayen ta duka 2 ta rike cikin nata fuskarta cike da tsansan farinciki tace " Hajara da gaske kike ?" "Gyad'a kai tayi ta kwakulu hawaye tace" Umma kin gan shi kuwa kaman wani balarabe ga gidan ma yanda kika San a kasar waje kike, ni dai gaskiya ki taimaka in kwace su duka a hannun ta" ta karasa tana goge hawayen ta "Alhamdulillahi!!! Allah nagode maka wannan mugun asiri da matar cushen tayi miki ya karye Hajara ta ta dawo gare ni" tace tana rungume ta harda kwallan farinciki a idon Gwaggo. "Asiri gaskiya ce ni shaida ce tunda gashi nagani akan 'yata mafi soyuwa a gare ni amma kiri-kiri aka raba mu ba kya son a ambaci sunan su koda da wasa da mutum ya tab'a su gwara mutum ya shararawa uwar ki mari goma" Gwwggo ke fadin haka cikin kuka dan da gaske take farinciki dawowar tan domin tun ada baya itace abokiyar shawarar ta daga baya Kuma da ta gane gaskiya sai taja baya da ita. Ta dad'e tana da burin yin wasu abubuwa da dama akai na da Inna ta amma ta rasa dawa zasu had'a Kai suyi domin Jameela kullum bata gida koda ta dawon ma a buge take shigowa. "Kinga yanzu 'yar uwar ki halin da ta zabarwa kanta kenan bana ma samun ganin ta sai bayan satika ko kwanaki koda na ganta ma ba a cikin hayyacin ta take shigo min ba sai cikin maye dama kece kad'ai kika rage min ta raba mu da mugun asirin ta sai dai ta Allah ba tata ba gashi komai ya karye Alhamdulillahi" ta karasa cikin tsantasan farinciki da ta dad'e bata ganta a ciki ba. Mayar hawayen idon ta tayi na tausayin mahaifiyar tasu sannan ta maye gurbin da murmushi tace " toh yanzu meye abin yi Umma?" "Tun kwanaki Lantana ta min alkawarin kaini wajan wani boka da aikin shi yake kaman kaifin wuka, dama rashin ki a kusa dani yasa na bar maganan amma tunda komai ya warware zanyi mata magana mu tafi cikin kwanakin nan komai da suka mallaka sai ya dawo gare mu ". *************** Shiru gidan kake ji kaman ba shine dazu take cike da mutane ba, duk sai naji babu dad'i Ina nan zaune a inda suka bar ni na kurawa tv da yake ta karaji shi kad'ai ido kaman kallon nake amma kuma hankali na ba anan yake ba ya tafi ga tunanin haka rayuwa ta zata kasance zama da wanda bai san daraja ta ba wanda yasha fada min da bakin sa ba sona yake ba, tunda aka kawo ni gidan nan ban abu wai shi farinciki ba ina dai zaune ne kawai in mun hadu banda mugunta ba abinda yake shiga tsakani na dashi. A da nima haushi yake bani kuma in yayi min muguntan bana samun kwanciyar hankali har sai na rama amma a kwanakin nan ban san me yasa ba ko me yayi burge ni yake maimakon inji haushin sa, in yana zaune a parlor ko yana cin abinci nakan buya inyi ta kallon shi tunda ya min iyaka da inda yake yace kada in kuskura in zauna inda yake, so must time ko ina parlour in ya shigo zan tattara in koma nawa inyi ta leken shi wani lokacin nakan ji haushin kaina tare da tambayan toh me hakan yake nufi amma babu mai bani amsa. Wani abin takaici ko cikin dare na tashi wani lokacin na kan leka d'akin shi,ina iya hango shi yana baccin shi cikin kwanciyar hankali, cikin d'an hasken dim light dake bari na gefen gadon shi ba na sanin ko minti nawa nake a wajan all I is ina dadewa sannan in koma in kwanta Sallamar shi cikin azzakar muryan shi naji ya daki kunne na duk da ciki-ciki yayi ta dan na san baiyi tsammanin da mutum ba a parlorn ba, kasa amsawa nayi saima bin shi nayi da kallo har ya shige , yayi min matukar kyau cikin wani lallausan yadi maroon da ya saka anyi mata dinkin zamani irin iya cinyan nan kan shi babu hula sai bakin gashin kan sa dake sheki yana d'aukan ido. Kara fitowa yayi sai dai wannan karon ya cire rigan sai farin vest ne a jikin shi murdadden jikin sa a wake, hannun shi d'auke da laptop yana duba wani abu gaba daya hankalin sa yana kai, ni kuma ina nan tsaye yanda ya barni na kasa motsawa a wajan duk da naga inda nake yake nufowa amma na kasa matsawa ina kallon yanda shima vest din ta zauna a jikin shi, wato shi komai ya saka sai tayi mishi kyau....... Ina cikin zancen zuci naji mutum ya fad'o min mukayi baya tare kan kujera dake bayana ya kasance yayi min rumfa da faffadan kirjin shi, wani irin yanayi da ban tab'a tsintan kaina a ciki ba yau naji ni a ciki ganl kamshin jikin shi da kuma d'umin jikin sa da suka had'u suka bada wani yanayi na musamman, lumshe ido na nayi Ina addu'an Allah yasa mu dauwama cikin wannan yanayin Mai wuyar fassara. Cikin wani irin zafin nama ya d'aga ni tare da hamb'are ni gefe na fad'i kasa dole na waro idanu na dana lumshe na sauke su a kan shi, kaman wanda ya tab'a Kashi haka yake ta kakkab'e jikin sa yana watso min mugun kallo kaman idanun shi zasu zubo kasa. "Wannan kuma wani sabon iskanci kika fito dashi kizo ki tare min hanya kawai dan wannan kazamin jikin naki ya rab'i nawa, how dare you tayaya ma zakiyi irin wannan tunanin ko ban fad'a miki matsayin ki ba kamin ma ki shigo" ya karsa yana zaro min ido waje cikin sauri nayi kasa da nawa domin na razana. "Wallahi kika kara bin hanyan da nake bi sai nayi mugun tsab'a miki da alamu ina raga miki dayawa shiyasa har kika samu daman baza kolin ki yanda kike so" still ni dai bance mishi komai ba sai kallon shi da nake ta kasan ido cos duk yanda naso hana kaina kallon shi na gagara. D'aukan laptop dinsa yayi ya dudduba yaga tana nan lafiyan ta qalau babu abinda ya same ta, Kara saka kafa yayi ya hamb'are ni yana " get out of my sight da idon ki kaman na mayu a wajan ana magana kin zuba min su kaman zaki cinye ni". Tashi nayi ba tare da nace mishi kala ba na wuce kitchen na hado mishi drinks da abinci na kawo na ajiye mishi na wuce daki ina jiwo muryan shi yana in dawo in kwashe jagwalgwalo na ko waiwayowa banyi ba balle yasa ran zan dawo in kwashe. A bakin gado na zauna a hankali Ina mai lumshe ido tare sakin kayataccen murmushi ni kad'ai yanayin da muka kasance yanzu Yana min gizo a ido, kwanciya nayi rigingine ina kallon pop saman d'akin with a blushing face sai juyi nake akan gadon. Zaune na tashi ina yamutsa fuska ni kad'ai tare da tambayan kai na what's wrong with me? Na rasa mai bani amsa nayi nayi ko zan samu haske amma ban samu ba, tagumi na zuba kawai na zauna shiru can naji zuciya ta na azalzala ta kan in leka inga ko yana cin abincin? Cikin sand'a na iso bakin kofan na leka ta bulin makulli, laptop din naga ya ture gefe yana ta kwasan gara harda lumshe ido alamun abincin yana mishi dad'i, rufe baki nayi da tafin hannuna kada dariyan da nake rikewa ya fito fili ya ji ni. Ina kallon shi ya cinye abincin tas ya kora da juice sannan ya tattara kayan ka Kai su kitchen yazo ya zauna ya cigaba da aikin da yake yi a laptop din, ni ko sai da naga ya gyara komai ya zauna sannan na fito nayi hanyan kitchen ba tare da na kalli inda yake ba . Da ido ya bini har na shige yana tunanin me zai fad'a wanda zai kare kan shi kan cewa ba shine yaci abincin ba, har na fito bai samu wata gamshasshiyar magana da zai gaya min in gamsu ba. Tafiya nake a hankali ina kallon shi da alaman tambaya akan fuskata na waye ya cinye abincin? Cikin kame-kame ya fara magaa " hey look don't think negative dan ko yunwa zata kashe ni banga abinda zai saka inci wancan jagwalgwalon ba I just gave it to the driver suka cinye ya dawo da...." Kasa karasawa yayi ya tsaya kallon yanda nake ta gyad'a mishi kai tare da murmushin rainin hankali. "Meye kika wani zuba min ido kina dariya kaman wanda ke miki karya?". Saurin girgiza kai na nayi Ina danne dariya da yake son kufce min. A fusace ya tashi yayi kaina yana " dariya kike min ni zaki maida mahaukaci?" Aiko Ina ganin ya mike na kwasa a guce ina sakin dariyan da na danne na shige bangare na gudu ban tsaya a parlour ba na wuce daki na fad'a kan gado Ina dariya sosai . Shima daya biyo ni da gudu bai san lokacin da ya saki murmushi har hakoran sa suka fito ba ya girgiza kai yana " lallai yarinya nan ta fara raina ni". Nagode da addu'oin ku Allah ya bar zumunci nd Alhmdlh jiki na yayi sauki sosai . [6/16, 9:21 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* Assalamu alaikum yan uwa da fatan munyi sallah lafiya, Allah ya karb'i ibadun mu ya nuna mana na gaba Ameeen. *39&40* "kada abinda kika gani ya tayar miki da hankali domin matan masu kud'in nan haka suke sun fi son 'ya'yan su su auri 'ya'yan masu kud'i kamar su, bakomai yasa kika ga tana mana wannan kallon ba sai dan sanin mu talakwa ne. Idan muka cigaba da yi musu addu'a sannan kuma ita Zareefa zata iya samo soyayya surukan ta wajan dagewa da kyautata musu tare da yi musu zallar biyayya" Maa ce take fad'awa Inna cikin kwantar mata da hankali. "Hmmmm hakane Maa har hankali na ya kwanta da tunda na dawo na kasa sukuni domin na san yanda wannan matsalar take" Inna ta amsawa mahafiyar ta cikin sanyin murya.. " Ki kara kwantar da hankalin ki saboda mun yarda da tarbiyan da muka bata ba zata tab'a yin abinda zai b'ata sunan ta ko na gidan ku ba" Maa ta kara tabbatar mata nan dai ta daura da shawarwari da hira masu sanyaya zuciya sai ga Inna da tazo mata wani cikin damuwa da sanyi jiki ta ware suna ta hira harda kyalkyalan dariya. Bayan kwana 2 Gwwggo Aisha ta had'a duk wasu 'yan kud'ad'e da suke hannun ta tare da sayar da wasu kayayyakin ta saboda ta samu isassun kud'in zuwa wajan boka, dama haka take duk tabi ta sayar da abinda take dasu dan ko dakin Inna Asabe yafi nata kyan gani domin ita ta fawwalawa Allah lamarin ta ta rungumi sana'an ta kuma alhmdlh tana samu daidai gwargwado domin tana sayan kayan daki da kadan kadan tana gyara dakin ta. Sun je wajan bokan ita da lantana da yake can jejin Goshe ko tsoro basa ji na yanda hanyoyin maiduguri suka lalace, sunyi sa'a sun same shi ya basu magani amma yace a abinci za'a zuba mishi na kwana 3 in dai har yaci abincin toh zai min wani irin tsana da bashi da iyaka ya min koran kare a gidan shi. Wani kullin maganin ya Kara miko musu yace shi wannan kuma a turare zasu saka Hajara ta rinka shafawa a duk lokacin da zata je kusa da shi , in har ya shaki kamshin toh shikenan an wuce gurin zata zama itace mace kad'ai a rayuwar shi ko uwar shi ba zai kara tuna ta ba. Cikin tsananin farincikin samun nasara ta dawo gida ta labartawa Hajara yanda sukayi da boka, nan kuwa ta hau murna kaman da gaske harda su rawanta wai ta kusa samun miji balarabe. *************** Kaman yanda ya saba kullum sai yaje ya gaida iyayen nashi yauma ya isa gidan nasu akan lokaci domin ya samu Abban shi a gida bai fita ba, cikin girmamawa ya isa gare shi ya zauna wajan kafafun shi sannan ya gaishe shi yana daura kan shi kan kafar Abba. Cike da so da kaunar tilon d'an nashi ya amsa yana mai shafa gashin kan shi, dan yanzu sosai suke shiri ba kaman da ba da kullum suke cikin rigima kan hallayyar shi ganin yayi auren yasa yake ganin ya natsu sosai. "Ina 'yata tana lafiya ko?" Abba ya tambaya bayan ya amsa gaisuwan nashi. "Tana nan lafiya Abba tace ma in gaishe ku" ya bashi amsa yana wani tsunne Kai kaman da gaske. "A'a ni gaisuwan nan ta ishe ni hakan nan tunda taki zuwa mu ganta koda yake bata da laifi kai ne kake mana rowan ta ko Hajiya?" Ya karasa yana maida hankalin sa kan Mom da take saukowa yanzu. Sai da ta tab'e baki ganin dukkan su basa kallon ta sannan ta kirkiro murmushi tare da karasawa gare su ta zauna kusa da Abban tana mai cewa " babu batun rowa ririta amaryar sa yake" ta karasa tana dariya kaman da gaske. Dariyan suma sukayi suka cigaba da hiran su har zuwa wani lokaci sannan ya mike yace zai tafi "Ya maganan da mukayi da kai sai yaushe zaka fara fitowa office?" Abba ya dakatar da shi. "Sai nan da 2 months" yace yana sosa keya, dariya suka mishi Abba yana " ja'iri wata 2 ai kaman kwana 2 ne yanzu zai zo ya wuce, amma ka tabbatar ka kawo min 'yata mun gaisa". Mom da duk haushi ya cika ta na me yasa Abba yake son gani na ta bud'i baki zatayi magana yayi saurin dakatar da ita wajan daga mata hannu ba dan taso ba tayi shiru tana gani har Zafar din ya fice zuciyar shi fari tass dama abinda yasa yace sai bayan wata 2 zai fara aiki kamin nan ya gama da chapter na ya Zama free man zaiyi abinda yake so. Ni kuwa bayan wannan incident daya faru tsakanin mu wanda ya kasa barin kwakwalwata bamu kara zama waje daya dashi ba sai dai da naji motsin shi zan l'eko in kare mishi kallo sometimes yana cin abinci sometimes kuma yana wannan danne- dannen shi a laptop, ni dai har yau ban san me yasa bana gajia da kallon shi ba. Yau tunda na tashi na gama aiki na zauna ina duba wani littafin Hadisi cikin litattafai na islamiya, wannan mayen kamshin nashi shi ya fara min sallama, wani irin zillo zuciya ta yayi kaman zai fad'o kasa jin wannan sassayan muryan yana cewa " ki shirya anjima da daddare zamu je ki gaida su Abba, nd saura in muka je kada ki kama kan ki kije kiyi ta musu kauyanci ki da kika saba kiga yanda zan tsaba miki ". Maimakon inji haushi ni dariya ma ya bani dan haka ban san lokacin da na saki wani kayataccen murmushi ba, wai nice zanyi mishi kauyanci ko ce mishi akayi daga kauye nake oho. Cike da takaici yake kallon yanda na sunkuyar da kai kasa ina murmushi, shifa wannan sabon dabi'a da na samu haushi yake bashi da duk abinda zaiyi min ko ya fad'a min baya bani haushi balle in nuna ko inyi kuka, in ya ganni ina kuka wani dad'i yake ji na musamman amma da yanzu bana nuna jin haushi sai yaji duk haushi ya kara cika shi. Cike da tsana ta ya hamb'are ya fice yana" duk abinda za'a mata sai ta zauna tanawa mutane dariya, mayya kawai ni dai ba zaki cinye ni ba" yana magana yana mai ficewa daga parlourn. Tashi nayi na karkad'e jikina still murmushin bai bar fuskata ba wai nice mayya hmmmm. Tunda yace zamu je gaida iyayen shi duk sai na kasa zaune na kasa tsaye ina tunanin me zan kai musu da zan burge su, abinka da masu kud'in nan ba komai zaka musu kayi gwanin ta ba. Duk tunani na ya tsaya ne kan girki, toh in banda girkin me nake dashi da zan kai musu, kitchen na shiga nayi tsaye ina tunanin what should I cook? Wai meye nawa da zan takura kai na kan sai na musu gwanin ta kwana 2 nan mantawa da nake cewa auren temporary nake zai iya sallama ta at any time tunda yanzu mun bawa wata d'aya baya, saurin kawar da wannan tunanin nayi saboda yanzu na tsani in tuno da hakan a cikin raina. Tunani na ya tsaya ne kan inyi musu abincin gargajiya maybe zasu fi son ci, ina da garin ndalayi da aka had'o min cikin gara ban tab'a amfani da shi ba,yau shi na d'auko na daura tukunya mai dan girma da ruwa dai-dai yanda nake so. Kamin ruwan ya tafasa na gyara kayan miyana na daura miyan a gefe, miyar kubewa danya da yaji zallar naman rago sannan na tuka tuwo bayan na wadata ruwan daya tafasa da man gyad'a, sabuwar warmers da ban tab'a amfani da su ba na ciro na zuba abincin a ciki bayan nayi malmala masu kyau sannan na Kara bin man su da man shanu na rufe. Ganin akwai sauran time yasa nayi samosa da meat 🥧 suma nayi package din su a wasu containers masu kyau, duk na jera su a cikin yalwataccen basket sannan na lullub'e saman da tumakasa mai kyau na fito da shi kan dinning sannan na wuce dan shiryawa. Cikin atamfa super fari tas da adon flowers blue na shirya kaina na zauna na dan yi make-up dina sama-sama harda kashe d'auri duk da Ina jin ana kiraye-kirayen sallah magarib ban dakata ba saboda ina fashin sallah, jewelries da na saka duka pure gold ne hakan sai ya kara haskani nayi kyau sosai abina . Sai da na gama kwalliya na sannan na tuna ashe ban ci abincin ba, fitowa nayi kitchen na zuba rabo na a plate shima na zuba mishi komai da nayi harda su snacks din dan a tunani na ba lalle bane yaci abincin gargajiyan da na girka. Ina cikin cin abinci na naji motsin ya shigo Kuma na tabbata yana dinning yana kwasan gara sai dai shegen girman kan shi yasa ba zai tab'a admitting cewa yana ci ba sai dai yace masu gadi yake bawa. Muryan shi ne ya katse ni yana in fito mu tafi, sai da na kara shafe jikina da humra mai dad'in kamshi na yafa mayafi blue mai dan girma na saka takalmi flat shima blue da poss din sa wanda wayata ce kawai a ciki sannan na fito hannu na dayan d'auke da plate din da na gama cin abinci, a tsaye na same shi shima ya shirya cikin kananan kaya riga ash color da wandon jeans fari sol. Ta gefen ido na kalli kan table din ga mamaki na tass ya cinye abincin ko tab'a su snacks din baiyi ba, fasa shiga kitchen din nayi na tsaya na tattara kan table din na wuce dasu Ina kallon shi ta gefen ido dariya na cina ganin yanda ya wani tsare gida wai shi ala dole ba shine yaci ba. Naso in tsaya in wanke plates da muka bata sai dai gudun masifan shi yasa na bari kan sai mun dawo, koda na fito shi har ya fice nima ban tsaya b'ata lokaci ba na d'auki basket da na jera abincin a ciki nabi bayan shi, a dan tsorace na isa ga motan da yake ciki duk da kasan zuciya ta cike yake da farincikin yau zan fita in ga gari dan tunda aka shigo dani cikin gidan nan ko bakin gate ban tab'a lekawa ba. Koda na iso bakin motan sai nayi tsaye na rasa ya zanyi in shiga kada in shiga baya yace na maida shi driver sannan ina gudun shiga gaba yace na raina shi, shahada nayi na bude gidan gaban na shiga ganin ko inda nake bai kalla ba saima mayar da kan shi da yayi yana duba wani abu a cikin locker, sai da na zauna sannan na mayar da murfin na rufe tare da neman inda zan ajiye basket d'in. Basket d'in hannu nawa yabi da kallo kaman zaiyi magana ko me ya tuna oho naga kuma ya mayar da kanshi gefe tare da jan motan muka fita a gidan ba tare da ya Kara kallo na ba. Shiru cikin motan kaman babu mutane a ciki har muka iso wani tangamemen gida wanda ko ta waje kasan masu gidan sun jiku da naira, horn d'aya kawai yayi sai ga mai gadi ya taho da gudu ya zuge mana gate muka kutsa kai cikin hadadden gidan, baki sake nake bin gidan da kallo ashe da gaskiyan shi da yake cewa kada na mishi kyauyanci. Talle min baki dana sake yayi da yatsa yana harara ta yace" wato baki yarda da abinda na gaya miki ba ko?" Yace yana jefa min mugun kallo, b'ata fuska nayi ina shafa baki na dan ba karya naji zafi sosai. Bai bi ta kaina ba saima bud'e motan da yayi ya fita abin shi, shiri na saita natsuwa ta na bud'e murfin motan nabi bayan shi ganin yana son bace min, tun kamin mu karasa ma'aikatan gidan nasu suke ta durkusawa har kasa suna kawo mana gaisuwa amma maimakon ya tsaya ya amsa gaisuwan cikin mutunci sai dai kawai inga ya daga musu hannu ya wuce abinshi a zuciya ta nace wato shi ko ina yake sai ya nuna wannan girman kan nashi. Wata mata ce ta karaso gaba na cikin sauri zata karb'i basket din hannu na nace mata ta bar shi amma ta nace sai na bata,ni kuwa ganin zata kusan sa'a da Inna ta yasa naki sake mata, dago kan da zanyi naga ashe bai shiga ba ni yake jira wani mugun kallo ya watsa min mai kama da warning yasa na sake mata basket d'in babu shiri na karaso inda yake jira na. Hannayen mu ya tsarke waje d'aya sannan yayi sallama muka shiga cikin parlorn ,ashe abin kallon na ciki banga komai ba, ban san yanda zan kwatanta muku ba amma gidan yafi gaban had'uwa da kyar na shanye kauyanci na wannan karon na daina kalle-kalle na kalli gaba na, a can tsakiyan parlour Abba ne da Mom zaune kan wani lallausan rug sun saka warmers a gaba da alamu abinci suke shirin ci muka zo. Abba fuskar shi d'auke da fara'a ta musamman yake amsa sallaman yayin da Mom Kuma baka gane yanayin da take ciki gata nan dai fuskan nan nata ba yabo ba fallasa, sau d'aya kawai na dago daga nan ban kara gigin d'agawa ba saboda kunya duk ya gama lullub'e ni yanda muka shigo hannun mu sarke nayi ta kiciniyan kwacewa amma bai bani daman hakan ba. Kusa da Mom matan nan ta duka har kasa ta ajiye basket din sannan ta fice, sai da muka zo tsakiyan parlorn sannan ya sake min hannu ya karasa kusa da Abban shi ya zauna yana zuba musu shagwaba kaman karamin yaro suna biye mishi. Ni dai daga dan nesa dasu na tsugunna Kai na a kasa na fara gaishe su, cike da kulawa Abba ya amsa yana in karaso kusa Mom in zauna mana ya zan zauna a nesa sai kace wata bakuwa,cike da jin nauyin su na matso na zauna ina Kara gaishe ta ganin bata wani amsa min ba. Sama-sama ta amsa min tana kokarin fara serving din mijin ta amma sai ya dakatar da ita yana mai cewa " dakata mana da zuba abincin nan, ga surkuwar mu ta kawo mana kayan dad'i shi ya kamata muci yau ki maida naki gefe sai wata rana" ya karasa suna dariya shida Zafar ni dai murmushi kawai nayi na kasa dago da kai. Yake kawai Mum tayi tare da maida warmers din ta rufe zuciyar ta na kuna ta yaya zata kwashi lokaci tayi mishi girki amma wai dan yaga nawa yace ba zai ci ba, bata musa shi ba ta jawo basket din ta fara cire warmers da suke ciki , tana bud'ewa kuwa kamshi duk ya cika parlorn na girkin dana man shanu. Ranta duk babu dad'i haka ta zuba mishi abincin ta ajiye a gaban shi tana shirin rufe su yace mata " ya zaki rufe baki diba ba?" " Zan diba ba rufewa nake ba" ta bashi amsa ta jawo plate gaban ta ta zuba malmala kwaya d'aya tak ta zuba miya kaman bata so ko mai kyankyamin abincin ta kai baki a ba zata sai da ta lumshe ido, dan abincin yayi mata wani irin dad'i domin batayi tsammanin zata ji abincin haka a tunanin ta tunda ni 'yar talakawa ce ban iya komai ba. Zafar da yake kallon duk drama dake faruwa ya saki murmushi domin shi shaida ne in ta girki ne bani da ta 2, Abba sai santi yake ta zubawa wai ya akayi na san yana son abincin gargajiya, ashe wai dole su daina ganin Zafar wajan neman abinci a gida bayan cika baki da yayi ta musu a baya ko mata 4 be dashi abincin Mom d'in shi kad'ai zai ci. Mom tana ji bata ce uffan ba koda suka gama Abba cewa a ajiye mishi snacks din nashi ne shi kad'ai, Mom sai tabe baki take tare da jin haushi Abba yana tsinka su a gaban wannan jinjirar yana abu kaman bai tab'a cin abinci mai dadi ba, ni kuwa duk farincikin ya lullube ni ganin yanda Abba yake ta yabon girki na dan ni nayi ne kawai banyi zaton zasu ci ba balle in samu irin wannan yabon. Tattare kayan Mom ta fara Nima nayi saurin mikewa dan in taimaka mata amma cikin tsare gida tace in bar su, duk sai naji jiki na yayi wani irin sanyi na kasa komawa in zaunan, muryan Abba naji yana min magana yace " zo nan ki zauna daughter akwai hirar mu ta musamman dake" ya karasa yana nuna min gefen sa da hannu. Da kyar na ja kafafu na zauna a inda ya nuna min yayi kasa da murya yace " kyale uwar nan taku haka take bata son in tana aikin mijin ta wani ya saka hannu wai ladan ta zai ragu shiyasa bata barin masu aiki suyi sai ita da kan ta" ban san lokacin da murmushi ya kwace min ba dan salon da yayi maganan dole ne yasa mutum dariya. Zafar dake d'ayan gefen shima dariyan yayi dan ko shi baiji dad'in abinda Mom din nashi tayi ba amma yanzu daya ga Abba yana min barkwanci sai yaji hankalin shi ya kwanta kuma yaji dadi har cikin ran shi. Wani envelope mai dan girma da yake kan kujeran bayan shi ya d'auko ya miko min yace " ga wannan tukuici ne daga gare ni kan yanda kika bada gudumawa wannan stubborned son nawa ya koma gentle boy". Kasa karb'a nayi sai bin foldern nake da ido ina imagining what could be inside? Zafaar da yake sauraron mu ya b'ata fuska cikin shagwaba yace" Abba pls mana". "Kwarai hakane my daughter ki karb'a Mana" yace ganin na kasa karb'a, hannu na rawa na saka na amsa tare da cewa " nagode Abba Allah ya kara girma da daukaka" Ameen my daughter" ya amsa min cikin jin dad'in addu'an da nayi mishi. Muna cikin haka Mom ta dawo ta zauna hankalin ta da imanin ta duk suna kan abinda ke hannu na wondering ya akayi yazo hannu na, ganin irin kallon da take min yasa Abba ya maimaita mata abinda ya faru tare da ce mata " saura kema ya kamata ki kawo taki gudumawar" Dama ance in talaka ya rabe ka in ba kayi sa'a ba toh kaima sai ka talauce, if not ya zaayî ya d'auko takardun company shi na buga ledodi dugurungum ya bada kyautan shi ma yar mitsitsiyar yarinya? Duk a cikin zuciyar ta take wannan maganan amma a zahiri kuma sai ta kirkiro murmushi tace" lalle Alhaji kana ji da wannan surkuwar tamu sai dai ai ko ni ban kara komai ba nakan ma ya wadatar kyautan company fa ai ya wuce wasa" ta karasa zuciyar ta na suya. "Company? Ni Zareefa aka bawa kyautan company?" Na tambayi kaina da kaina hawaye na kokarin zubo min amma na shanye ina kara kasa da kai. " Ga complimentary card dina daughter duk private numbers dina suna jiki a duk lokacin da yayi miki ba daidai ba ko kina bukatan wani abu kada kiji nauyi ki Kira ni Kai tsaye ki fad'a min kinji ko?" Yanzu Kam sai da hawayen yayi nasaran zubo min nayi saurin saka gefen gyale na goge na saka hannu na amsa kamin in samu bakin magana naji muryan Mom da ta kasa hakuri tace " kaima dai Alhaji sai kace kaga wani alamun rashin zaman lafiya a tare dasu ko Kuma wacce bata da iya..." Wani kallon ki shiga hankalin ki da Abba yayi mata yasa ta had'iye sauran zancen nata tare da kawar da kai gefe, saida ya maye fuskar shi da murmushi sannan yace " ta riga da ta shigo wannan family dan haka muma iyayen tane ko kin manta ita zata haifo mana magajin gidan nan a gaba?" A razane take kallon Abban Jin wannan furucin da yayi me yake nufi kenan, duk shekarun da ta b'ata tare da shi ya tashi a tutan babu? Lallai ko sai ta kara tsayawa da kafafun ta ko ayi mata tsakiyar da ba ruwa. Amma a zahiri sai ta gyara fuskarta da nemo aron murmushi da ya tsaya mata a iya leb'e tace " hakane Alhaji Allah ya kara bud'i". Gaba d'ayan su suka amsa da "Ameen " daga nan Abba da Zafar ne kad'ai suka cigaba da hiran su game da business daya yake taya shi a gida ,zuwa kusan karfe 10 Zafar yace zamu tafi Abba yana ta saka mana albarka ita kuma Mom cewa kawai mu gaida da gida. Ga mamaki na har muka shiga mota bai kara hantara ta ba saima murmushi da yake ta faman sakewa shi kad'ai yana tukin sa cikin kwanciyar hankali ni kuma zuciya ta tana wani waje daban Ina rike da complementary card din Abba ina ayyana abubuwa da yawa a raina. [6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* *INNALILLAHI Wa INNA ILAIHI RAJI'UN Muna taya 'yar uwar mu PRINCESS FATIMA MAZADU na babban rashi da tayi wato yayan ta HRH. ALH ABUBAKAR MUHAMMAD KWAIRANGA ( SARKIN FUNAKAYE) UBANGIJI ALLAH ya jikan shi da rahama yasa mutuwa hutu ce a gare shi AMEEEN* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *41&42* Bakomai ne yake raina ba sai yanda zan rama zalunci da yayi min, domin na yarda da maganan Yesmin da take fada min na cewa yana matukar tsoron Abban shi saboda nima gauce yanzu ba jiyau ba, ya wani natsu sai abubuwan mutanen kirki yake alhali kuwa mugu ne na bugawa a jarida. Har muka karaso gida ko ci kan ki bai kara ce min ba nima na share shi na wuce d'aki na, kayan jiki na na fara ragewa sannan na shiga na watsa ruwa na fito nayi shirin bacci na kwanta amma sai na kasa samun baccin, tunanin wannan company da Abba ya bani shi ya fad'o min a rai toh ni ya zanyi da companyn nan? kawai bari in bari in an kwana 2 sai in fad'awa Inna inji me zata ce. Lumshe ido nayi da niyyan bacci haka kawai Yaya na ya fad'o min a rai, ko a wni hali yake ciki, ko meyasa ya guje ni?? Tunanin hakan da nayi yasa na fara hawaye sosai harda shasshek'a dan ji nayi abin ya dawo min sabo fil zuciya ta sai kuna yake, duk halin da nake ciki a yanzu shine sila da bai guje ni ba da wannan mugun ko kallo na ba zai samu daman yi ba balle har in shigo gidan shi. A wannan dare da kyar na samu bacci ya d'auke ni mai cike da mafarkai kala-kala. Ko dana farka da safiyan nan sai naji duk raina a cunkushe yake fuskata babu walwala sam, iya d'aki da parlor na kawai na share nayi kwaciya ta ko kitchen banida niyyan lekawa balle inyi batun girki. Zuwa kaman karfe 10 naji yunwa na neman hallaka ni dole yasa na fito main parlour na had'a tea mai kauri akan dining na d'auki mug d'ina da niyyan komawa d'aki naga mutum a zaune yana waya ko kallon inda yake banyi ba nayi wucewa ta na bar shi baki bud'e cike da mamakin abinda nayi yake bi na da kallo har na shige. "Toh wai me ya hau kan yarinyan nan yau? Zaman da nayi anan ya kusa 1 hr ina jiran inga ta girka wani abu in samu inyi breakfast in fita shine taki yin komai saima tea da ta had'a ta wuce ko gaishe ni batayi ba, ko dai ta gane bana iya cin abincin kowa yanzu sai nata?" Zafar kenan shi kad'ai yana sumbatun sa a cikin ran shi. Zuruf ya mike yana cewa naga kwana 2 yana d'an sake min shiyasa na fara kawo mishi raini bari ya shiga ya gyara min zama, yana maganan ne tare da nufan d'aki na. Hankali kwance nake sipping tea na naga mutum ya shigo min babu sallama sai wani had'a fuska yake wai shi ala dole zai tsoratani. "Ke tsaban kin raina mutane shine har zaki shigo ki fita ba zaki gaida mutane ba?" Ya fad'a cikin tsawa. Sai da na turo baki na dan kalle shi na watsar nace" ni dai banga mutane ba,mutum daya na gani a parlorn". Mamakin da yake fuskar shi kasa boyuwa yayi yana bina da wani irin kallo, had'iye abin shi yayi ya Kara wani tsare gida yace" ohk in ma mutum dayan kika gani ba zaki gaida shi ba kenan, nd what do you mean by ki shiga daki ki zauna shan tea sauran mutanen gidan ba zakiyi musu girki bane?" Sai da na kuma kurban tea na hankali kwance sannan na bashi amsa " I don't feel like cooking today" "What!! Ni kike fad'awa u don't feel like cooking, kin ga ina bin ki a hankali shiyasa ko jira ni ina zuwa zaki min bayanin yanda ya dace" yana fad'an haka ya fuce fuuu kaman zai tashi sama, tab'e baki nayi na raka shi da ido wai ni zai rainawa hankali wai mutanen gidan me zasu ci, yace min dai me zai ci?. No Abba da tun jiya nayi saving a wayata na kira na saka a handsfree na ajiye kusa da ni muna gaisawa Ina karasa shan shayi na daya rage ya shigo dakin a zafaffe da belt a hannun shi har zai bud'i baki yayi magana jin muryan Abban shi yasa yayi tsit yana zare ido, kallon up nd down na mishi ina murmushi Abba yace" da fatan kin tashi lafiya my daughter" Kara kwantar da murya nayi sannan na amsa mishi da" yau na tashi da jiri da amai da zazzab'i Abba ko tashi bana iya yi shine na nemi alfarman ba zan iya shiga kitchen ba yau amma yake ta min fad'a" "Mene! Yana ina, ki bashi wayar in yana kusa" Abba ya karasa a d'an zafaffe. Ina kif-kifta ido kaman da gaske nace " gashi nan Abba" tare da mika mishi wayan, sai a lokacin ya dawo hayyacin sa ya saka hannu ya karb'a yana min mugun kallo, ni kuwa ko a jikina saima murmushin mugunta dana bi shi da ita. "Assalamu alaikum Abba barka da safiya" yace cikin sanyin murya. " Wa'alaikum salam son me nake ji haka kada ka kasance cikin mazan da basa kyautatawa iyalin su mana kayi koyi da manzan Allah dan ya kasance mai kyautatawa iyalan sa,ko kaga haka muke da Momyn ka?" Bai iya bude ya bashi amsa sai girgiza kai da yayi kaman yana gaban Abban. "Kada in kuma jin irin haka try to be a good husband ok, nd get something for her tayi breakfast". Insha Allah Abba" ya amsa cikin sanyin murya sannan ya katse kiran. Ina jira inga ko zai hau kaina da wannan masifan nashi amma ga mamamki na sai ajiye min wayan yayi ba tare da yace komai ba ya fita daga dakin, murmushin nasara nayi tare da gyra kwanciya ta kan kujera na d'auko wayata na shiga watsApp. Bayan fitan shi kaman da minti 30 sai gashi ya kara shigowa da sallama da wasu shopping bags a hannun shi ya ajiye min harda na pharmacy a ciki da alamu magani ya sayo. "Ga breakfast dinki da drugs ki sha bayan kin gama nd pls next time in baki da lafiya let me know" yana gama magana ya fita, ni abin ma sai naji shi wani bambarakwai wai yau Zafar ne yake min magana a nitse babu tsawa harda wani pls? Hmmm tab na yarda da maganan Yasmin da tace yana bala'in tsoron Abban shi daga waya sau 1 har ya sauya. But sai nake jin kaman ban kyauta ba da na had'a shi da mahaifin shi har yayi mishi fad'a, wani bangare na zuciya ta na kara ingizani cewa sai me ai shima lokacin da yake takura ni bai tausaya min ba. Bud'e ledan eatary nayi naga manyan package na take away guda 2 na farko cike da chips da kwai sai na biyun kuma cike yake da pepped chicken sai kamshi suke ba b'ata lokaci na d'iba na fara ci ina zuba santi,sai da nayi nak sannan na tattara sauran na kai kitchen ban gan shi a parlorn ba ban kuma bi ta kan shi ba nazo na cigaba da charting na. ****************** Washe garin ranan da suka dawo daga wajan boka Gwaggo Aisha tasa Hajara wanka da sassafe ta shirya wai ta taho gida na su fara aiwatar da kudurin su tunda wuri, bata musa mata ba ta shirya tsab tayi kwalliyar ta cikin doguwar rigar ta na atampa daya amshe ta sosai,tana bari tayi breakfast kamin ta fita amma ta hana ta tace in azo nan gidana taci. Haka ta fito wajan 8 da wani abu ba tayi nisa da gidan namu ba ta samu kwata ta jefa maganin a ciki tayi wucewar ta, bata son zuwa gidan da sassafe haka ta san duk yanda akayi kila ko farkawa daga bacci bamuyi ba, tunda ta shigo anguwan da nake ta fara jan kafa dan bata san kowa a anguwan ba da ta shiga ta dan ja lokaci har sai Zafar din ya fita kamin ta shigo. Dole haka ta karaso kofar gidan tayi knocking mai gadi yazo ya bud'e mata kofan ta shigo daga ciki sannan ta gaishe shi cikin girmamawa da yake ya dan manyan ta, amsa mata yayi cikin kulawa kasancewar yaji dad'in yanda ta gaida shin. "Dan Allah Baba masu gidan sun tashi kuwa?" Ta tambaya shi lokacin yana shirin komawa dakin shi. "Gaskiya bana jin sun tashi dan sai kusan goma sannan muke kin motsin farkawan su" ya amsa mata. " Toh dan Allah zan zauna a nan kamin su farka" tace tana nuna mishi wasu kujerun roba da suke can gefe cikin furanni. "Toh toh shikenan ki zauna sai sun fito" yace yana shigewa dakin shi, karasawa tayi ga kujerun ta zauna tana ajiyar zuciya samun relief ta ciro wayar ta daga cikin jaka ta fara game dan ya rage mata zaman kad'aici, ya ko taimaka matan dan bata san lokacin da taja a wajan zaune ba hankalin ta duk yana kan wayan taji saukan ruwa kaman daga sama a jiki ta, a firgice ta mike tana " innalillahi wa Inna ilaihi raji'un" a masifance ta juyo da niyyan ciwa wanda yayi mata wannan danyen aikin mutunci sai dai tana jiyowa idanun su suka sarke dana juna shima ya taho da niyyan bata hakuri saboda sam bai kula cewa da mutum a zaune a wajan ba domin kullum yazo haka zaiyi aikin shi ya koma ba tare da yaga wani na gidan ba gwara shi Zafar din sukan had'u wasu lokutan. Da kyar ya samu bakin bata hakuri cikin sanyin muryan shi da ya zame masa jiki, sai a lokacin Hajaran ta dawo hayyacin ta ta janye idon ta akan shi a kunyace tare da ce mishi babu komai. Ajiye tiwon hannun shi da yake bawa flowers ruwa dashi yayi cikin sauri ya koma can inda ya ajiye kayan shi wajan Baba mai gadi ya d'auko wani babban handkie ya dawo duk tana tsaye tana bin shi da ido yazo ya goge mata ruwan da ya jika kujera da take kai sannan ya dube ta wannan karon fuskar shi d'auke da murmushi yace " ki zauna Hajiya kiyi hakuri wallahi ban lura da mutum a wajan bane d z an kullum Ina zuwa aiki ban tab'a cin karo da wani a nan zaune ba shiyasa". Zama tayi a hankali itama fuskar ta d'auke da murmushin tace " kada ka damu na san ba da gangan kayi ba, nima na zauna a nan ne kamin masu gidan su farka daga bacci, ba matsala ka cigaba da aikin ka nagode". " Toh Hajiya nima nagode" yace yana komawa kan aikin shi sai dai tunda ya fara hankalin shi gaba daya yana kan ta haka itama ta kasa natsuwa hankalin ta kacokan yana kan shi sai kallon shi take ta kasan ido dan ba laifi shima kyakkyawa ne gashi da hasken sa dan yafi ta haske sosai. Suna had'a ido sai su sakarwa juna murmushi a haka har ya kammala aikin shi ya dawo wajan ta yana ko ya taya ta zama ne tunda har yanzu da sauran lokaci, bata musa ba ta bashi dama ya zauna sai gashi suna hira kaman sun dad'e da sanin juna kamin Zafar ya fita har sunyi exchange na phone number tsakanin su. Zafar ya fito zuwa gaishe da iyayen shi kaman yanda ya saba ya shiga mota ya wuce su sun ga fitowan shi Amma shi sam hankalin shi bai Kai kan su ba yaja motan shi ya fita bayan mai gadi ya bud'e mishi gate. Koda Zafar ya fita sai da suka kara kusan minti 20 tare kamin su rabu ta samu daman shigowa cikin gidan a lokacin ni kuma na gama breakfast nazo nayi kwanciya ta naji salkamar ta, cikin ihun murna na fito na rungume ta zan iya cewa bayan yinin bakwai da akayi sai yau wani nawa yazo min dan haka cike da farincikin na tarbe ta ina tambayan ta Inna ta da mutanen gida tace min duk suna lafiya. Bayan gama gaishe-gaishe na gabatar mata da sauran abincin da na rage ta fara ci muna hira cikin tsananin farincikin da kewar juna. Shi kuwa Zafar tunda ya tafi gidan su hankalin shi na kaina dan ya kasa sakin jiki suyi hira kaman yanda suka saba, bini-bini sai kallon agogo yake har Abban shi ya gano shi yace" ya kamata ka tashi ka koma gida son dan my daughter tana bukatan kulawar ka musamman a halin da take ciki yanzu". "Wani hali take ciki kuma?" Mom da tundazu taki saka baki a hiran nasu ta tambaya a d'an rikice. "Ke kuwa ai zaki fimu sanin halin da take ciki tunda ke macece, yau ta tashi bata da lafiya wai tana fama da jiri da ciwon kai kinga alamun ciki sun bayyana a tare da ita amma fa a nawa hasasshen kenan ko kunje asibiti?" Abba ya amsa mata da wadatattacen murmushi saman fuskar shi yana kallon Zafar daya duke kai shima yana murmushin tare da girgizawa Abba kan shi. "Ja'iri ji wani murmushi dan Allah Hajiya yaran yanzu da shegen son 'ya'ya suke" ya karasa yana dungure mishi Kai. Mom da tayi suman zaune ko jin abinda yake fad'a ba tayi ba har yayi musu sallama ya fita ya bar ta baki bud'e. Anan Kuma nida 'yar uwata sai hira muke zubawa yanda tun daga kofar shigowa zaka ji hayaniyar mu ba dan komai ba sai na labarin sabon saurayi da tayi na gidan mu take tana yayi mata amma tana gudun kada yaji ta tab'a aure da haihuwa ya guje ta... Ni kuwa ina kara karfafa mata giwan cewa babu wanda zai kalle ta yace ta tab'a aure balle har ace ta haihu, muna cikin haka Zafar ya dawo gidan jiki a sanyaye amma tunda ya fara jiyo murya ta cike da nishadi muna hira yasa ya shigo da karfin shi, sallama yayi ya tsaya daga bakin kofa fuskar shi d'auke da tsantsan farincikin samu na a haka da yayi, bude min hannuwa yayi alamun inzo gare shi har zan watsa masa harara na tuna cewa ashe fa in a gaban mutane ne drama muke yi hakan yasa banyi musu ba na taso cikin wani yauki da ban san na iya shi ba na nufe shi tare da kashe da wani sexy smile. Kafe ni yayi da ido ko kiftawa ba yayi yi har na iso gaban shi kaman zan shiga jikin shi sai na zille ina dariya nace" ga Yaya ta nan ku gaisa" Shafa suman kan shi yayi da hannnu daya dayan hannun kuma yasa ya rike min hannu sannan ya kai duban shi ga Hajara da duk kunyan abinda ke faruwa ya rufe ta yace " babbar Yaya barka da zuwa" har da d'an risinawa kaman da gaske, cikin jin nauyi Hajara ta amsa suka gaisa duk yana rike da hannu na. "Zo muje ki had'a min ruwan wanka wifey" yace yana kokarin jan hannu na zuwa parlor, tirjewa na fara kokarin yi tare da nuna mishi nayi bakuwa zan zauna wajan ta ya tafi kawai banyi aune ba naji ya d'aga ni cak in a bridal style yayi waje dani. " Naji dadi sosai da nazo na same ki cikin koshin lafiya" yace yana bin ko ina na jiki na da kallo ,muna karasa fitowa parlorn na watsa mishi harara tare da kokarin sauka a jikin shi nace " Mallam kana over acting fa sauke ni dan Allah sai kace da wanda yake ganin mu a nan". Cikin wani yanayi na sanyin jiki ya sauke ni kamin yace min wani abu na bar shi nan tsaye na shige kitchen nemawa Yaya ta abinda zata ci da rana , jiki a mace ya koma ya zauna tare da dafa kan shi tsakanin jiya da yau din nan bai san me yake damun shi he feels a different person. [6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹 🦚 *BA SONTA NAkE BA* 🦚 🦚🌹 🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹 _A story about love and sacrifice._ _Written by_ *UMMEE YUSUF* _(Maman Yusuf)_ _*From The Fantastic Writer of*_ ```FARHAT``` ```KAMACE``` ```UKUBAR KISHIYATA``` ```UMMU~SALMA``` ```UWANI``` *_And now_* *_BA SONTA NAKE BA_* ✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍ https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/ *w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* *w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,* *s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.* *Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.* Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa. *INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?* *NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.* Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko. Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa. *Bismillahir Rahmanir Raheem* *43&44* A wannan rana a nan parlourn ya yini kaman an dasa shi yana zaune sai kurb'an ruwa yake duk inda zan wuce kuwa sai yayi ta bina da ido kaman ya samu tv, ni dai ko kallo bai ishe ni ba dan yau wani tashen rashin mutunci nake ji dashi. Sallah azahar kad'ai naga ya fita yayi a masallaci ya dawo a lokacin ni Kuma fitowa ta kenan daga kitchen hannu na d'auke da wani tray mai d'an girma da na d'aura kayan dad'i dana girkawa 'yar uwata, wuce shi nayi zuwa parlona inda na bar Hajara zaune tana kallo,nan tsakiyar parlour na ajiye na fita na had'o drinks masu sanyi a fridge na kara wucewa ta. Ya d'an jima zaune wai ko zan dawo in kawo mishi rabon shi yaji shiru, murmushi yayi kawai tare da kad'a kai ya d'auki makullin mota ya fita ba jimawa sai gashi nan ya dawo da kaya niki-niki a hannu leda d'aya tak ya ajiye a parlorn ya wuce da sauran parlona ya same mu mun fara cin abincin muna hiran mu, ajiye kayan hannun sa yayi ya d'an kalle ni yace " pls ga kada ki manta da drugs d'in ki in kin gama cin abincin ki sha sannan ga fruits suma ki sha zaki ji dad'in bakin ki" gyad'a mishi kai kawai nayi ya juya ya fita yana waiwaye na. "Zareefa gaskiya kinyi dacen miji nagari a wannan zamani da maza ba abinda suka iya sai wulakanta matan auren su, amma ki ga yanda yake tarairayen ki" cewar Hajara kenan, murmushi kawai nayi mata ba tere da na bata amsa ba na fara bud'e ledan fruits d'in a raina ina baki san waye shi bane har kike yabon sa. A can main parlour kuwa Zafar zaune ya saka fried rice nd chicken daya sayo dan yaci amma ya kasa kwata-kwata bai fi spoon 3 yayi ba yaji abincin ya fita ran shi, tsaki yaja yana hararan inda muke bai san ya akayi haka ta faru ba daya saba da cin abinci na har baya iya cin wani abincin wani. Kara kallon abincin yayi gashi dai so color full ya sha veggies amma sam bai ji wani taste ba a bakin shi,tattre su yayi ya ajiye a gefe ya sha fruits d'in daga baya duk ya kwashe su ya mikawa Baba mai gadi. Har kusan la'asar muna tare da Hajara sannan tace zata koma amma zatayi kwana 2 a jere tana zuwa saboda akwai wani waje da Gwaggo Aisha take Aiken ta ita kuma bata son zuwa shiyasa zata rinka zuwa nan as ta tafi inda ta aike ta, ni kuwa cikin murna da jin dad'in zan samu mai taya ni hira har na kwana 2 na amsa mata da ina jiranta tazo da wuri. Duk sauran kayan ciye-ciye da Zafar ya kawo ita na tarawa nace ta kaiwa su Ibrahim, ta amsa tana ta godiya na rako ta har bakin kofan main parlorn ta tafi. Tana zuwa gida ta tarar da Gwaggo Aisha a tsakar gida tana jiran ta, ganin ta da manyan ledoji yasa ta fara washe baki domin taga alamun nasara a aikin bokan ta. "Ya kika dad'e haka Hajara, kin gan ni nan tun d'azu nake zaman jiran ki" ta fad'a cikin d'aga murya yanda sauran 'yan gidan zasu ji. Cikin kara fad'ad'a farar ta ta karaso gaban ta tare da ajiye kayan hannun ta murya kasa-kasa tace" gashi nan yace in kawo gida yana gaishe ki". Wani irin shewa Gwaggo Aisha ta saka tana dariya tace" wannan duka yace ki kawo min lalle sirkin nawa ba wasa" murmushi kawai Hajara tayi ta shige ciki ta bar ta a nan sai bud'e su take d'aya bayan d'aya tana kara bud'a murya tana yabon kayan tare da yad'a habaici. Dare nayi suna zaune suna hira da Gwaggo Aishan wayan ta ya fara ringing ganin number sabon saurayin ta ne yasa ta d'aga tana murmushi bayan sun gaisa yake ce mata bata ma tambayi sunan shi ba, nan itama tace ai ba sai ta tambaya ba shi ya kamata ya fad'a mata nan yace mata sunan shi Amadu. Tashi tayi zuwa bedroom d'in su ganin Gwaggo Aisha ta ishe ta da waye ya kira ko Zafar ne? Da kai kawai ta amsa mata ta karasa shigewa daki ta barta tana ta murna. ***************************** Da daddarem ma kin girkin girka komai nayi na kwanta Ina kallon wani series da nake matukar so a zee world ya shigo min da sallama na amsa mishi ciki-ciki kaman yanda shima ya min, tsaye yayi kaman me son cewa wani abu ko me neman wani abu ni dai bance mishi kala ba na mayar da hankali na kan tv. "Ya jikin naki?" Naji muryan sa kaman daga sama. " Na warke" na bashi amsa ba tare da na kalli inda yake ba. Bai kara cewa komai ba ya fita nabi bayan shi da harara, a raina ina wa zai kara kula ka kaci zalin shi ko ka mishi mugunta da ka saba. Shirin bacci na nayi bayan na gama kallon, na sha bacci cikin kwanciyar hankali sab'anin Zafar daya kwana cikin wani yanayi da shi kan shi ba zai ce ga inda ya dosa ba shi dai kawai so yake ya zauna kusa da ni ko kuma inda zai samu yayi ta kallo na, tun yana d'aukan abin da sauki har ya fara jin haushin kanshi wai me yasa ya damu da wani lamura nane? in ya kalle ni uban me zan bashi illa ma in b'ata mishi rai da sabon rashin kunya da na samo, bayan wannan ma tun lokacin da ya d'auke ni ya fito dani parlor jiki na da nashi da ya had'u yake kewar d'umin jiki na tare da kamshin jikina mai sanyi da tsayawa a rai sai dai dole ya matse gudun kada raini ya shiga tsakanin mu. Ya san bakomai yasa ya damu da lamurana ba maybe tausayi na da ya fara jine kawai dan yaji bani da lafiya, " hakane ma" ya furta a sarari yana mai kara bawa kanshi karfin guiwa da kyar dai ya samu bacci yayi nasaran sace shi a wannan daren. Da washe gari na tashi da sauki dan wannan nauyin da zuciya ta yayi jiya yayi sauki hakan ne ya bani daman fara aiyuka na kaman yanda na saba, bayan na gama share ko ina tass na gyara sannan na shiga wanka ban dad'e ba na fito light make-up nayiwa fuskata na shirya kaina cikin English wears riga da skirt pink color anyi mishi ado da flowers blue hakan yasa na yane kai na da blue vail, kayan bai wani matse ni ba amma ya zauna das a jikina ya min kyau sosai. Zagewa nayi ina girki sanin cewa Hajara zata iya zuwa at any moment,kayan dad'i nake dafawa dan haka gidan ya cika da kamshi masu dad'in shaka,kamshin nan shi ya fito da Zafar daga d'akin shi sai bud'e hanci yake yana lumshe ido tsohon yunwar shi ta jiya na dawowa sabo fil. Kofar kitchen d'in yazo ya tsaya yana kallon yanda nake aiki gaba daya hankalina yana kan aiki ban san ma da zuwan shi ba,shi kuma controlling d'in kan shi yake akan abinda zuciyar shi take ingiza shi ya aikata dan ji yake kaman yaje ya rungume ni yaji wannan d'umin jikin nawa da wannan daddadan kamshin mai sanyaya zuciya amma ya daure yayi gyaran murya Wanda ya d'an firgitani na juyo a d'an razane na ganshi tsaye cikin kayan baccin sa farare kal da alamu tashin sa kenan ko wanka baiyi ba. Kaman ana min dole nace mishi" Ina kwana" saboda ganin babu wasa a fuskar shi, maimakon ya amsa min sai cewa yayi " ki tabbata kinyi da rabon masu aiki tunda kin samu lafiya" sai da na turo baki sannan na bashi amsa da cewa " ni bada su nayi ba dan Hajara zata zone shiyasa nayi girkin". Kara had'a fuska yayi yace" try anything stupid and see"Yana gama fada ya juya ya fita ba tare da ya jira amsa ta ba, " zaka gani kuwa ai ka daina cin abinci na a gidan nan tunda kai d'an wulakanci ne"nace ina cigaba da aiki na. Bayan kaman 30 minutes na kammala komai na jera su kan try na fito na wuce parlour na ba tare da nabi ta kan shi da na gan shi zaune a main parlour ba, shirya su nayi anan tsakiyar parlour na tare da kara saka turaren wuta na dawo inda na shirya kayan abincin kenan sai gashi nan ya shigo da fuska kaman an aiko mishi da sakon mutuwa. "Ina na masu aikin da na gaya miki?" "Banyi dasu ba na amsa mishi ina kara gyara zamana a gaban warmers d'in, bai saurare ni ba direct kai tsaye ya karasa shigowa da niyyan zai d'auke warmer d'aya, cikin azama na kai hannaye na duka biyu na rungume su a kirjina tare da turo baki ina " ni wallahi ka bar min kayana". Bai saurare ni ba yana zuwa yasa hannu ya d'agani cid'ak kaman wata karamar yarinya zai ajiye ni a gefe na rike shi gam ina "wallahi ba zaka d'auka min ba ni banyi da rabon ka ai na san cewa kai kake cinyewa ba wasu masu aiki da kake bawa". Yanayin yanda na cukuikuye shi na rike sai ya haifar mishi da kasala kuma dama abinda tun jiya zuciyar shi ta kwad'aitu da shi kenan,da gangan yayi fara kiciniyan kwace kan shi ni kuma ina kara rike shi akan ba zai d'auka ba kan kace me kokuwa ya kaure tsakanin mu anan yayi amfani da wannan daman hannayen sa babu inda basu je ba a jiki na, ni kuma a hauka na ban kawo komai a raina ba na zata duk cikin kokarin kwace kan shi yake a hannu na. Sallaman Hajara ne yasaka shi saki na cikin sauri ya tashi itama Hajara cikin sauri tayi hanyan parlour dan tunanin ta wani abu daban ya bata, murmushin mugunta shimfid'e a fuskar shi yace " ga tsaraba nan kin tari yayar ki dashi,sai ki san bayanin da zaki mata "sai a lokacin na fahimci abinda ya faru duk sai naji kunya ya rufe ni me ko zan cewa Hajara ai babu abinda zan fada in wanke kaina,dafe kaina nayi cike da takaicin abinda ya faru tare da dana sanin me yasa na biye shi dana sani da barin shi nayi ya d'auki abinda yake so. Plate ya d'auka ya bud'e warmers d'in ya d'ebi abinda yake so ya fita abin shi ba tare da na sani ba domin nayi nisa cikin tunani,ita kuma Hajara bata tsaya a main parlour ba direct fita tayi ta zauna a inda ta zauna jiya tare da dafe kai duk Gwaggo Aisha taja mata wannan abin kunyan asuban fari ta taso ta kan ta shirya tazo kada ya fita aikin su ya koma baya. Hankalin shi kwance yaci abincin sa yana ta sakin murmushi shi kad'ai kaman wani sabon kamu,he really enjoys what happened between us now, fitowa nayi main parlour ganin zaman ba zai fice ni ba . Wani tukikin bakin ciki ne naji ya tokare min wuya ganin yana ci min abinci,duddubawa nayi ko zanga Hajara amma ko alamarta ban gani ba. Komawa nayi cikin Ina ta kumbura saboda haushi na san kila ta koma gida shikenan ya rusa mana budget ina ta murna yau ma zamu yini muna shan hiran mu sai gashi ko gaisawa bamuyi ba ya kore ta. Zaman ta kaman da 15 minutes sai ga Amadu yazo yin aikin sa, maimakon yayi aikin suka bige da hirar su cike da son junan su har Zafar yazo ya wuce da mota bai gama aikin ba ganin sa ne yasa ya maida hankali kan aikin sa,tana zaune ya kammala itama ta mike tace zata koma gida tare suka fito ya rako ta har gida sannan suka rabu cike da kewan juna. Baba Yana zaune a majalisar shi tare da 'yan maula daya samu yana d'an miko musu da na cefane,daga nesa suka hango motocin sojoji har guda 2 sun nufo su, Baba Yana ganin su cikin sa ya murd'a ya mike jiki na b'ari yace "yau kuma me ya kawo wa'yan nan azzaluman cikin anguwan nan" yana magana ne yana nufan hanyan gida amma ko ten step baiyi ba motocin suka karaso tun kamin motan ya tsaya suka fara durowa daga ciki tare d'aga musu tsawa "kada wanda ya motsa daga nan". Cak Baba ya tsaya yana tsiyayen gumi duk ya firgice. "Waye Mallam Hassan a cikin ku?" Suka tambaya. A tare mutanen wajan suka nuna baban mu da yake tsaye yana karkarwa. "Kai ne Mallam Hassan ?" Kai kawai Baba ya iya gyad'a musu. " Common my friend oya! oya! shiga mota mu tafi"wani daga cikin motan ya fad'a, wasu guda hud'u nufo shi fuska a murtuke babu alaman sun tab'a koda murmushi balle dariya, hannu Baba ya shimfid'a yana kokarin rokon su tare da basu hakuri , d'ayan ya d'aga katon bindigan hannun shi yace yana musu gardama wallahi zasu harbe shi a wajan su wuce kuma sun harbe banza. Gudu-gudu Baba ya nufi wata bakar mota da sai yanzu ya lura da ita suka hankad'a shi ciki babu b'ata lokaci suka fice daga anguwan da matukar gudu. " Allah ya kiyaye mu da basu d'ubi kowa daga cikin mu ba sai shi kad'ai suka nema" inji wani dattajo cikin 'yan zaaman majalisan. "Ni dama wannan kud'i na Mallam Hassan akwai ayar tambaya ace mutum yayi kud'i lokaci d'aya"? Wani ma ya kara nashi. " Ai ko yanda suka ciko motoci saboda shi kad'ai kuma kun san abin azimun ne" " Kunga yanzu ba lokacin wannan bane mu watse kamin su canza ra'ayi su dawo su had'a da mu" fad'an hakan ke da wuya duk suka watse cikin abinda bai fi kiftawar ido ba, nan da nan labari ya cika anguwa cewa sojoji sun kama Baba sun tafi dashi. Downloaded from NovelsHQ.com This Novel is downloaded from https://NovelsHQ.com to download more hausa novels visits our site at www.Novels.Com For feedback and support Facebook : https://facebook.com/NovelsHQ.com Twitter : https://twitter.com/NovelsHQ.com Telegram : https://t.me/NovelsHQ.com