Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://NovelsHQ.com to download more hausa novels visits our site at www.NovelsHQ.com For feedback and support Facebook : https://facebook.com/NovelsHQ Twitter : https://twitter.com/NovelsHQ Telegram : https://t.me/NovelsHQ ο»Ώ[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: 🌲🌳🌿☘️ *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *2k complete a telegram. What'sapp group 1k* *0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *101* Muka cigaba da tafiya a gidan babu annashuwa da jin dad'in da ma'aurata kan jiyar da junansu. Ya sauko sosai ya yi tubis da shi domin salon horon da na d'auka ba karami ba ne. Gashi har yanzu bai cewa Hauwa komai ba dangane da zamanta a gidan domin da ya mayar da auransu a k'alla zai samu jin sau'ki ta 'bangaranta. Ya mayar da ita bai mayar da ita ba Allah ne masani, suna dai zaune a haka ita tana wasan 'buya dashi shi kuma yana nuna mata isa da iko irin na d'a namiji tabbas ko bai fad'a ba nasan jiranta yake ta kai kanta ita kuma girman kai ya hanata ta lallaba ta bashi ha'kuri. Amma yadda yake ta kokarin ganin mun zauna lafiya ni da shi na tabbatar da cewar ya d'auki shawarwarin Baban Saude domin ya rage wasu abubuwan sosai da yake yi mussaman akan yaran. Ba su dai dawo gidan ba, amma a sati sukan shigo sau uku ko hud'u mussaman ranar juma'a muna yini tare da su uwar rik'on na su ta had'o su da kayayyaki masu yawa wai su kawo mana. Ban iya cewa su mayar mata ba domin ita Hauwa kallo ba su isheta ba, kusan ni nake diban turarukan ni ma kyautarsu nake yi sauran na ce Baba Tabawa ta yi amfani da su. Ban ta'ba tambayarsa yaushe zai dawo mana da yaran gabad'aya ba, kawai na zuba masa Ido domin ganin iya gudun ruwansa Yadda na ri'ke wuta nake watangaririya da rayuwarsa abin har mamaki yake ba ni. A tsukin Allah Ya jarabce shi dani ainun, ni kuma na'ki bada dama yana ta dai lallaba ni domin idan ma ya yi fushin bai wuce na kwanaki biyu zuwa uku ba zai sauko ha'kuri kuwa ya ba ni ya fi a irga. Dad'i nake ji na ganshi yana karyar mini da kansa sai na yi ta tuna irin rashin mutuncin da ya dinga tsuga mini a can baya. Matar da ya ratayawa fulawar so dama can ita ba wani kwanciyar aure yake yi da ita ka'in da na'in ba da bakinsa ya gaya mini hakan ba matsa shi na yi ba.Ashe ni da ya mayar towon tushe nice marufar asirinsa domin kuwa tuntuni ni nake iyawa da fitinarsa ko Hauwa ba za ta nuna mini komai ba. Dama tuntuni na gama fahimta cewa ta wannan sigar ake gane rauninsa domin babban abinda yake daga masa hankali ya zo da buk'ata naki amincewa ko kuma idan muna yi na'ki taimakawa da wasu abubuwan da za su ba mu nishadi bakidaya hakan ma na kara rikita shi sosai Gabad'aya ya nune koyaushe ya shigo gidanmu ba shi da wani kuzari tafiyarsa Legos ta dinga tangal-tangal domin ya turza-turza da ni na'ki amincewa da na bi shi, na gaya masa har abada kafata ta sake taka garin nan, idan lallai sai na yi zaman auran da shi to ina nan." Saura kwana daya ya tafi Lagos din ya ritsa ni a d'aki. Da farko rarrashi ya fara yi da ban baki tare da alkawarin ba zai sake kai ni kara ba. Kamar koyaushe hakan bai sanya ni na sassauto ba domin kuwa a duk lokacin da zan daga kaina na kalleshi wallahi duhunsa nake gani, a ganina zamana a gidansa kamar takura kai ne tunda shi kam ai kansa ya sani, idan ma ya ce ya tuba da tafiya tayi nisa sai ya koma ruwa Bai wani ba ni tausayi ba duk kuwa yadda yake rausayar da kansa da muryarsa hakan bai burge ni ba. Da ya lura duk abinda yake yi ban saduda ba sai fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba. Har da cewa ba zai ka'ra nema na ba har ya mutu na je za mu tsaya a gaban Allah ranar lahira idan har yana da hakki mala'iku za su yi mana sheda domin kuwa ba zai ta'be yafe mini hakkinsa ba. Ban damu ba ina zaune ina kallonsa ya kama hanya ya fice cikin b'acin rai. Sai bayan fitarsa kuma na ji wani iri a jikina a lokacin da yake had'a ni da Allah. To ban san yadda zan yi na huce takaicin da ya jima yana kunsa mini ba, kuma ni so nake ya gyara tunda ya zame mini takalmin kaza, ba zai yiwu ya saba take mini hakki ya kwana lafiya ba, Ubangiji zuciya yake dubawa domin ba ni da k'arfi ta kowane bangare sai ta wannan hanyar itace damata kuma hanyar da za ta sadudur masa da jikinsa gabad'aya. Da zai tafi ko sallama bai yi mana ba, sai da ya kwana uku ma da tafiya tukkuna muka samu labari a bakin Masa'udu cewa ya tafi ban ji komai a jikina ba, dalili na riga nasan irin rabuwar da muka yi ta rashin arziki ba zata bari ya shigo ya yi mana sallama ba. *** To kwanaki suka cigaba da tafiya har aka fara lissafin watanni da tafiyarsa bai kira waya ba haka zalika mu ma ba mu kira ba. Cikin zuciyata nake fad'in mai hali baya fasawa, aka ce idan ka kwana biyu baka ga mutum ba idan kun hadu to ka tambayeshi halinsa. To sai na so tsokanar Hauwa tukkuna zan ce mata ta kira shi a waya ta ji yana lafiya. A lokacin zan ga b'acin ranta ta dinga fad'in mijinki dai Amina, ki daina danganta ni da wannan rikitaccen tsohon. Na yi ta dariya idan tana hayaniya a raina nakan ce jinin jikinku kuma yana yawo a junanku tunda duk rintsi a ba za a canzawa towo suna ba. Babu wata ala'ka da ta sake had'a mu da Momi, tun bayan abubuwan da suka faru. Sai dai ko bayan tafiyarsa ba ta fasa turo mana yara ba, itama Hauwa ba ta sake maganar dawowarsu ba ban san abinda yake cikin zuciyarta ba kuma yanzu. Wannan littafin na kudi ne Hajiya kada ki karanta mini ba tare da kin biya ni hakkina. Har yanzu kadaran kadahan nake jin ta a zuciyata. Kuma ba na jin haushinta ainun sai dai irin kishin nan da ba za a rasa ba. A ko'ina zan fad'a alheri ta yi mini don yara sun shiga tsakaninmu hakan ba zai sanya ni na mance ba. Na dai nesanta yarana da ita shikkenan sai a zauna lafiya. Sosai Nusaiba da Salim suka d'auki gaba matsananciya da mu. Adam ne kawai yake iya daurewa idan tsautsayi ya sanya mun had'u ya gaishe ni, amma tun ranar da su Yusi suka bar garin gabad'aya ya gaina shigowa gidanmu. Salim da 'yar uwarsa Nusaiba kam abin na su ya yi nisa idan za mu had'u sau goma cikinsu babu wanda zai dubi inda nake balle na sanya a raina cewa za a gaishe ni. Yusi bai ta'ba gaya mini ce wa Adam ya ziyarce shi har sau biyu ba duk kuwa da cewa yakan kira ni a waya sa'i da lokaci mussaman a ranakun da ba su da makaranta tunda tuntuni sun cigaba da d'ora karatunsa a bayaro wasu lukutan ba su da isheshen lokaci mussaman Kamalu da ya ri'ke b'angare biyu. Karatu yake yi sosai irin na da'awa sosai yake bin Malam sunna domin samun ilimi kwanaki satinsa guda a Bauchi wurin Sheikh Guruntum. sai bayan da ya dawo tukkuna yake gaya mini da na tambaye shi dalili ya ce mini yana zuwa neman fatawa ne. Yanzu dai yana tare da Shaikh Abdullahi gadon-k'aya yana daya daga cikin yaransa da suke take masa baya. To a bakin Hamusu nake samun labarin zuwan Adam din don har yake gaya mini irin kayan da Momi din ta aikawa da Gwaggo ta hanyar Adam din. Na yi mamaki sosai kuma jikina ya kara yin sanyi da lamarinta a yi alheri da kyauta hannun hagu bai sani ba. Duk yadda na nuna mata rashin 'kara da kawaici akan yaran nan k'okarinta zumuncin nan da take ta nanata mini ya cigaba da tabbatuwa. Ubangiji Allah Ya ba mu ikon yin abu dominsa. Haka dai rayuwar ta cigaba da tafiya a hangunce ta fannin maigidan namu kam yadda ba mu neme shi ba shima bai neme mu ba. Tun abin baya damuna har ya fara damuna sai na fara fargabar kada ya sanar da Baban Saude cewa ga abinda na tsiro dashi dukda akan gaskiyata ne, to amma nasan ba ni da hujja Mai karfi idan baban Saude ya titsiye ni dalilin abinda ya sake nake haka Koda na gaya masa dalili zai ce mini Mai yasa ban fad'a masa ba ranar da ya zo ya sasantanmu tunda kafin ya tafi sai da ya dinga tambayarmu idan da wata matsalar mu fad'a bayan wadda muka gaya masa. Ga bikin Fadila babbar diyar anti Yagana ya tashi. An yi bikin Yusura sati shida da suka gabata lokacin muna tsaka da rikici dalilin da ya sanya ma kenan ban tambayeshi ba domin kuwa nasan zai huce fushinsa akan hakan ya samu damar gasa mini maganar da ransa yake so kuma ya hana ni zuwa, saboda kada dukan ya zama biyu ya sanya na k'yale shi. Hajja da kanta ta kira ni a waya game da zuwa bikin Fadila da suke shirye-shiryen tafiya ita da Gwaggo tare da yaran wato su Kamalu ai anti Yagana mutuniyarta ce don haka ban yi mamakin nuna za'kuwarta akan sha'aninta ba. Rasa abinda zan ce mata na yi na kama inda-inda da kyar dai na ce mata ni ma ina nan ina shiri amma wata'kila za su riga ni yin gaba. Ba ta fahimci cewa da matsala ba muka yi sallama na ajiye waya cikin zullumi da tunanin yadda zan sanar da shi tafiya maiduguri ya bar ni kai tsaye. Da kunya kusan wata hud'u da tafiyarsa ban kira shi ba bayan kuma nasan da tsananin fushina ya tafi yanzu kuma na kira shi nace masa me?" Haka kwana biyun nan na kasance cikin yanayi na tunani har sai da Hauwa ta fahimta ta tambayeni na gaya mata halin da ake ciki. A lokacin itama jikinta mutuwa ya yi ta dinga fad'in lallai a wannan ga'bar baki da bakin magana Amina. Bikin Fadila kuma ai ke ce kirjin biki, idan ba ki halarta ba akwai matsala gaskiya. To katsam ina cikin wannan halin ya zo ba tare da tsammanin zuwan nasa ba, tunda ka'ida wata shida muke yi a can legos din mu dawo, wai ashe Momin ce babu lafiya hawan jini da sugar har sai da ta kwanta a asibiti tsayin kwanaki goma ba mu sani ba, na yi mamaki sosai domin yarana suna zuwa dukda a satin bai fi sau biyu suka zo ba amma babu wanda ya gaya mana. Kenan a hannun masu aikinta yaran suke har ta fito daga asibitin ko da yake dama sune suke dawainiya da su Mairo da Taburni yaran suna yawan kiran sunayensu Masa'ud shi ya gaya mana wannan labarin domin kuwa shi din ma ya tabbatar mana da zuwansa kamar yadda ya tabbatar mana da tafiyarsa. Bai shigo mana a ranar ba sai washe gari da rana wajan daya da minti biyar lokacin ma daka gani daga massalaci ya fito. Muna falo gabad'aya muka yi masa barka da zuwa ya amsa kadaran kadahan babu fushi haka zalika babu cikakkiyar walwala. Ya tsaya suna magana da Baba Tabawa kamar yadda suka saba har yana ba ta labarin rashin lafiyar Momi din da yadda ta ji jiki. Sosai ta dinga jajantawa tana k'ara tabbatar masa da cewa gabad'ayanmu ba mu sani ba. Wannan karon Hauwa ba ta tashi ba ban sani ba ko nauyin da jikinta ya yi mata ne oho, tunda cikinta a cikin wata na takwas yake ya fito sosai idan ta jibge a wuri d'aya da kyar take tashi. Ya kama hanyar samansa babu wadda ya sake kalla a cikinmu. Amma yanayinsa kadai ya tabbatar mini da cewa lalurar da matarsa take ciki ta dame shi saboda ga yanayin yadda yake bawa Baba Tabawa labarin ciwon tabbas ya ci jikinta da k'arfi. Bayan shud'ewarsa daga wurin da kamar minti goma na tashi na bi bayansa zuciya cike da zullumi da fargaba. A kwance na same shi kawai ya tsirawa rufin d'akin ido. Gabad'aya sai gwiwa ta yi sanyi (wai shin me cece ma duniyar nan ne) tausayinsa ya d'an kamani, amma bari tasirin hakan ya raunarta da ni ba. Har yanzu da sauran takaicinsa a cikin zuciyata. A nutse na zauna gefan k'afafunsa. Ya dube ni bai ce komai ba sai ya janye idanuwansa. Na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." Wallahi ba mu san ta yi ciwo ba, ashe har kwanciya ta yi a asibiti babu labari ai da mun shiga mun dubata." Ya yi shiru bai ce mini komai ba. Sai na janye idona daga kansa na yi kasa da kaina ina dan wasa da yatsun hannuna. Shiru d'akin ya yi na minti kusan goma kafin na sake dubansa yanzu idonsa a lumshe yake kamar mai shirin bacci ganin haka sai na tashi da niyyar fita. Ba tare da ya bud'e idon ba ya ce." Koma ki zauna ina son magana dake.... *Yau fa mutumin ko ni ma ya ba ni tausayi πŸ˜†πŸ˜’πŸ€­ Amina a sassautawa Babanmu mana.* *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: 🌲🌳🌿☘️ *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *2K COMPLETE ON TALGRAM.* *VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *102* Na zauna din kamar yadda ya buk'ata. Ya tashi zaune tare da sauke k'afafunsa kasa. Ya dube ni a nutse kafin ya furta." Akwai matan da annabin rahama ya fad'a cewa ya gan su a can karkashin wutar jahanama, kuma suffofinsu sukan bayyana tun a duniya. Akwai kuma matan da tun a duniya za a dinga yi musu ishara da nuni da cewar aljannar Firdausi madawamiya ce a gare su. Sune muminai wad'anda ayyukan alherinsu yake bayyana ga ko'ina." D'akin ya yi tsit bayan ya gama maganarsa. Na dube shi tare da furta." Ni ina a wane babi kenan, ko kuma na ce a wane ajin ka ajiye ni ai ba kai kake bada aljannar ba." "Tabbas ba ni nake bada ita ba, amma tana k'asan kafafuna haka annabin rahama ya fad'a." Na jima ina dubansa da mamaki wato yabi duk hanyoyin da zai raunatar mini da zuciya bai ci galaba ba shine ya fara wa'azi. Ni abin ma dariya ya so ya ba ni, Ashe ya sani yake takewa da yake hakkinsa ne, ashe da ciwo kuma babu dadi. Na daure sosai kafin na furta." Ayyukana ba su kai ka daga mini kafarka ba kenan?" Ya gyada kansa yana ce wa." Gaskiya ba su kai ba har yanzu. Momi ce ko yau ta fad'i ta mutu wallahi na yafe mata ki shaida aljanna da izinin Allah zata tabbata a kanta." Na yi shiru zuciyata tana hantsilawa saboda tsabar bala'in b'acin rai. Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un na cigaba da nanatawa ban sake mayar masa da martani ba, kuma ban tashi daga wurin ba na ji gyaran muryarsa yana cewa." Kwanaki mun yi waya da Hajja take sanar da ni za su tafi maiduguri da yaran zuwa hidimar bikin 'yar anti Yagana hakane ko." Ban dube shi na ce." Hakane yau saura kwana tara, jiya dai Hajja take ce mini ranar alhamis za su tafi." Shiru ya d'an ratsa wurin kafin ya nisa ya sake ce wa." Yanzu nawa ki ke ganin zamu ba su gudumawa ni dake?" A takaice na furta." Duk abinda Allah Ya hore maka." "Ai shawara na tambayeki ni Allah Ya hore mini tuntuni. Kawai ki gaya mini abinda za a ba su ai auran fari za su yi ko." Na kalle shi babu sukuni na furta." Ya za a yi na yanke maka abinda za ka bayar, ai ba kudina ba ne, naka ne, kuma dai daidai gwargwado sun yi hidimarsu ni ma kuma tuntuni na tura mata da tawa gudumarwar abinda ka ga dama shi za ka ba su." Ya gyada kansa yana fad'in." Ok na ba su 5m ya yi ko?" "Idan haka ka yi niyya ni ina ruwana?" Na fad'a tare da d'auke kaina domin har ga Allah zuciyata zafi take yi mini game da irin mummunan fatan da ya gama yi mini yanzu. Ya ce." Kada ki gaya mini magana Amina, ba na son rashin kunya da fitsara ko kin ga na ta'ba jikinki ne, kin ga alamar sha'awarki a k'wayar idona, ina ce wannan shine yake kawo mini raini a wurinki to ki ri'ke kayanki ba na so." Na fashe da kuka tare da cewa." To ai dama ban ce ka nemi shawarata ba ni ma, kuma ban ce ka neme ni ba, abinda ka yi niyya shi za ka yi, ni ma abinda na yi niyya shi zan yi, aljanna dai kuma babu wani bawan da yake bada ita ta Allah ce, ta hanyoyin alheri ana samunta ba sai ta dalilin wani ba." "Na ji abinda ki ka ce ta shi ki tafi." Na tashi haka kawai na tsinci kaina da buga siket din da yake jikina na kama hanyar fita raina a masifar 'kuntacce. Ban sauka ba tukkuna sai da na daidaita yanayina na sauka na same su suna nan a wurin suna hira Hauwa hannunta ri'ke da apple tana ci babu abinda ya dame ta sai addu'a da ko'karin rabuwa da cikin jikinta lafiya. Ban zauna falon ba kai tsaye d'akina na nufa na yi zaune zugum a gefan gado zuciyata na ta yi mini sa'ke-sa'ke masu kyau da marasa kyau! Lallai cikin wannan duniya babu komai face rikici da tarin kalubale. Babu yadda ban yi ba da Hauwa akan ta shirya bayan magriba mu shiga mu duba Momi amma fafur taki tace itama abar dubawa ce domin kuwa bata kaita jin jiki ba. Ganin taki fahimtata ya sanya na kyaleta kawai muka shirya da Baba Tabawa muka tafi dubanta. A harabar gidan muka riski Salim da Adam a tsaye suna magana. Da sauri shi babban ya d'auke kansa yayin da karamin ya sassauta a nutse ya dube mu da ladabi yake fad'in." Mama ku ne." Na ce." E, mune Adam mun shigo duba Momi ne. Sai ya yi yar dariya wadda babu annashuwa a cikinta ya furta." To shikkenan mu je na yi muku jagora." Gaba ya yi muka bi bayan shi yayin da Salim din yake ta ciccin magani har da jan tsaki. Murmushi kawai na yi a zuciyata gabad'aya yaron ma ni tausayi yake ba ni, domin kuwa ya d'auki lamarin da zafin gaske. Falo muka zauna ya nufi bedroom din ta yana fad'in ."Bari na sanar da ita." Ba mu kai minti biyar da zama ba daya daga cikin masu aikinta ta fito daga kicin da wata madaidaiciyar roba a hannunta Hassana da Minal suna biye da ita. Ganinmu a zaune ya sanya yaran suka tsaya. Ita kuma mai aikin ta karaso wurin da muke har sai da ta risina kafin ta gaishe mu gabad'aya. Ina kallon yadda Baba Tabawa take jan yaran da wasa da tsokana amma suna can nesa da mu sun tsaya suna ta kallonmu kamar sun ga dodanni. Duk da akwai sabo a tsakaninmu dalilin shigowar da suke yi amma ganinmu a gidan sai ya zame musu wani banbarakwai Raina ya 'baci nan take zuciyata ta dinga raya mini abubuwa marasa kyau to idan ba an zauna da yaran an fadi wata magana ba mai zai sanya k'ananun yara irin wad'annan su dinga yi mini wani irin kallo. Abin b'akinciki da takaici ma har da 'yar cikina 'kiri-'kiri saboda kin gaskiya. Idona na zare musu sosai na ce." Tsayuwar ta mecece idan ba za ku gaishemu ba to ku daina kallonmu, ko mun yi kama da tibi ne.'' Matashiyar mai aikin da take jigila da su tana dariya ta furta." Ke Hassana ku zo ku gaisa Mama ce fa." Na ce." A'a rabu da ita kada ta zo mu gaisa ta tsaya." Usaina ta fito daga kicin da shafceciyar wuk'a a hannunta tana fad'in." Mairo ga wukar ki yanka mana." Shiru ta yi tana kallonmu yayin da mai aikin ta je ta da sauri ta kar'bi wukar tana fad'in." A can sama fa na d'orata yanzu Usai sai da ki ka d'aukota." Ba ta ce mata komai ba ta nufo wurin da muke zaune tana zuwa sai ta dora kanta a cinyata tare da zura yatsanta babba a baki tana tsotsa. Na yi shiru ina sauke ajiyar zuciya yayin da na d'ora hannuna a saman kanta. Ganin haka ya sanya Hassana da sauri itama ta zo ta yi yadda Usainar ta yi dama tuntuni Kamalu ya gaya mini kishi ne da su, duk abinda daya tayi to babu shakka yar uwata ma sai ta yi. Da hannu na yi wa Minal alama ta zo wurina. Ta kuwa taho kataf-kataf domin yanzu itace take tashen ki'ba a cikinsu. Na ri'keta sosai Ina fad'in." Ina Khalil yake?" Cikin yanayin maganarta ta furta." yana can gidan anti Nusaiba." Baba Tabawa sai murmushi take yi tana jan su da wasa. Hassana da Usaina iyayen miskilanci ne, Minal din ta fi su sakin fuska da son mutane. Tunda suka dora kawunansu saman cinyata babu wadda ta dago sai da suka ji muryar Babansu tukkuna. Tare suka fito da Momin kallo daya na yi mata gabobin jikina suka shika wata irin rama ta yi mai ban tsoro kanta yana nema ya rinjayi gangar jikinta abinka dama da siririya idanuwanta sun yi kuru-kuru ta d'ashe k'warai da gaske ta yi fau, babu shakka babu k'arya a cikin lalurarta yadda mijinta ya dinga jadadda ciwon ya ci karfinta yanzu na sake gazgata kammaninta duka sun canza ta hadu da ciwuka masu hatsarin gaske sugar da hawan jini. Ta zauna tare da taimakonsa suka zauna kujera d'aya yana dan gyara mata 'kafafunta ko daga inda nake zaune Ina kallon yadda jikinta yake rawa. Ban ji haushinsa ba ko kad'an domin a yanzu dai babu maganar kishi ga matar da take cikin irin wannan yanayin na halin ciwo mai tsanani. Ta dinga fara'a a zahiri tana nuna jin dadinta. Muka gaisa cikin kulawa da mutunci. Na yi mata sannu da jiki haka zalika ma baba Tabawa ta dubata sosai. Ta dinga dariya ganin yadda twin's suka yi mini farincikinta ya kasa 'boyuwa ta ce." Ai maigidan yake gaya mini ba ku ji labarin na kwanta a asibiti ba, ku yi hakuri don Allah da yake ni kaina lokacin ba ni hayyacina sai da na kwana na yini tukkuna na fara gane wanda yake kaina. Ko da na tambayi Nusaiba da Nabila shin an sanar daku suka ce mini eh sun sanar daku halin da ake ciki, na gode sosai Amina Allah Ya bar zumunci." Cikin nutsuwa da kulawa na ce." Allah Ya sawwa'ke yasa kaffara ne amma maganar gaskiya babu wanda ya gaya mana cewa baki da lafiya balle mu ji cewa kin kwanta a asibiti na tsayin wannan kwanakin." Na yi shiru Ina mayar da numfashi kafin na cigaba da cewa." Tabbas da mun sani me zai hana mu zuwa asibiti mu duba ki, babu niyyar wulakanci ko kuma nuna wariya a tsakaninmu dake kuma ciwo ake ce kin ga kuwa lalura ta kori komai, Ubangiji Allah Ya sawwa'ke, Hauwa ta ce a duba ki da kyau kuma tana yi miki sannu da jiki itama kwana biyu da yake ta yi nauyi sosai ba ta jin dad'i ne." Yanayinta ya nuna alhini da damuwa a zahiri abinda ta nuna kenan. Sai ta gyad'a kanta a hankali ta ce." Babu komai Amina komai ya wuce kuma na ji sau'ki sosai wallahi sai dai rashin 'kwarin jikin da yake d'an damuna yanzu, a cewa da Hauwa ina amsawa Allah Ya raba lafiya." Na ce." Za ta ji in sha Allahu rabbi." Tun kafin mu yi sallama take yi mini godiya har sai da jikina ya mutu tsabar tausayin halin da take ciki. Mairo ita ta janye yaran ta tafi dasu tana yayyanka masu mangwaron da tun farkon shigowarmu suke he rigima a kansa....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *2k ON TALGRAM* *VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *V-VIP AREWAPEN* *Wsp Gruop 1k* *103* Duk abinda muke yi bai ce mana komai ba, mun dai gaisa amma tun bayan gaisuwar bai sake magana ba, sa'i da lokaci dai yakan amsa waya idan an kira shi. Misalin takwas da wani abu muka fito daga gidan tun a hanya muke alhinin yanayin da muka risketa Baba Tabawa dai kasa daurewa ta yi a hanyarmu ta shiga gida ta fashe da kuka da sauri tasa gefan jihabinta ta rufe fuskarta . To ni ma dai kukan zucci nake yi domin na shiga rud'ani ba karami ba ganin yadda Allah Ya mayar da baiwarsa. Idan kudi na sayan lafiya nasan da ba wannan maganar ake yi ba. Wannan da duniya ta yi mata sheda cewa mutuniyar kirki ce wadda tun a duniya mijinta ya ce ya yafe mata itace cikin irin wannan yanayi to ina ga wanda ya shure umarnin Ubangiji kuma, Ubangiji Allah kasa mu dace Amin. A haka muka shiga gidan Hauwa na kwance saman kujera 3str tana kallo abinta. Ganinmu sukuku ya sanya ta tashi zaune tana tambayar lafiya. A takaice na ce." Lafiya lau." Na shige d'aki domin yadda kafafuna ke rawa ba zan iya tsayuwa a wurin ba. Na zauna gefan gado tare da rafka tagumi wani abu ne ya zo ya tsaya mini a wuya na tsananin fargaba da tashin hankali mace ta koma sai kace mai cutar kanjamau! ko mai farfadiya sai an rirriketa. Hawaye suka fara sauka a kumatuna. Haka kawai na ji duniyar ta fice mini daga raina gabad'aya. Shigowarta ya sanya na daga kaina na dube ta. Ta zauna gefana babu babu fallasa ta ce." Ashe kema kukan ki ke yi Amina." Sai ta sa dariya kafin ta cigaba da cewa." ga Baba Tabawa can ma tana yin nata, ni kam matar nan ko dame take yawo wallahil-azim kurwata tafi tata d'aci, wallahi ni zan yi maganinta." Na gyada kaina ina ko'karin ture kutittiran abinda ya tsaya mini a wuya na ce." Hauwa k'ullaci da tsananta gaba da k'iyayya wallahi babu inda zai kai ki sai tashar dana sani. Matar nan dai duk rashin Imanin mutum ya ga halin da take ciki sai ya tausayata mata don Allah mu dinga sassautawa kanmu Hauwa." Ta ja tsaki tare da furta."lalura fa kowa yin ta yake yi, wallahi na fita jin jiki, ni mai yasa ban lanjare ba, saboda ba ni da hakkin kowa a kaina, ita kuwa bari na gaya miki abinda ta shuka ne take girba tun a duniya hakkin mutane ne wallahi." Na jima ina kallonta tare da auna maganganunta. Yadda take tabbatar da abinda ba ta da tabbas akai shine abinda ya fi daga mini hankali da lamarinta. Wace irin kiyayyace wannan. A ganina wannan abin da take yi jahilci ne tsantsa da rashin sanin abinda ya dace. To ba ni da bakin magana domin kuwa yadda ta yi nisa irin haka babu wani kalami da zan yi mata ya sanya ta sassauto daga irin kiyayyar da take yi wa matar nan wadda alherenta suke dabaibaye damu bakidaya. Ganin ban ce mata komai ba ya sanya ta tashi tana fad'in." Matsantawa kai ne kawai kowa ya kashe wutar gabansa. Shi kuma ai hakkin rai tun a duniya Ubangiji yake fitar da shi wallahi tallahi yanzu ta fara gani. Sai kawai na saki bakina ina kallonta har ta fice daga d'akin ban d'auke idona ba. Na jima a zaune Ina tufkewa da warwarewa kafin na tashi jiki a sabule na shiga bandaki domin watsa ruwa a jikina. Gabad'aya cikina ya cushe babu dandano a bakina ko kad'an yunwar ma sam ba na jin ta, daga zarar na tuna halin da muka riski matar nan a ciki sai hankalina ya tashi. A haka na shirya cikin kayan bacci ina tsaye gaban madubi ina busar da gashin kaina. Ya turo kofar d'akin ya shigo. Ban yi zaton shigowarsa ba. Muka had'a Ido ya nufo wurin da nake tsaye daf da ni ya tsaya na gama abinda nake yi yana ta kallona ta madubi na juyo kirjinmu ya hadu waje daya. Kusan a tare muka sauke ajiyar zuciya. Ya riko hannuna muka zauna gefan gado. Yanayin fuskarsa kadai shi ya nuna mini cewar ya ji dadin abinda na yi. Ya furta." Kin kyauta sosai kuma na ji dadin abinda ki ka yi, idan haka kuke yi mini kara akan abinda nake so mai zai sanya ni ma na 'bata muku ai babu abinda ya fi zaman lafiya dadi ko." Kanzil ban ce masa ba. amma maganarsa ta d'an dake ni wato shi baya jin nauyin gaya mana irin son da yake yi wa matar nan tasa. Ya d'ora hannunsa a tudun kirjina wanda tun zaman da muke yi a wurin hankalinsa yake kai. Ya nisa kafin a kasalance ya furta." Momi ba ta da lafiya Amina cikinta da wajenta wallahi, tausayinta nake ji sosai domin lalurai sun gama dabaibayeta." A nutse na furta." Allah Ya yaye mata, da sauran al'ummar musulmi." Ya amsa da Amin kafin ya dora da cewar." Kin san yanzu wani result din ya sake fitowa bayan gwajin da aka yi mata satin da ya wuce cancer bakin mahaifa." Da saurin gaske na dube shi. Ya gyada kansa "Wallahi ni kaina na kad'u Amina na tausaya mata k'warai da aniya yanzu haka za mu yi booking domin zuwa india akwai kwararrun likitoci a can da za su caje mini ita sosai." Jiki a masifar sanyaye na furta." Tabbas Ubangiji shi yake saukar da ciwo ya kuma saukar da maganinsa, ina yi mata fatan alheri tare da addu'ar samun lafiya madawamiya, kai kuma Allah Ya baka ladan jinya." Ya sake amsa da "Amin Ya Allah." D'akin ya d'auki shiru har yanzu hannunsa na saman kirjina yana dan tattabawa. Ban hana shi ba kawai dai ina mamakinsa ne a ganina yanayin alhinin da yake ciki da damuwa akan rashin lafiyar maid'akinsa bai kamata a ce wani abu na jin dad'in duniya yana bijiro masa ba, to mai ma zai fahimta bayan yana cikin tashin hankali a haukana fa kenan Na dube shi yana lumshe idonsa kamar wanda ya samu audiga na dan ture hannun nasa muka kalli juna a sa'rke na ce." Dama ina son magana da kai." Kai tsaye ya furta." Idan har akan zuwa maiduguri ne to kada ki bata bakinki babu inda zakije.... Na kudi ne littafin don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Na ce." To saboda me, kafi kowa sanin matsayin anti Yagana a wurina ko?" Ya gyad'a kansa a tsanake ya ce." Da dai ban rantse ba ne sai na bari ki je, amma wallahi na riga na rantse ki yi hakuri bayan bikin sai ki je ki ga d'akin amarya." Zuciyata ta dinga tiriri na dinga danne abinda yake yun'kuro mini domin ba ni son na nuna masa damuwata a kan haka a gaba ya samu abinda zai k'untata mini idan wata matsalar ta faru a tsakaninmu. Na gyada kaina tare da furta." Shikkenan mu ajiye wannan maganar ina so ka gaya mini matsayin zamanka da Hauwa a gidan nan, domin ni har yanzu na kasa gane abinda kuke nufi da kai da ita." Ya dube ni sosai kafin ya ce." Ke ina ruwanki kuma?" Na ce." Ni ce kuwa nake da ruwa tunda duk wata mas'ala da kuka samu da kai da ita a kaina ne, yanzu a matsayinka na babba mai hankali da jagoranci abinda kuke aikatawa daidai ne." Ya ce." Ai taki ta amince da cewar ta yi lefi, sannan taki ta bi umarinina idan tana so magana ta shige mai yasa bata biyo ki zuwa duba Momi ba. Ta cigaba da zama a haka duk ranar da ta gaji sai ta nemawa kanta mafita." "Gaskiya hakan ba daidai ba." Ya 'bata rai yana fad'in." To nuna mini daidai Amina." Shiru na yi ban sake magana ba. Ya ja tsaki yana fad'in." Na yabe ki sallah za ki kasa alwala, Hauwa ai ba yarinya ba ce idan tana son zama da ni ta ba ni ha'kuri ta kuma bi umarina." Na ce." To ai kaine babba ha'kurinka shine zai fi rinjaye." "Na yi iya wanda naga zan iya yi a kanta Amina, wannan ya zama na farko ya kuma zama na karshe, kada ki sake titsiyeni akan lamarin Hauwa ko ni din sa'anki ne?" Shiru kawai na yi Ina kallonsa. Ya cigaba da ce wa." Dangane da maganar kwanan aure kin ga Momi bata da lafiya ya kike ganin za a yi?" Na ce." Yadda muke yi mana." Sai ya yi shiru yana tunani kafin daga bisani ya furta." Shikkenan sai a cigaba da tafiya a hakan, zan kwana biyu ban koma legos ba, domin idan na kai ta asibitin na dawo zan dan jinyaceta." Uffan ban ce masa ba, ya tashi tsaye yana kallona cikin sigar kulawa ya furta." Ki same ni a sama zan shiga in yi wanka." Ban iya ce masa komai ba har ya fita daga d'akin Ina zaune zuciyata ta kasa tsayuwa wuri d'aya. A daran na gurzu a hannunsa k'warai da gaske kamar wata sabuwar amarya sai da na yi ruwan d'umi domin kusan sau uku ya yi mu'amula da ni. Farkon dare da asuba bayan ya dawo daga sallah. Still Yana gama breakfast nan ma ya sake yin wani haka na sauko daga saman a galabaice. Na yini ciye ciyen kayan da zasu saukar mini da ni'ima domin na tabbatar da cewar a wannan daran ma ba zai daga mini kafa ba.. *** Bayan kwana biyu da misalin biyar na yammar ranar talata muka yi ba'kuwa a gidan. Hajiya Aziza sunanta matar abokinsu ce Alhaji Sulaiman duk dai abotar tafi karfi tsakaninsa da Alhaji Amadu mai rasuwa dalili shi da girmansu suka hadu ba abotar kuruciya ba ce. Sai bayan rasuwarsa tukkuna abotar ta maye gurbi akan shi da yake ba ni labari. Uwargidansa ce kuma tare suke da maigidan sun zo duba jikin Momi ne tunda ko bayan rasuwar Alhaji Amadun suna yin zumunci dalilin da ya sanya ma kenan Alhaji Sulaiman din yake binbinin abotartasu ta yi karko kamar yadda ta yi da Alhaji Amadun. Shigowarta kenan ya kira wayata ya yi mini wannan bayanin wai ta ce za ta shigo ta gaishe mu kafin su tafi yanzu shi suna tare da maigidan nata a can gidan Momin. Na ce masa in sha Allahu babu matsala. Sosai na marabceta na sanya Baba Tabawa ta kawo mata abinci tana fad'in a 'koshe take ta ci abinci kafin ta fito nace ta daure ta sanya mini albarka. Hauwa ta fito suka gaisa sama-sama cikin rashin sakewa ta koma dakinta. Na kira Baba Tabawa domin ta zo ta kwashe kayan abincin da ta jera wanda kad'an ta ci daga ciki. Duk da babu sabo a tsakaninmu amma na lura tana da kirki kuma ta girme mu gaskiya zata iya yin sa'a da Momin ina tambayarta yara ta ce suna nan lafiya biyu suna d'akin mazajensu kenan ta auran da yara biyu akwai hud'u a gida uku maza sai 'yar autarsu mace. Su uku ne a wurin maigidan ita ce Uwargida. Ta ce." Ai na ga yaran a can gidan Hajiya Maryam twins sun yi wayo sosai sun zama 'yan mata, Ubangiji Allah Ya yi musu albarka." Na amsa da amin Ya Allah, ai kam duk sun yi wayo." Ta gyada kanta da d'an murmushi a fuskarta kamar wadda aka tsikara ta ce." Allah dai ya sawwa'ke abinda ba zai shige ba ni Hajiya Aziza." Kallonta na yi ban ce komai ba. Ta sake yin murmushi kafin ta ce wani abu kira ya shigo wayarta tana d'agawa na ji tana fad'in." Halisa har na fito ma daga gidan, a alhamdulillahi jikin nata da sauki wallahi, eh na gaya mata sa'konki ta ce ta gode." Ta yi shiru tana sauraranta kafin ta ce." To ya za a yi lalura aka ce fa Halisa kin kyauta ai Allah ma yana son masu wannan zuciyar irin taki Ubangiji Allah Ya sa mu fi karfin zuciyarmu." Daga can ta amsa da Amin kafin su yi sallama da juna ta dube ni tana fad'in." 'Kanwata ce Halisa.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *2K ON TALGRAM.* *VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *104* *Whasap Gruop 1K* Na ce."Allah sarki a takaice ina d'an wani nazari a zuciyata sai na ji maganarta tana fad'in." Halisa k'anwata ce cikinmu daya ai da da rabo kuma Allah Ya yi wa Alhaji Amadu tsayin rayuwa suna tare da Maryam din domin kuwa sun yi soyayya k'warai kuma har iyaye suka shiga maganar har da yarjejeniyar aure a tsakani domin sadaki ne kawai bai biya ba lamarin ya rushe. Shiru na yi ban ce mata komai ba. Ganin haka ya sanya ta cigaba da ce wa." Alhaji Amadu ya so Halisa sosai kuma ya yi mata hidima k'warai farko a gidana suka had'u ya nuna yana sonta sanin halin tsananin kishin matarsa ya sanya da maigidanmu yake sanar mini da buk'atar abokinsa na ce a a gaskiya dalili na farko Maryam k'awata ce muna zumunci sosai saboda abotar mazajenmu. Duk da ba mu zaune a gari daya amma muna ziyartar junanmu sa'i da lokaci kuma muna yin zumunci ta waya bayan haka kuma tsaye take a kan yarana kamar yadda ni ma nake tsaye akan yaranta. Shiyasa ban yi mamakin ganin yaranku a gidanta ba domin zahiri macace mai son yara da gaske da hidima su. Da yake 'yar kasuwa ce mai zafin nema ba zan manta ba tasha yi mini fad'a sosai idan muka hadu tana fad'in ko ba zan nemi kudi don yarana ba dalilin ubansuya tara musu na tashi na nema domin iyaye da 'yan uwa da kuma gajiyayyu. A duk lokacin da wani abu ya fito na ya yi muddin ta yi odarsa to kamar yadda za ta d'ibarwa Nusaiba kaya haka zata d'ibarwa Asiya da Madina kaya irin na yarinyarta babu bambamci ko kad'an. Sosai take yi mini kara akan komai ni kaina na sheda tana da kyauta da kirki daidai gwargwado Maryam duk wanda ya ra'be ta zai dandali arzikinta. Sai dai kin san an ce d'an Adam tara yake bai cika goma ba nasan dai tuntuni Maryam ba ta son kishiya tasha gaya mini a rayuwarta abinda tafi tsana kenan dalilin da ya sanya lokacin da maigidanmu zai 'kara aure ta dinga ba ni shawarwarin yi masa tutsu da wasu dai shawarwarin da nake ganin za su iya kaini ga halaka. Lokacin na tsananta da addu'a sosai domin mu gaskiya gidanmu gidan malamai ne Amina ba mu ta so mun ga iyayenmu na yawon bin malamai ba. Addu'a dai da yin nafilar tsakiyar dare ita iyayenmu suka koya mana tare da azkar a duk lokacin da wata matsala ta tunkaro mana. Gaskiya ban yarda na bi sharwarin da take ba ni ba na dai dage da addu'a sosai akan idan auran da mijina zai yi akwai alheri ina rokan Allah Ya hada ni da abokiyar zama tagari dalili tunda?a na ta so gidanmu mata hud'u ne a ciki kuma mahaifinmu tsayayye ne da wuya ma a cikinmu wata ta kaso auranta ta dawo masa gida da zumar yin zawarci daidai gwargwado mun samu kula da tarbiya. Sosai Alhaji Amadu ya makance da soyayyar Halisa ya zama duk bayan sati biyu daga nan abuja sai ya je Jigawa gidanmu hira wurin Halisa a lokacin itama bai kwanta mata a rai ba ta zo tana gaya mini abinda yake faruwa ni lokacin ma ban san yana zuwa zance ba tunda mun gama magana da Babansu Madina akan zai gaya masa cewa ta tsayar da wanda zata zaura kuma gaskiya ne akwai wanda suke soyayya a lokacin sai dai bai kai ga turowa ba, Amma dai gidanmu sun san da maganar mahaifinmu ma sun yi magana da mahaifinsa akan hakan. Na dinga mamaki sosai sai dana tambayi Babansu Madina akan mai yasa bai gaya masa ba sai yace ya gaya masa ya'ki ha'kura ya ce tunda har yanzu shi wancan din bai fito ba shi ba zai janye ba. Na kira ta zo na ce da ita duk lokacin da ya sake zuwa kada ta fito ta yi masa kora da hali domin a gaskiya ba ni son abinda za a yi shi daga baya rai yana b'aci Muna mu'amula da Maryam sosai a tsukin na tabbatar da cewar ba ta san abinda yake faruwa ba, kuma ba na son abinda zai ta'ba zumuncinmu. Idan lallai ya zama dole mijinta ya kara aure to ya nema a wani wurin amma ba daga b'angarena ba. Sati uku da yin wannan maganar ta sake zuwa gidana tana kuka sosai ta ce mini ya sake zuwa kuma Babanmu ya saurare shi. Wata dabi'a ce ta mahaifinmu son bawa mai aure d'ansa. Ni kaina don dai lokacin da maigidan nan ya fito da niyyar aurena da gaske yake domin gabad'aya ya shigo da na tabbatar da cewa mai mata Babanmu zai bawa ni. tana gaya mini sun yi magana sosai da Babanmu har ya ce ya jira shi zai yi magana da iyayen Murtala saurayin da suke soyayya idan har da gaske yake yi to ya fito a cewarsa masu son auran da gaske suna fitowa ba za a ce za a zauna jiran wani lokaci ba. A lokacin shi Murtala din baya gari ya tafi can kudu Benin suna harkar gwangwani. Amma ya ce mata yana dawowa zai yi magana domin a zo a kawo kudin aure. Da ta gayawa Baban namu haka ya ce sai ya ji ta bakin mahaifin Murtala din tukkuna zai yanke hukunci. Dole ta ha'kura ta tsaya sauraransa. Lokacin Malam Shu'aibu bai rufe komai ba ya gayawa Babanmu cewa. Har yanzu Murtala ba shi da taku daya wanda idan ya yi aure zai ajiye iyalinsa. Can kudu (Benin) da yake zuwa tare da abokansa sana'a suke yi ta inada da 'karafuna da robobi, wannan shine amma tunda manemi ne arziki na Allah ne. Shi ba zai hana idan mijin aure ya fitowa yarinya ta yi auranta ba domin tauye hakki ne a ce mace ta zauna jiran namijin da bai zama lallai ya yi mata adalci a gaba ba, tunda da yawa hakan ta faru samari su yi alkawarin aure da budurwa su tafi neman kudi idan sun samo sun dawo gida sai su ga ai sun fi karfin ajin wannan budurwa da suka bari a gida. Wannan maganganun na Malam Shu'aibu maihaifin Murtala ya zaburar da Babanmu a cikin satin da Alhaji Amadu ya je gidan namu suka yi magana ya ce idan har da gaske yake kuma ya shirya auran ya turo magabantasa. A tak'aice dai Amina na gaya miki da ni da Halisa sai ji muka yi an kawo kudin auran dubu dari biyun shekarun baya mai d'anko. Kuka sosai Halisa ta zo gidana ta na yi mini kamar ranta zai fita tana fad'in ita kwata kwata bai yi mata ba tsoho ne. A lokacin da take wannan koke-koken babu abinda nake tunani sai yadda za ta zauna da Maryam domin na fi kowa sanin yadda ta k'yamaci kishiya a rayuwarta. Sosai na tausheta da rarrashi da ban baki har Babansu Madina ma da ya dawo ya sanya bakinsa yana ta kwarzanta mata nagartar abokin nasa yana fad'in ta kwantar da hankalinta ta yi mijin da za ta yi alfahari da shi. Muka rarrasheta sosai ta ha'kura kwanta uku a gidan namu da yake duk gari daya muke gidan iyayenmu na kazaure gidana kuma a dutse a kwana na hudun Alhaji Amadu ya zo gidan wata'kila ya je can gidanmu aka ce masa tana nan lokacin da rarrashi da ban baki na tursasa Halisa sauraran Alhaji Amadu suka dan jima a d'akin bakin maigidan suna hira kafin su yi sallama ya tafi ta shigo mini da kwalin waya sabuwa dal black berry mai kyau da tsada da kudi dubu hamsin wai kudin zance. Na taya murna sosai a lokacin na kuma bata sharwari akan ta dage da addu'a domin duk lamarin da Babanmu ya kar'be shi da hannu biyu to tabbas ya yi istahara a kai ya gano alherinsa don haka idan tace zata tayar da fitina za ta fita zakka a cikinmu tunda ba ita kadai aka ta'ba yi wa irin haka ba. Sannu hankali soyayyar Alhaji Amadu ta kar'bu a zuciyar Halisa yadda shi ma yake hidima da ita da gidanmu na tabbatar da cewa da gaske lallai auranta zai yi domin duk bayan sati biyu ko kwana goma yake zuwa wurinta har aka tsayar da maganar daurin auransu wata shida farkon watan maulidi. Abinda ya fi tsaya mini a raina dangane da al'amarin shine yadda mu'amulata da Maryam bata raunana ba na shiga mamaki sosai jikina kuma ya yi sanyi k'warai na tabbatar da cewar duk wannan abinda yake faruwa Maryam bata sani ba domin kuwa da ta sani dole zan ga canji daga wurinta dalili kuwa shine na fi kowa sanin abinda tafi kyama kenan kishiya. Na gayawa Babansu Madina cewa ni fa hankalina gabad'aya bai kwanta da neman auran nan ba, domin kuwa ina zargin abokinsa da munafurtar uwargidansa. Da ya tambayeni mai yasa nake zargin hakan na ce masa naga ko kad'an ban ga canji a wurinta ba muna zumunci sosai domin ma a satin da aka sanya ranar daurin auran ta aikowa da yara kaya kowanne set biyu da muka yi waya ta ce mini sabuwar order ce shine ta d'ibar musu. Shi kansa ya jinjina al'amarin sosai amma daga lokacin bai kara tayar da maganar ba ni ce dai abin ya dame ni a zuciyata domin sai nake ganin kamar duk ranar da ta san abinda yake faruwa za ta yi mini kallon munafuka ko kuma mai sonta kanta, ba kuma zata ta'ba yarda da cewa mijinta ne ya ga Halisa yace yana so ba za ta yi zargin cewa ni ce na had'a su. Wallahi na shiga damuwa sosai da sosai domin kuwa ga'barar da Alhaji Amadu ya d'auka ta neman auransa ba mai kyau ba ce a ganina yafi alheri ya fito ya gaya mata akan ya 'boye mata. Na kasance cikin zullumi da tunani a koyaushe nazarin da nake yi shine idan har Maryam ta samu labarin mijinta zai auri k'anwata wane kallo za ta yi mini. Katsam watarana na ga text message d'inta ina dubawa na ga ta rubuto mini Aziza na gode sosai ashe tsakanina dake ba zaman amana, kema kin boye mini abinda yake faruwa, na d'auka ni dake yanzu mun zama 'yan uwana na ji don kin gaya mini mijina na neman auran k'anwarki Halisa menene ko kin d'auka zan tsananta kishi a kanta, ai abin gudu a kishiya shine a d'auko maka kwarkwasa wadda ba ka san ni ba, amma ni kam na sheda halinki kuma ina fatan haka Halisa take da kyawawan halaye idan har da akwai alheri a zamana da ita Ubangiji Allah Ya kawota cikin gidana, ke kuma na gode da 'boye mini da ki ka yi." Jikina ya yi sanyi sosai da na gama karanta sakon data turo mini na zauna ina ta tunani da mamaki. Dama nasan tuntuni ba ta san abinda yake faruwa ba sai yanzu da daurin auran bai wuce wata biyu da kwanaki ba sannan ta samu labari. Hakika kowacce aka yi wa haka dole zuciyarta ta sosu Amma sai na dinga mamakin yadda ta sadada har ta samu damar yi mini text kuma cikin nutsuwa bata kalubance ni akan had'a baki muka yi da mijinta ba. Na kwana da tunanin hakan a raina sai da gari ya waye tukkuna na kira ta a waya ta daga babu jinkiri muka gaisa sosai cikin ko'karin kare kaina na fara yi mata bayanin abubuwan da suka faru tun farkon neman auran har zuwa yanzu. Ta dinga fad'in ai na d'auka ni dake babu rufi Aziza babban abinda ya ba ni haushi kenan yadda kike biye masa kema ki ka yi mini shiru wato sai dai kawai na ji an d'aura auran kenan kun yi mini adalci. Na shiga bata ha'kuri da tausarta Ina nuna mata cewar ban san ta yadda za a yi na iya tunkararta da maganar ba domin ni duk a tunani na mijinta ya gaya mata. Ta ce mini bai gaya mata ba ita ta fahimta da kanta yana neman aure da kuma ta yi bincike ta gane Halisa ce k'anwata. Yadda muka fahimci juna sosai a wayar ya sanya mini kwanciyar hankali da nutsuwa a zuciyata na amince da cewa Maryam ta sakko ta kuma yi na'am da cewa kishiya abokiyar zama ce kuma hukuncin ne na Allah....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: 🌲🌳🌿☘️ *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *2K ON TALGRAM.* *VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWA PEN* *07084653262* *105* Ta yi d'an murmushi tana fad'in." Kina mamakina daga zuwa na ishe ki da surutu ko Amina?" Ni ma murmushin na yi wanda babu nisha'di a cikinsa kuma cike nake da fargabar sauraran karshen labarinta dalili yanzu ni gabad'aya ba kasafai nake son abinda zai daga mini hankalina ba. Ta nisa kafin ta sauke zazzafar ajiyar zuciya ta sunkuyar da kanta kasa tana dan yi wani murmushi irin mai ciwon nan ta cigaba da cewa." Muka cigaba da mu'amula da Maryam cikin fahimtar juna tunda ni tsakanina da Allah ban d'auka cewa ta 'kullaci wani abun a cikin ranta ba ganin yadda ta nuna mini a lokacin da ta samu labari. Sai da bikin ya rage sati bakwai daga bangaranmu nuna ta shirye-shirye. Halisa ta zo tana gaya mini cewa Alhaji Amadu ya kwana biyu bai zo ba kuma kiran wayar ma da yake yi ya jima bai yi ba. Sai nace mata wata'kila akwai dalili domin mutum ne shi mai sabgogi kada ta damu zai kira ta a waya kuma zai zo ai tunda bikin ma ya matso dole abubuwa su yi masa yawa. Da wannan na kwantar mata da hankali ta tafi gida. Abubuwa suka 'kara mikawa mu nan mun dage da shirin biki ango ya d'auke kafarsa ya daina zuwa ko ta kira wayarsa bata shiga. A lokacin ne hankalina ya fara tashi abubuwa da yawa suka fara dawo mini na farko yadda a can garin namu da sauran wad'anda ba su son auran ke ta surutun cewa Babanmu kudi ya duba ya d'auki Halisa ya bayar da ita ga tsoho bayan ga saurayinta da suka jima suna soyayya dan bashi da kudi aka hana shi. Na biyu kuma yadda lamarin auran yake kwan gaba kwan baya ta bangaran angon. Na sanar da Babansu Madina halin da yake ciki, sai yake gaya mini ai baya ma k'asar tsayin sati uku ya yi tafiya zuwa chaina. Na ce ai da sai ya gaya mata tunda ya san halin da ake ciki Muna nan muna shiri. Sai ya ce mini kada mu damu domin sun yi magana dashi kafin ya tafi daga zarar ya dawo za a kawo lefe da sadaki a dauran aure. Jin haka daga bakin Babansu Madina sai hankali ya kwanta na kira ta a waya na gaya mata tare da sake kwantar mata da hankali. To bayan kwana shida da maganarmu da Babansu Madina yake gaya mini ai sun yi waya dashi ya gaya masa ya dawo a jira shi zai turo in sha Allahu. Hankalina ya sake kwanciya sosai gefe guda kuma dangantarmu da Maryam na sake yin karfi sosai domin babu wani abu da ya raunana kamar koyaushe sa'i da lokaci idan za ta gudanar da wani abu da ya danganceta mussaman akan kasuwancinta ko 'yan uwanta takan kira ni a waya ta nemi shawarata ni kuma ina bata shawara mai kyau ni ma haka duk abinda ya dame ni ina neman hanyar da zan warware zan gaya mata idan ma har ta fahimci matsalata ta kudi ce ko ta wani abu wallahi sai dai naga ta turo mini ta bankina tunda tsakani da Allah ta fi ni k'arfin dukiya sannan mijinta ya fi Babansu Madina abokai ne dai sai dai kowa da yanayin karfinsa kuma suna taimakawa juna sosai Babansu Madina yana da tasa dukiyar daidai gwargwado amma bai kai Alhaji Amadun ba. To cikin ikon Allah satikan da suka rage na wa'adin da iyaye suka d'auka a matsayin lokacin daurin aure suka shude babu labarin Alhaji Amadu babu aikensa kamar yadda ya fad'a gabad'aya ya ba'ce bat ya d'auke 'kafarsa baya zuwa haka zalika baya kiran wayarta. Hankalin dangi ya tashi domin a tarihin gidanmu ba a ta'ba sanyawa budurwa rana an d'aga ba. Mahaifinmu ya ce na sanar da abokinsa yana nufin Babansu Madina na gaya masa halin da ake ciki. Na ce duk abinda yake faruwa ya sani sai dai na sake tuna masa. Koda na gaya masa sakon Babanmu sai da raina ya baci domin maganar da yaga mini akan lamarin ta 'bata mini rai wai Alhaji Amadu ba yaro ba ne shine ya ga Halisa ya ce yana son auranta idan kuma yanzu ya janye ma'ana ya fasa sai a kyale shi yarinya ta samu wani ta aura. Muka dinga musayar yawu da shi a daran har sai da na yi kuka saboda b'akinciki dalili shi ma na lura yana so ya goyi da bayan abokinsa ne, duk wannan hanya hanyar da suke yi mana suna so su tozartamu ne. Ana cikin wannan tashin hankalin Halisa ta fara ciwo a tsayayye da farko da ciwon kai ta fara ba zan manta ba ni na kaita asibiti aka bata magani na mayar da ita gida. Kwana biyu Mamanmu ta kira ni da wayar Halisan take gaya mini tunda suka tashi da ita a ranar tana kwance a shimfida ta kasa tashi an yi an yi ta mike tsaye ta kasa amma tana magana. Ban kawo abu mai razanarwa ba a cikin raina na ce ta bata wayar mu yi magana ta kar'ba muka gaisa nake tambayarta yanayin jikinta ta ce mini kan nata da sauki sai dai ta yi ta yi ta tashi tayi tafiya ta kasa taka kafafunta baya ga haka kuwa babu abinda yake yi mata ciwo. Na ce wa Mamamu su kaita asibiti gobe da safe ta ce mini sai abinda maigidan yace tukkuna tana nufin Babanmu. Haka muka yi sallama cike da damuwa da tashin hankali. A dai ranar Maryam ta kira ni a waya take ce mini ta saya mana wani swiss lece da za mu yi fitar biki da shi ni da ita za ta bayar dinkw mana a can abujan. Na yi kokari sosai wurin danne damuwata na yi mata godiya ban nuna mata halin da ake ciki ba. Mun d'an ta'ba hira a takaice kafin mu yi sallama. da Babansu Madina ya dawo na gaya masa cewa Halisa fa babu lafiya domin dai ni yini na yi da abin a raina daga ciwon kai sai ace an kasa tafiya. Ganin shine yake kiran wayar abokin nasa kai tsaye ta shiga ya sanya na ce ya gaya masa Halisa babu lafiya ga abinda yake damunta. Ya ce mini shikkenan zai gaya masa. Washe gari na kira waya domin tambayar halin da yarinyar take ciki abun babu dadi domin ihunta ne ma ya fara yi mini sallama a kunnena. Sai da Mamanmu ta bar wurin take gaya mini tun daran jiya take buge-buge tare da ihu! yanzu haka ma kafafunta sun nannad'e jan jiki take yi kuma a yinin ranar ta yi fitsari ya fi sau d'ari abu ne yake zuba daga gabanta kamar fitsari kamar kuma wata najasar. Kuka na kama yi ina kiran sunan Allah. Na kashe wayar ban jira koma ba na zura hijabina na fito daidai lokacin Babansu Madina ya fito daga sashen abokiyar zamana zai fita ganina a hargitse ina kuka ya tayar masa da hankali ya rike ni yana tambayata. Ina kuka nake gaya masa halin da Halisa take ciki. Shima hankalinsa ya tashi kwarai da gaske ya ce maza na shiga mota muje gidan. Wallahi Amina na shiga rud'ani da tsananin rikici a lokacin da naga yadda kammanin Halisa suka sauya gurguwa fa ta zama sosai cikin kwana biyu kacal d'akin da take sai zarni yake yi da karni-karni tana bacci a zaune kafafu a shanye ta yi wata iriyar rama. Kuka dai a gidan namu kamar ana zaman makoki domin ba mu ta'ba ganin irin wannan tashin hankalin ba. Shi kansa Babansu Madina yana ganin haka ya ce shafar aljanu ne abinda kowa yake ta fad'a kenan. Kaf gidanmu mu ashirin da hud'u Babanmu ya haifa mata da maza babu wanda ya ta'ba nuna alamun iska jinnu tundaga kuruciya har zuwa girma sai yanzu. Kowa ya dinga tofa albarkacin bakinsa wasu na fad'in wata'kila gamo tayi da su, wasu na fad'in ko ture aka yi wa Babanmu tunda yana harkar malunta ko sun dawo masa ne. Shi Kuma ya ce kafin ya fara harkar malunta sai da ya kafe kansa da gidansa da iyalinsa bai yadda akwai wata iska da za ta cutar da shi ba sai dai idan turo ta aka yi. Amina in takaice miki labari wallahi mun sha wahala sosai da Halisa sai da ta kai ta kawo Babanmu ya had'a da wasu Malaman domin kuwa ba'kar iskar da aka had'a Halisa da ita mugwaye tafiya suke yi su dawo kuma sun ki yadda su yi magana abinda zai tsorataki kuwa shine yadda suke tsotse mata jini a lokacin abinka da mace mai garin jiki wallahi ta komade sai 'kashi da jijiiya duk sun kad'e mata gashin kanta. Duk abinda aka yi Alhaji Amadu bai zo ba kuma Babansu Madina ya tabbatar mini da cewa ya gaya masa ke da aka tsananta ma sai ya kawai ya fito ya gayawa Babansu Madina cewa ya sanar da Babanmu cewa ya janye duk abinda ya kawo da zummar auran Halisa ya bar mata. Ni kuka Mamanmu kuka saboda tsabar b'akinciki da takaici. Ya fasa auranta ga matarsa ta yi wa yarinya makaru(asiri) ta had'ata da iskokai masu mugunta sun nakasata. Ni nasan Maryam ce da wannan aikin ban fito na fad'a ba amma da yawa kowa abinda yake cewa kenan Maryam ce ta yi mata asiri saboda kada ta auri mijinta. Wasu sun gazgata hakan wasu kuma suna fad'in kada a d'auki alhakinta jarrabawa ce kawai daga Allah. Kuma fa cikin wannan halin babu wata alama da Maryam ta nuna mini daga bangaranta muna yin waya sosai kuma tana yi mini aike kamar yadda ta saba amma ta daina yi mini maganar bikin ni ma kuma ban ce mata komai ba. Amina mun ci ba'kar wahala da Halisa kafin Allah Ya kawo k'arshen masifar a ka yi nasarar magana dasu dukansu arna ne su dari da d'aya. Ki ga aljanu arna dari har da daya aka d'ora su akan yarinya kamar Halisa. Sun fita da suka ji wahala sun ce yanka aka yi musu domin su shiga jikinta su wahalar da ita. Ba su fadi suna ba amma sun ce macace ta sanya su aikin. Aka ce wai ba a yadda da maganar jinnu ni dai kam Amina a wannan karon na yarda da maganarsu domin kuwa ko kaffara ba zan yi ba Maryam ce ta yi wa Halisa wannan turan. Tsayin wattani shida Halisa ta d'auka cikin jinyya sai da ta sake yin sama da wata shida kafin ta dawo hayyacinta domin kuwa ko da aka samu nasarar raba ta da su wallahi mun ci ba'kar wahala kafin ta daina firgita tafiya kuwa sai da aka dinga koya mata har yanzu kafarta ta hagu bata dawo daidai yadda take ba tana d'an janta a 'kasa. Da 'kyar ta mayar da jikinta gabad'aya dabi'unta kamar an canza mata su ta dawo shiru shiru mara son hayaniya da surutu kullum tana kwance a d'aki kana dai kallonta zaka tabbatar da cewa bata da ishshiyar lafiya. To alhamdulillahi tunda an yi nasarar rabata da su tana tafiya da k'afafunta tana kuma ibada ruwan najasar da suka sakar mata ya d'auke sai dai ta zama kamar kurma don sai ta yini ba ta yi magana muddin ba a yi mata ba hakan ba damuwarta ba ne. Allah ba yadda baya shirya lamarinsa kuma mun gode masa amma tun daga lokacin na janye jikina da Maryam kuma na tsorata sosai da abinda ta aikata akan umarnin Ubangiji tabbas za ta iya aikata komai akan abinda ranta baya so ashe duk alherinta da nake gani jama'a suke gani zata iya aikata wannan mummunan aikin akan son rai. Murtala ya sake dawo wa a karo na biyu domin auran Halisa Babanmu duk ya gaya masa abinda ya faru da halin da take ciki a yanzu ya ce ya ji ya gani zai aureta hakan mahafinsa ma ya ce dama matarsa ce shiyasa Allah Ya shirya hakan don haka a shirye suke wata uku kacal a ka sanya daidai gwargwado suka yi abinda al'ada ta ce a yi aka daura auran. Wallahi Amina washe garin ranar da muka kai Halisa gidan mijinta Murtala sai ga Hajiya Maryam a gidana da kaya kiriga guda wai gummuwa ce ta kawowa Halisa tunda ban gaya mata bikin ba ta ji labari ta zo yi mini Allah Ya sanya alheri.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *07084653262* Wallahi Amina duk yadda na so da ganin na sakar mata jiki kasawa na yi duk tsananin sabon kuwa da yake tsakaninmu sai ta dinga ba ni tsoro daga zarar na kalleta sai na tuna irin mawuyacin halin da Halisa ta shiga. Duk da zato zunubi ne amma tsakani da Allah kenan na fi gazgata cewa itace ta jefi Halisa ta kuma juyar da hankalin mijinta akan lamarin gabad'aya. Haka nan muka yini da ita kadaran kadahan domin hausawa suna cewa idan ba ka iya kama b'arawo ba shi sai ya kama ka shiyasa kawai na kyaleta ban iya ce mata komai akan lamarin ba tunda ai a duniya muke akwai kuma ranar tsayuwa idan har ita ta cutar da Halisa ta d'ora mata muguwar jinyya mai wahala ubangiji zai fitar da hakki. Muka rabu kowa zuciyarsa cike da tunani domin kuwa ko bata fito ta fad'a tabbas ta fahimci na canza mata ba kamar yadda muke a da can baya. Lokacin da na gayawa Babansu Madina zuwanta da kayan da ta kawowa Halisa da yara ya yi godiya kawai daga haka bai sake cewa komai ba Amina kin san su maza ba su yarda da irin wannan muddin ba gani suke yi a zahiri ba domin da farko da na gaya masa nuna zargin Maryam akan ciwon dake damun Halisa ya dinga fad'a yana cewa shikkenan lalura ba zata samu bawa sai a jingina hakan da wani mutuniyar kirki ce wadda ba ta da abokin fad'a sam baya tsammanin za ta aikata haka. Duk yadda na so na fahimtar da shi ya kasa fahimta nagartatta kawai yake fadi shi ma ya sheda ayyukan alherinta a zahiri. To sai kawai na kyale shi domin ba zai yarda ba zai ce muna neman tayar da fitina ko mu had'a shi da abokinsa. Tun daga ranar da ta zo taga sauyi a tare da ni sai ta janye jikinta itama. Amma ba gabad'aya sa'i da lokaci tana kirana a waya mu gaisa ko kuma na ga aike mussaman idan zata turo kaya garin nan to za ta had'o da sakon yara mai delivery ya kawo mini har gida. Duk shekara kuwa idan ta fitar da zakka tana turo mini ta ce na duba family din mu wanda suke da k'aramar sana'a na ba su domin su tashi da kafarsu. Wannan shine zan fad'a akan Maryam Amina amma ban ta'ba zarginta akan dukiyarta ba dalili nasan macace mai zafin nema mussaman a lokacin da iyayensu suka rasu ya kasance girma ya hau kanta duk itace take tsaye a kan 'yan uwanta kuma mijinta ya tsaya mata sosai har ta kafu kwarai ta tsaya da k'afafunta ko a lokacin da muke mu'amula sosai nasan tana da manyan shaguna uku daya a garinsu biyu a garin Abuja. Amma yanzu labarin da nake ji a tsakanin matan abokan mijinmu ta mallaki wurare da yawa a rassa daban daban da ake mata hurd'a ta kasuwanci. Lokacin da na samu labarin auranta da Alhaji Tajo na yi mamaki sosai ya aka yi ta amince da zama dashi a matsayin ma'aurata bayan yana da iyali ita kuma da bata son kishiya. Sai babansu Madina yake gaya mini wasiyyar da Alhaji Amadu ya bari kenan amma ba zan boye miki ba wallahi na shiga tashin hankali ganin da na yi mata a yau sai na ji gabad'aya duniyar ta fice mini daga rai lallai d'an Adam ba a bakin komai yake ba. Dama na sanar da Halisa kafin mu zo shine fa ta ce idan har na zo na ce tana gaisheta da sannu da jiki wallahi lokacin da nake gaya mata sakon Halisan sai hawaye shaaa suka sauka a kumatunta har na yi danasanin gaya mata ta ba ni tausayi sosai lallai Allah ya jarrabeta da ciwo mai wahala muna ro'kon Allah Ya bata lafiya ya kuma yafe mata kuskuranta." Ajiyar zuciya na saki a hankali na ce." Amin suma Amin, muna nema mata afuwa da sasaauci wurin Allah, ai d'an adam sai dai idan ba hallice shi a duniya ba Hajiya amma tunda annabawan Allah suka kuskurewa Ubangiji kowane bawa ba zai tsallake ba, sai dai mu yi addu'a akan Allah Ya sa kada son zuciya ya sanya mu cutar da wani tabbas ban so jin wannan labarin ba wallahi ba zan boye miki ba hankalina ya tashi amma komai dalili yake yi. Momi ta aikata abu mafi muni shirka shine had'a Allah da waninsa cutar da wanda bai ji ba kuma bai gani ba. Idan na ce miki ta yi mana wani abu mai razanarwa na yi mata sharri domin ni dai a zamana da ita ban hangi wani babban lamari kwatankwancin na Halisa ba. Kamar yadda kika fad'a macace mai alheri domin ta ri'ke mini yarana da ubansu ya rasu don 'karamin ma ya fi shekara shida a hannunta babban ne bai wani jima ba wani dalili ya katse zamansu a hannunta. Idan kin ce ta gwanance wurin kissa da kisan mummk'e wannan zan bada sheda akan haka domin halin da muke ciki kenan da ita koda take kwancen nan maigidan hankalinsa yana wurinta kuma tsayin zamansu gaskiya bai ta'ba kawo mana wani korafi ko aibu a kanta ba asalima boye sirrinta yake yi ko fad'a suka yi ba ma ganewa. Gabad'aya ya za'be ta ya fifita akanmu. Kuma kin ga ni dai a zahiri mun fita kuruciya da komad'a amma wallahi a kanta ko 'ya'yanta sai ran kowa ya 'baci a gidan nan. Ni matsalata da ita kenan. Amma ta fanni asiri ni ban yi imani da cewa jifanta zai yi tasiri a jikina ba koda tana yi din wallahi ba a zaune nake ba nima ina ko'karin kare kaina da addu'a da neman tsari. Ban 'ki ba shi maigidan domin a wasu lukutan abubuwan da yake yi kamar mai rangwamin hankali. Amma duk ba wannan ba yanzu ta lafiyarta ake yi domin sai da lafiya ake komai. Duk abinda muke zargi ko hasashe a kanta idan har tana aikatawa muna roka mata gafara daga wajan Allah mu ma ba mu wuce mu tsinci kanmu akan hanyar da ta bi ba ba mu da wayo ko dubara sai ta Allah. Allah ya yafe mata da mu bakidaya." Ta amsa da Amin Ya hayyu ya 'kayyymu, ai in banda na zo na ga halin da take ciki hankalina ya tashi wallahi babu wani dalilin da zai sanya na tashi maganar nan in banda yanzu kin ji babu wanda na ta'ba zama da shi na gaya masa sai dai zargi da hasashe da mutane suke yi a kanta, sannan da wasu maganganu da na ji ana yi a kan ku wai kun had'e mata kai ba ku sanyata a cikinku kun wareta kin san maganar duniya bata 'buya shine fa abin ya ba ni mamaki cikin zuciyata nake fad'in yadda nasan Maryam da wayo da kissa anya za ku iya kai ta 'kasa kuwa." Da mamaki mai yawa na ce." A a wallahi ba mu ware ta ba sharri ne kawai irin na mutane amma ke don Allah a ina ki ka ji wannan maganar." Tana yar dariya ta furta." Wallahi a gari na ji ni ma shine nake ta mamakin Hakan saboda nasan Maryam ba zata ta'ba yarda ta yi boranci a tsakaninku ba." Na girgiza kaina da damuwa mai yawa na ce." Aikuwa masu fad'in haka sun d'auki hakkinmi ba mu ware Maryam ba wallahi, sharri ne kawai irin na mutane idan an ce babu jituwa a tsakaninmu na yarda amma babu maganar mun had'e mata kai ko mun ware ta." Ta ce." Allah Ya kyauta dai yanzu gashi Halisa yaranta hud'u fa a gidan Murtala shine ai nake cewa Allah ya tsine abinda ba zai wuce ba." Kafin na bud'e baki na yi magana suka shigo su biyu maigidan ne da mijin nata Alhaji Sulaiman. Sai yanzu na sheda fuskarsa lokacin haihuwar twins da ya shirya walima na gan shi ya zo da kuma lokacin d'aurin auransa da Momin na ga hotonsu a tare ashe shine. Suka iso wurin da muke zaune Alhaji Sulaiman din ya fad'in." Uwargida ta gidan Tajo ina 'yar uwar taki take ne?" Ina d'an ya'ke na ce." Hauwa tana ciki ba ta jima da tashi ba, ina yini ya hanya mun gode sosai fa." Ya ce." Ai ta ce za ta shigo ku gaisa ina can tsaye ina jiranta kusan minti talatin me kuka tattauna ne?" Ya kΓ rasa maganar da barkwanci sai na yi dariya ganin mutum ne shi mai raha ba irin abokin nasa ba na ce." Hira muke yi ta duniya idan kana so ku ji abinda muka tattauna sai ku gaya mana abinda kuma ku ka tattauna a waje." Sai kuwa ya fashe da dariya yana dukan kafadar abokin nasa kamar wani kurma yana tsaye yana kallonmu cikin dariyar dai ya ce." Ka ji fa mutumina to mu ai ba zai wuce sabgar kasuwanci muka tattauna ba ko ba haka ba ne?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." Ita fa kishi ne da ita shiyasa take bugun cikinka ko tana tunanin aure zan 'kara." Hajiya Aziza ta yi caraf ta ce." A haf yanzu gashi babu wanda ya matsa bakinka ka fad'a abinda yake zuciyarka kenan zaka kara aure tunda ya baka labarin yana neman cike gurbi ko." Yasa dariya yana cewa." Wallahi ya gaya mini kuma wai budurwa ko?'' Ta ce." Budurbazar dai ba budurwa." Sai suka fashe da dariya a tare. Na yi sakato da baki Ina kallonsa yadda yake ta kyalkyala dariya yana tambayar Hajiya Aziza wai menene budurbazar ita kuma tana ta jin haushi domin daka ga ni da gaske mijin nata auran zai yi kuma budurwa." Yana dariya ya dube ta yana fad'in." Ke in banda abinki ai abinda ake ya yi kenan kuma tsoho da kudinsa sai ya sha shagali ko ba haka ba ne mutumina." Alhaji Sulaiman yana gyara babbar rigarsa ya ce." 'Kwarai kuwa Alhaji to menene sunna ce fa mai karfi kuma iyayen yaran nan ma yanzu sun fi so su bawa irin mu aure." Na ce." Makwad'aitan iyaye ba, amma gaskiya kuna da budurwar zuciya kai fa har jikoki ne da ka, amma shine za ka d'auko musu magana." Maimakon maganata ta bashi haushi sai ma ta bashi dariya tunda na lura mayen dariya ne tunda ya shigo bakinsa a bud'e yake ya ce." To shine me? Amina daga kawai ina da jikoki uku sai aka ce na tsufa a ah ni yanzu ji na nake yi kalau da ni wallahi." "Um!" Kawai na ce na juyar da kaina gefe abin yana damuna. Ko dai Shima neman auran yake yi ne ganin ba a tambaye shi ba ya fallasa asirin zuciyarsa. Wata zuciyar ta ce mini a a hankalinsa fa yana kan matarsa ba ma shi da nutsuwar duba wata mace da sunan aure matarsa da yake tsananin so bata da lafiya. Anya wannan hasashen na zuciyata ya yi daidai kuwa. Na ji maganarta a tsakiyar kunnena tana fad'in. " Amina za mu gudu kuma ba ki ba ni lambar wayarki ba. Da sauri na dube ta sai na ganta a tsaye tana gyara jakarta dake rataye a kafadarta. Na mike tsaye da sauri ina fad'in." Har tafiyar ta tashi kenan, to mun gode sosai Ubangiji Allah Ya ba ku ladan ziyara da dubiya." Ta amsa da Amin tana miko mini wayarta. Na karba na sanya mata lambata ba don raina ya so ba dalili na fahimci tana da surutu idan ba haka ba mai zai sanya daga zuwanta babu wanda ya tambayeta ta fara zuba. Gabad'aya ma ni sai na ji zuwanta bai yi mini dadi ba na farko labarin da ta ba ni akan Momi ba wai na k'aryatata ko na gazgatata ba, nasan hakan na iya faruwa abin ya tsaye mini a rai ainun! sai kuma wannan wasan da ya kasance wanda suke daukarsa kamar barkwanci ni kuma abin ya d'an sosa mini rai wata'kila da gaske shima neman auran yake yi kuma budurwa tunda gashi abokinsa yana fad'a mutum da kudinsa kuma iyayen yara yanzu sun fi so su bawa mai aure yaransu a ganinsu za a fi kula da su. Iyakacin rakiyar da na yi musu bakin kofar falo lokacin ma dab ake da kiran magriba. Shi ya bi su a baya ni kuma na koma ciki kai tsaye d'akina na shiga na zauna gefan gado tare da tallafe ha'ba. Oh hasashen da ake ta yi akan matar nan yana nema ya zama gaskiya tabbas akwai abinda take yi ko ta sanya malamanta ke yi mata akan jama'a, ai 'yar kasuwa ce mai hurd'odi da yawa mafi akasari kuwa duk eani dan kasuwan da ya yi shura a duniya yana neman jama'a walau ta hanyar Allah ko ta hanyar halaka. Ni dai nasan ina tsananta rokona ga Allah akan ya kawo mini kasuwa da jama'a masu k'aunar abinda nake sayarwa ko a can baya ma da na dinga fafutukar tsayuwa da kafafuna addu'ata kenan Allah ka d'ora ni akan masu sayan kayana, Ubangiji Allah ka haskakani Allah ka ba ni nasibi da jalabi abinda nake roka kenan a wurin Allah ban ta'ba kauce hanya domin tara mutane ta kowace siga ba. Tabbas ana neman jama'a ana kuma karawa da farin jini da kwarjini babu shakka akwai daya daga cikin abu biyun nan da na fad'a tana yi ko kuma tana sanyawa a yi mata. Asirin mallaka kuma za ta iya yi masa tunda labari yazo akan cewa ba ta son kishiya idan ba mu fita ba to ita ta fita zakka a cikinmu ta zama mad'aukakiya a wurinsa. Wannan shine tunani na akanta. Bayan sallar Isha'i ya shigo ban ji ma da idar da sallah ba ina ma zaune saman daddumata da carbi mai lamba makale a hannuna. Sai da ya jira na kammala tukkuna muka shafa addu'a a tare ya ce." Abinci za ki ba ni yunwa nake ji wallahi tun safe rabona da abinci Amina." Ina ninke dadduma ban kalleshi ba na ce." Tun safe lallai da ka sani kawai ka d'auki azimi." Ya d'an riko gefan hijabin jikina cikin sigar tsokana ya furta." Idan na yi azimi ke kanki kin san gajiya nake yi da daddare ba ni iya aikata komai kuma yau na jarabtu dake." Ya'ke na yi ban ce komai ba. Ya sake janyo hijabin nawa a karo na biyu har sai da na yi tangal-tangal na ce." Menene hakane?" Ya cika gefan hijab din yana fad'in." Je ki kawo abincin mu yi magana." Ban ce komai ba na fita kai tsaye kicin din na nufa Baba Tabawa ta gama shirya komai jallof din shinkafa ta yi ta ji alayyahu da busashen kifi ta yi kyau sosai tana ta kamshi ta had'a zobo shima da ya ji kayan kamshi Baba Tabawa akwai tsafta da gwanancewa wurin shirya abinci mai rai da lafiya. Na shirya masa duk abinda ya kamata a tire na d'auka na fita daga kicin da takaicin abubuwa da yawa a raina. Yana kwance saman gadona yana waya na dire tire din hannuna tare da zama can gefe ya d'an jima yana wayar kafin ya kammala ya sauko kasan kafet yana fad'in." Ki zo mu ciyar da juna mana." "Ka ci kawai zan ci an jima." Bai sake magana ba ya zuba abincin da kansa bai nemi dana zuba masa ba lemon ma shi ya tsiyaya abinsa ya yi Bismillah a nutse ya fara cin abincin. Na d'auki wayata ina dubawa sai na tsinkayi maganarsa yana fad'in." Hirar me kuka yi ne da Aziza Amina?" Ya fad'a tare da dubana. Na kalleshi da mamaki namiji da son jin gulma kai tsaye na ce." Hirar matarka muka yi.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: Ya ce." Hirar matata kuma?" Na ce." E, mun yi hira akan lalurarta da kuma wata mas'alar da ta shafe ta.'' Ya d'an kalle ni kafin ya mayar da hankalinsa kan abincin da yake gabansa ya furta." Ku fa mata ba a raba ku da gulma Amina wace mas'ala kuma?" Da mamaki na ce." Ka ji ka da wata magana ai yanzu gulma ta tashi daga kan mata ta koma kan maza wallahi." Ya kalle ni na wani lokaci kafin ya ce.'' To ba ni na sha wace mas'ala ce?" Yadda ya fadi maganar cike da son jin labarin sai ya ba ni dariya sosai na ce." Ka gani ko? dama na gaya maka gulma ta tashi da ka kan mata." Sai ya 'bata rai yana cewa." Me ki ke nufi ?" Nasa dariya tare da cewa." Ai ban ce maka magulmaci ba misali na yi kawai." Murmushi ya yi kafin ya cigaba da cin abincin d'akin ya d'auki shiru na wani lokaci na ji gyaran muryarsa na dube shi ya gama cin abincin ya ta so ya zo kujarar da nake zauna ya nani'ke ni sosai yana fad'in." Bari na zauna kusa dake sosai zan fi fahimtar gulmar yadda ya kamata." Murmushi na yi ban ce komai ba. Ya kamo hannayena yana dubawa kafin ya ce." Wai ke ba ki jin kunya ne?" Na kalleshi da sauri kafin na ce." Me kuma na yi maka?" Ya bud'e tafukan hannayensa yana fad'in." Ya kamata ace hannayena da naki sun bambamta ki dinga yin lallai na gaya miki yana yi mini kyau." A jiyar zuciya na d'an sauke a nutse na ce." To zan yi in sha Allahu.'' Wayarsa aka kira ya je ya d'auka daga tsaye ya amsa kiran na d'an wani lokacin kafin ya kammala yana kashe wayar yake fad'in." Lokacin madam ne yanzu kashe wayoyin zan yi gabad'aya sai Allah Ya kaimu kuma." ina kallonsa ya kashe duka wayoyin nasa kafin ya dawo ya zauna kusa da ni yana cewa." Ba ni labari." Sosai na dube shi kafin na ce." Kasan Halisa k'anwar Hajiya Aziza?" Ya d'aga kansa yana fad'in." Kwarai na san sunanta amma a zahiri ban ta'ba ganinta ba. Na gyada kaina a sanyaye na furta." Labarin abinda ya faru da ita ya ta'ba mini zuciyata." Sai ya ce." Ta ba ki labarin Alhaji Amadu ya ta'ba nemanta ne?" Na ce."E, wallahi, amma yadda aka kusa sabauta mata rayuwa shine abinda ya rikita ni, kai Allah dai ya yafe mana." Cike da rashin gane inda na dosa ya ce." Shikkenan kuma saboda Allah bai kaddara an aureta ba sai a sabauta mata rayuwa komai yin Allah ne fa, tabbas na ji labarinta wurin alh Amadu lokacin jim kad'an da rasuwar matata ta biyu Ayush ba na gari ma yake gaya mini yana neman auran kanwar Aziza matar Alhaji Sulaiman daga baya kuma ya ce mini ya janye saboda wasu dalilai." Na ce." Bai gaya maka gaskiya ba matarsa ce ta jefe ta ta d'ora mata muguwar jinyya mai razanarwa." Ya gyad'a kansa kafin ya furta." Abinda ta gaya miki kenan?" Na ce." Kwarai kuwa, Kuma gaskiya akwai 'kamshin gaskiya a maganarta domin wallahi zan gaya maka a sammace kake Maryam ta gama da kai." Dariya ya fara yi yana kallona kafin ya furta." Ai ni kafin ki ga mace ta gama da ni wallahi sai ta yi da gaske Amina." Na ce." Au haba?'' "K'warai kuwa, yanzu dai mu bar wannan maganar mu yi ibada domin mu samu lada." Na ce." Magana fa ba za a bar ta ba, saboda kasan gaskiya Hajiya Aziza ta fada shiyasa kake bagarar da maganar wallahi ko ka 'ki ko ka so Maryam mashirika ce." Da sauri ya ce." Subahanallahi!" Na juyar da kaina gefe na ji yana fad'in." Ki daina ba ni so ranar lahira Ubangiji ya tsayar mini dake domin ki bada sheda shin kin ta'ba ganinta tana shirka da Idonki." Na girgiza kaina a hankali kafin na ce." Ban ta'ba gani ba ayyukanta ne suka nuna haka a zahiri." Jim ya yi yana nazari kafin ya ce." Kin ga wad'annan maganganun Amina na jima ina jin su akanta tun kafin ma na aureta da yawa an kawo mini suka akanta na rintse idona domin cika wasiyyar da abokina ya bari na kuma yi imani da cewa babu wani kulunboto da za ta yi yayi tasiri a kaina don haka kada ki gazgata kema tunda ba ki ta'ba gani da idonki ba, ki dubi alherinta kawai idan ma tana yi wannan tsakaninta ne da Allah." Shiru na yi na wani lokaci kafin na ce." Allah Ya kyauta amma tsakani da Allah wasiyyar nan da aka bar maka ba ta yi mana rana ba shi kuma duk cikinku ya rasa wanda zai bar wa wasiyyar auran matarsa sai kai, anya babu lauje cikin nad'i kuwa." Ya 'bata ransa sosai Yana fad'in." Amina ba ni son abinda zai daga mini hankali a yanzu, na gaya miki maganar nan tun farkon fari wallahi tallahi babu wani dalili da zai sanya na ci amanar abokina wai da ransa na kwadaitu da matarsa kuma shi ya rubuta wasiyyar nan da hannunsa ni kuma na yi kokari cika ta domin na gaya miki ko ni na fadi na mutu zan yi farinciki ace shi ya maye gurbina a wurin iyalina dalilin aminci da sha'kuwar da take tsakaninmu." Na ce." To na ji amma ai tun kafin ya rasu kake yabonta tare da fad'in kyawawan halayenta har cewa kake yi ta iya soyayya." Ya dafe kansa kafin ya ce." Na fadi hakane saboda ki yi koyi da ita domin ni mutum ne mai son a kula da ni a kuma tarairayeni da soyayya. Zan gaya miki gaskiya wannan ma yana daya daga cikin dalilan da suka sanya nake yabonta saboda ba ta tsallake umarnina kuma duk abinda na nuna masa soyayya tana yin fiye da yadda na yi idan kara na ajiye bata tsallakewa ke kanki da ta fahimci ina sonki ta taya ni sonki domin ban ta'ba ganin kishinki a tare da ita ba." Murmushi na yi na takaici na yi shiru ban ce komai. Idan ki ka karanta ba ki biya ni hakkina ba ina bin ki bashi. Ya rike hannuna yana fad'in." Maganar nan don Allah kada a sake tashinta matar nan tana cikin halin rai da rayuwa ni dake da duk wani makusanci a gare ta adduarmu take buk'ata, kada ki yadda zantukan mutane su rusa miki tunani da Imani, ita kuma Hajiya Aziza na raina wayonta wallahi ai Maryam sanin da nayi 'kawarta ce sosai Aminiya abokin b'arawo ai b'arawo ne Amina mai zai sanya daga zuwa kawai ta gaya miki abinda ya jima.. Ubangiji ya hana fallasa asirin bawansa mussaman idan bawan nan ya yi tabbatacccen tuba." Da mamaki na ce." Har yanzu dai ba zaka daina take gaskiya ka fifita karya ba ko, kai tsaye ka ki ka aminta da zantukan da suke yawo a gari akan matar nan, kai ma da bakinka ka fad'a cewa an gaya maka amma sai kame-kame kake yi kana kare ta Hajiya Aziza ai ba ta yi lefi ba tunda komai dalili yake yi.". Ya ce." Ba wai kare ta nake yi ba Amina na ce miki Allah ne ya yi hani da cewa idan daya daga cikinku ya aikata kuskure ku yi shela a duniya mussaman idan bawan nan ya tuba babu wanda yake shiga tsakanin mahallici da bawansa." "Ka tabbatar da cewar ta tuba?" Da tsawa ya ce." Ke Amina maganar nan ta isa haka na ce miki wai ke wace irin yarinya ce ne, idan har ba ki nemi fitina ba ba kya jin dadi a rayuwarki ke ba za ki ta'ba ba ni nutsuwa da kwanciyar hankali ba." Cikin dauriya na ce." Babban abinda ya daga mini hankali yadda har ka iya rufe Idonka ka gaya mata cewa Kamalu ya ta'ba yin fitina irin ta 'kuruciya a baya, sannan ka fitar da rikicin da ya faru a gidan nan har jama'a suna yamadidi da mu cewa mun had'e mata kai ni da Hauwa ba ma yin mu'amula da ita." Ido ya tsira mini a rikice ya ce." Yanzu wanene ya kawo maganar Kamalu anan?" Na ce." Ni ce na kawota domin na yi iyakacin bakin kokarina akan na ga na danne maganar a zuciyata na kasa abinda ya sanya ni sake gazgata cewa kai ka gaya mata a ina mutane za su samu labarin zaman da muke yi har su zage mu akan mun ware matarka tuntuni ka nuna hadin kan dake tsakanina da Hauwa baka so saboda ba mu sanya matarka a cikinmu ba har ka gaza ha'kuri ka fitar da maganar duniya." Ya jima yana kallona cikin tashin hankali kafin ya ce." Ni ko Hajja ban ta'ba gayawa sirrin gidana ba mahaifiyata kenan. Baban Saude shine mutumin da nake ganin zan gayawa matsalar da ta shafe ni ya ba ni shawarwari saboda na yarda da nutsuwa da adalcinsa kuma ki ji tsoron Allah Amina Idan har za ki yi mini adalci ki fadi gaskiya akaina kada neman fitina ya sanya ki haddasa mini ciwo, ki fadi gaskiyar abinda ki ka sani a kaina na daga da'bia na tabbatar da cewa tsayin zamana dake zaki gane abinda zan aikata da kuma wanda ba zan aikata ba mai zai sanya kawai na zaunar da Maryam na gaya mata abinda ya faru a baya me yasa zan yi haka? Uhm me yasa zan aibata Kamalu a wurin Maryam saboda soyayya ta yi mini dadi." Ya kai karshen maganar cikin yanayi na damuwa da alhini." Na ji hawaye sun zubo kumatuna ban goge ba na ce." To a ina ta samu labari idan ba kai ka gaya mata ba, ita kuma ta gayawa yaranta." Ya yi d'an jim kafin ya furta." A lokacin da abin ya faru ke kan ki fa kin yi dogon rubutu a social media wato fecebook rubutun da ya zagaye kowace kafa ta sadarwa wanda bai san akan wane dalili ki ka yi rubutun akaina ba zai je ya bibiyi ba'asi kin manta da haka? kin manta cewa Salim zai iya cin karo da labarin ke ma fa kin bada gudummuwa wurin 'kara rura wutar lamarin domin dai kin san matsayina rubutunki kuma ya janyo cecekuce da yawa, me yasa za ki d'ora mini lefi?'' Shiru na yi ina kuka domin bakin cikin abinda ya faru ne gabad'aya ya taso mini. Ya tashi tsaye yana fad'in." Ke duk yadda mutum ya so da ya zauna lafiya dake ba za ki ba shi damar hakan ba, ba ki iya rarrashi da tarairaya ba sai neman fitina." Ya tafi ya je ya kwanta saman gadona tare da rufe k'afafunsa da bargo. Kuka na ci na koshi yana kallona bai ce mini komai ba. Na shiga bandaki na yi wanka na fito duk idonsa biyu na shirya jikina da kayan bacci. Abinci na zauna na ci kad'an kafin na kwashe kayan na kai kicin na dawo d'akin yana dai kwance amma bai yi baccin ba. Gefansa na zauna ina d'an kallonsa gabad'aya ya yi sanyi yanayin damuwa ya bayyana a fuskarsa. Ban ce komai ba na ra'ba daga gefansa na kwanta ina jin bai fi sau uku ba ya ta'ba kwana a d'akina ba. Ya mik'a hannu ya kashe fitilar gefan gado kafin ya janyo ni jikinsa sosai ya matse ni a kirjinsa muka sauka ajiyar zuciya kusan a tare jikinsa na dan rawa na ji maganarsa a hankali cikin taushi da rarrashi Yana fad'in." Da zan iya ha'kuri dake Amina da tuni na yi, Allah Ya jarrabe ni da sonki kada ki ga haka ki nemi halaka ni don girman Allah." Shiru na yi ban ce masa uffan ba ina jin dai yadda hannunsa keta zarya a sassan jikina. yana mika bakinsa wuyana yana sumbata cikin sar'kewar murya yake fad'in." Mu yi soyayya irin wadda na Annabi s.a.w ya koyar Amina kada mu cutar da wani sashe na jikinmu ina buk'atar kulawa a yau ta mussaman kada ki yi mini 'kwange ki marabce ni da zuciya da gangar jikinki." Na dai yi masa shiru ban tanka ba zuwa lokacin ma na fara bin layinsa. Ya dago fuskata yasa bakinsa yana ta sumbatar kumatuna kafin ya fara ko'karin had'a bakinmu wuri d'aya. Hannayena na sanya a tsakaninsa na janyo shi sosai muka had'e bakinmu cikin wata masifaffiyar runguma wadda take motsa duka ga'bban jiki. Washe gari da safe kafin ya fita har da yi mini wa'kar soyayya ta Hamusu bireka tun ina daurewa har dai na gaza na dinga kyalkyala dariya ganin yadda yake ta rero wa'kar (Ashe da rai nake sonki jaruma ba da zuciyata ba, komai ruwa da iska akan ki ba za na daina kewa ba, idan na same ki.....) Na tambaye shi a ina ji ya wa'kar har ya haddace baitikan irin haka ya ce a gari ya ji shima. Kai na ci dariya sosai da ya fita na ce lallai na cinye wasan a daran jiya kenan irin wannan wa'ka haka......✍️ 2k complete on telegram via 0542382124...binta Umar gtbank *07084653262* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: Na jima kwance kafin na ji shigowar sa yana shafa bayana ban motsa ba "Ki yi hakuri My Lima, na je wurin Anna ta fada mini abin da ta fada miki. Kin san sha'anin manyan nan ki yi hakuri." Na tashi zaune na fadi "Ya wuce." Yawwa my lima zo ki hada mini garin." Na mike na fita na hada mishi ya sha ya sha magani sannan muka kwanta. Na dade barci bai dauke ni ba ina tuna maganganun Anna, duk da ina jin a matsayin ta na suruka bai kamata ta fada mini ba, gefe guda kuma sai na ji tamkar allura ta yi mini ta kuma farkar da ni. Ba zai zama abin damuwa wurin Mama ba in haihu ta ki yi mini abin da ya kamata, har wanda yan'uwa suka hada ta hada ta rike. To ina mafita? Na tambayi kaina, "Allah ka ba ni mafita." Na furta a hankali. Da gari ya waye ranar zan fita girki, tun da na fito da safe Fauza ke ta kai da kawo tana kalkale falonta ga kamshi na musamman ta sanya, girki ma tun a sannan ta fara da na tabbatar shi ma na musamman za ta yi. Kirjina ya cushe ina lissafin da garin mu nake in tafi gidanmu ko gidan yan'uwa. Hamid da ya shirya fita da wuri na tambaye shi zuwa gidan Innar su Aminu, ya ce A'a bai son yawan fita. Komai ban ce ba ballantana ta kai ni ga magiyar ya bar ni, na gyara na kwanta. A dakin na wuni ko abinci ban fita na nema ba. Na idar da sallar la'asar ina zaune kan sallayar wayata ta dauki kara na juya inda take sai na dauko ta, sunan Aminu ke yawo saman Screen din na daga bakina dauke da sallama ya ce "Aunty ina waje na zo gaishe ki." Na dan yi murmushi "An shigo garin kenan? Ina zuwa." Na yunkura sai na mayar da mayafin doguwar rigar da ke jikina na taka na fita dakin. Kamshin girkin Fauza da kamshin turaren falon ya hadu ya ba da kamshi na musamman, ba kowa falon na koma dakina na ciro plastic chair da na saya guda biyu ko da zan yi bakon da dole sai na zaunar da shi a falon sai na sanya mishi. Na fita har zuwa zauren gidan inda na tsinkaye shi, da fara'a nake yi masa sannu da zuwa tare da yi masa jagora muka shiga ciki, a saman daya daga cikin kujerun na yi masa tayin zama, na wuce kitchen na kawo masa ruwa, sannan na zauna a daya kujerar muna gaisawa na ce "Ina amarya? Ba ka kawo mani ita ba, sai wani za shi daga gidan Inna, in bi shi na gano ta." Ya yi murmushi "Zan ma kawo miki ita Aunty." Daidai nan Fauza ta fito daga dakinta ta dube mu, muka dube ta, ganin ta yi hanyar kitchen ya ce mata "Ina wuni? Lafiya kawai ta ce ba tare da ta waiwayo ba. Hira muka yi da ba ta wuce ta mintuna biyar ba ya mike bayan ya ajiye mini Envelope a kujerar da ya tashi. Na bi shi ina mai godiya a gare shi, sai da na dan taka masa sai na juyo na koma dakina na bude envelope din rapper guda ce ta yan dari biyar"Dubu hamsin." Na fadi wani tunani na shiga kwanya ta. Na janyo wayata na yi ma Hajara flashing don ba kudi a tawa wayar. Ba bata lokaci ta biyo tana mini tsiyar na shige Karfi na yi shiru. Na tambaye ta yaranta da mai gidanta da can wurin Inna ta kuyanbana sai da muka tattauna har kan Haj Iya da ciwon kafarta ya motsa sannan na gangaro kan dalilin da ya sa ni kiran ta. "Wasu kudi na samu Hajara, shi ne nake so na turo miki ki samu wani abu da ya danganci masu haihuwa ki saya mini." Kamar ya ban fahimce ki ba." "Ina nufin abin da ake kawo ma mace idan ta haihu daga gidansu." "Lallai ma Halima mu duk yawan mu aikin me muke da ba za mu yi miki ba har sai kin kawo kudinki? Na ce "Ba haka ba ne, ki dai yi hakuri zan dinga turo miki da na samu, kin san sha'anin gidan yawa, ga kishin sauri, ga uwar miji, ga kishiya a gefe." Ta ce "Na fahimce ki. Allah ya raba ku lafiya." Sai kuma ta fara mini iya shege "Iyee ta Hamid din ba, Karfi ta amshe ki har kin fara tara kudi? Na yi yar dariya na katse kiran ina tunanin wanda zan ba kudin ya kai mini wurin masu POS, shigowar sako daga wayata ya sa na dubi wayar Hajara ce ta sanya mini Credit na 500 na ji dadi na tura mata sakon godiya sai na kira Haj Iya na tambaye ta kafa na kashe na kira kanwata Bilkisu, muryar Naana na fara ji cikin kukan shagwaba tana fadin a kai ta wuri na. Na lallashe ta na ce ta bari a yi hutu kasan zuciyata kuma zullumi ya rufe ni, Naana ta zo a wannan hali da ake ciki akwai kura, yaro bai san babu ba, ina kudin da za mu yi mata yadda ta saba? Bilkisu ta karbi wayar tana fadin "Allah Aunty yar nan taki tana ba ni ciwon kai." Na ce "Me take miki Aunty Billy? Ta ce "Na kusa fara zane ta." Na ce "A'a ba a yi haka ba me take yi? Ta ce "Sangarta mana. Yanzu haka ta sa na fara tunanin da zan samu aiki." Na ce "Aiki kuma ko karatun ba a kammala ba? Don Hamid ya nema mata gurbin karatu a ABU Zaria ya roki Baba ya bar ta ci gaba da karatu ita kanta ba kananan kudade ya kashe mata ba duk don tana kula masa da Naana. Ta ce "Hmm ba za ki gane ba Aunty. Yau tun da ta dawo Sch ta sanya ni gaba sai na fita da ita ta sha Ice cream, Uncle dinta Abdullah ya ba mu 2000 na samu na aika aka kawo mana Ice cream din. Ta kwanta tana kuka sai na kai ta Smart kick ina na ga kudin motar zuwa KD da abin da za mu kashe? Na ja ajiyar zuciya "Zan turo 7k Aunty Bilkisu, ki rike ku lallaba kina saya mata abin da take so." Shi kenan Aunty mun gode. Amma Naana ba ta san a lallaba ba. Teddy dinta yaron Aunty Sakina ya taba daga zuwa ta birkice ba ta so yanzu ita zan samu na saya mata kullum sai ta yi mini kukan banza Na ce "A yi hakuri Aunty Billy. Ina jiyo muryar Mama tana sababin hidimar Naana da muka sakar musu. Naana ta karbe wayar tana ba ni labari, duk wani abu da aka yi mata sai ta fada mini, da kyar na samu ta bar ni ba ta cinye kudaden wayar ba. Na ajiye ta ina son fita in nemi abin da zan sanya ma cikina amma ba na son haduwa da Fauza, na daure har sai da na yi sallar magrib ina kan sallaya Hamid ya shigo wanda tun fitar shi da safe sai yanzu ya dawo na gaishe shi ya tambaye ni gobe zan koma Hospital na ce E ya ciro kudade ya ba ni na karba da godiya tare da ba shi labarin zuwan Aminu, ya fita ya ce mini zai je ya ci abinci. Na tashi daga inda nake na hau katifa amma cikina ya ki ba ni hadin kai, da gasken gaske yunwa nake ji. Na mike kamar mai tafiya kan kwai na fita dakin, ba kowa falon na shiga kitchen, ina da sauran Indomie ita na dafa cikin sauri na juye a flate na dauki ruwa na hada na fito, idona ya yi kyauyawan gani Hamid da Fauza suna cin abinci ta sheka ado cikin wani kankararren leshi wuya da hannu suna ta shekin sarka da yan kunne, na kawar da fuskata na wuce daki. Na zauna ina cin indomie a hankali zuciyata na can ga tunanin kwalliyar da Fauza ta caba, ji na yi zuciyata na nadamar suturuna da na kyautar, yanzu sai dai na yi kallon Fauza na cancada kwalliya yayin da nake fama da suturu masu rangwamen kudi. Na yi nisa cikin nadamar sai na ji kamar an mintsine ni, take na dawo cikin nutsuwa ta, istigfari na shiga kirgawa da yatsun hannuna. Ba karshen nadama da ta wuce ka tashi gaban Ubangiji ka rayu da cin haram, suturar haram. "Zan jure komai ya Ubangiji." Na fadi kamar mai magana da wani. A daddafe na cinye Indomie na sha ruwa sai na yi shirin kwanciya. Wayata na dauka ina dannawa sai na ji bugun kofa da na san Hamid ne na kasa motsawa don wani sake-saken daga zuciyata har ya gaji ya tafi na gyara kwanciyata ina jiran gari ya waye a yi wacce za a yi. Da na tashi da asuba na yi sallah ban fita neman abin da zan karya ba kamar yadda na saba yi a cikin yan kwanakin nan, na dai bude kofa sai na koma na kwanta, kamar jira Hamid ya shigo sanye da jallabiya mai yankakken hannu. Ta kasan ido na dube shi sai na lumshe ido, ya iso ya zauna "Lafiya ba ki tashi ba? Na bude ido "Na tashi." "Lafiya kike? Na daga masa kai. "Amma ba ki tashi kin fara shirin asibitin ba? Na ce "Za ni, ina son yin magana da kai." "Ok ina jin ki." Na ja ajiyar zuciya "Gaskiya ban aminta da kayan Fauza a falo ba." Ya dube ni da alamar rashin fahimta "Ban gane ba to ina za ta kai su? "Ko'ina. Amma ina son filin falon ni da ita kowa ya yi amfani da shi, ba ta gaje ita kadai ba, ni ina rabe." Why Lima me zai sa ki yi haka? Tun kafin ta sanya kayan za ki yi magana ba sai yanzu ba.". Na ce "Ta kwashe ban amince ba." "Hakuri za ki yi daga ba ki yi magana a farko ba." "Ba zan yi ba." Na fadi ina tashi zaune "Wai me kike ji ne haka ina taro ki kina fada mini magana? Wuri dai nawa ne ba na wani ba da za a sanya mini doka." Na mike tsaye. Tabbas naka ne. Amma ni ma ba za a tilasta mini zama da kayan ba, daga na ce ba ni da bukata." "Me kike nufi? "Komai ma." Daga haka na fara tube kayan jikina ya bi ni da kallo har na shiga wanka, ban tunanin zan fito na same shi ba sai na same shi zaune, na tsane jikina na fara shiri, kwalliyar doguwar rigar atamfa na yi na sanya farin hijab da farin takalmi na dauki jakata na kama hanyar kofa ya kira sunana ba tare da na waiwayo ba na taaya "Ina za ki? Ban amsa ba na kama hanya, ban san yana biye da ni ba sai da na fito Fauza na tsaye da alama cikin bacin rai mai yawa take "Aikina ka shiga dakinta tun asuba wallahi ba zan yarda ba." Na wuce shi ma bai tanka ta ba ya bi ni "Ba ki rufe dakinki ba Halima." Ya fadi daidai kunnena "Daki ai naka ne kamar yadda ka tabbatar mini." "To ina za ki hospital? Na yi mishi shiru ya juya cikin sauri na ci gaba da tafiya ta cikin sa'a na samu abin hawa ba bata lokaci ya haye titi. [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: A cikin kwanaki biyun da suka kasance na girkina mun yi abin arzi'ki sosai ni da shi ya dinga lalla'ba ni tare da ko'karin ganin wata matsala bata faru ba wadda zata janyo mana k'ananun maganganu . Washe garin ranar da girki ya bar hannuna kafin na sauko daga saman na sake tuntu'barsa maganar zuwa maiduguri ganin d'akin Fadila ya ce ai ya riga ya rantse na yi hakuri har su je su dawo daga asibitin da za su je shi da Momi tunda yanzu abinda ya sanya a gaba kenan idan ya dawo sai ya raka ni mu je maidugurin tare, shima sai ya gaishe da su Dada da sauran 'yan uwana, Na ce amma maganar yara fa kai tsaye ya ce mini suna tare da Nabila a gidan domin ta d'an kwana biyu da zuwa wurin 'yar uwata, amma ba da ita za a yi tafiyar ba zata zauna ta kula da yaran gabad'aya har da su Salim da Adamu. Rashin abin fad'a ya sanya ni kawai zuba masa ido, wace irin masifa ce ne wannan jama'a, shin yaushe yaranmu za su dawo hannunmu ne ni Aminatu?" Ina zaune har ya gama kintsa jikinsa muka sauko tare babu kowa a falon Baba Tabawa ta gama aiki tun da wuri ta shige dakinta. Hauwa ba ta fito ba. Har zai fita sai ya tsaya yana kallona kafin ya ce." Ina Hauwa ne?" Kai tsaye na ce." Ba kasan inda take ba?" Ya zura mini ido na 'yan sakkoni kafin ya gyad'a kansa ya kama hanyar fita yana fad'in.'' idan ba ki yi tsiwa ba ai ba sunanki Amina ba." Ya fice a gaggauce don da alama yana da wani babban uzurin da ya hana shi tsayuwa ma ya karya kummalo. Ina juyawa da zummar shiga d'akina Hauwa ta fito cikin kayan bacci da alamar ba ta jima da tashi ba hankalinta na wurin cin abinci. Tana hamma ta furta." Wata mashahuriyar yunwa ce ta tashe ni Amina." Na ce." Ai fa wannan abinda yake cikin naki acici za mu sanya masa Hauwa." Dariya ta yi tana fad'in." Na dai kusa saukewa na sha ibada wallahi." Cike da kulawa na ce." Ubangiji Allah Ya sauke ki lafiya, yanzu nan kuwa maigidan da zai fita yake tambayarki." Ta yi sororo tana kallona. Na gyad'a kaina ina fad'in." A shawarce Hauwa tun kafin manya su ji wannan abin ku shirya tsakaninku don Allah ke ce 'kasa dashi dole ki sauke girman kan ki." Ta ce." To so ki ke yi na je na ce masa ya yi hakuri ya janye sakin da ya yi mini Amina?" Na ce." E, mana menene a ciki idan kin ce masa ka yi hakuri." Ta'be bakinta ta yi ba ta ce komai ba ta nufi wurin da abin kari yake a shirye tana fad'in." Zancen ki ke so Amina." Na bita da kallon mamaki kafin na girgiza kai na wuce d'akina da tunanin abin a raina. Da alama shi ya fara sakkowa tunda har ya tambayeta na tabbatar da cewa yanzu ya fara neman zaman lafiya a gidansa. Ranar da za su tafi har gida ya yi mata jagora domin ta yi mana sallama. Zamanta ke da wuya Hauwa ta yun'kura ta tashi ta shige dakinta. Hakan kuwa bai yi mata dad'i ba, amma dai ba ta ce komai ba, muka d'an ta'ba hira sama-sama kafin ya sauko daga saman suka fita tare. Sosai na yi mata addu'a da fatan alheri ta dinga godiya da murmushin nan nata wanda duk rintsi baya ta'ba d'aukewa daga saman fuskarta. Bayan tafiyar su da kwana ashirin da shida Hauwa ta haihu. Cikin ikon Allah ta haifi d'anta namiji kama da ubanshi har ta 'baci duk abinda ya kamaci ta yi wa kanta ta yi tunda haihuwar gida ta yi kuma lafiya lau ita da yaron da ta haifa, a matsayinta na ma'aikaciyar lafiya taimakon da muka yi mata kad'an ne. Sai bayan da muka samu nutsuwa gabad'ayanmu ni da ita tukkuna na nemi maigidan da yake koda suka tafi ba kasafai yake kiran waya ba sai dai mu had'u ta whasap to baya jurar typing sai da vedio call. Sai na ajiye masa sa'ko ta whasap din tare da hoton yaron nasan daga zarar ya hau zai gani. Ina idar da sallar la'asar na bud'e sakonshi ya shigo yana online din muka sake gaisawa na tambaye shi mai jiki ya ba ni amsa mai dadi jiki yayi kyau domin a karshen watan da muke ciki ma za su dawo domin an d'orata akan maganguna kuma alhamdulillahi an samu cigaba. Sai ya d'ora da fad'in wai na yi wa yaron hud'uba da sunan Ahmadu domin shine sunan da ya rad'a masa. Rashin abin cewa ya sanya ni yi masa shiru kawai domin tunda Hauwa ta haihu take kiran yaron da sunan mahaifinta wato Ishak, ban san kuma mai zan ce mata ba gaskiyar magana kenan. Ganin na yi shiru ban ce komai ba ya sanya shi kiran sunana na kalle shi tunda bidiyo call ne ya furta." Ko akwai wata matsala ne domin na karanci damuwa a cikin kwayar Idonki." Na girgiza kaina a nutse na ce." Babu matsala amma gaskiya ba zan iya gaya Hauwa ga abinda ka yanke ba, mai zai hana kai ka gaya mata naga tare kuka samar da yaron nan ku biyu mai zai sanya ni ka saka ni a tsakiya. Hauwa tunda ta haihu take kiran yaron nan da sunan babanta, to ni mai kake so na ce kuma." Ya yi shiru yana kallona kafin daga bisani ya ce." Shikkenan zan gaya mata hukuncin dana yanke hakan ya yi ko." Na gyada kaina ina fad'in." Ya yi shine daidai sai ku tsayar da matsaya a tsakaninku, Allah Ya raya mana shi." Ya amsa da "Amin. Yana mai zuba mini ido." Ni ma na zuba masa nawa idon nan na fahimci canzawar da ya yi har da wani kumatu fatar nan ta sake yin fresh duk da bidiyo call yana sanya mutum muni da duhu to shi ban ga hakan ba, kamar ba wanda ya tafi jinyya ba ya yi kama da ango wanda ya tafi yawon sha'katawa da amaryarsa. Ajiyar zuciya na sauke yayin da nake ko'karin kawar da abinda na ji yana yun'kuro mini a game dashi na ce." Na canza kammanni ne Allah Ya taimaka ka." Sai ya rausayar da kansa yana ce wa." Sosai kuwa, wata na gani anan asibitin da muke mai kama dake duk sanda na yi ido hud'u da ita sai hankalina ya tashi wallahi yanzu ina cikin tsananin damuwa na yi missing d'inki my love dina." Na dan bata rai tare da cewa." Matar kuma idan tana da aure fa, kana raya abun da bai dace ba akan matar wani daidai kenan a wurinka." Kansa ya girgiza kamar karamin yaro ya furta." Ba daidai ba ne, amma ba na tsammanin ai tana da aure budurwa ce, wallahi ba zan munafurceki ba Amina ba na iya d'auke kaina daga kanta domin yanayin hallitar jikinku daya 'yar duma-duma ce mai yawaltaccen kirji da tudun mazaunai." Dariya maganar ta ba ni na danne ban yi ba domin ganin abin nasa yana nema ya wuce makadi da rawa na ce." To sai ka tuntubeta idan ba ta da aure ka aurota ko?" Ya girgiza kansa yana ce wa." A'a ai ba musluma ba ce addinin hindu ce." Na ce." To menene a ciki sai ka musuluntar da ita." Kansa ya girgiza tare da furta." A a, abinda ya sa ki ka ji ina yi miki maganarta kamar da kuke yi da ita ne ya b'aci da gaske idan na ganta ina shiga yanayi na buk'atuwa sosai." Shiru na yi ban ce komai ba. Sai ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Ina nan dawowa my love za mu sha soyayya ko?" Na kashe idona tare da fad'in." Sosai ma irin wadda kake so za mu yi." Sai ya zuba mini idanuwansa babu kiftawa. Na kama dariya ina fad'in." Ka na ji kamar ka d'auko ni daga cikin wayar ko?" Ya gyada kansa yana lumshe Ido. Hakan ya sake jefa ni a damuwa da sha'awa na sauke ajiyar zuciya a kasalance na furta." Ni ma na yi missing din Baba Yallabai baban soyayya." Kafin ya ce wani abu kiran da aka yi masa a wayar ya katse video call din. Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefe Ina sauke ajiyar zuciya gabad'aya hirar nan da muka yi ta tayar mini da hankali wani irin nake ji a jikina. Sai gefin magriba na fito falon daga cikin d'akin Hauwa na ji kukan yaron ya tsananta da saurin gaske na shiga d'akin na same shi kwance cikin net dinshi yana ta wutsil-wutsil towel ya toshe masa hanci. Da azama na zuge net din na d'auko shi fuskarsa ta yi jazur saboda da alama ya jima yana kukan. Na zauna gefan gadonta ina jijiigashi gabad'aya ya shid'e a tunanina tana bandaki na tashi tsaye dashi a kafad'ata na tsaya kofar band'akin ina kiran sunanta shiru bata amsa ba kuma babu motsin ruwa. Sai kawai na kutsa kaina ciki wayam babu alamunta. Da sauri na fito gabana na dan fad'uwa na tsaya ina rarraba idanuwana a d'akin ban ga alamun komai ba.. Na fita kai tsaye kicin na nufa Baba Tabawa ta kammala abinci dare tana gyara kicin din. Cikin kasala da sagewar gwiwa na furta." Baba ina Hauwa?" Sai kawai ta tsaya tana kallona kafin daga bisani ta furta." Ba ta dakinta ne Amina?" Na furta." Kwarai kuwa, fitowata daga d'aki kenan na ji kukan yaron nan koda na shiga d'akinta bata nan." Ta sanya hannunta ta kar'be shi a sanyaye ta biyo bayana muka tsaya a tsakiyar falon. Ina Hauwa za ta tafi to. Ni nake tambayar zuciyata dalili tunda ta haihu ban ga alamun fitina a tattare da ita ba asalima wani babin annashuwa da farinciki ta bud'e. Baba Tabawa ta sanya babban towel ta goya yaron ni kuma na d'auko hijabina na sanya na fita can harabar gidan. Daga nesa na tsaya ina hangen securitys a bakin gate. Masa'udu ya shigo da mota ya ajiye a wurin da motocin suke ya fito daga motar ganina a tsaye ya sanya shi da sauri ya nufo ni. Ya risina yana gaishe ni na amsa tare da fad'in." Daga ina kake domin kuwa zuciyata ta fara hasashen wani abu......✍️ *2k complete a kan telegram via 0542382124...Binta Umar gtbank* *07084653262* *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: A cikin kwanaki biyun da suka kasance na girkina mun yi abin arzi'ki sosai ni da shi ya dinga lalla'ba ni tare da ko'karin ganin wata matsala bata faru ba wadda zata janyo mana k'ananun maganganu . Washe garin ranar da girki ya bar hannuna kafin na sauko daga saman na sake tuntu'barsa maganar zuwa maiduguri ganin d'akin Fadila ya ce ai ya riga ya rantse na yi hakuri har su je su dawo daga asibitin da za su je shi da Momi tunda yanzu abinda ya sanya a gaba kenan idan ya dawo sai ya raka ni mu je maidugurin tare, shima sai ya gaishe da su Dada da sauran 'yan uwana, Na ce amma maganar yara fa kai tsaye ya ce mini suna tare da Nabila a gidan domin ta d'an kwana biyu da zuwa wurin 'yar uwata, amma ba da ita za a yi tafiyar ba zata zauna ta kula da yaran gabad'aya har da su Salim da Adamu. Rashin abin fad'a ya sanya ni kawai zuba masa ido, wace irin masifa ce ne wannan jama'a, shin yaushe yaranmu za su dawo hannunmu ne ni Aminatu?" Ina zaune har ya gama kintsa jikinsa muka sauko tare babu kowa a falon Baba Tabawa ta gama aiki tun da wuri ta shige dakinta. Hauwa ba ta fito ba. Har zai fita sai ya tsaya yana kallona kafin ya ce." Ina Hauwa ne?" Kai tsaye na ce." Ba kasan inda take ba?" Ya zura mini ido na 'yan sakkoni kafin ya gyad'a kansa ya kama hanyar fita yana fad'in.'' idan ba ki yi tsiwa ba ai ba sunanki Amina ba." Ya fice a gaggauce don da alama yana da wani babban uzurin da ya hana shi tsayuwa ma ya karya kummalo. Ina juyawa da zummar shiga d'akina Hauwa ta fito cikin kayan bacci da alamar ba ta jima da tashi ba hankalinta na wurin cin abinci. Tana hamma ta furta." Wata mashahuriyar yunwa ce ta tashe ni Amina." Na ce." Ai fa wannan abinda yake cikin naki acici za mu sanya masa Hauwa." Dariya ta yi tana fad'in." Na dai kusa saukewa na sha ibada wallahi." Cike da kulawa na ce." Ubangiji Allah Ya sauke ki lafiya, yanzu nan kuwa maigidan da zai fita yake tambayarki." Ta yi sororo tana kallona. Na gyad'a kaina ina fad'in." A shawarce Hauwa tun kafin manya su ji wannan abin ku shirya tsakaninku don Allah ke ce 'kasa dashi dole ki sauke girman kan ki." Ta ce." To so ki ke yi na je na ce masa ya yi hakuri ya janye sakin da ya yi mini Amina?" Na ce." E, mana menene a ciki idan kin ce masa ka yi hakuri." Ta'be bakinta ta yi ba ta ce komai ba ta nufi wurin da abin kari yake a shirye tana fad'in." Zancen ki ke so Amina." Na bita da kallon mamaki kafin na girgiza kai na wuce d'akina da tunanin abin a raina. Da alama shi ya fara sakkowa tunda har ya tambayeta na tabbatar da cewa yanzu ya fara neman zaman lafiya a gidansa. Ranar da za su tafi har gida ya yi mata jagora domin ta yi mana sallama. Zamanta ke da wuya Hauwa ta yun'kura ta tashi ta shige dakinta. Hakan kuwa bai yi mata dad'i ba, amma dai ba ta ce komai ba, muka d'an ta'ba hira sama-sama kafin ya sauko daga saman suka fita tare. Sosai na yi mata addu'a da fatan alheri ta dinga godiya da murmushin nan nata wanda duk rintsi baya ta'ba d'aukewa daga saman fuskarta. Bayan tafiyar su da kwana ashirin da shida Hauwa ta haihu. Cikin ikon Allah ta haifi d'anta namiji kama da ubanshi har ta 'baci duk abinda ya kamaci ta yi wa kanta ta yi tunda haihuwar gida ta yi kuma lafiya lau ita da yaron da ta haifa, a matsayinta na ma'aikaciyar lafiya taimakon da muka yi mata kad'an ne. Sai bayan da muka samu nutsuwa gabad'ayanmu ni da ita tukkuna na nemi maigidan da yake koda suka tafi ba kasafai yake kiran waya ba sai dai mu had'u ta whasap to baya jurar typing sai da vedio call. Sai na ajiye masa sa'ko ta whasap din tare da hoton yaron nasan daga zarar ya hau zai gani. Ina idar da sallar la'asar na bud'e sakonshi ya shigo yana online din muka sake gaisawa na tambaye shi mai jiki ya ba ni amsa mai dadi jiki yayi kyau domin a karshen watan da muke ciki ma za su dawo domin an d'orata akan maganguna kuma alhamdulillahi an samu cigaba. Sai ya d'ora da fad'in wai na yi wa yaron hud'uba da sunan Ahmadu domin shine sunan da ya rad'a masa. Rashin abin cewa ya sanya ni yi masa shiru kawai domin tunda Hauwa ta haihu take kiran yaron da sunan mahaifinta wato Ishak, ban san kuma mai zan ce mata ba gaskiyar magana kenan. Ganin na yi shiru ban ce komai ba ya sanya shi kiran sunana na kalle shi tunda bidiyo call ne ya furta." Ko akwai wata matsala ne domin na karanci damuwa a cikin kwayar Idonki." Na girgiza kaina a nutse na ce." Babu matsala amma gaskiya ba zan iya gaya Hauwa ga abinda ka yanke ba, mai zai hana kai ka gaya mata naga tare kuka samar da yaron nan ku biyu mai zai sanya ni ka saka ni a tsakiya. Hauwa tunda ta haihu take kiran yaron nan da sunan babanta, to ni mai kake so na ce kuma." Ya yi shiru yana kallona kafin daga bisani ya ce." Shikkenan zan gaya mata hukuncin dana yanke hakan ya yi ko." Na gyada kaina ina fad'in." Ya yi shine daidai sai ku tsayar da matsaya a tsakaninku, Allah Ya raya mana shi." Ya amsa da "Amin. Yana mai zuba mini ido." Ni ma na zuba masa nawa idon nan na fahimci canzawar da ya yi har da wani kumatu fatar nan ta sake yin fresh duk da bidiyo call yana sanya mutum muni da duhu to shi ban ga hakan ba, kamar ba wanda ya tafi jinyya ba ya yi kama da ango wanda ya tafi yawon sha'katawa da amaryarsa. Ajiyar zuciya na sauke yayin da nake ko'karin kawar da abinda na ji yana yun'kuro mini a game dashi na ce." Na canza kammanni ne Allah Ya taimaka ka." Sai ya rausayar da kansa yana ce wa." Sosai kuwa, wata na gani anan asibitin da muke mai kama dake duk sanda na yi ido hud'u da ita sai hankalina ya tashi wallahi yanzu ina cikin tsananin damuwa na yi missing d'inki my love dina." Na dan bata rai tare da cewa." Matar kuma idan tana da aure fa, kana raya abun da bai dace ba akan matar wani daidai kenan a wurinka." Kansa ya girgiza kamar karamin yaro ya furta." Ba daidai ba ne, amma ba na tsammanin ai tana da aure budurwa ce, wallahi ba zan munafurceki ba Amina ba na iya d'auke kaina daga kanta domin yanayin hallitar jikinku daya 'yar duma-duma ce mai yawaltaccen kirji da tudun mazaunai." Dariya maganar ta ba ni na danne ban yi ba domin ganin abin nasa yana nema ya wuce makadi da rawa na ce." To sai ka tuntubeta idan ba ta da aure ka aurota ko?" Ya girgiza kansa yana ce wa." A'a ai ba musluma ba ce addinin hindu ce." Na ce." To menene a ciki sai ka musuluntar da ita." Kansa ya girgiza tare da furta." A a, abinda ya sa ki ka ji ina yi miki maganarta kamar da kuke yi da ita ne ya b'aci da gaske idan na ganta ina shiga yanayi na buk'atuwa sosai." Shiru na yi ban ce komai ba. Sai ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Ina nan dawowa my love za mu sha soyayya ko?" Na kashe idona tare da fad'in." Sosai ma irin wadda kake so za mu yi." Sai ya zuba mini idanuwansa babu kiftawa. Na kama dariya ina fad'in." Ka na ji kamar ka d'auko ni daga cikin wayar ko?" Ya gyada kansa yana lumshe Ido. Hakan ya sake jefa ni a damuwa da sha'awa na sauke ajiyar zuciya a kasalance na furta." Ni ma na yi missing din Baba Yallabai baban soyayya." Kafin ya ce wani abu kiran da aka yi masa a wayar ya katse video call din. Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefe Ina sauke ajiyar zuciya gabad'aya hirar nan da muka yi ta tayar mini da hankali wani irin nake ji a jikina. Sai gefin magriba na fito falon daga cikin d'akin Hauwa na ji kukan yaron ya tsananta da saurin gaske na shiga d'akin na same shi kwance cikin net dinshi yana ta wutsil-wutsil towel ya toshe masa hanci. Da azama na zuge net din na d'auko shi fuskarsa ta yi jazur saboda da alama ya jima yana kukan. Na zauna gefan gadonta ina jijiigashi gabad'aya ya shid'e a tunanina tana bandaki na tashi tsaye dashi a kafad'ata na tsaya kofar band'akin ina kiran sunanta shiru bata amsa ba kuma babu motsin ruwa. Sai kawai na kutsa kaina ciki wayam babu alamunta. Da sauri na fito gabana na dan fad'uwa na tsaya ina rarraba idanuwana a d'akin ban ga alamun komai ba.. Na fita kai tsaye kicin na nufa Baba Tabawa ta kammala abinci dare tana gyara kicin din. Cikin kasala da sagewar gwiwa na furta." Baba ina Hauwa?" Sai kawai ta tsaya tana kallona kafin daga bisani ta furta." Ba ta dakinta ne Amina?" Na furta." Kwarai kuwa, fitowata daga d'aki kenan na ji kukan yaron nan koda na shiga d'akinta bata nan." Ta sanya hannunta ta kar'be shi a sanyaye ta biyo bayana muka tsaya a tsakiyar falon. Ina Hauwa za ta tafi to. Ni nake tambayar zuciyata dalili tunda ta haihu ban ga alamun fitina a tattare da ita ba asalima wani babin annashuwa da farinciki ta bud'e. Baba Tabawa ta sanya babban towel ta goya yaron ni kuma na d'auko hijabina na sanya na fita can harabar gidan. Daga nesa na tsaya ina hangen securitys a bakin gate. Masa'udu ya shigo da mota ya ajiye a wurin da motocin suke ya fito daga motar ganina a tsaye ya sanya shi da sauri ya nufo ni. Ya risina yana gaishe ni na amsa tare da fad'in." Daga ina kake domin kuwa zuciyata ta fara hasashen wani abu......✍️ *2k complete a kan telegram via 0542382124...Binta Umar gtbank* *07084653262* *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: Follow this link to# join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CDBG34xpZRZ5dZR86m1ftp?mode=gi_tmuna Bada sarin kaya muna saida pies kuma a farashi mai sauki muna aikawa ko Ina afadin nigeria dama wasu kasashe idan da bukatar hakan ku kasance a makawa collection zakuji dadin sayen kayanmu domin akwai sauki da Rahusa muna lagos komai da kike bukata inshaa Allah zaki samu a garemu cikin aminci πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯° πŸͺ¨ FUREN BADO πŸͺ¨ ZAINAB IDRIS MAKAWA BISSIMILLAHI RAHAMMANIN RAHIM,,,,,,,,,,,,, 7️⃣8️⃣ GA MAI SON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI NAIRA DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZENETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , , YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , , HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO PLEASE,,,,,,,,,,,,, *ZEE MAKAWA NOVELS* 1- TAKARI✈️500 2- FUREN JUJI🌼500 3- TARKOπŸ•ΈοΈ500 4- BAMU KADAI BANE...πŸ§Ÿβ€β™€οΈ500 1- SARAUTAR MATAπŸ«…πŸ»500 2- MURICCIN KAN DUTSE...πŸŽ‹ 500 3- BAHAGON RAYUWA 🩸500 4- KANIN AJALI πŸ‘¨πŸ»500 5- LOKACIN MUKE⚽ 500 6- MIJIN BUZUWAπŸͺ500 7- SARKA...πŸͺ’500 8- ABU CIKIN DUHU⚫ 500 9- ANA DARA...🐟 500 10- KARAN DAFI...🌾500 11- TUMFAFIYA...🌱 1000 12- DUBA MIN BAYA FAKON BIRI..πŸ‘€ 1000 13- JA YA FADO JA YA...πŸ”΄ 1000 14- MURFIN JALLO 🏺1000 15_ HAWAYEN KADA🐊 *Account* No *ZAINAB* *IDRIS* *MAKAWA* 2254380105 *ZENETH* *BANK* *PHONE* *NO* 08036959257 Mama da zancen yarta ke cin zuciyarta kasa daurewa tayi hakkuri tayi cikin mamaki ta daga waya ta kirata bugu daya a na biyu ta daga wayan. Suka soma gaisawa bayan gaisuwa take tambayan yan jikokinta kamar kullum take fadin suna part din kishiyarta suna wasa da yan uwansu. Amma baby kinsan na fada maki zancen zuwan yar uwarki garin nan ko kuma kinsan haihuwa tayi kece kuma kadai a cikin tan uwan ki garin nan amma baki zo kin mata andawo lafiya ba ko barka da arziki ansauka lafiya ? Dan juyawa tayi ta dubi mijinsu dake zaune yana cin abinci a gefenta tayi taga hankalinshi bai kanta nan ta soma fadin. Nicema zanzo na gaida ita mama ita bata san gidana bane salma fa tun batayi aure ba kin san namu baizo daya da ita ba abinda yasa ya dago kai ke nan ya dan dubeta a cikin mamaki ? Baiji me mahaifiyar namu ke fada ba a lokacin ya daiji amsan da matarshi ta bayar a lokacin cewa idan ta samu lokaci ai zata gidan ta duba mu. Ta kashe wayan a cikon bacin rai ya tareta da fadin badai salmace ta dawo ba kamar ba zata bashi amsa ba sai da kyat bakinta ya bude tana fadin itace ai ta kusa sati da zuwa garin nan . Shine bakije kun gana sa yar uwarki ba hindatu ina har haihuwa naji ance tayi a can kwanaki amma haka baisa kinje kin dubata ba don Allah ? Wai meke damunkine da wanan halin da kika dauko a cikon yan uwa hindatu kina matsayar babba a garesu amma kina abin assha haka don Allah ? Yau ni naji mutum don Allah yar uwarka ko yar uwata Alh ina ruwanka da shiga harkan yan uwana don Allah tunda ni ban shiga naka ba ? Ohh haka kikace tayi shiru bata amsa mashi ba shima ya gama ya shareta ya fice dakin tsuki taja tana binshi da harara tana bakar magana har ta kwashe kayan zuwa cikin kitchen dinsu . Bayan gama wayansu da mama kasa hakkuri maman mu tayi inda ta kira yaya farida da fada tana fada mata abinda ke faruwa a lokacin na kinzuwa dubamu da yayan mu batayi ba har lokacin. Haba mama me zaisa ranki ya baci kuma kema kinsan halin yaya ai da miskilanci halinsu daya aida salma din don itama rashin zuwan nata aiko a jikinta nagani data damu datayi min maganan haka ai. Amma kinsan hakan da zafi fatida ace kowa na zuwa wai babyce bataje ba meke damun yarinyan nan ne wai a rayuwa ta dauki akidan banza ta sakawa zuciyarta mara amfani. Har yan maganan can su hafsatu da tawagarta sunje sunyi abinda sukeyi duk da dai ai sun hadu da salma din da taje tana kusa ai hakan ba zai faru ba yarinya kamar wace iska ya hau kanta. Babu iska sai iskanci kawai da bin mugayen abokai da take ganin sunfi mata yan uwa a yanzu shine kawai abinda ke damunta. Tana kwasan sirin mu tana fada masu suna bata mugun shawara a kanmu din sun nuna duk bamu kaunanta a yanzu ni har mamaki yadda ta zama haka nakeji ? Kinga salma ko bata fada min cewa su gwaggo suje gidan sun kwasa ba fa sai zancen uwar mijinta da taje ta daurawa yarinyar zare take min . Tsuki mama taja tana fadin shine a ranta yasa ta fada maki hakan ai hjy innan ta iya da ita tasan likitace ba yarda zatayi ba zata dauki hakan da camfi yasa ta daura mata shi a inda ba,a gani ai tazo gidan nan tana min korafin hakan na kwabeta. Abune da manyan masana suka ta,amalli dashi ana daukan hakan a matsayin camfi ba kuma camfi bane tunda an yarda da akwai kandun baka a addini to me zai magance hakan ga mutane yanzu tunda jar ansan akwashi. Yadda yar nan nata take kamar kazan agric bul bul da ita ai ido da baki zaiyi yawa a kanta har yai mata illa basu sani ba batama isa ta cire ba tunda uban yar ya soma fada min da kanshi ai hjynsa ta daurawa yarinyar abin baki yace. Kai ya sulaiman shima yana biyewa salma suyi ta shirme wani lokacin ni abin nasu har dariya yakan ban wallahi tun dai lokacin da take da ciki din nan a can ? Bini bini ya bugowa babansu boy waya a tambayeni tace tana jin kaza saida nace dashi ya fita batunta don Allah haka ko wace mace take ji yayin ciki ai. Wai No wanan dabanne fa gashi babu kowa a kusa da ita kuma shiya hana zuwan ita inna din lokacin don sun shirya zata tafi daga baya yace kuma a,a ta zauna ni dai nagaji na koma fadin ban sani ba idan sun tambaya. Yanzu haka bata ma san yana wanan tambayan bama wallahi shi daine da kidimewarshi yake faman rawan jiki kamar wanda za aiwa haihuwan fari a gida ? Murmushin jin dadi irin na uwa da yarta mama ta sake tana fadin ke kuwa farida autan mamace fa ko kema kishin hakan kika soma yamzu ? Allah dai ya sauwaka abinsune na yan fari dana karshe sukeyi ni meya kaini shiga cikin shirmen can zan kira yayan mu din ai idan mun gama waya dake mama inji meya hanata zuwa har yanzu ? Karki soma ki kirata bance dake a kirata ba idan taga dama kada taje wa hakan ya dama a yanzu wanan ruwanta ai matsalantace bata dai canza yan uwa. To shike nan mama tunda kince hakan amma nayi niyar da mun gama wayan nan in kirata ai don hakan ba kyau don in ita akaiwa ba zataji dadi ba ai. Ni dai ban san ya sukayi ba don muna kaucewa dan uwa abinda zai bata mashi rai a tsakanin mu don haka antyna bata fada min komai ba game da zance. Muna zaune tare dashi bayan sallah azahar ranan sai aka turo wai anawa maigida sallama wani mutumne da mata yazo maigadinshi yazo ya sanar mashi Allah yasa ya gama cin abinci ke nan ya shigo sanar dashi din hakan . Matan ba zasu shigo bane ya fada yana mikewa tsaye don duba suwaye saiga matan suna shigowa gidan da farko ban shedasu ba na daiyi masu sannunsu da zuwa a cikin mutunci na basu wajen zama tare da umurtan Lamishi mai aiki data kawo abinsha suke fadin ai ba nisa suka fito ba. Ita antyna Na,ima uwargidansu na soma shedawa a cikinsu nake fadin lah antyna kune tafe ashe wallahi ban shedaku ba tayi dan murmushin nan nata tana fadin ai naga alaman baki shedamu ba ? Ga hjy cewa da uwar mijinsu na juya wajenta ita da yar uwarta ina masu sannu da zuwa suke min barka duban zainab nayi ina fadin ta miko masu yarinyar nan da sai lokacin ta mika yar garesu . Sun karba suna yabawa suna kuma mamakin girmanta kamar yadda hjy inna tayi min bayani za a yaba bada niyar komai a rai ba amma kasancewar bakin wani dafine sai hakan ya zamowa yaro matsala daga baya a rasa gane kanshi kuma ? Tare suka shigo gidan shida Alh Rufa,i nayi murnan ganinshi kwarai da gaske don ban manta alherinsa garemu muna kanana a lokacin. Duk da gwaggo hafsatu da gwaggo Asiya sunyi muna iyaka da zuwa gidanshi amma haka zai biyomu har gida da sunan yazo ganin mu yai muna alheri irin ta banjita ya kawo muna sabulan wanki omo da manshafawa dasu taliya yace a dafa muna don zuwa makaranta lokacin da inna ta barmu a garin ta koma kaduna da zama. Sosai naga mahaifiyarshi ta kara manyanta tayi min tsufa sosai a yadda na santa a baya ashe wai bata da lafiyane har nake tambayan meke damunta anty Na,ima ke fadin matsalan dai kamar ba,a ganr kai ba amma idan zai taso mata ciwon cikine yakan soma damunta dai haka. Sunan wani magani na fada kafin na danja tsuki ina fadin Allah yasa a sameshi a nan garin amma bari in rubuta a gani saidai yana da tsada sosai gaskiya. Tsohuwar na fadin a dai rubuta mata din a gwada ko za a samu din saita nemi kudin saya ai idan babu shi a garin nan sai a tura abuja ko za a samu a can din ko ? Yaya sulaiman ya fada nace zainab ta miko min hand bag dina domin in rubuta masu sunan maganin a duba nsn danta ke fadin hjy kinga biyomu ko yayi rana daga gidanta muke munje gaida ita mukace nan zamuzo gaisheki muyi maki barka tace zatazo itama don tynda kikai aure bata zo dakin ba ? Ashe zuwan namu alherine nayi dan murmushi ana ta hira ina rubutuna na mikawa anty naima ina fadin idan ba a samu wanan ba sai a nemi wanan din ayi amfani dashi. Kamar maganin na bata kyauta a lokacin tana tayi min godiya naji tausayinsu ya shigeni sosai nake fadin amma gaskiya babba idan son samune aje asibiti babba a dubaki a can zaifi . Kafin na rufe baki take fadin asibiti babba yar nan shine dai zai kaini kuma yanzu lamarin nasa sai a hankali bari a gwada wanan din mu gani. Da ace kin soma shiga office ne idan mun koma sai azo da ita abuja din yanzu kuma tana cikin hutune bata soma aiki ba a dai gwada wanan din kafin lokacin na fada. Na mike zuwa daki tsaraba na hado masu na kwarai na fada na kawo masu har mijinsu din muka fito da ledoji manya guda biyu ina fadin banga mai sunan antyna Azizzah ba amma gashi nan na hada da nata wanan kuma nasu babbane Alh ga naka. Mamaki sukeyi sosai suna fadin tsaraba haka kamar mun kawo maku wani abu wanan shine abin munji dadu sosai da zuwan nan naku yaya ya fada a cikin farin cki. Zasu tafi nake fadin Alh sai yaushe zaka leko kuma kafin mu tafi yace zaku kwana biyu a nan ke nan nace to zamu kai sati biyu zuwa uku dai insha Allahu munzo ganin gidane. Ka dai leko zuwa gobe ko jibi ko jnka samu lokaci don akwai maganan da nake son muyi dakai din yace to shike nan suna gadiya muka rakasu har waje bakin motarshi sai lokacin na kara yarda da suna cikin yanayi gaskiya. Mun dan jima a waje muna hira dashi kafin shigowan baba yaro dayasa muka koma gida nida zainab muka barsu a wajen karshe kwasa sukayi suka fita zuwa nasu tsabgogin. Suko basu je gida ba saida sukayi yawon shaguna suna neman maganin basu samu ba sai wani aka nuna masu kudinsa kuma har yafi yadda nake zato ashe ? Sun bugo min waya suna fada min dama kamar nasan haka zai faru na amshi layinsu na kira suka samu nawa shine saukin communication a yanzu dama waya. Nace su karba din nake tambaya a nawa aka samu ya fada min nace turo min account din ka Alh in turo kudin ya tsaya cewa ayi haka kuma salma ba komai nima ina son albarkan uwata na fada cikin wasa. Bayan na turo mai kudin har dana cefane ya gani yake fadin masu abu na inda suke mama yarinyar nan kudi ta turo min haka masu yawa fa yanzun nan. Da alama ba daya suke da yar uwarta ba ai don alama ya nuna hakan ko cikin fahintarta yanzun nan dana ganta . Hindatu nan ta bata kanta wajen bakin rowa da kin son mutane naso yarinyar nan amma ta bata rawanta da tsale da mugaiyan halaiya marasa kyau da ba,ason musulumi dashi. Rowa ai bala,ice babba ga mutum kace kai ba a taba cin abinka saidai ya lalace ka zubar ai kinga hakan baiyiba a rayuwa. Sai bayan sun koma gidane yayan mu kejin cewa sunje gidan mu ai barka sun samu taro na arziki daga wajena sosai ga tsaraban dana basu har azizzah da bata tafi ba take nuna mata nata ita Na,iman take fadin harsu hjy muka tafi suma sun kwaso rabonsu. Rantane ya baci sosai da jin tankar kaunan da mijin nasu yayi mata watau ya shanmaceta ke nan yakai matanshi har da mahaifiyarshi ba tare da sanin ta ba ? Inda take fafin yayi hakane ya nuna min iyakata sai kishiyar tayi mamaki tace iyakar me kuma hindaru ina sonki dai aka tafi wajen nan ai ? Da domin nice maman Abba ai zai fada min zaku tafi ko tunda yasan banje ba har yanzu na subosu ? Bakije ba hindatu saboda me ta tambaya cikin mamaki tace abubuwane sukai min yawa yasa ban samu zuwa ba har wanan lokacin. Gashi ya kwashe ku kunje ai sai ace wani abune hakan gaskiya ni dai ba a kyauta min ba indai anyi sanoda nine ta fada a hasale tana wucewa kayan ma bata tsaya ta duba ba don takaici Ganin hakan yasa uwargidan nasu fita daga part din cikin mamaki taja bakinta tayi shiru ba tare data fadawa kowa wani magana ba akai. Inma tana da magana ta samu mijinsu shi da ya kwashesu yakaisu don yayi mata gwaninta gashi hakan ya zamo laifi a wajenta kuma don da itace farin cikin hakan zatayi don an mutunta ta a nan. Amma sai gashi taga ita ba haka bane a wajenta ke nan akwai wani magana a kasa wanda bata sani ba ita. Itako hindatu tana shiga daki waya ta dauka ta dannawa Ramatu kira bayan ta dauka take fada mata abinda ke faruwa da tarkacen da Na,ima ta kawo mata an basu tsaraba. You see abinda nake fada maki ke nan kinki ki gane gashi ai wanan banzayen sun tafi da sunanki sun kwaso arzikinsu kina kallo. Wai Ramatu baki ganewane nifa tarkacensu baya gabana na fada maki suyi min irin wanan cin fuskan kuma in koma ina lakata a karkashin yar karaman kanwata ta baya don Allah ? Kina da ja da ubangiji ke nan besty kamar kin nuna baki yarda tsarin ubangiji bane a kanku har yanzu ? Hakan shine daidai a wajen Allah ke ki fita gidanshi ita ta shiga taji dadin duniya tare daku dama haka lamarin Allah yake idan ya tashi abinsa. Wai besty ke da bakinki kike fadin haka a yanzu da salma wata babbace can ko wata mai bin bokaya da sai jnce ta mallake har dake wallahi. Ba hakana bane hindatu na fada maki ummah tayi min nasiha kan zancen nan shiyasa kike jin ina cewa kiyi hakkuri ki tafi kawai naji ta fada don ba zata iyawa kawar nata gardama ba . Yadda ta kyale mijin nasu bata yi mai magana ba shima haka ya shareta bai fada mata cewa sunje wajen salma ba ai saima mamaki da duk sukeyi da junansu. Inda ita tana mamakin yadda ya iya zuwa gidan sulaiman din to yace mashi me yaya zai gabatar mashi da kansu a lokacin matsayinshi na mijinta a wajenshi. Tsuki taja tana rayawa a ranta cewa sai dai in salma zata fada mashi ba ji yadda ya koma yanzu daya talauce dinnan ita kanta yanzu haushi yake bata sosai wallahi kamar bashi bane dan kwalisa a baya da kake so dagani amma yanzu duk ya koma wani jagal dashi haka babu dadin gani ai sai yasa sulaiman din jin dadin hakan a yanzu. Shikan Alh Rufa,i cefane yayo da kudinsa yakaiwa mahaifiyarshi nata ya kawo gidanshi dama ranan Naimace zata karbi girki ta shige kitchen ta shiga dahuwa abinta tana daki duk haushi ya kumeta a lokacin. Bayan mun gama wayan dashi ya bugo min yana ta zabga min godiya nan nake tunane ta zan taimakawa bawan Allah nan nima. Don bani manta alherinshi akan mu a baya ya taimaki rayuwan mu a lokacin da muke cikin bukatan a taimake mu din don banda shi da kawu hassan da kanzo dubamu ya kawo muna abu wanda a karshe baba zaisa mu fito da abjn yace a raba dukka gida muda matanshi wanan yasa yaya fadila ta soma dabaran boye wani abin idan an bamu a lokacin don ya dan wadace mu. Ban fadawa kowa shawaran dana yanke ba amma nayi alkawarin zan taimaka mashi din hakan yasa na shawarci mijina kan zance kada yazo yaji daga baya hakan bai mai dadi ba. Lokacin dana fada mai shawaran dana yanke din sai cewa yayi kin rigani ke nan nima nayi tunanen a taimaka mai ko ya dan farfado ya kama iyalinshi ko don saboda ita hindatu din da yake aure ?. To kuma sai naga kada yayi tunanen mun raina mashi ga hakan da muka ganshi ba laifi zan kara maki wani abu idan yazo din kunyi shawara dashi . Mai karatu ban tabo maki bangaren jamila ba don mun hadu ranan da naje gaida hjy inna gidanta ina jin wani ya fada mata cewa gani gidan ai. Sai gata ta shawo kwalliya ta shigo tana fadin wai inna tana da dan goro ta bata zuciyarta ke tashi tun safe ? Goro jamila yaushe rabona da goro ai tunda likita ya hanani ci na kiyayeshi ko an ban kyautarwa nakeyi don ma kada in gani a kusa dani inci. Ta juya inna din ke fadin baki ga bakin ku bane sunzo gaudamu jamila ga yarki can a hannun zarah ke miko mata ita ta ganta mana ? Baki suwaye kuma ta fada tana wani abu kamar irin manta nan yan dandi inna tace jam salma din ne abokiyar zamanki baki gane ba ga yarki nan ai bakutu da ita. Humm inna ke nan kina son wani zance aini banda wata abokiyar zama kema kin sani saidai in nashi abokiyar zaman zan yarda. To haka abin yake lokacin na dakatar da wayan da nakeyi nace haka zalika don bansan da wata shara a gidan mijina ba irin haka ? Banda surutu amma kuma bani barin kota kwana ga duk wanda yaso kawo min raini a take nake mayar da martani ga mutum haka halina yake. Ta zata zatayi min iskancinsu da fitsara irin da nasan su gwaggo dashi tun a baya sunawa mutane na cin fuska shine itama ta yafa tazo zatayi min a lokacin. Sai na fahinci idan na biye mata a wajen yadda take haukan nan zamu zamo daya da ita a lokacin mu bamuzo wajenki ba gurin uwata nazo don ke baki da matsayin da zan tako zuwa wajenki dama. Na kara fada mata daga haka nayi shiru ina dakilan wayata itako sai abinda ta manra yake fitowa bakinta zagi harda iyayye da duk wani shakikina take hada min a lokacin. Ita ko inna sai fadi take da nasan rashin mutuncin da zakuyi ke nan da ban furta hakan ba a gabanki ? Ni dai banyi magana ba ban kuma san wanda ya kirashi ba na daiji muryanshi ya shigo yana fadin dama na fada maki duk kikai min haka a gida ba zan kyale ko waye ba yanzu meya kawo ki nan wajensu ko sun shiga bangarekine ? Kazo ka shigar matane na taba yar gwal ko toka shigar mata din mugani ai ina iyawa daku duka dama kai ka ja min raini har take gani kamar tafi kowa a yanzu ? Duk wanan abin nice na jawoshi ko jamila nidana nuna maki yarku shine kika mayar da abjn fita inna ke fadin hakan a cikin damuwa lokacin. Ki fice nan ki basu waje ko yanzu ranki ya baci dake da duk wani na tare dake kuwa a garin nan meye haka son Allah kin koma kamar mahaukaciya saboda kishin banza da wofi ? Dama ai iyaka kace zaka sakeni sanoda ita ko ka sake din ita kuma ta samo zani ta goya ka dashi ta kewaye garin nan tasa ka sakeni taji dadi ? Inns sai kolarin fitar dashi waje takeyi nikan hankalina yana a waya ban kula da haukanta ba don na zuba mata dafi a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *2K Complete ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP 1K...0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *109* Kai tsaye ya furta." Na kai Hajiya k'arama tasha zata bi mota zuwa bauchi don haka na ji tana fad'a a waya kafin mu isa." Ba tare da na sake cewa komai ba na kad'a kaina na koma ciki gidan raina a masifar b'ace. Anya kuwa Hauwa tana da hankali ta haihu kwana biyu kacal saboda mugun abu ta gudu ta bar jaririn da ta sha dawainiya da wahala a kansa kafin ya zo duniya ta kuma ci kwakwa duk a kansa tare da tsallake siradi. Ga kuma d'aita irin ta haihuwa da rashin kwari a jiki, wannan ba tunani ba ne gaskiyar magana a wannan karon ba ta kyauta ba, shi jariri ina ruwansa kuma hakkinsa kad'ai ba zai bari ta samu nutsuwa ba a duk inda take. Baba Tabawa ta dinga sallallami tana fad'in." Wannan wane irin sakarci ne Hajiya Amina, to shi wannan din da ta tafi ta bar shi ai hakkinsa ba zai bar ta, ina ruwansa da abinda ya faru." Ban ce mata komai ba na shige na je na d'auko wayata layinta na dingi kira wayar a kashe na kira ya kai sau goma amma is switch off. Na zube saman kujera ina Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un, wace irin masifa ce wannan ne? Na jima cikin wannan yanayin kafin na d'auki wayata dake saman cinyata kai tsaye lambar Dr Sailuba na nemo itace tsayayyiyar likitan da take duba ni a duk lokacin da na samu ciki mussaman cikin baby Nana ta taka muhimmiyar rawa kwarai da gaske. Abu na farko da zan yi shine samarwa da yaron abinci matsalar raino wannan mai sau'ki ne. Bayani na yi mata sosai amma ban sanar da ita cewa uwar yaron ce ta ajiye shi ba. Ba mu yi sallama da ita ba sai da ta tabbatar mini da cewa da kanta za ta shigo ta kawo mini duk abinda ya dace. Na kashe wayar tare da zubawa Baba Tabawa idanu tana ta faman safa da marwa a katafaran falon duk domin hillatar yaron da yake ta kusurkusur da alamun kuka. Sai da bacci ya d'auke shi tukkuna ta zo ta zauna a gefana tana fad'in." Ko a tarihi ban ta'ba ganin shashashar uwa irin Hauwa ba Hajiya Amina lallai ta gwadawa wannan yaro rashin Imani." Shiru na yi Ina nazari kafin daga bisani na furta." Tana so ta huce fushin abinda ubansa ya yi mata shine ta dire shi ta yi tafiyarta. Abin mamaki kuma ita da mijin nata jini guda ne mamansa ta cika nono ta bawa Mamanta wace irin zuciyace wannan." Kai tsaye ta ce." Zuciyar kafurai ce." Muka yi shiru cikin alhini kafin ta cigaba da cewa." Ita kanta na tabbatar da cewa wallahi hankalinta ba zai ta'ba kwanciya ba ciwon jiki da ciwon nono ma ya isheta. Murmushi na yi tare da cewa." Ciwon nono mai sau'ki ne a wurinta tunda likita ce tana da hanyoyin da zata magance abinta ciwon jiki kam zata sha ai haihuwa ba wasa ba ce." Haka muka kasance cikin zullumi da tararrabi har Dr Sailuba ta zo ta tafi muna zaune a falon cikin wani irin yanayi na mamaki da takaici. Ba ni da niyyar sanar da kowa wannan lamarin amma dole maigidan ya sani domin duk wanda ya sayi rariya ya san za ta zubar da ruwa, domin duk abinda yake faruwa shine sanadi me ake yi da zuciya irin tasa ta riko da ba'kar gaba, ita dashi duka kanwar ja ce shi ba'kar zuciya da gaba ita girman kai da rashin tsinkaye. Sai da daddare tukkuna yaron ya gama kiciniyar kukansa Baba Tabawa ta goya shi ya yi bacci sannan na samu sararin bude data. Na duba shi ta What'sapp din bai jima da sauka ba. Sallama na yi masa tare da barin datar a bud'e na ajiyar wayar na tashi na je na leka d'akin Baba Tabawa tana zagaye a d'akin bayanta goyo da yaron. Tausayinta ya kama ni haka kawai sun sanya tsohuwa wahala lokacin da suka jiyar da junansu dadi har suka samu 'karuwa bata sani ba, yanzu kuma sun haihu sun barwa wasu da raino. Ta juyo tana kallona a dan sanyaye na ce." Ya yi baccin ne?' Ta gyada kanta a hankali ta furta." Ya yi da farko dana kwantar da shi shine fa ya tashi na sake mayar dashi na goya." Na sauke ajiyar zuciya tare da fad'in." Ki yi hakuri Baba an tashe ki a tsaye." Sai ta yi dariya tana fad'in." To menene a ciki ni na kar'bi ladan Amina duk da ban ta'ba haihuwa ba ai na iya raino an sha kawo mini yara na yaye su ki tambayi Hajiya Sahura ni ce na yaye Yasir kanin Yusura." Da d'an murmushi na furta." Ai na ga alama duk da haka dai idan ya yi bacci sai ki kwantar da shi kema ki huta da tsayuwa." Ta furta." Haka za a yi in sha Allahu." Na juya na fita zuwa d'akina. Ina d'aukar wayar na duba naga sakon shi voice note ne na buda na saurara yana gaya mini Momi ta samu sau'ki sosai ta ce tana so mu gaisa. Ban mayar masa ta hanyar murya ba na rubuta masa a rubuce "Hauwa ta ajiye maka jaririnka ta tafi." Yana karantawa kuwa sai ya kira ta What'sapp din na daga. Ya ce." Me ki ka ce?" Na ce." Hauwa ce ta tafi Bauchi ta bar jaririn a gida." Cike da wani irin yanayi na rikita ya ce." Ta tafi Bauchi ta bar jariri bisa umarnin wa? Me yasa ba ku da hankali ne Amina?" Da mamaki a tare da ni na ce." Ba mu da hankali kamar yaya? Ni kuma ina ruwa don na gaya maka sai hakan ya zama lefi idan na yi shiru kuma nan ma ya zama lefi." Ya ce." Da zata ta tafi mai yasa ba ki hana ta ba, ashe ba za ki iya tsaya mini a gidana ba idan ba na nan?" Dan murmushin takaici na yi kafin na furta." Wallahi ni kaina ban san lokacin da ta tafi ba, kuma tunda ta haihu ban ga alamun fitina a tare da ita ba, sannan da kake cewa na hana ta ni na isa? zaman idda take yi fa tunda duk cikinmu babu wanda ka gayawa ka mayar da ita don ta haihu ta ajiye maka d'anka lefi ne, tun kafin ta haihu kake da dama a hannunka ba ka yi amfani da ita ba." A d'an raunana ya furta." Ba ki ga lefinta ba kenan Amina tare da hadin bakin ki Hauwa ta yi mini wannan wulakancin." Na furta." Kada ka d'auki hakkina wallahi ban sani ba, bata kyauta ba ai ko babu komai ta duba yaron ta tafi dashi idan ma ba zata zauna ba." Ya ce." Yanzu ina yaron yake?" Kai tsaye na ce." Na aikawa da Nabila shi." ''Kin aikawa da Nabila shi?'' Ya maimaita amsar dana bashi cike da mamaki. Na ce." Kwarai kuwa sai ta had'a gabad'aya ta ri'ke da 'yan uwansa ko ba haka ba ne tsarinka." "Ke ba za ki iya ri'ke shi ba kafin na dawo na yanke hukunci.'' Ya fad'a cikin sanyi murya tabbacin ya ji ciwon abin." Na ce." To ai gani na yi ba ni da nonon da zan ba shi, kuma ban iya raino ba da kula ba shiyasa na aikata mata dashi ta had'a shi ta ri'ke." Ya furta." Kin so kema ki tozarta ni Amina, na gode bisa wannan abu da kuka hadu ku ka yi mini Allah Ya saka mini." Bai jira jin abinda zan ce ba ya datse kiran ya ma sauka daga Whasap din gabad'aya. Na yi kasa'ke da waya hannuna ina dariya wai Allah Ya saka masa ashe da ciwo kenan. Hauwa ta kyauta bata kyauta ba, lallai abinda ta yi ya ta'ba shi ainun ganin bakinsa ya mutu ya rasa abinda zai ce. Kafin na kwanta sai da na sake zuwa na leka d'akin baba Tabawa yaron ya yi bacci cikin net din sa, itama ta kwanta amma ba ta yi baccin ba tukkuna na tsaya muka d'an yi maganar kad'an kafin mu yi sallama na je na yi shirin kwanciya. Da safe ina bud'e data sakon shi ya shigo yana gaya mini jiya ya tambayi Nabila ta ce ita yaron baya hannunta. Ina muka kai masa d'ansa. Dariya na yi kafin na rubuta masa cewa." Gidan marayu muka kai shi." Yana dubawa kuwa ya kira bidiyo call. Bai bari ma mun gaisa ba ya fara fadin." Kin ga ki gaya mini gaskiya don Allah ba ni son abinda zai daga mini hankali jiya ban yi baccin kirki ba Amina ban san ba ku da Imani ba sai yanzu." Idan ki ka karanta ba ki biya ni hakkina ba ina binki bashi. Ina kallonsa da gaske din a rikice yake yanayinsa ya nuna alamun damuwa da tashin hankali. Daki ne na mussaman shi da matar tasa don ina hangenta a can wani gado a kwance irin na marasa lafiya shi kuma yana wata kujera. Na ce." Ba mu da imani fa ka ce?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." Kwarai kuwa ba ku da shi wallahi, kin ga yanzu yadda za a yi tunda ita ta gudu ta bar shi ke ki yanke abinda ki ke so na biya ki ki kula mini da shi kafin na dawo." Na ce." A a daka bar shi a hannun Nabila zai fi alheri, idan zan kula da shi har sai na kar'bi kudi a hannunka mai ka mayar da ni." Ya ce." Nasan ki da alheri ai, don girman Allah idan yaron nan yana wurinki ki sanar da ni hankalina zai kwanta jiya na gaya miki mun yi magana da Nabila ta ce mini ba ki kai mata shi ba." Ganin yadda yake had'a ni da Allah ya sanya ni cewa." Yana hannunmu ni da Baba Tabawa cikin kulawa da koshin lafiya kuma tun jiya na kira Dr Sailuba ta had'a mishi duk abinda aka buk'ata." Ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Na gode sosai my love life Allah Ya yi miki albarka. A dan sanyaye na ce." Babu komai." Ina hangen Momin ta tashi zaune daga can wurin dake tana kallonshi shi ya juyo mata baya ya dage sai kalamai yake yi mini na dadin baki. Na ce." Ka juya ka ga ta tashi fa." Ya d'an juya a hankali yana fad'in." Ok jiya na ce miki tana so ku gaisa ko, amma bari mu bari zuwa yamma zan sake ta'bo ki sai ku gaisa." Na ce." To shikkenan a ma sha Allah na ga jikin ya yi kyau Allah Ya kara sau'ki." Ya amsa da Amin Amin mun gode giwa Allah Ya yi miki albarka." Na ce." Amin a takaice. Ni na fara datse wayar saboda ganin kamar tana buk'atar magana da shi. To yaro dai na d'auka tunda ta tafi ta bar shi zan yi iyakar bakin kokarina. Bayan ubansa babu wanda nake jin zan gayawa ko Hajja kuwa amma tabbas nasan Hauwa rikici da gangami ta shiryawa kanta, dalili kuwa shine yadda abin nan da ta yi ya kidima shi ba zai kyaleta ba, to ma ji ma gani dai Allah Ya kyauta. Sai bayan sallar azuhur tukkuna na samu Hauwa a waya. Ta daga hankalinta a kwance domin ban ji alamun nadama da danasani a muryarta ba. Jikina ya mutu sosai da kyar na furta." Kina ina Hauwa?" Kai tsaye ta ce." Ina nan Bauchi." Na danne takaicina tare da cewa." Ashe kin shirya hakan tuntuni to hakan da ki ka yi a ganinki daidai ne ko?" Da d'an murmushi ta ce." Shine daidai Amina, domin wa'adin zamana ya kare a gidan tunda na haihu yaro kuma ai gidan ubansa ne tunda ba dashi na zo ba, mai zai sanya na d'auko shi na kawo shi inda babu tarbiya ba Amina sunan Amadu fa ya fi sunan ubana an ce mini ubana ba komai ba ne a lokacin da na nuna shi din wani abu ne, tuntuni na gaya miki dama ba zan jure wannan rashin mutuncin ba." Cike da takaici na furta." Amadu fa aka ce shine Mahmudu Muhammadu. Ki tuna mai wannan sunan shine wanda aka yi duniya dominsa Annabi Muhammadu S.a.w a ganina wannan abin alfahari ne a wurinki." Ta yi murmushi tana cewa." A a ba da wannan niyyar ya sanya sunan Amadu ba. Abokinsa mai rasuwa fa shi yayi wa takwara na ce masa ina son sunan mahaifina tunda na farko ya sanya sunan mahaifinsa daga fad'in haka ya fara gaya mini magana tabbacin dama haushina yake ji to menene saura a tsakaninmu na fita daga iddarsa da dama." Na gyada kaina ina danne abinda nake ji a raina na ce." To kina ganin Allah ba zai kama ki da hakkin yaron ba shine ina ruwansa." Ta yi dariya tare da furta." Allah Ya yafe mini shi kuma idan rayayyene Allah Ya raya shi." Na yi shiru domin kamar kalaman bakina sun kare da kyar na ce." Yanzu mai ki ka gayawa inna Uwani." Da sauri ta furta." Tun daga farko a har karshe wallahi ban boye mata komai ba, Amina ai na yi hakuri na yi kuma biyayya, ke kan ki ban shure shawararki ba, na yi ta ha'kuri tsayin wattanin dana d'auka a matsayin sakakkiya mutumin nan baya kula ni kuma bai furta ya mayar da ni ba, duk wata dama ya samu bai yi magana ba yanzu kuma ai komai ya zo karshe na gaya mata komai haka zalika ma babu wanda bai sani na a family din Babanmu." "Kenan Hajja ta ji komai?" Na tambayata cikin zullumi. Ta furta." Kwarai kuwa d'azu nan suka gama waya da Inna." Na yi shiru Ina nazari kafin daga bisani na furta." Hauwa idan zu'kata sun huce a daidaita don Allah kuma yaron nan da kaina zan kawo miki shi gobe in sha Allahu rabbi, ki yi hakuri don girman Allah ki kar'bi d'anki kada ki wulakantashi domin bakisan baiwar da take tare dashi ba." "Na rantse da girman Allah a yanzu dai Amina ko kin zo da yaron nan sai dai ki koma dashi don wallahi tallahi ba zan karbe shi ba sai ubansa ya zo da k'afafunsa ya nuna nadama akan abinda ya yi mini, idan har ke za ki iya jure wulakancinsa ni kam ba zan iya ba. Ki ri'ke shi kawai na bar miki." Bakina ne ya mutu murus na rasa abin cewa tunda har ta riga ta rantse nasan abu ne mai mutukar wahala ko na kai mata yaron ta kar'ba......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *2K ON TALGRAM WHAT'SAPP GRUOP 1k VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *110* To wannan lamarin na su sai dai na ce Allah ya sawwa'ke har ga Allah ban so rigimar tasu ta yi tsayin da har magabatansu su shiga ba. Saboda daga shi har ita babu yaro duka sun mallaki hankalin kansu su din masu yi wasu gyara ne, duk da mas'ala ta aure akan sameta a kowane gida amma abinda yake cikin gidan nan namu sai dai mu godewa Allah daga wannan sai wannan ashe kalmar hakurin nan da manya suke nanata mana akoyaushe tana da tasiri gabad'aya sha'ani na aure a yanzu ya zama abinda ya zama domin kuwa k'alubalan da ke cikinsa ba kowace macace zata jura ba. Zawarawa sun yaiwata wad'anda mazajensu suka rasu ga 'yan mata nan birjik a gari suna yawo idan ma kana murna ka aurar da d'anka to ka bi shi da addu'a kawai domin kuwa zamani ya zo da mata da yawa suke ganin gwara su rayu babu aura akan yin sa saboda riskar rikici da tashin hankali idan ba a yi dace ba. Abu ne a bayyane ba kowane a yanzu zamu bud'e baki mu gaya masa cewa ba ma cikin nutsuwa ya aminta ba. Dalili ana ganin Ubangiji ai ya yi mana gamnakatar da auran attajiri wanda ba mu rasa komai ba na jin dad'in duniya tabbas ba mu rasa komai na jin dadi ba amma mun rasa kwanciyar hankali domin kuwa idan ana murna an kashe wannan wutar sai ya sake kunno wata da kansa. Kwanaki biyu ba ni ganinsa a online hankali ya tashi domin tunda suka tafi tsayin sati uku kullum sai mun yi magana. Na shiga damuwa sosai na kuma kasance cikin duba wayata a akai-akai. Misalin goma da rabi na yi shirin kwanciya don ban jima da fitowa daga d'akin Baba Tabawa ba na d'auki wayata na duba sakon voice note din shi ya shigo na bud'e ina saurara yana gaya mini suna kan hanyar dawowa gobe domin sun gama shiri kuma alhamdulillahi ta ji sau'ki." Jin haka ya sanya hankalina kwanciya domin tsakani da Allah kwana biyun nan na yi sune cikin fargaba da tunanin halin da suke ciki ko kuma na ce yake ciki tunda ta hanyar wayar ne kawai muke magana. Washe gari da wuri kuwa na kira yarinyar nan da ta yi mini 'kunshi ta zo ta zana mini baki da jaa kafafu da hannayena. Ya yi kyau ainun. Na ce da Baba Tabawa ta shirya masa towon somovita ayi miyar kuka domin duk cikin kayan kad'i ya fi sonta. Tare muka shiga kicin na taimaka mata tana goye da yaron a bayanta yana bacci muna d'an ta'ba hirar rashin lafiyar Momin har muka kammala tsaf towo semo da farfensun kayan ciki tunda shi ma yana daya daga cikin abinda yake so domin shi kam ya fi kauri ga abincin gida. Lemo kam ba kowanne yake sha ba ya ma fi jin dadin zob'on da Baba Tabawa take yi masa mai cike da kamshin citta da kaninfari. Na riga ta fitowa daga kicin din wanka na yi a gurguje na d'aura alwala tunda daf ake da kiran sallar magriba na shirya jikina a cikin atamfa java kalar sararin samaniya mai d'auke da adon zaiba da stones a tare fittedgwon ce ta d'an kama ni amma ba sosai ba. Yanzu ina iya sanya matsatstsun kaya dalilin maganin tumbin da na yi amfani da shi wanda ya narkar mini da mugun tumbin da ya yi mini zuguda a ciki. 08089965176 wurin GARKUWAR MATA na sayi maganin yana da kyau sosai kuma harbel ne ba shi da side effect. Ban yi cikakkiyar kwalliya ba domin can dama ban fiye fenta fuskata ba na dai shafa hoda tare da sanya kwalli na sanya jan janbaki a le'bena. Na gyara gashin kaina sosai kafin na daura d'ankwalin daidai da zamani. Ni ce har da had'a kankana da zumar mata ta goron tula itama dai duka order ce daga wurin GARKUWAR MATA na hada da madara na cika kofi na shanye wannan hadin idan na yi shi yana bala'in saukar mini da ni'ima sosai gefe guda kuma ga ruwan kaninfarin da nake yaiwata sha shiyasa kusan koyaushe a jike nake don ba ni da matsalar bushewa balle matsi da koyaushe idan wata mu'amula za ta kasance sai ya yi kiki-kaka kafin ya samu damar ratsa jikina. Idan ki ka karanta ba ki biya ni hakkina ba ina bin ki bashi. Sai wajan takwas da rabi ya kira ni a waya yana gaya mini suna airport saukarsu kenan. Cike da kulawa na ce." To, shikkenan Allah Ya kawo ku gida lafiya." Ya amsa da kulawa kafin ya datse kiran. Na ajiye wayata ni ma na fita falon shiru Baba na dakinta. Zamana a falon da kamar minti goma ta fito har yanzu yaron yana goye a bayanta na ce." Wai Baba har sallah ma da yaron nan ki ke yi a goye?" Tana ko'karin zama kusa da ni take fad'in." Wataran ba, amma dai idan na ga baccinsa ya yi nisa ina sauke shi sai dai fa kafin na idar da sallar ya tashi, ai ya tsani kwanciya sai dai goyo." Ina dariya na ce." Dama ai duk abinda aka sabawa da yaro shikkenan sai ya tasirantu da shi ki dinga kwantar da shi ko zai saba." Ta furta." Ai rik'on hannu ga yaro irin wannan shine matsala Hajiya amma goyo daidai kenan, kuma idan dare ya yi sosai na kwantar da shi baccin mu muke sosai sai da asuba yake farkawa. Aikuwa kamar yana ji sai ya fara motsi ta ce." Af kin ji shi ko? shi fa baya so a goya shi a zauna zai kama tsalla ihu." Na ce."Sakko shi mu gaisa." Ta kwanto shi daga bayanta tsaf dashi a cikin kayan sanyi masu d'umi yana ta k'amshi ni kaina sheda ce yaron yana samun kulawa wurin Baba Tabawa tamkar yana rayuwa a hannun uwarshi. Na kar'be shi Ina d'an jijjigashi da fad'in." Yau za ka ga babanka yaro." Ta mike tare da fad'in."Bari na d'auko masa abincinsa." Ta nufi dakinta da saurin gaske. A kafadata na sanya shi ina d'an jijjigashi maigidan ya shigo tare da Sukairaju a bayanshi. Yana cikin suit ya zanzare sosai ya yi kyau da kayan dukda bai fiye tu'ammuli da su ba amma duk ranar da ya sanya irinsu ni kaina yana burge ni. Farin gilashinsa na ka'ida yana sakaye da idanuwansa na mike tsaye da yaron a kafadata yayin da shi kuma ya juya yana kar'bar yar wasu takardu daga hannun Sukairajun ya ba shi umarnin tafiya. Baba Tabawa ta fito hannunta ri'ke da fida cike da madara ta washe bakinta tana fad'in." Sannu da zuwa sannu da hanya ranka ya dad'e fatan an dawo lafiya?" Ya amsa da kulawa. yana fad'in." Lafiya lau Baba mun same ku lafiya? Ya kokari kuma na gode sosai Allah Ya saka da miki da alheri." Ta d'an sunkuyar da kanta tana fad'in ." Babu komai wallahi, ai babu buk'atar godiya Alhaji." Bai ce komai ba ya dubi wurin da nake tsaye na saki fuskata sosai Ina fad'in." Barka da zuwa." "Barkanmu dai Allah Ya taimake ki." Ya fadi hakan cikin sigar tsokana kafin ya fara ko'karin haurawa samansa. Na kar'bi fidar yaron dake hannun Baba Tabawa na bi bayansa. Na same shi yana ta ko'karin cire safar dake kafafunshi. Ya dago yana kallona kafin ya furta." Amarya." Ban ce komai ba na zauna gefanshi ya miko mini hannu yana fad'in. Ba ni abokina mu gaisa." Na mika masa yaron ya kar'ba ya tsira masa ido sosai kafin ya gyad'a kansa yana fad'in." Wallahi Amina Hauwa ba ta da imani ko kad'an." Na yi shiru Ina kallonsa ya sanya bakinsa a kunnan yaron hagu da dama ya jima a haka kafin ya sake duban fuskarsa ya ce." Amadu shine sunanka, ina ro'kon wanda ya ba ni kai ya rayaka tafarkin addinin Islama, ya raya mini ku bakidaya." Na amsa da "Amin Ya Allah." Ya miko mini shi yana fad'in." Ina can hankalina yana nan Amina Amma alhamdulillahi na ji dadin ganinku cikin nutsuwa da kwanciyar hankali lallai Allah Ya azurtani da matar rufin asiri kuma Mar'atussaliha, na godewa Allah na kuma gode mini bisa abinda ki ka yi mini." Maganganunsa sun sanya mini mutuwar jiki, na dube shi karon farko da na ji tausayinsa ya tsirga mini. Na janye idona daga kansa can kasan zuciyata ina ji tana fad'in cewa ba matausaya ba ne ba fa. Na danne dai tare da furta." Ya mai jikin, koda yake alamar karfi tana ga mai 'kiba wai ka gan ka kuwa yadda ka wani zanzare wai kuma jinyya ka tafi gaskiya ka fi kama da wanda ya tafi yawon sha'katawa." A sakarce ya kalleni yana ko'karin cire gilashin idonsa ya ce." Wane sha'katawa bayan babu babbar sha'katawata a kusa da ni, ai ke ce karshen sha'katawa Amina." Murmushi na yi ina kallonsa. Ya ce "Da gaske nake gaya miki kece sha'katawata, na ga kin yi kama da amarya yau tunda na kalle ki nake ganin kamar sabuwar amarya na yi." A gajarce na ce." Wani Abu ya canza a jikina ne?" Ya furta." Kwarai kuwa ga lalle an ranga'da mini, an yi mini kwalliya na yaba sosai sai a fadi nawa ne kudin lallan na biya." Na furta." Ai ba zaka iya biya ba." "Me yasa?" Ya fad'a yana ko'karin mi'kewa tsaye.'' Ban ce komai ba ni ma na tashi ina fad'in." Bari na mik'a yaron nan wurin Baba ta goyo shi bacci zai koma." Ya furta." Ya yi, zan yi wanka yanzu na sauko cin abinci sai mu sake gaisawa ko." Na ce." To shikkenan sai ka sauko." Hanyar fita na nufa ina d'an jijjigashi yana ta motsin kuka. A falon ya same ni muka nufi wurin cin abincin tare yana fad'in." Hauwa ta kai k'arata wurin Hajja Amina, don Allah tsakanin ni da ita wanene mai gaskiya." Na gyara masa kujera ya zauna yana ta kallona. Ban tanka masa ba wai don ba ni da abin fad'a kawai maganar ce ta ishe ni haka, na ma daina sanya musu baki abinda ya shafe su ne wannan tunda shi har yanzu gani yake yi yafi ta gaskiya. Duk yadda ya so da mu yi maganar Hauwa akan abinda ta yi ban biye masa ba, ya gaji da takalo maganar ya bari ya shiga wata ina d'an taya shi kafin a kira wayarsa. Momi ce ban san me ta gaya masa ba na ji dai yana fad'in." Subahanallahi, bari gani nan zuwa kada ki sake tashi tunda jiri na dibanki bari na zo yanzu." Ya kashe wayar yana kallona ni ma shi din nake kallo da 'yar damuwa yake fad'in." Bari na sake dubo mai jiki na dawo Amina." A tak'aice na ce." A ce ina yi mata sannu. Ya mike ba tare da ya kwashi wayoyinsa ba ya nufi hanyar fita yana fad'in." Yanzu zan dawo in sha Allahu." Ban ce masa komai ba illa ido da na bi shi da shi har ya fice, ina d'an mamaki jiri kuma? Allah dai ya kawo mata sau'ki shine abinda za a ce. Dama kusan tare muka ci abincin don haka ko minti biyar ban kara a wurin ba ni ma na tashi tare da diban wayoyinsa da ya bari na shige d'aki wanka na sake yi na shirya da kayan bacci na zauna jiran sa.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *2K Complete a TALGRAM WHAT'S APP GRUOP 1K VIA 0542382124.... BINTA UMAR GTBANK.* *V-VIP AREWA PEN* *07084653262* *111* Wayata na d'auka ina dubawa amma hankalina gabad'aya yana wani wuri. A k'alla yanzu da fitarsa kimanin minti talatin kenan, a ganina idan ba wata gagarimar matsalar ba ce ya ci ace ya dawo kuma idan kuma ba acan din zai kwana ba. Zuciyata ta dinga yi mini sake-sake abubuwa da yawa ina dojewa ba ni so na aminta da sashenta ya zamana kuma ba hakan ba ne, uzuri akan ciwo abu ne mai kyau wanda hakan yake da tabbacin kai ma ba ka wuce a jarrabe ka ba. Amma tabbas zai dawo komai dare tunda duka ga wayoyinsa a hannuna. Sahura na ga ta turo mini voice note na shiga da sauri na kunna ina saurara. Ni sai abin ma ya ba ni dariya wallahi.. Cikin jajantawa kanta da alhini take gaya mini wai Idiris an yi musu rabon gado wata tsohuwar gonar mahaifinsu aka gano a wani k'auye shekarun kusan talatin da biyu da ya sayi wurin ya jefar abinka da mutanan da tunda ya sayi wurin babu wanda ya ta'ba d'auka a cikin manyan yaransa ya nunawa ko 'yan uwansa ba su sani ba tun a wancan lokacin ya kai takardun wani tsohon banki da ya daina aiki a yanzu da yake dukiyar ta halak ce bincike dai har mahukunta suka tabbatar da gonar mahaifinsu ce tunda da sunansa a rubuce a takardun da aka binkito takardun gonar a bankin Yanzu dai tana gaya mini an sayar da gonar miliyar sittin da biyar Idiris ya samu miliyan takwas shine wai ta ga alamar wai yana neman aure. Na ci dariyata na k'oshi cikin zuciyata ina fad'in." Idan ban da tarangahuma ta da namiji fisabilillahi nawa miliyar takawas take da har za a rakito aure a kanta. Matsalar Malam bahaushe kenan daga zarar ya dan samu fargaba ko yaya ne sai ya ce aure zai kara. A tunanina wannan dama ce da idiris ya samu da zai juya kudin domin dogaro da kansa. Ba a ce masa kada ya yi aure ba amma ya bari ya tsaya sosai da k'afafunsa tunda zahirin gaskiya Sahura tana kokari sosai kusan ita dashi rabi da rabi suke yi kan harkar karatun yaran ma ta fi shi kokari sosai da sosai ni kaina duk wata na kan tura mata abinda ya sawwaka tunda nasan tana da d'awainiya sosai. Wannan dalilin ne fa ya sanya wasu matan cire tausayi da imani akan mazajensu domin wallahi duk namijin da ka nunawa soyayya daga karshe yana samun dama zai yi kokarin jefa ka a rana. Ganin ban bata amsa ba sai kawai ta kira na dubi agogo goma da ashirin da biyar na dare. Lallai abin yana damunta tunda ta gaza ha'kurin bari gari ya waye Na daga ina fad'in." Sahura." Ta ce." Shine don wulakanci na turo miki sa'ko kin bade kin saurara kimanin minti goma ina ganinki a online din amma ki gagara ba ni amsa." Muryarta na d'an rawa ta kai k'arshen maganar. Ta d'an ba ni tausayi na danne dariya da nake so na yi na ce." Wallahi na saurara Sahura kaina ne kawai ya daure shiyasa ki ka ji na yi shiru mamaki ne ya ishe ni, in banda abin Idirs nawa miliyan takwas take da zai rakito aure maimakon ya juya kudin su ninku ba mu hana shi ba amma ai sai ya bari mu murmure tukkuna." Ta furta." Wallahi da ni yake zancen Amina muddin ya ce zai yi aure a irin wannan yanayin sai dai ya sake ni domin ba zan iya zama da butulu ba." Na ce." Ki saurare ni Sahura, ki bi komai a hankali dan Allah, kin san yanzu idonsa a rufe yake yana ganinsa da 'yan canji zai iya aikata komai. Kada fushi ya sanya ki zo kina nadama daga baya, ki yi hakuri ki bi a sannu ba ni son wata matsala ta faru dake." Sai kawai ta fashe da kuka tana fad'in." Wallahi Amina ban ta'ba tsammanin Idiris zai mini haka ba, ki duba ki ga fa irin wahalar da nasha da yawon haya da ba don kin ba ni wannan gidan ba da tuni fa muna can zaune a wannan tsukakken gidan da masu shi suke yi mana wulakancin duk lokacin da suka zo kar'bar kudinsu. Kin dai sani ke kanki kin sha cika mana kudi idan lokacin biya ya yi. Yanzu yana ganin bashi da matsalar biyar kudin haya. An aurar da Yusura kuma ina d'aukar albashi tare da samun kayan abinci sa'i da lokaci a wurin aiki shine ya sakar mini wahalar gida ta sauran yaran da ya samu kudinsa bai yi tunanin komai ba sai na aure yanzu don Allah Amina idiris ya yi mini adalci." Na ce." Bai yi ba wallahi, kuma ya yi butulci, ai shine na ce miki ba mu hana shi ya kara aure ba amma ya bari ya tsaya da k'afafunsa sosai yanzu ba lokacin da zai rakito wata ba ne. Amma kin san yawanci tunaninsu daban ne da namu kuma idan idon su ya rufe akan mace suna aikata komai a yanzu Sahura ba fata nake yi ba don Idiris ya rabu dake ba wani abin ba ne wallahi tunda baya hankalinsa." Cikin dusashewar murya ta ce." Na gaya miki wallahi duk ranar da ya daura aure da wata to ni kuma na gama zama da shi har abada kuwa." Bata bari na yi magana ba ta datse waya. Na yi sororo da tawa a hannu Ina mamakin al'amarin. Gaskiya Idiris bai kyauta mana ba wallahi. Ina binki bashi domin littafin nan na kudi ne. "Wallahi jiri ne ya d'ebe ta ta fad'i, Allah ma yasa ina d'akin da ban san abinda zai faru ba." Nabila ce take yin wannan maganar yayin da take zaune kusa da 'yar uwarta dake kwance a sambal a gado sai kace matacciya. Ya ce." Dama ai kamata ya yi ki kasance tare da ita a koyaushe saboda jikin nata babu kwari har yanzu, sai kin kula sosai." Ya kai karshen maganar yana duban dirowar da take gefan gadon da Momin take kwance wata madaidaiciyar jarka ce cike da rubutu da kofin gilas a ajiye. Ya dubi Nabilan yana fad'in." Ta ci abinci?" Ta ce." Yanzu dai zan kawo mata?" Ta mike da sauri tare da kama hanyar fita. Ya zauna kusa da ita a hankali ya kira sunanta "Maryam." Ta bude idonta tana ko'karin tashi zaune ya sanya hannu ya dago kafadunta ta tashi." Me yake damunki yanzu?" "Ba ni jin komai sai jirin fa, daga zarar na mike zan ji hajijiya baya ga haka kuwa sai dai nace alhamdulillahi." Ya gyad'a kansa cikin kulawa ya furta." Za ki daina ji in sha Allahu daga zarar kin ci abinci kin sha magani yanzu, amma menene a wannan a gefanki." Ta dubi wurin da yake kallo a hankali ta ce." Sanyawa na yi aka rubuce mini al'kur'ani mai girma. Ya d'an jima yana dubanta kafin ya ce." Hakan yana da kyau, kina ji ko dole fa sai kin rage yawan tunani da damuwa, ba ke kad'ai ce ke d'auke da wannan cutar ba kuna da yawa ko a asibitin ma ai kin ga wad'anda suka fi ki jin jiki, cuta ba mutuwa ba ce za ki samu sau'ki in sha Allahu, ki dinga sanya hakan a ranki." Sai ta sanya kuka tana fad'in. Anya kuwa, ga ni nake yi mutuwa zan yi wallahi, ba fa na jin dad'in duniyar gabad'aya, ciwon nan shi zai kai ni." Ya ce." A a, mutane nawa ne suka yi jinyya mai tsanani kuma suka tashi ki daina sanya damuwar hakan a ranki za ki ji sau'ki in sha Allahu." Ta dinga share hawaye tana girgiza kanta har Nabila ta shigo da plate din abinci madaidaici ya kar'ba ita kuma ta juya ta fita. Kusa da ita ya matsa sosai da kansa ya bata abincin da maganganunta ta sha. Ya sanyata a jikinsa sosai yana rarrashinta cikin tausasawa kamar yadda ake yi wa mai ciwo. Kusan sha d'aya da arba'in sha biyu saura kenan ta yi bacci ya fito Nabila na falon tana kallo ya ce ta shiga su kwana tare. Sallama ya yi mata a gurguje ya fita. Cikin baccin da ya kwashe ni na ji motsin shigowarsa d'akina. Na bude ido ina kallonsa yana zama gefana kamshin turare biyu ya gauraye hancina k'amshinsa daban ne kuma ya zauna a jikinsa tuntuni duka kayansa k'amshin suke yi yanzu hancina na shako mini wani kamshin na daban. Na tashi zaune ina d'an dubansa na dubi agogo sha biyu saura minti goma sha biyar ya samu kimanin awa uku babu wani abu a can. Na ce." Ashe za ka dawo?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." E, me zai sanya ni na kwana bayan ga amaryata tana jira ko ba ki yi kewa ta ba?" Ya fad'a yana d'an matsowa kusa da ni. Sai na ji kawai haushinsa ya kama ni, na tsani munafurci wallahi ko bai fad'a mini ba ya rungume matar nan a jikinsa tunda ga k'amshin turaranta nan a jikinsa. Na ce." Aikuwa da ka sani ka kwanta a can kawai dubi agogo fa ga gani." Ya rike hannuna yana murzawa ya ce." Kada mu yi wata hatsaniya dake a wannan daran Amina, ki ba ni hadin kai da k'warin gwiwa don Allah kada kishi ya sanya ki zobe lada da albarkar da nake ta shi miki tunda na dawo kike faranta mini rai, ina ta murna Allah ya amshi addu'ata a kanki, ki ru'banya ladanki kafin gari ya waye." Baki na zum'bura na ce." Me ka ji na fada yanzu, cewa na yi fa da ka sani ka yi kwanciyarka a can shine ya zama lefi bata fa da lafiya." Ya girgiza kansa yana fad'in." Ba ni da wani dalili da zan kwana a can, ai ta ji sau'ki kuma kwana na nawa a tare da ita, ai kina da hakki a kaina ni ma ina dashi a kanki kamata ya yi mu raya wannan daran ya zama ma mussaman a gare mu har ya fi na ranar amarcinmu daraja." Shiru na yi ban ce komai ba ya d'an shafa dokin wuyana yana fad'in." D'azu dana shigo na gan ki rungume da yaron nan a kafadarki sai dana na ro'ki Allah subahanahu-wata'ala da ya ba ni namijin ko'karin samar da makamacinsa a daran yau, za ki ba ni hadin kai ko?" Ya fad'a hucin numfashinsa na sauka a jikina. Na kalle shi na ga ya wani saki gabad'aya kansa a langa'be ido daya a kanne. Cikin zuciyata na ce." Yaudara da iya kalamai sai ka ce goggagen d'an bariki. Ya had'e hannunmu waje daya yana sakin ajiyar zuciya tare da d'an sake shigowa jikina. Ya kamo daya hannun na yana duba lallan yasa bakinsa ya sumbuta yana fad'in." Ko wannan da ki ka yi mini na ji dad'i har na ce Allah Ya shi albarka abinda za a ru'banya miki lada ne. Yanzu za ki cika she ladanki ina so ki nuna mini kwanzonki a wannan daran mai albarka." Na dube shi duk ya kanainayeni. Na ce." Wane k'wazo zan nuna kuma?" "Ya dago da sauri yana fad'in." Ki cinye ni a wasan gabad'aya hajiyata." "Umm" Kawai na iya cewa jikina duka ya shika. A hankali ya mik'a hannunsa ya kashe fitilar gefan gadon da ta d'an haske d'akin. Sai ya yi duhu sosai. Ya rike ni da kyau tare da d'an tura ni na kwanta ya yi mini rumfa shikkenan daga lokacin ni ma na kwarkwace muka zama kamar tuburarrun mahaukata. Da safe da wayar Hajja ya karya. Ga yanayin yadda yake amsa mata magana ya sanya mini kasala. Suna gamawa ya dube ni yana fad'in." Zan je kano yanzu Amina Amma ina sha Allah zan dawo yau idan kuma wani dalili ya sanya ni kwana zan kira waya na sanar dake in sha Allahu." Na ce." To shikkenan." Na yi shiru ina kallonsa yana kimtsawa. Na dai kasa daurewa da nace ba zan sake sanya musu baki ba, amma na gaza ha'kuri na ce." Ka ga abinda nake ta guje muku kai da Hauwa ko?" Ya dube ni yayin da yake sanya links a hannun rigar da take jikinsa ya ce." Ai dole dama za a zo wannan ga'bar na sani, kada ki damu ni babu abinda zai faru sai alheri ni dama ai ban ce ina sonta ba, sune suka dage za kuma ta san ni ta yi wa wannan wulakancin ai." Na ce." Kenan a ganinka itace mai lefi kafi ta gaskiya, ko da suka dage suna son auranka ka fad'i tsakaninka da Allah da annabi cewa kai ma baka sonta." Kai tsaye ya furta." Wallahi Samira nake so ba Hauwa ba Amina, ai na gaya miki tuntuni Samira da ita na fara soyayya nasan menene so, Allah Ya k'addara ba mu zauna ba ta rasu. Hauwa kam ba ni yi mata soyayya fitacciya gaskiyar magana" Na ce." To mai yasa ba zaka maye gurbin soyayyar da kake yi wa Samira zuwa ga 'yar uwarta ba, ka ji tsoron Allah wallahi yanzu da bakinka kake furtawa baka sonta. Amma mai yasa kake rayuwar aure da ita har ku haihu, menene bambacin Samirar da Hauwa tunda duka uwa daya Uba daya suke." Ya girgiza kansa yana fad'in." Da bambamci Amina, babu dalilin da zai sanya ni maye gurbin son da nake yi wa Samira akan Hauwa, me yasa lokacin da ta rasu ta'ki maye gurbin 'yar uwarta, na fa san komai Amina, don haka ba ki da ruwa akan wannan abinda yake faruwa tsakaninmu. Ba a yi macan da za ta yi mini wannan iskacin ta kwana lafiya ba." Na ce." To ai zumuncin da yake tsakaninku za ka duba." Ya furta." Ita ta duba zumuncin ne?" Na yi shiru ina kallonsa. Ya girgiza kansa kafin ya bud'e ma'adanar da yake ajiye gilasansa ya d'auko daya ya sanya kafin ya kwashi wayoyinsa ya zuba a aljihu. Ya dube ni sai kuma ya kama hanyar zai fita na bi bayansa ina fad'in." Za ka tsaya ka yi breakfast ko?" Ya ce." A a yanzu wurin Momi zan shiga mu gaisa na wuce kawai zan ci abinci a can gidan Hajja in sha Allahu." Muka sauko a tare ina fad'in." Shikkenan to don Allah a ce ina gaishe da Hajja da kyau tare da su Kamalu." Ya furta." Za su ji, zan gaya musu sa'konki in sha Allahu sai na dawo." Ya fice da saurin gaske. Na juya na shiga d'akina jikina duk a mace. Ubangiji Allah Ya sa mu ji alheri.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* "Yanzu don Allah Hajja abinda Hauwa ta yi shine zumunci? nasan duk wannan fad'an da ki ke yi akan hakan ba zai wuce ace kina gudun lalacewar zumunci ba. Amma ki yi nazari akan wannan abinda Hauwa ta yi Hajja ko mahaukaciya fa ta san d'anta ki ga yadda ake yi musu ciki akan titi A Amma su haihu a yi ta dambarwa da su wurin 'karbar jaririn daga hannunsu. Sannan kin ga yadda dabbobi idan sun haihu suke tattalin abinda suke haifa ai ko babu dangantaka ta jini a tsakaninmu da yarinyar bai kamata ta yi mana haka ba. Wannan wulakanci ne da rashin mutunci da kuma rashin tarbiya." Hajiya Saratu ce take wannan maganar cikin yanayi na damuwa da bakincikin abinda yake faruwa. Hajja ta d'an gyara zamanta tana fad'in." To tunda gashi nan a zaune sai mu ji menene dalili saboda ai k'arfe d'aya baya amo! ba wai ina goyuwa da bayan Hauwa akan abinda ta yi ba, ban ji dad'i ba kuma bata kyauta ba amma wata'kila duk ta yi hakan ne domin huce fushin abinda ya aikata mata. Ai ya nuna mata iyakarta ni ma kuma ya nuna mini ba ni da wani muhimmanci dangane da rayuwarsa tunda har zai iya yanke irin wannan hukuncin ba tare da ya nemi shawarata ba. A ganina kome Hauwa ta yi masa ta ci albarkacin jini da dangantaka ko." Ta girgiza kanta tana cewa." Hajja Hauwa fa bata da kunya ba wai ina 'kin ta ba ne a a halayenta munana sun rinjayi kyawawan domin duk mai zuciyar imani da tausayi ba zai aikata abinda ta yi ba a yanzu kamar yadda na gaya miki ko daga waje Tajo ya auro Hauwa ba mu cancanci wannan iskancin ba." Sai ta dube shi tana fad'in." Ka na jin mu baka ce komai ba, wai shin mai ya yi zafi ne tsakaninka da Hauwa da har ka saketa ko kana so ka nuna mini cewa ni ban isa ba ko kuma na ce ka d'auki hanyar lalata zumuncin da yake tsakanina da 'yar uwata da ta rage mini a duniya." Ya ce." Hajja a yi hakuri amma ina ganin zan ha'kura da Hauwa kawai domin wallahi ban da tayar mini da rikici babu abinda take yi a gida." Ta ce." Akan wane dalili shine abinda na tambayeka, kai yanzu baka ji kunya da nauyin gaya mini hakan ba da wane ido zan kalli Uwani.'' Ya yi shiru bai ce komai ba. Sai ta cigaba da fad'in." Ka gaya mini mai ya had'a ku da har ta yi wannan fushin ta ajiye jariri d'anyar haihuwa ta gudu, duk abinda za ka ga uwa ta aikata haka ba k'aramin abu ba ne ." Cike da b'acin rai ya shiga warware mata duka matsaltsalun da suka dinga faruwa wasu ta san da faruwarsu wasu kuma bata sani ba mussaman akan rikicinta da Maryam da kanwarta duk ya gaya mata abinda ta dinga yi har sakin ya ratsa. Ta ce." To ai kai ma kana da lefi me yasa za ka raba su da yaransu hakan bai isheka ba ka had'a da duka da cin mutunci don haka ta gayawa uwarta ni ma ta gaya mini shin jaka ce ita da zaka dinga dukanta ko ka manta cewa diyar wani ce itama, kana so ka aurar da yaranka a dinga dukansu." Ya ce." Wallahi Hajja sau daya na mare ta, amma ni ba ni dukan iyalinsa sharri ne kawai irin nata." Ta ce." To marin ma kada a sake yin sa ban yarda ba, dukansu amana ne aka bamu bakidaya Hauwa ko ba ta ci darajar komai ba sai ta ci albarkacin zumunci da haihuwa ai ta zama kai ka zama ita haihuwa uku ba wasa ba ce." Ya gyad'a kansa yana fad'in." In sha Allahu ba za a sake ba. Falon ya d'auki shiru na wani lokaci kafin ta ce." Menene matsayin auranta a yanzu? Ya furta." Tuntuni na mayar da ita ai tun kafin ta haihu har yanzu tana nan a matsayin matata." Ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in." Alhamdulillahi yanzu ka je can bauchi wurin Uwani ka basu hakuri don ta fusata sosai har suna fad'in ka aiko musu da takarda domin su ajiye sheda." Ya ce." To yadda ki ka ce haka za a yi in sha Allahu." Tare da 'yar uwarsa Hajiya saratu suka shirya tafiya Bauchin da wajan la'asar bayan sun yi sallah tafiyar mota za su yi suna fitowa harabar gidan Hajja Yusi ya shigo akan sabon machine wanda Hamusu ya saya masa domin shige da fice zuwa makaranta da kasuwa tunda sun bud'e sabon shagon sayar da takalma na mata da maza a kasuwar kwari to Yusin ke kula da shagon shi da Saminu. Cike da kwarin gwiwa ya je ya kafe babur din shi kuma Baban sai dariya yake yi ya zuba hannuwansa duka biyun cikin aljihun tazarcen dake cikinsa. Gabad'aya hankalinsa yana kan yaron fuskarsa kamar gonar audiga. Ya 'karaso wurin da suke tsaye da sassarafa sai suka rungume juna. Ya d'an dinga dukan kafadarsa yana fad'in." Abokina." Shi ma yana abokina?" Suka cika juna amma hannunsu a hade yake ya risina yana fad'in." Baba barka da yamma yaushe ka zo ne?" Ya dafa kafadarsa yana fad'in." Ban ji ma da zuwa ba, ni ma ina zuwa na tambayi Hajja tace mini ka fita tun safe mutumin ya zama d'an kasuwa." Yasa dariya yana cewa." Wallahi ai da na san da zuwanka da sai na zauna domin mu gaisa sosai." Ya ce." Idan kana so mu gaisa sosai ka zo abuja idan ka d'an yi free tunda nasan kana karatu ga kasuwa ko ta hana ka zuwa ne?" Ya yi shiru yana murmushi kafin ya juya gefan da Hajiya saratu take tsaye tana ta dariya ganin yadda suke cafkewa dama tuntuni akwai wannan sha'kuwar mai karfi a tsakaninsu. Ya d'an risina yana gaisheta ta amsa tana dariya kafin ta wuce wajan motar da Sukairaju yake tsaye yana jiran zuwansu ya bud'e mata gidan baya ta shiga ta zauna. Ya ce." Yanzu Bauchi muka nufa amma ina so ka zo abuja kamar yadda na gaya maka duk lokacin da baka da wani uzuri ka duba Momi bata da lafiya, ta kwanta a asibiti jiya muka dawo gida. Amma alhamdulillahi ta ji sau'ki akwai buk'atar ka zo ka dubata ko?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." Zan zo in sha Allahu Baba, mun yi magana da Adam kwanciyarta ta farko asibiti shi ya kira ni ma yake gaya mini ban samu zuwa ba. Ya yi fushi bai gaya mini ba yanzu, in sha Allahu idan Kamalu ya dawo da daddare zan gaya masa." Ya ce." Hakan yana da kyau, amma baka ba ni amsar dana tambayeka ba mamanka ce ta hana ku ziyartarmu." Ya ce." Ko daya wallahi Baba, ba ita ba ce kawai dai tunda muka dawo nan din ne ba mu samu zama ba shine kawai dalili amma idan ya dawo zan gaya masa zan kuma sanar da Baba Hamusu." Ya ce." To madallah aboki Allah Ya ba da sa'a, Allah Ya sa ina gari lokacin da kuka shirya zuwan." Ya amsa da "Amin Baba." Wajan motar suka nufa a tare Sukairaju ya d'an matsa da sauri kafin ya bud'e masa motar Yusi ya yi saurin riga shi. Ya shiga ya zauna kusa da 'yar uwarsa da bismillahi yana fad'in." A gaishe mini da Kamalun idan ya dawo a gaya masa sa'kon Mamanku cewa tana gaisheku gabad'aya." Cike da ladabi ya ce." In sha Allahu zan sanar dashi Allah Ya tsare Baba." Ya d'aga masa hannu Yana amsawa da "Amin." Koda suka sauka a garin bauchi Hajiya Saratu ce kadai ta yada zango a gidansu Hauwa domin shi kam tun a mota ya ce tunda dare ya yi Sukairaju ya kai shi hotel din da ya saba sauka idan ya shiga garin suka kwana da safe a hadu. Hajiya Saratu ita kadai Sukairaju ya kai gidansu Hauwa bayan ya zartar da umarin da aka yi masa. masu karanta littafin nan ba ku biya ni hakkina ba ina binku bashi ba wai don baku dashi ba ne. Na kudi ne yi kokari ki sauke hakki domin abu kad'an da ake rainawa sai ya hana ki kwanciyar hankali. Allah Ya datar damu. Dama Hajja ta sanar da Inna Uwani zuwan na su don haka da ta ga Hajiya saratu ita kadai ta shiga tambayarta mai gayya mai aikin ta ce mata tare suke Amma da safe zai shigo kamar yadda ya fad'a. Inna Uwani sosai ta marabceta ta yi wanka ta yi salloli ta ci abinci Hauwa tana kwance a cikin d'aki ba ta fito ba ta gaisheta ba kuma tana jin motsinta. Itama kuma inna Uwanin ba ta yi mata magana ba ai ko babu komai tunda ta ganta a gidan tasan akwai dalilin zuwanta Kuma ko banza ta girmeta ta kuma girmi mijin nata yayarsa ce. Hajiya Saratu abin ya yi mata ciwo sosai amma sai ta share tunda sulhu suka zo bai kamata ta yi wani abin da zai sake harzuka zuciyoyinsu ba. Da yake d'akuna uku ne a d'akin d'aki daya inna Uwani ta gyara mata da katifa da mashinfidi ta shiga ta kwanta sai da asubahi tukkuna da suka gaisa suka fara tattauna maganar inna Uwani tana fad'in." To dukansu dai babu yaro idan sun yi hakuri sun rungumi auransu sai sun fi kowa mora kuma yaransu su tashi cikin annashuwa tare da tsalle da dara a gidansu domin duk inda uwa da uba suka rabu yara sukan kasance a lalace. Kuma ban ga dalilin da zai sanya Tajo ya dinga kwashe musu yara yana bawa wata ajiya ba, Saratu ki dubi lamarin nan fa da kyau ki ga ni akwai son zuciya, ba ni so na fiye magana a ga kamar ina goyon bayanta, tana da gaskiya a wannan ga'bar domin abu ne mai wahala uwa ta yarda a d'auki danta a bawa kishiyarta cikin gadara da iko, a kuma biyo ta da ba'kar magana da zagi." Ta ce." Ni kaina ban goyi da bayan hakan ba Inna wannan dalilin ne ma ya sanya da Hajja ta ce masa ya zo nan din ya baki hakuri na ce ya bari mu zo tare domin bibbiyu tafi dad'i amma tsakani da Allah ita abinda ta yi ta kyauta Inna ki fadi gaskiya. Daga kowane bangare fa akwai lefi ko musulunci abinda ta aikata rashin imani ne da yin butulci ga Allah." Inna Uwani ta ce." Umm! to ni dai gaki nan ga Hauwa Saratu idan tana ganin ta gaji da zama da Tajo bisimillah sai ta share d'aki ta zauna. Idan kuma za ta koma auransa sai ki tambayeta ni dai babu wanda ya isa ya shiga tsakanina da 'yar uwarta a cikinsu." Tana gama fad'in haka ta tashi tana fad'in. A dama miki kunu ko kuma shayi za ki sha." Ta ce." Kunun dai zai fi dama-dama Inna amma a turo mini Hauwan mu yi magana." Ta juya ta fita tana fad'in." To bari na turo miki ita." Ta shigo sanye da hijabi babu yabo babu fallasa ta zaune gefan katifar da take zaune ba ta kalle ta ba ta ce." Ina kwana." Hajiya Saratu ta'ki amsawa tana fad'in." Ba zan amsa ba Hauwa ai kin nuna mini matsayina kamar ni na zo gidanku domin ke amma har na kwana ban isa ki fito ki gaishe ni ba, ke ba za ki canza dabi'u ba ko." Ta yi shiru ba ta ce mata komai ba. Sai ta girgiza kanta tana fad'in." To magana ce akan abinda yake faruwa ta kawo ni nan, Hauwa duk wani abu da ki ke jin an yi miki ki yi hakuri ki koma dakinki domin shine farincikin iyayenmu, tare muke da Tajo nasan an jima kadan zai shigo, ya tabbatarwa da Hajja cewa ya mayar dake tun kafin ki haihu kin ga yanzu baki da wata hujja da zata hana ki komawa." Ta nisa kafin ta cigaba da cewa." Yanzu ke ba ki ji kunya ba a ce bare wad'anda aka auro a waje sun fi ki matsayi da shiga zuciyarsa. Ke ya kamata fa ace kin fifita a cikinsu amma kina wasa da damarki. Zan gaya miki gaskiya ba ki kyauta ba, abinda ki ka yi ba daidai ba ne, kuma kin ba mu mamaki, yanzu Hauwa ko da babu aure a tsakaninki da Tajo ba za ki iya kula masa da yara ba? Ko daga waje ya auro ki bai kamata ki yi abinda ki ka yi........... Ta katseta kafin ta kΓ rasa tana fad'in." Anti Saratu ban ga lefinki ba don kin kare shi, ai nasan babu wanda zai ta'ba goyon bayana balle a nuna masa cewa bai yi mini adalci ba, ya kyare ni, ya tsangwame ni a gidansa, ya fitar da hannu ya dake ni, ya kira ni jahila mara tarbiya duk a gaban matayensa . Ya nuna musu kan dole yake zaune da ni, na haihu ya nuna mini iko akan abinda na haifa baiwa ce ni, ko kuma jaka ce, ai kudi na hauka ba ne, kuma itama Amina ai ubanta talaka ne mai yasa ya fifita ta a kaina, mai yasa yake rangwanta mata. Idan ya daukaki Maryam domin yana ganin tana da dukiya daidai take da shi, ai ta wani gefan na fi Amina usuli tunda kaf dangin mahaifina fana uwata babban family ne, ya za a yi na yi rayuwar 'yanci da jin dadi a tsakanin kishiyoyin da aka nuna sune suke da mutunci a kaina." Ta sassauta tana fad'in." Ita Aminar ce ta gaya miki cewa ta daban ce a wurinsa. Ko kuwa kina ganin ta wuce ya yi mata shegantaka idan har tsiyarsa ta motsa, to idan har ma kina tunanin haka ki bari domin kuwa babu wata mace da za ta gaya miki cewa mijinta na yi mata yadda take so ba tare da yana guma mata ba. Shiyasa ai nake fad'in na raina wayonki da gogewarki tunda har ki ka kasa karantar yanayin zamantakewa da wanda Allah Ya had'a ki zama da shi, ba wai ina fad'a miki haka ba ne saboda Ina kin'ki ko Kuma na nuna miki cewa d'an uwana nake goyawa baya. Shima mun nuna masa kuskuransa kuma ya d'auki niyyar gyara tunda har ya tako kafarsa garin nan to tabbas ya aminta da cigaba da zama dake. Hauwa ki yi karatun ta nutsu kowane aure akwai kalubale a cikinsa ki kara hakuri akan wanda ki ke yi, ke da dan uwanki kada ki bari abokanan zamanki suga wallenki har su yi miki dariya a fakaice. Har yanzu Amina da Maryam sun fi ko way........" Kin ga anti Saratu don Allah ki kyale ni na ji da bakincin da yake damuna kada ki kara mini dama tuntuni ni duk abinda zai faru ba kya ba ni goyon baya kin sha nuna mini Amina ta fi ni mutunci gaskiya ba zan iya komawa ba shiyasa ma na ajiye masa d'ansa ya nemi mai shayarwa." Cike da tsananin bacin rai Hajiya saratu ta ce." To shikkenan Hauwa kada Allah Ya sa ki koma din, ki yi ta zama tunda haka kike ganin ya fi miki, yaro zai rayu ko dake ko babu ke, dana san abinda za ki yi mini kenan da ban shiga sabgarki ba, duk abinda zai sake biyo baya ba zan sake sanya bakina ba ki yi yadda kike ganin ya yi miki." Ta mike tsaye tana fad'in. Gashi na yi hakan shine ya fi mini kwanciyar hankali da nutsuwa ba zan iya zama dashi ba idan yana tare da wannan tsohuwar mushirkar matarsa." Ta ce." Ki je mana kada ki zage ni Hauwa tunda kin yankewa kanki hukunci wanene ya isa, Allah Ya bada sa'a." Ta kama hanyar fita bayan ta ja mata wani tsaki mai tsayi wanda ya yi mata mutukar ciwo a zuciya. Hauwa ce yau tsare kerere a gabanta tana gaggaya mata magana har da tsaki abin ya tsaya mata ranta sosai har da 'yar kwallarta ta goge tare da d'aukar wayarta dake gefenta. Tana kiransa ya daga Yana fad'in." Na shirya tsaf gani nan zuwa. " Cikin rawar murya ta ce." A a, ka zauna anan hotel din, ko da yake ba zan hana ka zuwa ka gaishe da Inna ba, da sai na ce ka zauna an jima kadan zan yi wanka ka turo Sukairaju ya d'auke ni." Jikin yadda muryarta take rawa ya sanya ya ce." Wani abin ne ya faru?" Ta gyad'a kanta tare da sanya yatsu ta goge hawayen da ya zubo mata. Domin daga zarar ta tuna tsakin wulakacin da Hauwa ta yi mata sai ta ji wani tashin hankali tunda take ba a ta'ba yi mata wannan iskancin ba da 'ya'yanta magidanta da kuma shekarunta, lallai karfin zumunci ya shallake komai amma da ba don haka ba tabbas da Hauwa ta raina kanta a yau, shikkenan daga gyara kayanka, Hauwa bata da mutunci ko kad'an. Ta ce."Bari kawai Tajo, Allah dai ya kyauta shine abinda zan ce." Ya gyad'a kansa yana fad'in." Zan turo Sukairaju ya d'auke ki yanzu kawai mu wuce Allah shikkenan." Ta amsa da "Amin." Kafin ta kashe wayar a sanyaye wanda Yayi daidai da shigowar inna Uwani da jug na kunu da kwanon silva sabo dal dashi da k'osai a ciki. Ta ajiye gabanta tana fad'in.'' Ga kunun Saratu k'osan ma da zafinsΓ  na d'ora miki ruwan wanka yanzu nan. A tak'aice ta ce." To na gode Inna Allah Ya saka da alheri.'' Har ta juya za ta fita sai kuma ta tsaya tana fad'in.'' Tajon zai shigo din ko domin yanzu nan Baffansu Tijjani wanda gidansa yake kallon namu ya shigo yana gaya mini zai fita aiki na ce ya d'an jira domin su samu damar tattaunawa akan abinda yake faruwa." Ta ce." E, zai shigo din ya jira shi" Ta fad'i Hakan ne domin ba ta san me za ta ce mata ba. Sai ta juya ta fita da sauri tana fad'in." Bari na gaya masa to." *2K Complete a telegram. Normal What'sapp group kuma 1k via 0542382124...Binta Umar gtbank* *07084653262* *GARKUWAR MATA ✍️* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *TALLAH* https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *PAID BOOK 2K COMPLETE ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA 1K VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* Kiranta kawai ya yi a waya ya gaya mata ga Sukairaju nan ya turo domin d'aukarta. Sukairaju da ya zo ya shiga cikin gidan tunda akwai sabo dalili amintaccen yaronsa ne duk a cikin masu yi masa hidima. Suka gaisa da inna Uwani har tana yi masa tayin abun kari ya ce a koshe yake ya fita ya tsaya jikin mota yana jiran fitowar Hajiya Saratun. Ta fito cikin shiri tunda dama ta yi wanka ta kintsa sama-sama ta iya yin karin kummalo dalilin takaicin rashin kunyar da Hauwa ta yi mata. Inna Uwani na zaune a tsakargida tana gyara kayan miya Hajiya Saratu ta fito tana fad'in." Inna tafiya zan yi." Ta juya da sauri tana fad'in." Tafiya kamar Yaya Saratu ina Tajon yake ne shi ake jira domin Tijjani har ajiye aikinsa ya yi saboda ya gan shi su yi magana." Ta ce." To ni kam ban san me zan ce miki ba Inna amma ina tsammanin Hauwa ba zata koma ba domin ta gaya mini d'azu da muka yi magana. Amma ki sake tuntubarta." Inna Uwani ta saki baki tana kallonta a sanyaye ta furta." Haka tace miki ba zata koma ba Saratu?" Ta gyad'a kanta tana fad'in." Ai da hakan ta gaya mini da sauki Inna ba zai dame ni ba amma babu komai Allah Ya sa hakan shi ya fi alheri, Allah Ya raya yara." Daga haka kawai sai ta kama hanyar fita. Inna Uwani ta bi bayanta tana fad'in." Ina Tajon yake ba zai shigo mu gaisa ba kenan?" Hajiya Saratu ta yi shiru ba ta ce mata komai ba. Haka ta fice daga gidan inna Uwani na le'kenta Sukairaju ya bud'e mata mota ta shiga ya ja suka bar wurin. Jikinta sanyi kalau ta koma cikin gidan kamar mara lafiya. Shi dariya ma abin ya bashi da Hajiya Saratu ta gaya masa abinda ya faru. Ya dinga gyad'a kansa yana jimanta fitsarar Hauwa ko shi ba ya iya tsalleke Umarninta kuma baya iya duban idonta ya yi jayayya da ita, sannan kuma yakan yi aiki da shawarwarinta amma yau an wayi gari Hauwa d'iyar cikinta ta ci mutuncinta saboda wani dalili. Abin ya ta'ba shi sosai mussaman yadda ya ga yanayin Yayar tasa ya yi tabbacin abin ya yi mata ciwo a rai. In banda umarni ne na iyaye bai ga dalilin da zai sanya shi zuwa bikon Hauwa ba balle rayuka su b'aci zahiri kuma ba a tara sani ga Allah da ya san abinda zai biyo baya kenan da bai aminta da auranta ba. Tun mota suka yi magana da Hajja shi ya gaya mata cewa zai wuce Bunkure gidan Malam 'Daha malamin mahaifinsu wato Alhaji Ibrahimu. Yana nan ya tsufa sosai amma da yake tsufan ya wanzu tafarkin addini da karatun al'kurani jin sa da ganinsa duka ba su raunana ba. Sai dai matsalar kafa da ya samu amma baya ga haka babu wani abu da ya samu tawaya a tare dashi sai tsufa wanda wajibi ne ga kowane musulumi. Tun yana saurayi rabonshi da ziyartar malamin yanzu kam ya zame masa dole domin yana buk'atar addu'a bayan wadda yake yi akan kansa. Sukairaju na sauke Hajiya Saratu a gidanta suka d'auki hanyar kauyen bunkure kamar yadda ya niyyata. Da k'yar ya iya sheda gidan dalili yawanci gonakin da suke garin an sayar an yi gine-gine na zamani tunda yanzu an samu cigaba a ko'ina kusan rabin garin ma ya zamananta da dama wasu na sauya fasalin gidajensu zuwa na zamani. A can daga gefe Sukairaju ya ajiye motar amma bai fito ba yana ciki a zaune dalilin ganin yadda jama'a suka fara taruwa masu wuce wa suna tsayawa. Ya ce da Sukairaju ya yi sallama a kofar gidan Malam din haka kuwa ya yi ya dinga kwad'a sallama wani magidanci ya fito cikin yar shara da fatanya a kafadarsa. Suka yi musabaha kafin ya tambaye shi. Ya ba shi amsa da eh gidan Malam 'Daha ne. Sai ya nuna masa motar yana fad'in." A gaya masa ba'ko ya yi Alhaji Tajuden ne na Alhaji Ibrahimu dambatta wato abokinsa da ya rasu." Mutumin ya washe bakinsa kafin ya nufi wurin motar da saurin gaske. Sukairaju ya bi shi cikin gaggawa ya yi saurin tare shi. Duk abinda suke yi yana kallonsu sai ya sauke gilashin motar fuskarsa a sake ya furta." Sukairaju matsa masa hanya mana mutumina ne." Da sauri Sukairaju ya bashi wuri shi kuma ya kΓ rasa bakin motar yana ta dariya tare da mamakin ganinsa. Ya bude motar cikin sauri ya fito ya rike hannunsa yana fad'in." Malam Rabi'u." Ya ce." Naam Alhajin Allah dama za mu sake ganawa." Yana dariya ya ce." Allah ya nufa gashi na ziyarce ku, na zo wurin Malam ne." Ya gyad'a kansa yana fad'in" Ya bayan rabuwa Alhaji ya harkoki da jama'a Ubangiji Allah Ya taimaka ya kara suttura." Ya amsa da "Amin Malam Rabi'u ya iyali fatan kowa lafiya?" Ya ce." Alhamdulillahi mata na hud'u ina da yara ashirin da biyu." Cike da mamaki ya ce." Mata hud'u yara ashirin da hud'u Rabi'u?" Sai ya kyalkyale da dariya yana fad'in." Kwarai kuwa Alhaji yanzu haka akwai shida mata dana aurar da su, suna d'akin mazajensu cikin aminci." Ya gyad'a kansa yana jimanta karfin hali irin na mutanan k'auye gashi dai bashi da wani karfi irin na su amma ya ajiye mata hud'u da tarin yara." Ya ce." Ka burge ni da gaske Rabi'u kuma kai namiji ne, yanzu dai ka yi mini jagora wurin Malam na zo mu gaisa ne." Ya ce." Ka kyauta sosai kuwa domin idan ban mata ba yanzu ka kai sama da shekara asirin rabonka da garin nan tun marigayi yana raye." Ya furta." Tabbas hakane domin karshen zuwan da muke yi tare da shi ne, tun bayan rasuwarsa kuma Allah bai nufe ni da sake zuwa ba." Suka nufi cikin gidan a tare suna magana cike da jin dad'in had'uwa. Babu girman kai ko kuma nuna ni isheshshene yanayin yadda ya gaisawa da jama'ar da suka tsaitsaya yana ta d'aga musu hannu haka suka shiga gidan da aka narka 'kasa irin ta da mai d'anko wurin gida shi. Gidan mai yalwa ne sosai irin dai ire iren gidajen Malaman addini mussaman na karkara har yanzu yana nan inda yake sai dai kwaskwarima da aka yi wa wasu guraran dalilin wasu daga cikin yaransa a ciki suke zaune da iyalinsu. Amma kuma sun gyarawa mahaifinnasu bangaran nasa tunda da alama yana yin manyan ba'ki mussaman abokai ko 'ya'yansu tunda fitacce malamin addinin musulunci ne da har yanzu tafsiri da karatun al'kurninsa ke yawo a wasu gidajen redion. Koda suka shiga wurin nasa yana zaune kafarsa ta k'wanshe da al'kur'ani kirar warshu a hannunsa yana karatu babu wata gigita ta tsufa ya gane wanene a gabansa. Rabi'u yana fad'in." Malam ga Tajuden na Alhaji Ibrahimu na kawo maka." Ya yi dariya irin ta manya kafin ya ce." kuna shigowa na gane shi ai ko baTajudden na Alhaji Ibrahimu ba." Ya ce." Ni ne Malam ina fatan na same ku lafiya ya bayan rabuwa kuma?" Ya amsa da "Alhamdulillahi ya iyali ya jama'a ya harkokin ina Hajiya Halimatu?" Yana nufin Hajja kenan. Ya ce." Tana nan lafiya lau ta ce a gaishe ka da kyau Malam." Ya gyad'a kansa tare da fad'in." Ina amsawa na kuma ji dadin ganinka Tajuden za mu sake saduwa kafin Allah Ya yi ikonsa." Ya furta." In sha Allahu rabbi zan dinga ko'karin ganin na kawo ziyara Malam abubuwa sai a hankali." Ya gyad'a kansa yana murmushi kafin ya ce."Allah Ya taimaka ya bada sa'a, na gode sosai Allah Ya yi albarka." Ya amsa da Amin suma Amin kafin wajan ya d'auki shiru Malam Rabi'u tuntuni ya fita. Malam din ya ce." Akwai abinda yake tafe da kai ne?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." Kwarai kuwa Malam muna buk'atar addu'a akan komai duk da muna yi akan kanmu, amma a kwanakin nan abubuwa sun yi yawa mussaman 'bangaran iyalina a taimaka mana da addu'a Allah Ya warware mana." A nutse ya ce." Za a yi in sha Allahu akwai buk'atar ka tsananta addu'a akan kanka, daga nan zan sanya al'majirai yin saukar al'kur'ani tsayin kwanaki bakwai sai ka yi sadaka, Allah Ya warware." Ya amsa da "Amin Ya Malam na gode sosai Allah Ya kara girma." Ya furta." Za ka shiga ka gaisa da mutanan gidan ko?" idan kin san kina karanta book din nan ba ki biya ni hakkina ba to Ina binki bashi. Ya yun'kura domin tashi Yana fad'in." E, zan shiga Malam zan yi magana da Rabi'u akan abin sadaka sai mu ga yadda za a yi." Har ya juya zai fita ya dakatar da shi ya tsaya sai ya ce." Ya iyalin Tajuden su nawa ne yanzu yaranka kuma nawa?" Ya ce." Allah shi gafarta Malam su uku ne yara kuma ina da biyar rayayyu d'aya ta rasu." Ya ce." Alhamdulillahi Alhamdulillahi Ubangiji Allah Ya yi musu albarka, Allah Ya raya mana su bisa tafarkin addinin islama. Idan har kana da buk'atar cika sunnar Annabi tunda su uku ne ka zo nan na zaba maka daya daga cikin yarana biyu da suka rage mini. Hakika ina sha'awar tabbatuwar zumuncina da Alhaji Ibrahimu. Duk da fad'in Allah ne kuma sunna ce mai kyau amma ba wajibi ba ne, abinda magabatanmu suka d'ora mu akai kenan lallai k'arshen duniya mata za su yawaita yayin da mazan auran za su yi 'karanci ko rashin ikon ga masu niyya. masu iko idan kuna da d'aya ku kara da ta biyu, masu biyu ku 'kara da ta uku, masu uku ku k'ara ku yi hud'u domin dakile mas'aloli masu yawa. Idan har ka niyyata tunda kana da iko kada ka manta ka zo nan zan had'a ka aure da nutsatstsiyar yarinya ko ba daga cikin yarana ba." Cikin wani yanayin ya furta." To shikkenan Ya Malam idan da yiwuwar hakan in sha Allahu zan zo sai a san yadda za a yi na gode sosai, Allah Ya saka da alheri" Ya amsa da "Amin cikin nutsuwa yana yi masa fatan alheri da sauka lafiya. Yana fita ya ciko karo da Rabi'u a tsaye ya ce ya yi masa jagora cikin gidan domin su gaisa. Ya dinga mamakin yadda gidan Malam 'Daha ya cika da tawagar yara 'yan mata da masu tasowa maza da mata sai iyayen tukuwane kangama-kangama dama can sanin da ya yi masa mutum ne mai arzikin gona ki a k'auyen don haka matsala ta abinci ba zata ta zama barazana a gare su. Malamin mahaifinsa ne kuma akwai abota sosai sai dai kowa tsarinsa daban. Mahaifinsa ko a can baya yana da wayewa sosai ta fannin boko da kuma addinin daidai gwargwado Hajja ita kad'an ta rayu bai ma ta'ba yun'kurin karin aure ba har ya rasu su biyu ya haifa. Shi kansa bai taba tunanin zai iya ajiye mata uku ba domin yadda ya tsara rayuwarsa tun daga kuruciya Samira kadai ta ishe shi, sai gashi Allah Ya na ta juya lamarinsa. Har gajiya ya yi da amsa gaisuwa domin dai daga sashe sashe ake zuwa gaishe shi. Rabi'u ya riko hannunsa suka fita duk da haka wasu daga cikin yaran sai da suka biyo bayansu. Bakin motarsa kuwa jama'a ne a tsaye Sukairaju yana ta fama da su. Daga bakin kofar gidan Malam din suka tsaya a dan gajiye yake fad'in." Rabi'u kana da asusun ajiyar kudi ko?" Ya ce." E, da akwai sai ya fito da wayarsa ya mika masa yana fad'in." Bismillah yi sauri sanya mini lambar a nan zan tura abin sadaka a bawa Malam sannan abinda ya yi saura ka yi amfani dashi a kuma sallami iyayenmu da k'annanmu da suke cikin gidan a ba su su sha ruwa." Ya kar'bi wayar da sauri yana fad'in." To Allah Ya saka da alheri mun gode Allah Ya kara arziki Alhaji." Bai ce komai ba har gama ya mika masa waya ya kar'ba a tsaye a wurin ya tura dubu dari biyar sannan ya bashi wayar a gain ya ce ya sanya masa lambar wayarsa domin su dinga gaisawa." Ya kar'ba a karo na biyu ya sanya masa lambar shi kuma ya yi serving da Malam Rabi'u Bunkure. Da haka suka yi sallama cike da girmama juna. Sai da suka fita daga karkarar tukkuna Sukairaju yake tambayarsa ina suka nufa domin shi duk a tunani shi zai sake kwana a kono din ganin bai fiye son tafiyar mota ba. Ya ce." Mu d'auki hanyar gida kawai yau komai dare a gidana zan kwana Sukairaju na huce gajiyar gabad'aya." Aikuwa da azama ya d'auki hanyar garin abuja kamar yadda aka bashi umarni. Ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya d'an gyara zaman shi a mota yana nazarin maganar Malam 'Daha wai ya zo cikin karkara ya nemi aure domin cika ta hud'u. Gabad'aya ma shi yanzu babu wannan lissafin a tare da shi bai sani ba ko nan gaba. Gabansa ya fadi lokacin da ya tuna iya rigimarsa Amina tunda suka yi sallama jiya sau daya suka yi waya da daddare kafin ya kwanta ya kira ta domin gaya mata ba zai dawo ba sai gobe. Yana duba wayar ya ga kiranta ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya sanya wayar a kunnansa Amina ta tsaya masa ransa sosai shi kansa ya tabbatar da haka...✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book complete 1k akan telegram normal What'sapp group kuma #700....via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *114* Muna tare da yara falo wai sun zo ganin 'kaninsu domin babansu ya gaya musu sunansa Sultan falon ya kacame Husaina da Minal har da kokawa ban ankara ba sai kukan Minal na ji da k'arfi lokacin ya yi daidai da fitowar Baba Tabawa daga d'akinta. Kukan Minal din ya zaburar da yaron shi ma ya tsanyare da kuka Baba Tabawa fadi take "A kul cizo ko Usai ba ki san 'kanwarki ba ce, ka da na sake gani kin yi cizo." Na juya da mamaki ina kallonta yayin da nake jijjiga yaron na ce." cizonta ta yi?" Hassana dake tsaye a gefe ta ce." E, ni ma tana cizo na ko Yaya?" Ta fad'a tana kallon Khalil da yake zaune hankalinsa kan tibi domin shi duk rigimar d'aukar yaron da suke yi ban dashi da suka shigo dai ya zo ya tsaya kusa da ni bayan mun gaisa har yana tambayata sunansa Sultan ko na ce masa eh daga haka sai ya je ya zauna. Yana da nutsuwa sosai kuma bashi da hayaniya irin ta 'kuruciya. Ya yi shiru bai ce komai ba wata'kila bai ga lokacin da ta yi cizon ba shiyasa bai yi magana ba. Na ce." Kai cizo take yi dama?" A hankali ya ce." Idan suna fad'a ba, itama Hassana ai mazilinciya ce ita ta koya mata cizon don ta fi k'arfinta" Na dube ta ta yi tsuru-tsuru! domin da alama ba a saba yi mata fad'a ba ko nuna mata abinda take yi kuskurene. Fad'an da Baba Tabawa ta yi mata ya sanya ta kyakykya'be fuska za ta yi kuka. Cikin tsawa na ce." Zo nan!" Ta'ki zuwa hawaye tuni sun 'kwace mata. Na ce." Ba za ki zo ba?" Ta ma'kale kafada tana kuka." Na mi'kawa Baba Tabawa yaron ina fad'in." Ki mayar da shi baya wata'kila ya koma baccin." Hassana ta je da sauri tana fad'in." Baba ba ni shi na d'auke shi." Cikin zare ido na ce." Matsa ki ba ni wuri babu wanda zai d'auke shi ai tunda ba za a ce ku bari ba." Ta koma ta zauna jikinta a sanyaye. Na janyo Minal da take shashshekar kuka na d'orata saman cinyata Ina rarrashinta har ta yi shiru na bud'e mata game a wayata tana wasa. Yadda suka takure a wuri d'aya hakan bai sanya ni na ji tausayinsu ba abinda ya dame ni shine rashin jin magana d'aya domin tun kafin a kai ga cizon nake ce musu su nustu zan bawa kowa yaron ya d'auke shi ban ankara ba har an kai ga cizo. Na mik'a hannuna da sauri na janyota gabad'aya ba su ankara ba sai suka fasa ihu a tare domin yadda na janyo Usai din shi ya zaburar da 'yar uwata Abinda ba su saba dashi ba kenan Khalil ya zubo mini ido da yanayi na damuwa kamar ya hana ni. Na kama kunnanta na mur'de shi da k'arfi. Ta tsala ihu! sai hawaye shar-shar! Baba ta fara ko'karin kwaceta. Na kai mata rank'washi da d'aya hannuna ina sake murde fatar kunnan na ce." Wallahi duk ranar da na sake ji an ce Usaina ta yi cizo zan sanya reza na yanke harshenta Khalil ka zama sheda idan ta yi ko a gidan Momin ne ka zo ka gaya mini." Da sauri ya ce. "Ba za ta sake ba Mama ki yi hakuri kin ji." Na cika mata kunnan ta matsa gefe kusa da 'yar uwar da take tayata kukan suka jeru suna yi cikin jan hanci da sauke ajiyar zuciya." Kiran da ya shigo wayata ya katse maganar da muke yi da Baba Tabawa akan abin duk yaro mai cizo ai babu yadda za a yi yayi farinjini ko yanzu hannun Minal ya yi shedar ha'kora ina dalili. Koda na duba maigidan ne. Na daga lokacin kukan yaran ya hana ni jin abinda yake fad'i mi'kewa na yi na nufi d'aki ina fad'in." Ina jinka ina yini?" Ya amsa a tak'aice kafin ya ce." Wacece take kuka Hassana ko Usaina?" Kai tsaye na ce." Dukansu ne?" Ya yi Jim kafin ya furta." Akan wane dalili Amina?" Na ce." Fada suka yi har da cizo shine don an yi musu fad'a suka had'a kai suna kuka?" "Idan wannan fad'an ne a junansu sun saba yi ai." Ya fad'a da yanayi na b'acin rai a maganarsa. Na ce." Da sau'ki idan a junansu suka yi tunda tare suka rayu ko a ciki daya. Usai ce ta ciji Minal a hannu?" Ya yi shiru bai ce komai ba haushi ya ji da alama sai abin ya ba ni mamaki da dariya. A gajarce na ce." Ka taho ne?" "E, kin ga Amina kada ki sake dukan yaran nan ba na so na gaya miki?" Na ce." Haka na ce maka na dake su? fad'a fa kawai na yi mata ita mai cizon shine ita abokiyar tagwaitakartata take tayata kuka bayan Kuma ita din ta tabbatar mini da cewa dabi'ar yar'uwartata kenan cizo a ganinka d'abia ce mai kyau?" "Na ce dai kada ki sake dukansu ban ce dabi'a ce mai kyau ba fad'a ya isa ban da duka." Na ce." To." kawai na yi shiru ina mamaki. "Gani nan kan hanya in sha Allahu ki yi mana addu'ar sauka lafiya." Na ce." Allah Ya kawo ka gida lafiya." Ya amsa da "Amin. " Kafin ya kashe wayar na fita falon ina mamaki ashe zai sake ru'banya domin babu kowa a falon har Khalil din. Na bi Baba Tabawa kicin ina fad'in.'' Ina yaran suke?" Ya juyo tana kallona kafin ta ce." Au ko sun tafi babu sallama." Na ce." Da alama gashi na fito babu su a falon. Sai ta sanya dariya tana fad'in." Kai jama'a yaran yanzu ba sa son fad'a, wato fushi suka yi." Na gyada kaina ina fad'in." Kada Allah Ya sa su 'kara shigowa gidan." Na fita daga kicin din raina a b'ace ni ba za a yi wannan sakarcin da ni ba. Daga jin kukan yara ya yi wani kicin-kicin yana fad'in magana a kumbure kada a dake su, aikam sai dai ba su yi abin dukan ba. Ki karanta baki biyani hakkina ba ina binki bashi Shigar k'ananun kaya na yi domin tar'barsa ina da ragowar kwana daya tunda shekaran jiya kawai muka kwana dole anan wurina zai kwana. Na tsaya gaban madubi ina duba kaina na juya nan na juya nan har abin ya so ya ba ni dariya ni kaina ba kasafai nake son sanya rriga da wando matsatstsu ba don sai na dinga ganina kamar wata inyamura yanzu na dinga kallon kaina a madubi ina tuna wata jarumar finafinan kudu na manta sunanta amma tana da wani irin hips mai tudu da mutukar daukar hankali. sam bata da kyawu a fuska amma tana da dirin jiki mai kyau. Kai na ji dadin maganin tumbin nan da nayi amfani da shi domin yanzu ina yin gayu sosai na matse ko'ina na jikina ya fita yadda ake so maganin ya daidaita mini yanayin jikina kwarai......08089965176 ga masu buk'atar su tuntubi wannan lambar. Misalin tara da arba'in na dare ya kira ni yana gaya mini ya d'an jima kad'an da dawowa yana gidan Momi zai shigo zuwa an jima na ce to shikkenan. Na bud'e wayata sakkonin Sahura suka shigo rututu na shiga ina dubawa ina kuma sauraran voice note din da ta turo mini yanzu haka tana gidansu. kuma ta sanyawa gidan sabon kwado Idiris sai dai ya nemi makwanci." Cike da mamaki na kira wayarta. Tana d'agawa na ce." Sahura me ya yi zafi haka? yanzu har sai sai ta kai ki ga tafiya gida ba za ki yi hakuri ba." Ta furta." Amina wallahi na rantse sai dai ya zab'a ni ko matar da zai auro da gaske fa aure zai yi wallahi da idona na ga yana had'a lefe." Na ce." To shine me wai? ke ba za ki iya ha'kuri na d'an wani lokaci ba Hajiya don Allah kada ki ba ni kunya mana." Cike da damuwa ta ce." Ke ma kin san babu adalci dangane da abinda Idiris yake ko'karin yi mini ko Amina." Na danne dariyar da take so ta kwace mini na ce." Na sani to amma ba mu da yadda za mu yi, ba za mu hana shi ba amma ai bari ba shegiya ba ce idan ta shigo kudin suka kare sai ta ga kwakwar da ake ciki a gidan. Ki yi hakuri don Allah ki koma. Yanzu ina yaran suke?" Ta ce." Suna can gidan Babarsa." Na ce amma abu bai yi dad'i ba wallahi, ki bari da safe za mu yi magana in sha Allahu gabad'aya kin tayar mini da hankali wallahi." Ta yi 'kwafa ba ta ce komai ba. Na ce." Da safe zan kira ki in sha Allahu rabbi." Ta ce." To shikkenan." Na kashe wayar na ajiye Ina mamakin yadda ta tayar da hankalinta wato idan ka ga mutum bai yi abu ba to bai zo kansa ba sai na tuna lukuta da dama da abubuwan da suka shude kai kishiya abar gudu ce, su kuma mazan suna fad'in abokiyar zama ce. To cikin shan k'amshi ya shigo mini ganin haka ya sanya ni ma na kama kaina. Na yi masa sannu da zuwa a takaice bai zauna ba ni ma ban yi masa tayin zaman ba tunda dama sai ya so yake zama har ma ya kwana d'akin nawa. Na dube shi yana ta jin haushi na yi tsai ina nazarin abinda ya sanya shi shigo mini haka idan don na yi wa yara fad'a yake jin haushi to yanzu kuwa na fara wallahi. Ya juya zai fita yana fad'in." Ina sama ki zo?" Ban amsa ba har ya fita. Na ja tsaki ina fad'in." Aikin banza harara a duhu. Sai dai ya yi kusan minti ashirin da fita na bi bayansa. Yana can kan kujera daga gefe yana duba Loptop dinshi na shiga. Ya amsa sallamata yana kallona har na je na zauna kujerar dake kallonsa bai d'auke idonsa ba. Ni ma kallonsa din nake yi cikin yatsine fuska. Ya sassauta yana d'an murmushi ya ce." Yau kuma baturiya ki ka koma Amina?" Na yatsuna fuska ban ce komai ba. Ya ce." 'Dan taso ki zo nan." Juyar da fuskata na yi ban ce komai ba kuma ban tashin naje din ba. Dole shi ya kashe Loptop din ya zo inda nake yana fad'in." Irin wannan gayun Amina ai ba zan iya komai ba." Na ta'be baki uffan ban ce ba. Ashe karyar cin magani yake yi. Ya rike hannuna tare da ko'karin d'aga ni wai sai na tashi tsaye." Na cire hannuna ina fad'in."Menene haka?" Ya lumshe ido kafin ya ce." To nuna mini kwalliyar na gani, na bawa idona hakkinsa." Na dauke kaina domin ganin ya fara gigicewa. Ya d'ora hannunsa saman kirjina da suka dan taso ana ganin tsagarsu. Na cire hannun da sauri ya sake jana da k'arfi har sai da na zamo daga saman kujerar na zauna kasan kafet tare da tankwashe k'afata. Saman kujera ya zauna ya sanya ni tsakiyar k'afafunsa ya rankwafo kaina tare da zuba gabad'aya hannayensa saman kirjina ya ri'ke da kyau. Dole babu shiri na tashi tsaye abinda yake so kenan ya mike shima ya rike hannuwana da kyau yana kallona. Duk sai na tsargu na dinga kame-kame daga nayi yun'kurin zama zai tsayar dani. Cikin iyashege ya fara dukan mazaunaina yana fad'in." Babar mota babbar giwa ba dai yaro. Hajiya da kanta wannan samun irinta sai an had'a da sallar dare." Duk yadda na kai ga cin magani sai da ya sanya ni dariya na shiga bige hannunsa ina fad'in." Don Allah ka bari dukana fa kake yi a fakaice gaskiya zan rama wallahi." Ya ci gaba da d'aka mini duka a mazaunai bai bari ba duk da buge hannunsa da na yi yana fad'in.'' Gaskiya na iya kiwo wallahi, wai tur'kashi Allah Ya ba ni wuyan d'auka." Dariya na dinga k'yalkyalawa shima ya sa dariyar yana fad'in." Haba Hajiya ko ke fa, kin yi lefi kina ci mini kunu haka ake yi." Ya rike hannuna muka zauna saman kujera yana yi mini wani irin kallo da na kasa tantance ko na menene a hankali ya ce." Kin yi mini kyau yau fiye da koyaushe na yaba sosai kuma zan bada tukwici. Na zuba masa ido ina kallonsa ya ciro wani zuben azurfa da yake yatsanshi na tsakiya zoben tunda na san shi dashi a hannunsa kusan koyaushe kamar k'ara masa kyau da sabunta ake yi azurface gangariya daga tsakiya an yi mata ado cikin wani salo. Da yake siraran yatsu ne dashi ya sanya yana sa mini ya kama ya tsayana wanda ya zauna ya yi cif cif ya yi kyau sosai. Ya sumbaci hannun yana fad'in." Ga tukuici idan bai isa ba sai na sake bada wani abin." Na dubi yatsana ina dan murmushi na furta." Aikuwa na gode sosai da wannan tukwici ya yi mini ba sai an bada wani ba." Sai ya hade hannunmu wuri d'aya yana fad'in." Kin san wani abu?" Na girgiza kai ina kallonsa ya ce." Kada ki sake dukan yaran nan ba ni so, a duk lokacin da wani abu ya shiga tsakaninsu ko suka yi abu na rashin kyautawa a zare musu Ido, a yi musu fad'a amma ban da duka ba na so, domin hakan ba tarbiya ce ba don wasu lukutan dukan yakan kangarar da yaro. Na daidaita yanayina tare da fad'in. " Wai wanene ya gaya maka dukanta na yi? fad'a fa na yi mata na dan murde mata kunne shikkenan duka." Ya ce." Ta gaya mini kin dake ta a kanta shin kin san illar duka aka kuwa?" Raina ya b'aci amma na danne na ce." Sai na dake a kanta domin na illatata ko?" Ya yi shiru yana kallona. Na ce." Ni ban yi mata dukan da zai firgitata ba a gaban Baba Tabawa komai ya faru. Ba ni son cizo domin yana da illa sosai dole a ja mata kunne." Ya ce." Ni ma ban hana ba, dukan ne kawai na ce ba na so kada a sake?" A tak'aice na ce." To shikkenan." Domin maganar ta mutu kawai amma ba yadda za a yi Ina raye kuma ina gani su yi abinda ba shikkenan ba na zauna ina yi musu lako-lako ni kaina ba a yi mini irin wannan tarbiyar ba, ba kuma zan yi wa yarana ita ba. Na ce." Ina Hauwa na d'auka tare za ku taho?'' Ya ce." Tana can gidansu wai ba zata dawo ba" Da mamaki na ce." Ba zata dawo ba?" Ya ce." Kwarai kuwa haka ta fad'a, na ce to shikkenan Allah Ya hada kowa da rabonsa." Kawai sai na zuba masa ido da mamakin maganarsa wai Allah Ya hada kowa da rabonsa ya fadi hakan cikin kwanciyar hankali tabbacin abin bai dame shi ba. Ni Kam sam lamarin bai yi mini sugar ba. Na ce." Don girman Allah ka yi hakuri." Ya dube ni da mamaki kafin ya ce." Ha'kuri ai na yi tunda har na mayar da ita amma ta ce a a, kuma ta yi mana shegantaka sai ta sha zamanta abinda ga matan nan da yawa me zai dame ni Amina." Na ce." Amma dai ba kamar ita ba." Ya ce." To yanzu ya za ayi?" Kai tsaye na ce." Ta dawo dakinta don Allah." Sai ya yi murmushi a hankali ya ce." To ki kira wayarta sai ki roke ta Ina ga haka zai fi." Daga haka sai ya tashi ya nufi gado yana fad'in." Zo mu yi wata magana." Na yi jim kafin na tashi na bi shi gadon ya janyo ni na kwanta a gefensa sai ya sanya hannu ya rungume ni sosai a jikinsa yana fad'in."Alhamdulillahi. Sai na rasa godiyar Allahn ta mecece haka dai muka raya daran cikin shau'ki da sakwarkwcewa. Da asuba yana fita salla ni ma sauka k'asa cikin gajiya da bacci a idona. Sai da na yi wanka tukkuna na yi sallah na nemi gado na kwanta domin mugun bacci ne a idona wanda zai iya zame mini ciwo muddin ban yi shi ba.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa *PAID BOOK 2K COMPLETE ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA 1K VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* Kirana da aka yi a waya shi ya tashe ni wajejan goma da ashirin da biyar na safe. Koda na duba lambace babu suna na daga tare da sallama sai na ji muryar Idiris mijin Sahura nan da nan na daidaita yanayina. Domin zahirin gaskiya ni ma haushinsa nake ji dangane da abinda yake ahirin aikatawa. Tabbas nasan kiran nasa baya rasa nasaba da matsalarsu. Muka gaisa jikinsa a sanyaye ya fara yi mini bayanin halin da ake ciki Sahura ta rufe gida sannan ta tattara yara da kayansu ta kaiwa mahaifiyarsa bayan tasan bata da k'oshin lafiya. Yanzu haka sai a shagon dake jikin gidan ya kwanta shagon da yarana suke d'inki kenan yana jadadda mini a cikinsu ya kwanta cike da alhini da damuwa. Ban katse shi ba har sai da ya kammala tukkuna na ce." To wallahi ni dai Idiris ba ni da tacewa akan wannan lamari. Ina ganin ka kyaleta kawai tunda tafi buk'atar rabuwar sai ka je ka yi rayuwarka da sabuwar amaryarka yara kuma ai duk sun girma babu wanda za a yi wa wahala a cikinsu." Da damuwa ya ce." Saboda fa kusancin da yake tsakaninku ya sanya na kira ki Amina, me yasa za ki gaya mini haka ke don Allah idan na ce zan rabu da Sahura ba za ki yi mamaki ba?" Na d'an yi murmushi babu nisha'di na ce." Babu mamakin da zan yi Idiris abinda aure na mutum biyu ne idan ka gaji da ita zaka sawwa'ke mata mana ko kuma ka nemi hanyar da za ka k'untata mata." Ya ce." Yanzu dai don Allah ki rarrasheta wallahi ba wai don na wulakantata zan yi auran nan ba. Ina son Sahura ina kuma buk'atar cigaba da zama da ita ki rarrasheta ki bata ha'kuri ta dawo mu cigaba da zama in sha Allahu babu abinda zai faru domin itama yarinyar da zan aura bata da matsala 'yar gidan tarbiya ce wallahi bata da fitina." Na yi dariya ina mamakin maganarsa tun bai zauna da yarinyar ba yana shedar halayenta tabbaci kenan ba zai janye ba. Na ce." To shikkenan zan yi magana da ita zuwa an jima in sha Allahu." Da sauri ya furta." Zan kira ki domin na ji abinda ku ka yanke amma don girman ki tausheta ta dawo na ware mata turmi biyu daga cikin lefen da nake had'awa sannan zan bata dubu hamsin sai ta sayi kayan kwalliya." Na ce." To shikkenan. Da takaici na katse wayar ban tsaya na kΓ rasa sauraran karshen maganarsa ba. A tunana ai Sahura tafi karfin turmin atamfa biyu da dubu hamsin, ita wahalar nawa ta yi masa tunda suka yi aure har yanzu ma cikin yi masa hidima take. Da yammacin ranar muka yi waya da ita na gaya mata Idiris ya kira ni a waya akan abinda yake faruwa. Kamar yadda ya buk'ata din na fara rarrashinta da kawo mata misalai ta yi shiru tana saurarena don har ina murna ina cewa ta sauko a zuciyata sai da na gama maganata tukkuna ta ce ." Ba ni buk'atar atamfofinsa ya ri'ke har da k'udin ya k'arawa amarya Amina, takarda zai aiko mini da ita yanzu zaman da nake yi kenan." Na ce" Sahura akan kishiya dai idan ki ka kashe auranki na kusan shekara ashirin da wani abu wallahi kin ba ni kunya kuma na raina wayonki, ki bari ta shigo mana ki ga kamun ludayin zaman. Haba don Allah ki jure mana." Kashe mini wayata ta yi ta barni ri'ke da tawa a kunne da mamaki. Bayan magriba Idiris din ya dinga kira wayata ina kan daddauma ina jan carki kamar yadda na saba. Koda na duba na ga shine na ajiye wayar kawai na cigaba da abinda nake yi shi kuma bai fasa kira ba. Hakan ya yi daidai da shigowar maigidan wanda shi ma tunda ya fita da asubahi bai sake shigowa ba. Ya d'auki wayar yana dubawa sai ya kalle ni kaina a sunkuye kawai sai ya daga tare da sanyata a kunnansa jin muryar namiji na ji yana fad'in." Wanene?" ban ji abinda Idiris din ya ce masa. Na ji yana fad'in." Mijin Sahura ne to bari ta kammala tana azkar ne zuwa an jima sai ka kira." Ya yi shiru na d'an wani lokacin kafin na ji yana fad'in." Amin Ya Allah, ma sha Allah, ka kira zuwa an jima kadan." Daga haka sai ya kashe wayar ya ajiye har na kammala na juyo ina dubansa ya ce." Mijin Sahura ne ya kira ki a waya ina fatan lafiya?" A tak'aice na ce." Lafiya ba lafiya." Ya dube ni sosai yana fad'in." Suna da matsala ne?" Ina ko'karin cire hijabin jikina na furta." Aure zai ka'ra shine take bore har ta tafi gida." Ya yi d'an jim kafin ya furta." Na kan rasa inda tunaninku yake tafiya wataran Amina, daga zai kara aure domin raya sunna sai ta ta tafi ta bar dakinta menene amfanin hakan." Cike da takaici na ce." Ai ba a ce kada ya kara ba, ya bari ya tsaya da k'afafunsa tukkuna bashi fa da cikakkiyar sana'a, wallahi Sahura wahala take sha a hannunsa kuma ta yi masa hallaci tunda suka faru a gidan haya suke shekara kusan ashirin da uku da auransu buge-buge yake yi itace karfin kula da gidan tun kafin ma ta samu aiki a kamfaninka haka take gwagwarmaya. Amma shine daka kawai an yi musu rabon gado ya samu miliyan takwas ko wata biyu fa ba a yi da raba musu kudin ba ya fara yun'kurin karin aure har yana tara lefe a dakinta. Ita kuwa ta kulle gidan ta gudu ta kai masa yaransa wurin Babarsa." Dariya ce ta sub'ce masa ya dinga yi har ina mamakinsa na d'auka ai zai cigaba da goya masa baya. Ya ce." A lallai bai kyauta ba kuma da gaske bai yi adalci ba. Yadda ki ka gaya mini yanzu ai ita ta yi masa hidimar da ta zarce ta miliyan takwas to me yasa tunaninsa bai kai ya saka mata da alheri ba sai da kishiya. Bai kyauta bai kuma yi daidai ba, in banda rashin tsinkaye ai ba aure ya kamata ya yi ba a yanzu ko?" Da sauri na ce." Kwarai kuwa abinda itama take ji wa haushi kenan zai bata turmin atamfa biyu da dubu hamsin abinda ya kara ba ni haushi dashi kenan." Ya ce." Kin ga kira mini Sahurar yanzu na yi magana da ita." Na zauna gefansa ya miko wayata na lalubi lambata bugun farko ta daga cikin bala'i ta fara fad'in." Amina ki kyale ni don Allah idan har kin san ba maganar arziki za ki gaya mini ba, na gaya miki na gama yanke hukunci, idan kema za ki goyu da bayan Idiris din sai nasan a wani aji zan ajiye ki." Ina binki bashi idan kin karanta ba ki biya ni hakkina ba Na ce." Yi ha'kuri mai da wukar sis, Yallabai ne zai yi magana dake." Ta yi shiru ba ta ce komai ba sai na mik'a masa wayar da sauri ya kar'ba a nutse ya kira sunanta "Sahura." Ina ji ta amsa cikin ladabi." Na'am ranka ya dad'e ina yini?" Ya ce." Lafiya lau ya kuke ina yara?" Ta ce." Kowa lafiya lau Sir." Shiru ya d'an biyo baya kafin ya yi gyaran murya ya ce." Kin san abinda nake so dake?" Ta ce." A'a. " Ya ce." Amina ta yi mini bayanin duk abinda yake faruwa, ki yi hakuri ki koma dakin mijinki ki cigaba da kula da yaranki, shi kuma ki kyale shi idan har kina da hakki sannu a hankali Allah zai saka miki. Ni kuma zan yi miki alheri domin ki zauna a wadace cikin walwala zan canza miki gida mai kyau sannan zan baki kudi ki dinga wata sana'ar a gefe sannan ki cigaba da zuwa aikinki kina taimakon yaranki da 'yan uwa, kada don mijinki zai kara aure ki yi fushi ki dasawa kan ki k'unci yaranki su shiga damuwa ki daure na wani lokaci komai zai wuce ." A sanyaye ta ce." Na gode ranka ya dad'e, Allah Ya saka da alheri, shikkenan in sha Allahu zan koma kamar yadda ka buk'ata." Cike da jin dadi kuwa ya furta." Ni ma na gode sosai Sahura, zan yi magana da Jamilu sakatare na nan kamfanin naku duk abinda yake da akwai zai yi miki bayani in sha Allahu maganar abinda na ce zan baki kuma za ki gani a daran nan." Ta dinga godiya har muryarta tana rawa. Ya mik'o mini wayar na kar'ba a d'an sanyaye na ji dad'i sosai da ya shiga lamarin gashi har da alherinsa ko babu komai yana da lada a wurin Ubangiji. Muka yi sallama da ita tana fad'in." Na kara yi masa godiya. Na dube shi a hankali na ce." Mun gode sosai Ubangiji Allah Ya saka da alheri." Bai kalle ni ba ya ce." Ba ni details dinta yanzu ." Ya miko mini wayarsa na kar'ba na sanya masa kamar yadda ya ce. Ya ce." Ke nawa ki ka bata gudummuwa?" Na ce." Gudumawa kuma?" ." Dannar kirji kuke cewa ko?" Dariya na yi na ce." Ban bata komai ba wallahi." Ya d'an Harare ni yana fad'in." To yaushe kuwa za ta saurari rarrashinki irin wannan ana had'awa da hasafi sai ki ga an shawo kan matsalar." Na dinga gyada kaina ina dariya lallai ne kudi suna iya sayan komai amma ban da rai da rayuwa. Miliyar biyar ya tura mata bai gaya mini ba amma yana tura mata da kamar minti goma ta kira ni a ki'dime har da rawar murya "Amina don girman Allah ki kara yi mini godiya yanzu nan na ga sa'ko 5m na gode na gode na gode Allah Ya saka da alheri ga sabon gida an ce za a ba ni." Dariya ta kama ni na ce." Sahura yanzu don Allah ina rantse-rantsen da ki ka dinga yi, Idiris fa aure zai ka'ra ko kin manta." Ta ja tsaki tana fad'in." Wallahi tallahi Amina saboda Yallabai ya saka ba ki a maganar nan zan koma zaman aure da Idiris amma wallahi ba don haka ba sai dai ya aiko mini da takardata." Ta kashe wayar ba tare da ta jira ta ji abinda zan ce ba." Ya dube ni yana fad'in." Ba ki kyauta ba Amina." Ina dariya sosai na ce." Don ba ka ji rantsuwar da ta dinga yi ba shine abinda ya ba ni dariya da mamaki." Ya gyad'a kansa Shima da d'an murmushi a saman fuskarsa ya ce." Ai tace saboda na sanya ba ki zata koma. Kuma wallahi na ji dad'i sosai tuntuni na fahimci cewa ai tana da kirki da saukin hali." A tak'aice na ce." Hakane kam Sahura mutum ce har da rabin mutum mun gode sosai ta ce na sake godiya ina yi akan kaina da ita Ubangiji Allah Ya sa kafi haka." Ya amsa da Amin suma Amin yana kallona. Na dan sauke ajiyar zuciya kafin na ce." Sai mu yi maganar Hauwa tunda mun sasanta wannan auran." Ya bata rai yana fad'in." Za ki bata mini rai kenan ko?" Na ce." B'acin rai kamar yaya?" Cikin 'kosawa ya ce." Maganar Hauwa ta ishe ni a gidan nan Amina, ya kamata ke ma ki bar ta kamar yadda na bar ta ba na son abinda zai rikita mini gida dama can itace husumiya yanzu da bata nan ba gashi kuna zaune kalau da Maryam ba." Haka kawai sai na ji rashin jin dadin maganarsa. A ganina kamar Hauwa bata cancanci haka daga wurinsa ba duk da bai gaya mini abinda ya faru ba a wajan sulhunsu amma na lura haushinta da yake ji ya sake ninkuwa. Zaman da na yi da ita na fahimci macace mai taurin kai da girman kai har shi eanda ya ajiyeta yi masa take kuma a cikin ayyukan da ta dinga yi a gidan nan da gadara da iko take gudanar da komai dalili tana ganin kamar ta fi kowa dangantaka mai karfi bayan ta aure duka na fahimceta. To amma ni wannan baya damuna tunda nasan matsayina a zuciyar mijina ko bai fito ya fad'a ba. Ba na sha'awar a ce sun rabu gabad'aya ga zuria a tsakaninsu mai k'arfi kamata ya yi a ce sun sulhunta junansu sun yi hakuri sun cigaba da zama. Ganin yadda ya had'e rai da nuna baya buk'atar sake maganar Hauwa sai na shigo da maganar zuwa maiduguri tunda shi ya yi mini alkawari ya ce za mu je a karshen wata amma daga mun dawo za mu tafi legos tunda Alhmdullhi jikin matar tasa ya yi sau'ki. *** Abinda ya faru kenan kamar yadda ya yi mini al'kawari cikin karamci da kara da kulawa muka je maiduguri tare. Ya bi dangin Mamana da alheri mai yawa. Baban Saude bayan gari a lokacin da muke je garin. Da yawa wad'anda ba su ta'ba ganinsa a zahiri ba suka yi tozali da shi tare da alherinsa. Ni kuma na sayawa Fadila sabuwar freezer 'katuwa da kenan d'inki domin yin sana'ar sayar da ruwa da 'kan'kara. Kwananmu biyu kacal a maiduguri muka yi sallama da su. A ranar da muka dawo a gidan Momi ya kwana washe gari ya shigo mini a hargitse yana gaya mini jikinta ne ya sake tashi jiya ba su yi wani baccin kirki ba suma ta yi sai gefan asubahi ta dawo. Ya ba ni tausayi sosai itama haka domin da gaske ne duk mai zuciyar imani idan ya ga halin da take ciki zuciyarsa sai ta motsa. Dole shiryin tafiyarmu Legos ya rushe yadda hankalinsa ya tashi da ciwon komai nasa tsayawa ya yi Kwana biyu a tsakani ya sake kwasarta suka sake koma can kasar hindu din asibitin da suka kula da ita a wancan karon domin sake duba lafiyarta.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *PAID BOOK 2K COMPLETE ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA 1K VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* A tsanake ta ce." A a ai tare duk muke tafe tun a waje ya ce Garba ya ajiye shi yana can tare da Adamu." Na gyada kaina ba tare da na sake cewa komai ba. Baba Tabawa ta kawo tire uku masu girma cike da abinci na taimaka mata wurin zubawa kowa Hajja ta ce ." Hajiya Saratu tana tafe in sha Allahu mun yi waya da Alhaji Sa'idu shi da d'an uwansa Alhaji Dahiru sun ce za su yi kokarin samun jana'iza." 'Yan uwan mahaifin maigidan ne wanda a yanzu su kadai ne suka rage musu a family din. Na gyada kaina a sanyaye na ce." Allah Ya kawo su lafiya. Kai na jima ban shiga tashin hankali da nadamar rayuwa ba sai a rasuwar baiwar Allah nan. Tunda gawar ta iso gabad'aya estate din namu ya cika da motoci jama'a daga kowace kusurwa abokanan maigidan dama wasu daga ciki abokan tsohon mijinta ne. Cikin gidanta cike da 'yan uwanta da zuriarsu tare da abokanan arziki da yaranta masu yi mata hidima na shagunanta. Ana ta koke koke masu dauriyar daga ciki kad'ane. Babbar yarinyata Nusaiba sumanta biyu har yanzu ba ta gane wanda yake kanta ba. Nabila kuma tana ta iskokai a wani d'aki da 'yan uwansu sun kulle-kulle kofa don kada ta fito daga inda muke a zaune muna jin ihunta. Cikin masu yi wa Momi wankan gawa har da Baba Tabawa lallai na yaba k'warai da aniya wurin jajuecewarta da dauriyarta koda yake yadda take ba ni labari a gaban idonta mahaifiyarta ta rasu kuma itace ta wanke ta. Wannan ya kara tabbatar mini da cewa Baba Tabawa tana daya daga cikin salihan matan da Ubangiji ya ce lallai yana jin kunyarsu a gidan duniya da lahira dalilin rashin haihuwa. Ban tashi tabbatar da cewa d'an adam ba a bakin komai yake ba sai da aka gama had'a Maryam tsaf cikin likkafani a mike cikin makara ta zama 'yar mitsitsiya a tsakiyar makarar tsabar ciwo ya cinyata ana ta lallabata sunanta gabad'aya ya shafe daga jiya zuwa yau din wasu na kiran ta da gawa wasu na kiranta da marigayiya. Yaranta da mijinta tare da yan uwanta sun kewaye makarar yayin da masu aikinta mata da muke tare da su a gidan suke gefe sun cure kansu wuri d'aya sai shar'bar kuka suke yi. Adamu dake tare da Yusi ya can gefe daya kuka yake yi sosai yana fad'in." Momi kin mutu da wa ki ka bar mu a duniya, ba mu da uwa ba mu da uba. Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!. Sambatun da yaron yake yi ya kidima ni sosai ya kuma ba ni tausayi ainun na yi saurin d'auke kaina daga kansu Yusi yana ta rirrike shi sun kasa zuwa gaban gawar ma gabad'aya. Hajja da Gwaggo suka nufi bakin makarar. Na yi na yi na ja kafata domin bin bayansu na kasa don wata irin juwa da Hajijiya nake ji idona na ganinsu garagara, Bayan haka kuma gabad'aya a tsarge nake ga yanayin kallon da na ga wata mata da na ji suna kiranta da suna Yabi take yi mini irin na wulakanci da neman fitina. Hawaye masu d'umi suka silalo kumatuna wanda ya yi daidai da lokacin da na yi hu'bbasa wurin sarrafa 'kafafuna amma suka doje ban san yadda aka yi ba kawai na ji ni a k'asa na zube a lokacin ne kuma naga kamar gilmawar wani abu daga sannan ban sake gane komai ba sai dana farka tukkuna na tabbatar da cewar suma na yi lokacin har an kaita makwancinta an dawo. Anti Yagana sun iso tare da Inna Uwani. Ban yi mamakin ganin yanayinsu ba domin akwai d'imuwa da tashin hankali na rasuwar da aka kwantsama. Ko baka da ji'bi da mutum fad'in Annabi ne mutuwarsa dole ta nasheka balle wannan matar da alherinta kowa yake gani. Hajja ta shigo d'akin da muke tana fad'in." To alhamdulillahi tunda ta tashi da ji da ganinta da kuma lafiya mun gode Allah Yagana taimaka mata sai mu koma can gidan nasu mu yi namu zaman domin nan din zaman zai zame mana fitina. Gwaggo da fitowarta daga bandaki kenan d'aure da alwala ta ce." Ni ma shawarar da na yanke kenan hakan zai fi alheri." Anti Yagana ta dube ni a d'an sanyaye kafin ta ce." Sannu ba dai kya jin komai a jikinki ko?" Kaina na gyad'a mata a nutse na ce." Ashe kun zo?" Ta ce." Mun zo mun tarar an d'auki gawar gidan a kacame ana ta hayaniya ke kuma gaki a sheme sai da likitanku ta zo ta dubaki fa dogon suma ki ka yi." Shiru na yi ina nazarin maganarta kafin na ce." Anti Yagana mai ya faru ne?" Ta'be bakinta ta yi ba ce mini komai ba. Na daga kaina na kalli Hajja dake tsaye jikin bango rumgume da hannunta a k'irji nan take na karanci damuwa da b'acin rai a saman fuskata. Ban sake wata magana ba na tashi zaune hijabi na da yake gefe anti Yagana ta miko mini na zura a jikina tana taimaka mini na yun'kura na tashi ta ri'ke ni. Na ce." Ki cika ni zan iya tafiya da kafafuna. Inna Uwani ta ce." Da dai kin bari ta rike ki jikin naki ai har yanzu bai gama daidaita ba. Hajja da Gwaggo suka yi gaba. Wani irin kallo dangin marigayiyar suke mini na tsana da kyama. Anti Yagana ta juyar da kanta ba ta ce komai ba. Ni ma ban ce musu komai ba na ji ita wannan matar mai suna Yabi tana fad'in." Kun kai ta kasa kun ji dad'i, sai ku jirayi hakki domin wallahi ba mu yafe muku ba, duk abinda za ki nuna a banza a wofi Maryam dai karshenta ya yi kyau ku kam in sha Allahu mutuwar wulakanci za ku yi." Maganganunta ne suka dinga yi mini amsa kuwawa! a kunne gabana ya dinga bugawa da karfi da karfi. Wannan babban kalubalen ban shirya tararsa ba a yanzu domin ba ni da hujjar da zan kare kaina Allah shine shahidi. Muka fita tun daga haraba cike da jama'a har zuwa waje mutane cike cikin manya manyan rumfunan da aka kafa. Kafafuna suka dinga hard'ewa gabad'aya sai na tsargu domin maganganun da matar nan ta yi sun sake dakusar da duk wani karsashi da kwarin gwiwata. Shin wane irin kallo jama'a suke yi mini a yanzu dana fito cikinsu. Cikin dubara na janyo saman hijabina na rufe fuskata dashi dama rike nake a hannun anti Yagana. Ina jin sanda Hajja ta tsaya suna gaisawa da ire-iren abokanan Yallabai din na ce da anti Yagana ta yi sauri mu wuce domin ba ni da wani k'umaji da nutsuwar da zan iya tsayuwa a gaban jama'a domin kar'bar ta'azziya. Muka yi gaba muka bar su ita da Gwaggo suna gaisawa. K'uryar d'akina anti Yagana ta dangane da ni na zauna kan gado kamar wata sabuwar amarya na yaye hijabin da ya katange fuskata. Muka had'a Ido nan take na rushe da kuka na ri'ke hannunta katamau! Jikina na kyarma na furta." Anti Yagana Hajiya Maryam ta mutu sanadiyar lalure-laluren da suka yi mata hijabi, ina tsoron kada 'yan uwanta da jama'a su jinginta rasuwarta da ni da Hauwa, ai kin ji abinda daya daga cikin 'yan uwanta take fad'a ko?" " 'Karamin tsaki ta yi kafin ta ce."Amina duk wanda zai alak'anta rasuwar matar nan daku to dama can ba masoyinta ba ne. Su kansu 'yan uwan nata da suke ko'karin tashin husuma ba kaunarta suke yi ba tunda har suke jingina rasuwarta da wani abu daban. Kishi halak ne kuma duk gidan da aka had'a mace fiye da biyu ana samun irin wad'annan matsaltsalun. A ganina wannan ba wani abun damuwa ba ne, rigima ce suke nema kuma in sha Allah rabbi har a share makoki ba za mu tanka musu ba. Ni gidan ma ba zan sake shiga ba tunda na lura duk yawansu babu mai dattako a cikinsu. Rashi kam ba su kadai suka yi ba mutane da yawa ne domin Hajiya Maryam bango ce majingina kuma uwar marayu har ma da masu uban. Don haka iyakacin k'aunar da za su nuna mata su bita da addu'a tare da rungumar abinda ta bari shine kawai sakamakon da za su yi mata bayan rayuwarta. Don haka ki samu nutsuwa ki kuma daina tunanin kina da hannu lokacinta ne kawai ya yi kuma babu wanda ya isa ya tsalle rana da sa'in komawarsa ga Allah." Maganganun anti Yagana sun d'an sanya ni mini nutsuwa kad'an amma har yanzu zuciyata ba ta daina yin tsalle akan abinda na ji yana fitowa daga bakin 'yar uwar marigayiyar ba. Babanmu suka iso tare da baba Sule da Ummansu Hadiza kamar yadda ya fad'a. Baban Saude ne har yanzu bai shigo inda nake ba, anti Yagana kuma ta gaya mini tare suke da Babansu Fadila har da Baba Madu wanda ya kasance babban yayansu Mamanmu, mahaifin Babandi. Kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Sai wajan biyar saura tukkuna suka shigo da d'an yawansu duk muna zaune a babban falo. Maigidan tare da iyayenshi biyu 'yan uwan mahaifinsa da kuma Baban Saude Baba Madu da Babansu Fadila. Falon ya cika da sabuwar gaisuwa tare da yi wa juna ta'aziya. Ta mussaman suka yi mini gaisuwar na amsa yayin da nake jin cikowar ruwan hawaye idona. Ina jin Hajja tana tambayar Alhaji Sa'idu Hajiya saratu ya ce tana can gidan mai rasuwar tunda koda suka sauka nan ta shiga ba ta fito ba kuma har yanzu. Suna ta tattauna hirar marigayiyar yayin da maigidan ke sake basu labarin irin wahalar da ta sha na jinyya farkon zuwansu asibitin a yayin da aka dora ta akan magani an ga sauyi sosai yanayin yadda yake magana da alhini shi yake nuna mutuwar ta dake shi kwarai da gaske kwarmin idonsa ya zurma fatar lebanshi ta bushe kamar wanda ya yi azimin shekara bai sha ruwa ba. Irin wannan yanayin ya shiga a lokacin rasuwar tsohon mijinta Alhaji Amadu da kyar ya dinga cin abinci. Yanzu ma ba na raba daya da biyu rabonsa da abinci tun da aka yi rasuwar kwana da yini kenan. Gabad'aya sun jajanta sosai kuma kafin tafiyarsu sai da Baban Saude ya jagorancemu gabad'aya muka yi mata doguwar addu'a wadda take d'auke da surorin da ake karantawa mamaci. Yamma likis suka yi mana sallama gabad'ayansu har da Hamusu da Babanmu domin cewa ya yi shi ma ba zai zauna ba tafiya za su yi tunda sun yi abinda ya kawo su. Shi kansa maigidan ya so su kwana ko daya ne amma gabad'aya suka ki har da kawunan nasa. Hajiya saratu ce kawai ta zauna ta ce sai an yi sadakar ukku tukkuna. Yallabai din ya bada umarnin mayar dasu Babanmu gida. su Baban Saude kuma dama a motarsa suke tafe. Sai bayan sun tafi tukkuna Hajja ta dinga fad'a wai mai yasa anti Yagana ba ta jagoranci Ummansu Hadiza zuwa gidan mai rasuwar ba. Anti Yagana ta ce mata mantawa ta yi shiyasa ni kuma nasan ba haka ba ne ita da kanta ta gaya mini k'afarta ba zata sake taka gidan ba. Gaisuwar da ta yi wa maigidan ma ta isa ba sai ta je ta yi wa 'yan uwanta ba tunda dukkaninsu taron tsintsinya ba share ne. Sai bayan magariba Hajiya Saratu ta shigo. Ina d'aki lokacin na idar da sallah ban ka ga tashi daga kan daddauma ba ta shigo. Na saki fuskata sosai Ina fad'in." Mai sunan Mamana ina yini?" Ta zauna gefan gadona a nutse tana fad'in." Lafiya lau Yayata kuma diyata." Na yi murmushi a hankali na ce." Ai tun d'azu aka ce kina can gidan marigiyar ina nan ina ta zuba idon ganin Mamana" Ta dafa kafadata tana fad'in." Ga ni na shigo ai Amina ya muka ji da hakurin Maryam lokaci ya yi Ubangiji Allah Ya gafarta." Na amsa da "Amin Ya Allah." Cikin wata iriyar murya. D'akin ya d'an yi shiru wanda ya yi daidai da lokacin da anti Yagana ta fito daga bandaki daure da alwala. Ta saki fuska tana fad'in." Hajiya kin shigo kenan?" Ta ce." E wallahi Yagana ya gida ya yaran, ya muka ji da hakuri?" Anti Yagana ta ce." Ha'kuri da godiya Hajiya Allah dai ya jikinta da rahama." Da Amin ta amsa yayin da take sake dora hannunta a kafad'ata. Anti Yagana ta d'auki daddauma da hijabi ta koma can gefe domin gabatar da sallar magriba. Ta ce." Ai ni ban fito ba daga gidan ba sai da na gabatar da sallata tukkun." Na yi murmushi kad'an ban ce komai ba. Sai ta ce." Amina akwai maganganun da nake so mu tattauna dake idan babu damuwa." Cikin nutsuwa na ce." Babu damuwa Hajiya Ina sauraranki." Ta sauke ajiyar zuciya a tsanake ta ce." Duk abubuwan da suke faruwa a zamantakewar gidan nan ina da labari. Da har Ina cewa tunda matsalar ta'ki ta'ki cinyewa zan wanko kafata takasan na zo naji komai daga gare ki nasan ke ba za ki yi mini karya ba, ba kuma za ki goyu da bayan mijinki ko ki goyu da bayan Hauwa ba, idan har kema kina da lefi za ki gaya mini gaskiya sanin da na yi miki tun farkon fari. Ta nisa kafin ta cigaba da cewa. Sai gashi kuma rasuwar Hajiya Maryam ta ratsa hakan sai ya kara ba ni k'warin gwiwar zuwa domin na ji komai daga gare ki, Amina da hankalinki za ki biyewa Hauwa da har yanzu ba ta san rayuwa ba, mai yasa kuka kasa bawa mijinku k'warin gwiwa da taimako wurin ganin ya rike amanar abokinsa. Jimawata gidan marigayiya Maryam tana da dalili domin 'yan uwanta ne suka zaunar da ni suna wassafa mini irin zaman da kuka yi da ita da irin abubuwan da kuka dinga yi mata na rashin kyautatawa, idan har hakan gaskiya ne Amina ban tsammata daga wurinki ba domin kallon da nake yi miki kin wuce a ce a yanzu an zauna a nuna miki abinda ya dace idan Hauwa ta yi hakan ba zan yi jayayya ba dama na san halinta da na ji sunanki a ciki ne sai hakan bai yi mini dadi ba, mai ake gudu ne a zaman tare irin wannan fa, yanzu ina Maryam din take ta mutu ta bar duniya to mai zai sanya ba za mu yi hakuri da rayuwa ba. Gashi Hauwa har sai da ta yi sanadin da Tajo ya saketa saboda kuma bata da hankali ta tafi ta bar yaro jinjiri fisabillahi ina hankali da tunaninku yake?" A nutse na dubeta tare da cewa." Mamana abubuwan da yawa sun faru masu dadi da akasin haka. Amma zan gaya miki wani abu da ba kowa ya san shi ba sai ni sai Ubangijin da ya hallice ni wallahi tallahi ban ta'ba kin Maryam a cikin raina ba. Tabbas akwai kishi kuma kowace mace tana da nata daidai gwargwado amma ni Amina ban zafafa shi akan matar nan ba duk sanda zuciyata za ta kitsa mini mummunan abu akan kanta nakan yi tirr da ita da take bijiro mini mugun nufi akan matar da alherinta ya fara riskata kafin wata mu'amula mai karfi ta ratsa tsakaninmu. Duk abubuwan da suka dinga faruwa yaranmu suka had'a amma ni da ita sa'insa mai muni bata ta'ba hadamu ba, kuma lafiya lau muka yi sallama da juna har ta koma ga Ubangijin talikai. Har yau har gobe ban k'ulleceta ba ban kuma k'ullaci yaranta ba ina jin tausayinsu kuma ina yi musu kallo irin na uwa." D'akin ya shiru bayan ajiye maganata na ja numfashi cikin bushewar ma'kogwaro na cigaba da cewa." Magana akan Hauwa kuma ni ba zan iya ce miki komai ba, abinda dai na sani shine Hauwa ta yi mini kokari kwarai kuma babu kishi da ganin kyashin juna a tsakanina da ita ni fa a tunanina kenan, domin Hauwa 'yar uwa na dauketa ba kishiya ba. Duk hanyoyin na bi domin na nuna mata abubuwan da take ba su da kyau na bi, na yi bakin kokarina amma ba ta ji ba. Dalilin rigimarsu da maigidan tana da ala'ka da ni da ita mai rasuwar da yaranta. Mun daidaita a wattanin baya har na so ni da ita mu je mu dubata a lokacin da ta kwanta a asibiti amma fafur ta'ki sai tare da Baba Tabawa na tafi mai aikinm kenan. Wannan shine abinda zan iya gaya miki Mamana bayan hakan ban san abinda yake tsakanin Hauwa da mijinta ba tunda tun kafin ta aikata haka na yi iyakacin bakin kokarina a kansu ita dashi amma babu wanda ya saurareni a cikinsu." *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *2k COMPLETE ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA 1K VIA 0542382124.... BINTA UMAR GTBANK.* *07084653262* Ta jima sosai kafin ta yi magana cikin yanayi na damuwa ta ce." Dangin matar nan dai a ciki suke da ku Amina domin gani suke yi bakincikinku ne ya kashe musu 'yar uwarsu duk wanda ya zauna ya tashi sai sun amayar masa da abinda yake cikinsu. Anti Yagana ta ja tsaki tana fad'in." To, abinda ya fi sai kawai su d'auki lasifika su fara bi sa'ko da loko suna shela tunda ba su da hankali, wannan ba k'auna ba ce abinda suke nunawa tsantsar jahilci ne kuma za su hana yar uwarsu kwanciyar lafiya a kabarinta muddin suka ce za su tashi rigima abubuwa da yawa ne za su faru. Dama zaman tare ai ya gaji haka dole a samu matsaltsalu ma bambamta sai dai kawai Allah Ya kyauta, ta wace hanya kike ganin za su hade mata kai ko su ware ta. Matar da ta samu soyayyar miji fiye da su, Hajiya Saratu ki duba maganar nan don Allah kaf fa yaransu suna hannunta basu da iko akan komai kina kwance kina jina Allah Ya jikanki, idan sun yi magana akan nuna rashin yarda ya goyu da bayanta. Ai ma sun yi hakuri da ita wallahi kuma son su ta da zaman lafiya domin da wahala a ce wata uwa an yi mata fin karfin a kan yaranta ta iya dannewa sun yi namijin kokari anan kuma na yana musu. Mu dama tsakaninmu da ita alheri ne, wallahi koyaushe Amina ta gaya mini halin da take ciki na damuwa akan zamantakewar gidanta akan tausheta tare da nuna mata cewa haka auran yake gabad'ayansa jarabawa ce a ciki jin dadinsa kad'an ne kuma ibada ne, kokarinmu ta yi hakuri ta zauna a yau ba wai don yar uwata ba ce ina yabonta sosai dalilin abubuwa da yawa da ta dinga cin karo na b'akinciki da b'acin rai amma ta yi hakuri ta jure. Don haka idan 'yan uwan Maryam sun zargi Amina da Hauwa wajen gumawa Maryam takaici har ta rasu to sun so kansu kuma zahiri ba su bukataci zaman lafiya ba domin dai duk mai hankali ya san matar nan ta sha jinyya kafin ta rasu. " Ta girgiza kanta tana fad'in." Hakane amma Yagana daidai ne Hauwa ta ajiye jariri sabuwar haihuwa ta shilla wata duniya ko a waje Tajo ya je ya auri yarinyar nan ya kamata ta aikata mana wannan rashin mutuncin. Jininmu ce fa ciki daya fa ba wasa ba ne Hakan ne ma ya sanya duk muka ture komai da jin zafin abinda ta yi Hajja ta ce mu je a bata ha'kuri bisa bin umarinta muke je can bauchi Hauwa ta rufe idonta ta yi mini dibar albarka zagi na ne kawai ba ta yi ba, hakan ya sanya na yi alkawarin cewa muddin da yawuna da shawarata Tajo ya gama zama da ita har abada tunda ta za'bi ta tozartamu shikkenan sai dai zumuncin ya lalace ." Anti Yagana ta ce." A a ba za a yi haka ba Hajiya, ai ko babu dangantaka ta jini an riga an zama daya tunda har yara suka ratsa tsakani. Don kyautawa Hauwa ba ta kyauta ba. A dai nuna mata kuskuran abinda ta yi a gyara ta dawo dakinta a ganina shine abinda ya fi dacewa." Ta gyada kanta ba tace komai ba tabbacin maganar anti Yagana ba ta gamsar da ita ba. Na ce." Anti Yagana idan Hauwa tana da lefi shima yana da lefi fa. Domin ya yi abubuwa sosai wanda ya kamata a ce ya gane kuskure ne a zamantakewa amma bai gane ba, ni na yi kokarin dannewa dalili nasan babu wani abun da yake dawwama sai ikon Allah wanda shi muka gani yanzu. Na yi ta ko'karin bata shawara kan cewa ta kawar da kanta ta kasa jimirin yin hakan har sai da bacin rai ya ratsa tsakaninsu. Ya kamata gaskiya a tsage Mamana. Shi kansa maigidan akwai tashi matsalar sai dai ace ta Hauwa ta rinjayi tasa." Ta ce." Ni dai da yawuna ba zan bashi umarnin dawo da ita ba duk hukuncin da ya yanke daidai ne." Tana fad'in haka ta tashi tana cewa." Zan je na watsa ruwa can wurin su Hajja jikina duk ciwo yake yi mini na samu nasa wani abu a cikina." Na ce." To shikkenan Mamana dama na ce da Baba Tabawa ta tu'ka mana towo don zai fi manΓ  dadin ci akan tsabar shinkafar nan." Ta ce."Aikuwa kin yi shawara mai kyau Amina don tunda aka sanar da ni rasuwar nan wallahi ko na sanya abinci a gabana sai dai na kalle shi ba na iya ci. Kai rasuwar baiwar Allah nan ta ta'ba ni wallahi." Anti Yagana ta ce." Ba ke kadai ba wallahi ni kaina na gigita kwarai da aniya Ubangiji Allah Ya yi mata rahama." Muka amsa da amin gabad'ayanmu kafin ta yi mana sallama ta fita daga d'akin, anti Yagana ta dube ni tana fad'in." Na so na tambayi Ummansu Hadiza labarinta amma na sha'afa wallahi, kuma don dai Babanmu ya ce sai sun tafi amma da ko kwana daya sai su yi tunda yanzu dole ne su kwana a hanya ina so mu sake samun lokoci mu je mu sake dubata ko ya ki ka ce." Na ce." Hakane anti Yagana ni kaina Hadiza tana raina wallahi, dalilin da ya sanya kenan na ce da Hamusu duk k'arshen wata ya dinga yi mata siyayya yana kai mata, zuwan namu yana da amfani ai hannunka baya rubewa ka yanke ka yar." Ta furta." Ni har fargabar ganinta nake yi wallahi saboda ina tuna irin kukan da ta dinga shirga a ranar da muke je kin san da kyar aka tura ciki muka fito, na jima ina kukan zucci duk sanda na tuna da halin da take ciki nakan shiga yanayi na damuwa mace a irin wannan wurin a ajiye Amina duniyar nan ta baci duk da ba ita kadai ba ce, amma su kansu ma'aikatan wurin wallahi wasu daga ciki ba su tsoron Allah." Cike da damuwa na ce." Anti Yagana lefin Hadiza na kisa ne ta kuma tabbatarwa da kotu gaskiyarta ba mu da wani yun'kuri da zamu yi domin ceto ta. Hakkin rai ba abin banza ne. Idan Allah Ya kar'bi tubanta kuma tana da ragowar rayuwa sai ki ga ta fito ta hanyar da ba mu yi tsammani ba. Idan kuma sun kasheta shikkenan sai ta riski Ubangijinta a wankakkiya. Ubangiji Allah Ya kare mu daga fadawa jarabawa da mummunar kaddara." Ta amsa da Amin Ya Allah da yanayi na damuwa da nadama. Misalin goma da rabi maigidan ya shigo tare suke da Kamalu ban yi mamakin ganinsu su biyu babu Yusi ba domin sai na ce ganina da Yusi daya kafin a d'auki gawar marigayiyar na hange shi tare da Adam a rakube a bayan kujera yana rarrashisa yanzu ma su Hajja da Gwaggo sai tambayarsa suke yi ina jin Kamalu na basu amsa da cewa yana can tare da Adam. Maigidan bai tsaya ba suna gaisawa ya haye sama hankalina gabad'aya yana kansa don haka ban yi jinkirin bin bayansa ba. Na same shi zai shiga wanka da babban towel a jikinsa. Muka zubawa juna ido. Na isa dab da shi na tsaye a sanyaye na ce." Ya karin hakuri tun d'azu nake ta so na yi maka gaisuwa ban samu dama ba, Ubangiji Allah Ya gafarta mata, kai kuma Allah Ya baka hakurin jure rashinta, Allah Ya albarkaci abinda ta bari." Ya dinga amsa da "Amin Ya Allah cikin jin dadi. Ya nufi bandakin na bi bayan shi na taimaka masa wurin had'a ruwan wanka. Kallo yake ta bi na dashi babu yabo babu fallasa, amma kallon ya fara sa'bata sai na tsargu na fara tunanin ko shima ya fara yarda da abinda 'yan uwanta suke fad'a akanmu wato da bakincikinmu ta rasu. Da na tuna kallon nasa babu harara da k'yama a ciki sai na d'an samu sassauci, na fito na bar shi a bandakin domin ya yi wankan. Na zauna jigum cikin zullumi. Ya fito yana tsane jikinsa na tashi da sauri na bude wardrobe dinshi jallabiya na fito masa da ita da gajeran wando. Na mika masa ya kar'ba na koma na zauna yana kintsa jikinsa ya ce." Ki kawo mini abinci Amina." Da sauri na mike ina fadin." Dama abinda zan tambayeka kenan, tun yamma na ce da Baba Tabawa ta yi towo zai fi dadin tafiya." A takaice ya ce." Kin kyauta kuwa." Ya d'auki turare yana fesawa a jikinsa. Na sauka kasa cikin nazarin abinda ya yi a ganina wane turare zai fesa a cikin wannan yanayin da matarsa ta rasu ko kwana daya ba ta yi a kabarinta ba Na koma saman da tire a hannuna mai d'auke da kwanonin abincin da duk abinda nasan zai buk'ata. Yana zaune gefan gado yana waya da Sukairaju na ajiye tiren hannuna a saman daddumar da yake zama domin cin abinci... Ina binki bashi idan kin san kina karanta littafin nan ba ki biya ni hakkina ba. Sai da ya kammala wayar tsaf tukkuna ya zo ya zauna saman daddumar da abincin yake a shirye. Na zuba masa guda biyu madaidaita ina ko'karin zuba miya ya furta." Wanene zai cinye miki wannan towon Amina?" Na dube shi a tsanake kafin na ce." Kai ne za ka cinye?" Sai ya gyada kansa yana fad'in." A a d'aya ya ishe ni, kada ki zuba miya a kai a b'ata shi ki yi addu'a d'ayan ma na iya cinye shi." Ban ce komai ba na cire dayan na mayar cikin fulas na fara ko'karin zuba miyar ya ce ki zuba ta yau'kin kawai kada ki sanya mini jar miyar, ki sanya mini man shanu akai wadatacce." Na yi yadda ya umarta Ina fad'in." To naman fa." Ya ce." Ki tsamo sai ki sanya mini." Ban ce komai na dinga tsamo naman ina zuba masa a saman towon har ya so yayi yawa." A nutse ya ce." Naman nan ya isa haka Amina, kina so na ci abinci jikina ya mutu ko?" Na girgiza kai a hankali na ce." Kallo d'aya na yi maka d'azu na tabbatar da cewa akwai yunwa a tattare da kai wallahi." Ya furta." Ba ki yi karya ba rabona da abinci tun yammacin jiya kuma ban wani damu ba wallahi." A nutse na ce." To yanzu dai ka daure ka cinye wannan har naman duka." Hannunsa ya sanya tare da bismillahi kafin ya ce." To ke ma sanya hannunki mu ci tare zai fi albarka. Na sanya hannuna a hankali na gutsiro na kai daidai bakinsa. Kallona ya yi na 'yan sakkoni kafin ya bud'e bakin na sanya masa towon ya fara taunawa a tsanake D'akin ya d'auki shiru na wani lokaci kafin na ji maganarsa yana fad'in." Ina mai sunan abokina ya 'kara wayo ko.?" Na ce." Ya yi wayo sosai su Hajja ma suka dinga mamaki girman da jikinsa ya yi suna fad'in kamar yana sha nono saboda jikinsa ya ginu babu motsewa ko wata matsalar gaskiya yana samun kulawa sosai a wurin Baba Tabawa ba shi da matsalar maraicin nonon mamansa." Da d'an jin dadi ya ce." Na gode Allah na kuma gode muku Amina ina mutukar godiya Allah Ya saka muku da alheri 'Dan tausayi ya ba ni domin yanayin yadda ya yi maganar ya nuna mini cewa har yanzu yana jin zafin abinda Hauwa ta yi kuma abin ya dame shi abubuwa ne da yawa suka yi masa dabaibayi. Ta bakin Hajiya Saratun Hauwa ko a waje ya aurota bai kamata ta yi wannan sakarcin ba. yaro d'anyar haihuwa ta ajiye saboda wani banzan dalili. Na ce." Ni kam banga abin godiya ba duk abinda na yi maka ai kaina na yi wa." Ya yi shiru bai ce komai ba yana dai ta kar'bar towon da nake bashi a baki har guda ya kusa k'arewa ya ce." Ban ga kin ci ba." "Na ce." Sai ka koshi my love dina." Ya sa dariya wadda ban yi tsammani ba yana fad'in." Na ga sai wani ji ki ke da ni Amina." Da d'an murmushi na ce." Tausayi ka ba ni." Ya gyad'a kansa da wani irin murmushi kwantacce a a tare dashi ya cinye malmalar towo daya na kara cire wani daga leda na cigaba da bashi bai hana ni ba. Jefi jefi muna d'an ta'ba hira mafi rinjaye kan marigayiyar ne. Da kyar na daure na soko maganar da take ta damuna na ce." Akan maganar da yan'uwanta suke yi akan mu ni da Hauwa wata'kila sun gaya maka kai ma ko?" Ya ce." Wace magana ce kuma?" Cike da damuwa na furta." Wai duk wanda ya shiga gidan domin yi musu ta'aziyya sai sun gaya masa irin zaman da muke da ita har suna fad'in bakincikin da muka jima muna guma mata ne ya yi sanadiyar rasuwarta." Ya yi jim Yana kallona kafin ya ja siririn tsaki ya ce." Ke waye ya gaya miki haka?" Kai tsaye na Mamana ce?" Ya san dama ina kiran yayarsa da sunan. Sai ya girgiza kansa yana fad'in. " Mata dai ba a raba ku da k'ananun maganganu da fitina baiwar Allah ga sanadin mutuwarsa amma an jingina da wani lamari domin tayar da husuma ba ni so na ji bakinki a ciki wannan maganar duk abinda za su yi kada ki biye musu ku daga mini hankali don Allah domin na lura basu da kintsi dukkaninsu taron sakarkaru ne me yasa ga gaskiya 'kiri-'kiri a take gabad'aya da ni da su da ke mun san yadda ciwuka suka cinye Maryam har ajalinta ya sauka to me ya kawo wannan maganar kuma?" Na ce." Ni ma abinda na gani kenan, kasan kuma dole ne na damu tunda ni ce a gidan yanzu, a ganina idan wasu basu yarda ba wasu za su yarda tunda Allah ne kadai ya san irin abinda suke fad'a a kanmu." Ya ce." To kada wannan ya dame ki, tunda har maganar ta dawo kunnena zan yi wa tufkar hanci, na gaya miki dai kada ki kula su ku zubar mini da mutunci a gari." A tak'aice na ce." In sha Allahu rabbi." D'akin ya sake daukar shiru na wani lokaci kafin na sake yin kundubalar yin magana abin kamar wadda Hauwa ta sammace idan ma nace ba zan sake yin magana ba sai na kasa jurewa gabad'aya idan na tuna bata gidan sai na ji gabana ya buga kuma a raina sai nake ganin ai lefinta bai kai ace an rabu da ita gabad'aya ba tunda shima ai yanayi mata lefi me yasa shi da yayarsa suka fi bata rashin gaskiya. Na ce." Don Allah tunda haka ta faru ku yi hakuri Hauwa...... Ban kai ga kΓ rasa abinda yake bakina ba ya katse ni da babban sauti." Amina." Ya kira sunana na amsa da "Na'am tare da zuba masa ido gabana na d'an fad'uwa ganin yadda ya yi bala'in shan kunu......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book complete 2k ne a telegram what'sapp Gruop Kuma 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank.* *07084653262* *119* "Na sha gaya miki cewar abinda yake tsakani na da Hauwa ba huruminki ba ne. Ko kuma lokacin da zan aureta na yi shawara dake ne? me yasa ki ke so k'ara mini damuwa akan wadda nake ciki, za mu samu matsala dake akan hakan ki kiyaye ba ni son maganar Hauwa a gidan nan daga yau." Da k'yar na ce." To shikkenan dama gani nay.... Ya sake daga mini hannu yana fad'in ." Menene lefina Amina ko kema kina so ki nuna mini abinda ta yi ba komai ba ne? ina k'ara gaya miki ni fa Samira na ce ina so ba Hauwa ba, zan gaya miki wata magana wadda ba ki santa ba har yau na kasa mantawa da matata ta fari Allah Ya jikanta domin soyayyar gaskiya ce a tsakaninmu. Ban ta'ba kallon Hauwa a madadin da za ta share mini kukan rashin Samira ba, kuma ban ta'ba yi mata kwatankwancin son da nake yi wa Samira ba. Idan na rabu da ita babu wata tangard'a da zan samu tunda ni nasan bata da wani gurbi mai girma a zuciyata don haka maganar Hauwa ta kare a gidan nan na gaya miki Amina" Duk yadda na so ganin na daure zuciyata daga barin jin zafin yadda yake yabon matarsa ta fari data mutu kasawa na yi sai na manta ma da maganar da muke tattaunwaa akai zuciyata ta fara tsalle tana tu'kuki tsabar zafin kishin da ya taso mini na ce." Maganar Hauwa kuwa ba zata 'kare ba bari na gaya maka. Itace uwar yaranka uku, ai k'aryar so ta 'kare kuma ko kana sonta ko baka sonta ya zame maka tilas ka kalleta a matsayin wata jigo da ta samar maka da wani ginshiki da ka jima kana nema wannan maganar da kake furtawa kamar gugar zana kake yi mana ni da ita Hauwan kawai ka fito fili ka gaya mini cewa Amina har yanzu ban samu madadin Samira ba, ai ta riga ta mutu kuma duk wanda ya riga ya tafi baya dawowa sai kawai ka ro'ki Allah Ya takaita maka kwana ka je ka risketa a can ku gina sabuwar rayuwar da za ka wanzu cikin farinciki." Ya zuba mini idonsa yana kallona. Na juyar da kaina gefe tare da sake had'e fuskata. Shiru d'akin ya d'auka bai ba ni amsa ba. Na tsame hannuna daga cikin abincin da nake bashi na ya gi tissue paper domin goge hannuna. A hankali ya ce." Ban k'oshi ba." Zumbura baki na yi na yun'kura na tashi tsaye sai ya riko hannuna tare da janyo ni jikinshi ya mike k'afafunsa na zauna saman cinyarsa. D'auke kaina na yi domin ji na yi ma sam bana son kallonsa saboda takaici wannan a cin fuska ne a takaice, haka kawai daga bada shawara. Ya ce." Amina kalle ni." Kallonsa na yi babu fara'a. Ya rintse idonsa a tsanake ya ce." Kin san jini a jikin d'an adam ko?" Na yi shiru ban tanka ba. Ya d'an matse ni a jikinshi yana sakin ajiyar zuciya cikin kunnena ya furta." A jinin jikina kike yawo. Ina can wata uwa duniya kina yi mini gizo Amina ina alkawarin soyayyar da ki ka ce za mu yi idan na dawo gida?" Da mamaki mai yawa a tare da ni na kura masa Ido. Ya sake matse ni a jikinsa yana me sanya fuskarsa tsakankanin wuyana wurin da yake bala'in so kenan a jikina. Jikina ya shika k'warai da aniya daga sannan na sallamawa sha'anin rijalu na sake yin lakwas ina ayyanawa a raina ko ni ce na fadi na mutu mutumin nan damuwarsa k'alilan za ta kasance babu wani abu na jin dad'in rayuwarsa da zai fasa. Ni gabad'aya ma ban san akan wane alkawari yake magana ba domin tunda suka tafi ba mu samu sukunin yin wasu hirarrakin soyayya ba. Saukar hannunsa da na ji a kirjina ya sanya ni zabura. Na cire hannun da sauri sai ya had'e yatsunmu wuri d'aya yana bina da wani irin kallo wanda yake ko'karin kassara ni. Nan take tausayin kaina ya rufe ni. Yanzu nan ya gama jadadda irin alhini da kewar tsohuwar matarsa jiya kuma matar da ni da Hauwa muke ganin ya fifitata a kanmu ta fad'i ta mutu yau aka binneta a kabari wai har ya gama alhinin da jimamin yana bijiro da wani shagali da jin dad'in da bai wuce na dan wani lokaci ba. Cike da kasala ya sake mayar da hannunsa saman kirjina yana tatta'bawa ban yi nawar sake cire hannunsa ba muka kurawa juna ido da kyar na furta." Ba ka ji wani iri ba? Lumsassun idanuwansa ya bude a dabarbarce ya ce."Na ji sun 'kara girma ko dan na yi kewarsu ne." Raina ya baci da jin amsar da yake ba ni. Wato ma bai fahimci akan abinda nake magana ba sai kawai na yi yun'kurin sauka daga cinyarsa ya kuwa ri'ke ni da kyau irin rikon da baki isa ki k'wace ba. Sosai na bude idona a kansa na ce." Gaskiya ni ka ba ni mamaki wallahi mutuwa fa aka yi maka mai zafi har alhinin ya bar gangar jikinka kenan." Ya gyada kansa yana fad'in." To ai ta riga ta rasu Amina, ni na isa na dawo da ita ne? Mutuwar nan kowa zai mutu to me zai sanya a tauyi rayuwa a bawa gangar jiki da ruhi abinda yake muradi kada ki manta ke fa ki ka yi mini alkawari idan na dawo za mu sha soyayya." Na ce" Da yaushe na yi maka alkawari abinda ma duka bai fi sau biyu muka yi magana ba tunda kuka tafi." Yana d'an shanshanar jikina kamar wani tsohon zakin da ya jima yana farautar nama ya ce. To ina jin dai a irin mafarke-mafarken da nake yi dake ne ki ka gaya mini za ki yi mini soyayya fitacciya." Na juya da kaina takaici ya hana ni magana a haka ina jinsa yana ta turmutsa hannunsa cikin rigata. Gabad'aya kaina ya kulle na rasa da wane ma'auni zan auna wannan lamarin ya gama goge mini duka haddar da na yi a kansa, ai na d'auka na gama karantar halayensa gabad'aya ashe da sauran abinda ban gama sani ba. Ya d'ora bakinshi saman lebunana ya sumbata kafin ya cire a hankali da wani irin yanayi ya ce." Abin nan yana d'auke hankali Amina zai mantar da ni abubuwa da yawa, bayan kiran sunan Allah a cikin k'unci da damuwa sai wannan lamarin domin ni a wurina ma gaba yake da cin abinci, a wannan dare babu abinda zan fasa ai a haka duniyar ta ginu tun kafin mu zo cikinta ake mutuwa ake muka sunnah irin wadda za mu yi yanzu, mu ji dad'i mu gamsu kuma Ubangijin da ya ce mu yi hakan ya ba mu lada mai yawa." Na yi k'asa da kaina dalili ba ni da wani karsashin da zan kalubanci maganarsa ta kowace siga ya fi ni gaskiya amma ai ana barin halas da kunya wallahi har yanzu matar nan idan ta fa'do mini a raina sai gabana ya fadi. Ya cika ni na sauka kasa yana bude fulas din abinci jikinsa har d'an rawa yake yi ya ce." AbiΓ±ci zan baki kici ki koshi kamar yadda ni ma ki ka ciyar da ni daga nan kuma sai mu sake ciyar da juna wani abincin na mussaman ko ba haka ba ne?" Na ce." Gaskiya ba zan munafurceka ba a yanzu wallahi ba ni da wani karsashin da zan tari wannan lamari daka bijiro da shi. Ka yi hakuri tukkuna dukkunimu hankalinmu ya daidaita sai irin wannan nishadin ya biyo baya." Ya gyara yanayinsa yana fad'in." Ni ina da karsashina, sannan kuma a cikin nutsuwa da hankalina nake, menene a ciki ne haramun ne, saboda kawai an yi mutuwa sai a ajiye ibadar Allah ba na son jayayya Amina a buk'ace nake ke daga ganin yanayina ma kin san da hakan to me zai sanya ba za ki sama mini da farinciki ba. Kuka na fara yi tsakani da Allah ni ban san yadda zan yi na tari abinda yake so ba har na taimaka masa ya nisha'dantu irin yadda ya saba, har yanzu jikina babu wani kuzari ni gabad'aya ma duniyar ta fice mini daga raina. Don dole na dinga kar'bar towon da yake ba ni a bakina ina ci ina goge kwallar da take fitowa daga idona. Da kyar na ci rabin malmala na turje na daina kar'ba muka shiga toilet a tare wai zai yi mini wanka nan ma sai da muka yi kokawa kamar sababbin amare ina share hawayen takaici haka na yi wankan yana tattabe mini jiki muka fito. Towel ne kawai a jikina a daure na d'auki kayana zan sanya ya kwace. Yana fad'in." Sanya kayan ai bashi da amfani Amina, bari tukkuna mu kammala ko?" Ya ja hannuna zuwa gadonsa zugwi-zugwi haka na bi shi cikin sagewar gwiwa da nadamar rayuwa. Wai shin ma ya za a yi ya nisha'dantu. Tambayar da nake yi wa kaina kenan. Ya tura ni na yi kwanciyar ringingine dogare kafafuna na yi da zummar tashi ya raba nasa kafafun a kaina ya dabaibayeni. Abubuwa na tashin hankali da gigita lissafi ya fara yi mini jikinsa na wani irin rawa. Na dinga matse jikina ina ya'ki da gangar jikina da zuciyata akan kin 'karbar abinda yake mini, amma ban yi nasara ba, cikin k'ankanin lokaci ya fitar da ni daga hayyacina na kasa gane shin a duniya nake ko ni din ma na shilla barzahu ne ban sani ba. Ki'dima kam da ficewa daga hayyaci mun yi tunda abin ai ba sabo ba ne a wurinmu ya riga ya gama zame mana jiki sosai ya gurje ni ya gamsu na gamsu babu 'karya. Ashe shima wannan lamarin ba a had'a shi da komai idan gangar jikin ya kar'bi sakon duk turjiyar da zuciya take yi akan hani bata samun nasara. Na dinga jin kunyar kaina da kaina domin kuwa ni kaina da na shiga shu'uni mantawa na yi da cewa rasuwa aka kwatsama mana a gidan sai da tunani da hayyacina ya dawo tukkuna na ji siraran hawaye na gangaro mini ina rayawa a raina idan na riga shi mutuwa haka zai samu wata macen ya cigaba da more rayuwarsa tunda ai gashi ya fad'a. Mata biyu da ya fifita a rayuwarsu har baya iya boye so da k'aunar da yake musu sun mutu yana kewarsu amma bai fasa gudanar da wani lamari ba. Idan kin karanta ba ki biya ni hakkina ba ina bin ki bashi. Da asuba na sauka k'asa bayan fitarsa sallah. Wanka na yi sosai da ruwan d'umi na gasa jikina. Anti Yagana duk tana zaune saman dadduma tana kallona na fito daga bandakin na kintsa jikina sannan na gabatar da sallah. Na shafa a nutse na juyo ina kallonta lokacin ta zame ta kwanta saman dadduma amma ba bacci take yi ba carbin da yake ma'kale a hannunta take ja. A tsanake na gaisheta ba tare da tashi ba ta amsa mini tana kallona kafin ta sauke ajiyar zuciya ta furta." Gobe da wuri zan kama hanya Amina, jiya da daddare Babansu Fadila ya kira yake gaya mini mijinta ya zo ya ga masa bata da lafiya har da su k'arin ruwa." 'Yar dariya na yi kafin na ce." Anti Yagana ta kusa goya jika kenan." Harara ta mako mini tana tabe bakinta." Na ce." E, mana anti ai idan ki ka ji an fara da haka to k'aruwa ce." Ta girgiza kanta tana fad'in. " Yaran yanzu ba sa saurarawa 'ya'yan mutane daka an kai maka yarinya wata d'aya biyu zuwa uku ka had'ata da lalura wasu fa ko shekara ba sa yi suke haihuwa." Da murmushi a saman fuskarta na ce." Hakane anti Yagana ai gwara matasan su yi auran da wuri ya fi alheri akan su dinga zinace-zinace kuma bari na gaya miki wani abu ba fa samarin ne kadai suke da wannan 'kawazucin ba har da 'yan matan wallahi dukkaninsu son auran suke yi." Ta yi shiru tana ta'be bakinta. Na ce." Kawai ki yi mata addu'ar Allah ya raba su lafiya, domin tunda ki ka ji an fara da haka to an gamu." Ta ce." To Allah Ya raba su lafiya." Na amsa da "Amin ko ke fa." Muka dan yi shiru na dan wani lokaci kafin ta ce." Wallahi ina tausayawa jama'ar da suke k'arkashin matar nan, da yawa akwai wad'anda suke d'aukar dawainiya mai yawa ta iyali iyaye da yan'uwa duka a 'karkashinta yau gashi ta fad'i ta mutu dole za su shiga wani yanayi wanda ba zai yi musu dadi ba. Su kadai nake tausayawa sosai dalili yaranku da suke ri'ke a hannunta ai jajensu k'alilan ne tunda kuna raye sai ku cigaba da kula da yaranku Amma jama'ar da suke ci da sha a 'kasanta Allah ne kad'ai ya san su." "Hakane anti Yagana to ya za a yi ne? Lokacin ta ya yi cikinmu gabad'aya babu wanda ya isa ya dakatar da komawarta ga wanda ya halliceta hakika ya fi mu sonta shiyasa ya kira ta zuwa gare shi." Ta girgiza kanta tana fad'in." Ubangiji Allah Ya sa mu dace amma mutuwa kadai wa'azi idan har za mu hankalta." Haka muka kasance a d'akin muna tattauna batutuwa da yawa har garin ya yi haske sosai Gidan Hajiya Maryam marigayiya. Yabi ta dube shi yana tsaye a jikin bango ya rungume hannuwansa a k'irji. Bashir ne k'aninsu namiji da ya rage musu a maza tunda d'ayan ya rasu sai shi kad'an yanzu yana can yawon barkinsa ya ji rasuwar. Dukkaninsu sun fi shekara Takawas rabon da su gan shi, amma dai suna jin labarinsa cewa yana can Legos agege yana harkar sayar da tabar wiwi da sauran kayan gusar da tunani. Jiya cikin dare ya sauka yau da safe suka wayi gari da tashin hankali domin ya ritsa su a d'aki gabad'aya har da yaran marigayiyar wai sai an raba gado an ba shi rabonsa ya koma bakin sana'arsa. Kana jin irin zantukan da yake yi za ka gane mugun d'an kwaya ne ga wani shegen aski a kansa wandon dake jikinsa duk ya zazzago da iyayen sark'oki rakwacam a wuyansa da tafka-tafkan zobuna a tsayun hannunsa. Su kansu don dai jininsu ne amma bai yi kama da musulunci ba. Anti Yabi ita ce take bin Maryam shiyasa girman ya koma hannunta gabad'aya yanzu ta dube shi tana fad'in. Malam yaushe aka yi mutuwar da zaka zo ka daga mana hankali, yaushe rabonmu da kai shekara kusan takwas fa babu wanda kake nema kana can kana yawon iskancinka, ko an gaya maka kowa ma mahaukaci ne irin ka." Rukky wadda take sakuwarsa ta ce." Anti Yabi rabu dan kutumar......Ba ta kΓ rasa ba kuwa ya kai mata duka a bakinta yana fad'in." Ni ne dai Bashir ban canza ba zan iya kashe ki anan dan babanki." Anti Saliha ta ce." Ka kasheta Bashir." Da sauri ya furta." E, dan babanta ta k'ara sa mini baki ina magana sai na cire mata ma'kogwaro wallahi." Nabila ta ce." Kai ka shiga hankalinka fa wallahi idan har ka ce za ka daga mana hankali zan sanya a rufe mini kai, haba ina dalili kuma ke anti Yabi da kuke maganar gado uban wanene ya ce muna da gadonta tana fa da miji da yara maza biyu a ciki a iya sanina ba mu da abinda za mu samu a dukiyar anti Maryam." Rukky ta ce." Ai dama dole ki fad'i haka mana tunda ke kin san kina tare da ita duk wasu muhimmai abubuwanta suna hannunki kin fi kowa sanin sirrinta da dukiyarta dole ne ki fad'i haka." Yabi ta ce." Wannan zancen banza kike yi Nabila kada ma ki kuskura ki zo da wannan maganar domin kuwa kin fi kowa sanin sirrin Maryam ko mun gaje ta ko ba mu gaje ta ba ba zamu tashi daga zaman makokin nan a banza ba. Nusaiba ta fashe da kuka! da sauri duka suka juya suna kallonta don wata'kila sun manta da cewa yaran suna wurin. Ta tashi da sauri ta fita tana goge hawaye Salim da Adam suka bi bayanta cikin damuwa mai yawan gaske. Suna fitowa suka ganta a tsaye a tsakiyar falo tana kuka tuk'uru. Salim ya ja hannunta da sauri suka nufi d'akinsu domin da akwai sauran bak'in da suka kwana a gidan dangin Babansu kakarsu ma Hajiya Ayya tana nan da wasu daga cikin 'yan uwanta. Tana kuka ta ce." Allah Ya sa duka katikan Momi na banki suna hannuna. Mukullin dirowar nan ne ban san inda yake ba. Amma tun ranar da za su koma asibiti na kwashe katikan bakinta." Salim ya ce." Yanzu ya za mu yi anti Nusaiba mu gayawa Hajiya Ayya ko Baba Tajo." Adam da tunda suka fara maganar bai ce komai sai yanzu ya ce." A a ba yanzu ba tukkuna tunda ko sadakar uku da ba a yi ba, mu bari mutane su watse sai mu sanar da Baba. Anti Nusaiba duk rintsi kada ki gaya musu cewa." Katin bankunan da take ajiya suna hannunki." Ta gyad'a kanta tare sanya hannu tana goge hawayen da ta kasa tsayar dashi cikin damuwa ta furta." Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wayyo Allah Momi!" Adam ya je ya rungumeta sosai suka zauna gefan gado yana rarrashinta Salim din shima ya zauna gefenta jikinsa a mutukar sanyaye......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book 2k complete on telegram what'sapp Gruop Kuma 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank.* *07084653262* *120* Yusi Ya fito daga toilet ya same su a zaune shiru. Ganin Nusaiba a d'akin ya sanya shi d'an sakin fuska ya gaisheta cikin girmamawa ta amsa da yanayi na damuwar da take ciki ta tashi ta fita. Adam ya mike babu kuzari ya shiga toilet din domin yin wanka. Shi kuma Salim ya tashi ya fita daga d'akin. Daga lokacin ya fahimci cewa bayan damuwar da suke ciki ta rashin mahaifiyarsu akwai wadda ta k'aru duk da bai ji komai ba ya san abinda suke tattaunawa a kai ba mai dad'i ba ne. Yana nan zaune cikin zullumi da nazarin yadda rayuwar 'ya'ya take sauyawa idan suka rasa wani jigo Adam din ya fito a gurguje ya shirya suka fito falon tare wanda ya yi daidai da lokacin da Mairo ta fito tare kaf da yaran kowanne cikin tsafta. Suka nufi masaukin Hajiya Ayya mahaifiyar Alhaji Amadu kenan wadda take tare da jama'arta. Bayan sun gaisa anan wajenta yaran suka zauna twins da Minal tunda Mairo tana can suna hidimar d'orawa da saukewa kamar yadda al'ada ta zama a gidan mutuwa. Yusi ya ri'ke hannun Khalil suka fita tare domin duk zaman da ake yi na makoki da yaron suke zaune gabad'aya gaban babansu suna kar'bar gaisuwar tare. Shi ma bai jima da zama a wurin ba suka fito can suka hange shi yana kar'bar gaisuwa daga jama'ar da suka yi dafifi domin jiran fitowarsa. Muna zaune a falo gabad'aya har da su Hajja duk sun yi wanka sun fito ina ta kallon yadda inna Uwani take nan nan da Hajja har goya Sultan a bayanta tana ta jijjigashi duk da ba kuka yake yi ba. Sai ta ba ni tausayi sosai domin duk tana yin hakan ne domin dakushe lefin 'yarta amma ai ba haushe yace tun ran gini ran zane Hauwa ta bata goma daya bata gyaru ba, duk da gaskiyarta babu wanda zai gani saboda abinda tayi a yanzu ya dusashe lefin da take ji an yi mata. Suka shigo a tare su uku har da Khali da ya d'an fara tasawa abinda yake burgeni da yaron nutsuwa sam bashi da hayaniya ba za ka ta'ba cewa Tajo da Hauwa ne suka haife shi ba. Har suka 'karaso wurin da muke zaune ban d'auke idona daga kansu ba, wannan abota da soyayyar ta Yusi da Adamu sai Allah had'uwar jini babu dangantaka ko kad'an sai ta addinin islama. Duka muka gaisa a tsanake don d'aya bayan daya suka bi suka gaisa da kowa. Na kasa janye idona daga kan Yusi ganin yadda ya kara zama saurayi wannan jikin da ake yi masa tsiya a kai duk ya rairaye da akwai dai amma ba kamar lokacin da yake tashar kuruciya ba. Ganin kallon da nake yi masa ya yi yawa ya sanya ya sunkuyar da kansa yana d'an kalato murmushi ya sake fad'in ." Mama ya karin hakuri." A tak'aice na ce." Ai ku zan yi wa ta'aziyya ko Adamu." Ya d'an saki fuska kad'an amma bai ce komai ba sai tausayinsa ya sake kama ni. Na ce." Allah Ya yi mata rahama Annabi ya san da zuwanta. " Gabad'aya muka amsa da Amin har ni da na yi. Addu'ar. Sun d'an jima a tare damu kafin su fita Adam yana tambayar Kamalu na ce ai shi tun sassafe ya fita don ya riga ma maigidan zama a wajen. Gabansa suka je suka zauna gabad'aya har Salim ya dube shi yana fad'in." Ku kunna wayarta ku sanar da rasuwar duk da nasan da yawa wasu daga cikin abokan nan kasuwancinta sun san ta rasu tunda an yi jana'iza da wasu amma dai a tambayi idan da wanda yake bin ta bashi ya fad'a a sauke mata nauyi daga nan zuwa ranar da za a yi addu'ar bakwai. Sannan ka nemi yaranta ina nufin wad'anda suke yi mata hidima ta kasuwanci idan da wanda yake da hakki a kanta ya fad'i a biya shi. Sanin da na yi ita mai bayarwa ce amma hakan ba zai hana a bibiyi abubuwan da ta wanzar a lokacin da take rayuwa ba, wannan shine gatan da ni daku zamu yi mata bayan addu'a." Ya amsa cikin ladabi tare da tashi da sauri can rumfar da ya hangi yaranta sun zauna jiya ya nufa wasu sun zo daga ciki wasu kuma ba su zo ba kawai sai ya nufi cikin gidan domin kar'bo wayarta dake hannun Nusaiba tunda Allah Ya taimaka har da manyan wayoyinta masu tsada ta kwashe a lokacin da ta had'a da katin cire kudinta. Yana nan zaune jama'a na 'barkowa ta ko'ina abokanansa wasu daga cikin abokanan tsohon mijinta da 'yan uwansa dama wasu sam da bai san daga ina suke ba sukan tsuguna gabansa da tafka tafka rawaninsu a kan su suna yi masa gaisuwa. Wani daga cikin masu rawanin ya sake komawa wajansa ya gurfana Yana fad'in." Allah Ya taimake yanzu yaron mai rasuwar na ji yana magana a wajan da muke zaune cewa idan da wanda yake bin marigiyar bashi ya fad'a, to ina daya daga cikin wad'anda ta sanya a aiki." Ya dube shi a tsanake kafin ya furta.'' Wane aiki ka yi mata, kuma nawa ne hakkin naka?" Ya gyad'a kansa tare da dan juyawa yana waiwaye akwai jama'a sosai don dai hayaniya tayi yawa amma duk da hakan ko da suke maganar bai fasa kar'bar gaisuwa ba tunda har yanzu shigowa ake yi. Cikin nazari ya ce." Ko akwai buk'atar sirri ne?" Da sauri ya d'aga kansa yana fad'in."E, kwarai kuwa Yallabai." Sai ya ce." To babu damuwa fita waje ka tsaya jikin gate zan fito yanzu na same ka." Ya kuwa tashi da sauri yana sa'be babbar riga ya kama hanyar fita. Ya bi shi da kallon nazari kamar akwai rashin gaskiya a tare da shi. Yaran duk suna gefensa a zaune ya tashi ya bi bayansa. Ya zuba hannuwansa duka biyun cikin aljihun tazarcen dake jikinsa tare da fad'in." To ina jin ka Allah Ya gafarta Malam." Ya risinar da kansa yana fad'in." Hakika Maryam ta sanya ni aiki babba a wannan tsukin da Ubangiji Allah Ya d'auki rayuwata. Mun gama magana da ita akan kudin kayan aiki da duk abinda za a buk'ata wurin biyan buk'ata dubu dari bakwai da ashirin to sai ta kwanta ciwon nan da bata tashi ba daga shi kuma ba ta turo mini kudin ba ni kuma na juya dana hannuna na fara aiki domin nasan bata da wasa akan samun biyan bukatarta wallahi yanzu haka daf nake da kammala aikin kwatsam sai rasuwarta na ji kuma dama a satikan da suka wuce ba ni samun wayarta hankali ya tashi wallahi domin na riga na juya mata kuma kaf abinda yake hannuna kenan." A tsanake ya ce." Wane aiki ne? kuma nawa ne kudinka." Ya yi dan Jim kafin ya ce ." Duka dubu dari bakwai ne da ashirin kamar yadda na gaya maka da farko abinda ya ja kud'i shine rago mai tozali da muka nema akan aikin. Sai fatar karsana sannan mun nemo zuciyar jemage, akwai kuma kaji da muka saya jan zakara, wake-wake ba'kar kaza da kuma turarukan da muka saya wurin yin aikin." Shiru ya ratsa wajan bayan gama maganarsa. Ya ce." To, na ji wane aiki aka yi akan hakan." Ya yi shiru tare da yin kasa da kansa sai da ya kara maimaita tambayarsa tukkuna ya ce." Alhaji a zahirin gaskiya ni ina daya daga cikin manyan Malam Hajiya Maryam kuma duk lokacin da ta buk'aci wani aiki muna ko'karin ganin mun gudanar dashi duk rintsi domin samun biyan buk'ata. Wannan sirri ne tsakani na da ita amma yanzu ta ta 'kare sai dai mu ro'ka mata gafara wurin Ubangiji. Dole ta sanya ni neman ha'kkina domin dai aiki gaf nake da kammala shi rasuwarta ta katse na taho. Kuma kudin hannuna sun yanke Hajiya Maryam aiki ta sanya ni na yi akan wata baiwar Allah mai suna Hauwa. Yadda take gaya mini cewa tunda take a duniya ba a ta'ba yi mata tozarcin da matar ta yi mata ba shine dalilin da ya sanya take so a d'ora mata jinyya mai tsanani ko kuma a shafe ji da ganinta ta yi mutuwar tsaye babu ji babu gani cikin biyu tace ayi daya. Duk abinda na lissafo maka da farko na saya na kuma fara aikin sai dai ban kammala ba, Allah ya yi mata rasuwa. K'warai da gaske ya tsorata tun lokacin da mutumin ya fara magana. Mazantaka kawai ya nuna tare da gogewa ta fannin mu'amula bai nuna masa razani ba. Ya ce." Yanzu ya ake ciki idan ka koma za ka kammala aikin ko kuwa?" Sai ya gyad'a kansa yana fad'in." Zan dakata gaskiya tunda Allah ya yi ikonsa akan wadda ta sanya ni sai dai da iska (jinnu) muke yi su kuma ba alkawari ne da su ba, idan na gaya musu mu tsaya da yin aikin bai zama lallai su tsaya kai tsaye sai sun gindaya abinda suke buk'ata amma ba zai wuce yanka ba." Ya girgiza kansa cikin d'an karan mamaki da al'ajabi cikin zuciyarsa tana nanata istigifari. Ya dube shi kafin ya ce." Ka kyauta da ka d'auki aniyyar dakatawa zan kuma biya ka hakkinka. Amma ba yau ba ina so ka dawo bayan sadakar bakwai kud'i hannu da hannu." Ya risinar da kansa yana ta godiya. Shi kuma ya yi ta nazarinsa cike da madaukakin mamaki gashi cikakken mutum cikin manyan kaya da kamala har da rawani ashe mushiriki ne ta'babbe ne, wato iskokan da suke yi musu aiki sune masu biyan buk'ata ba Allah ba. Ya sanya hannu cikin aljihu dubu ashirin ya bashi kafin ya ce ." Ka yi kudin motar komawa gida amma kamar yadda na gaya maka bayan an yi addu'ar bakwai ka zo ka kar'bi kudinka." Ya kar'ba da sauri yasa a aljihu yana ta godiya ya mika masa hannu wai su yi sallama bai kar'ba ba kawai sai ya daga masa hannu yana fad'in "A sauka lafiya." Daga haka ya koma cikin gidan cike da tunani da nazari.. Ya samu Bashir tare da su Salim da Yusi a zaune. Kallo guda ya yi wa yaron ya hangi kama sosai da Maryam domin duk irin fuskarsu daya sai dai shi fuskarsa ta yi duhu sosai da lebensa tabbacin wiwi ta ratsa shi. Ya dinga sunkuyar da kansa kasa kamar munafiki ya fara gaishe shi cikin ladabi irin wanda suka saba. Ya amsa yana dubansa tare da fad'in." Ko kaine Bashir din ne?'' Da sauri ya ce." Ni ne, eh ni ne?'' Ya fad'a yana wata dariya da sosa kansa. Shigowar Alhaji Sulaiman gidan da iyalinsa ya d'auke masa hankali, da kansa ya tafi domin tar'barsa tun kafin ya karaso rumfar da suke zaune. Tare muka yini da Hajiya azizi da abokiyar zamanta mai suna Hajiya Salamatu da Halisa 'kanwarta da ta ba ni labarinta kwanakin baya. Muka yini dasu a gidan sai wajan uku na rana bayan sun ci abinci sun yi salla muka yi sallama da su kan cewa za su shiga can gidan Maryam din domin yi wa danginta ta'aziyya na yi ta mamaki ashe ba su shiga ba sai yanzu da suka tashi tafiya. Alhaji Sulaiman ya shigo har gida ya yi mana gaisuwa ni da Hajja ya d'an jima a tare da Hajja suna hira kafin ya yi mana sallama ya fita. Daf da magriba mun d'an samu sau'ki shige da fice na mutane domin duk wanda ya je can gidanta ya yi gaisuwa sai ya shigo mini mussaman mak'otanmu dama wad'anda muke cikin estate din a tare. Na shiga d'aki sallah na samu Anti Yagana har ta idar ta kashingida tana fad'in." Gobe ana yin addu'a da safe zan d'auki hanya da wuri Amina." Na ce" Ba za ki ta ya ni zama ba anti Yagana kina ji su Hajja ma fa gobe suke cewa za su tafi." Ta furta." Na so hakan Amina Amma hankalina ya yi gida saboda Fadila ban san a wane yanayi take ciki ba tunda an ce har da karin ruwa." Na ce." Hakane kuma to shikkenan Allah ya kaimu zan gayawa maigidan idan ya shigo in sha Allahu." Ba tace komai ba. Na shige band'akin domin d'aura alwalar sallar magriba. Har bayan isha'i muna tare da anti Yagana a d'aki muna tattauna mas'aloli masu yawa. Hajja ta shigo d'akin da kanta tana fad'in." Yagana tun safe da ki ka fito mu ka gaisa ki ka auri zaman d'aki ko ba kya jin dadi ne." Ta mike zaune tana yar dariya kafin tace." Wallahi lafiyata lau Hajja kawai gajiyar tafiya ce bata sake ni ba." Itama da murmushi da kulawa ta ce." To ku fito mu ci abinci, ke Amina kema tun d'azu nake hankalce dake kowa ya ci abincin rana babu ke, maza ku fito mu had'u mu ci abinci yanzu nan Tabawa ta kammala har ta fito mana dashi." Na ce." To shikkenan Hajja.'' Anti Yagana ta yi murmushi bayan fitarta daga d'akin tana fad'in."Baiwar Allah nan tana sona Amina, ko da yake k'aunar da take yi miki ne ta shafe ni." Na ce." K'warai kuwa na sheda soyayyata da Hajja ta daban ce, amma shekarun baya anti Yagana an so a juyar mata da hankali wallahi na d'an fuskanci gizago daga wurinta da na ri'ke addu'a kuma sai abin ya shud'e kamar ba a yi ba." Ta ce." Muddin baka nufi kowa da sharri ba Amina to ko shi ya nufe ka dashi ba zai yi tasiri ba, addu'ar nan dai da ki ka rike ki ajiye a ranki cewa itace makaminki." Na ce." In sha Allahu anti Yagana." Tare muka fito falon duk suna zaune wannan karon Sultan yana hannun gwaggo tana d'an jijjigashi. Kafin na zauna na ce." Gwaggo yau kece ki ke auran kenan." Tana dariya take fad'in.'' E, ai yau yace da ni yake auran." Ina Uwani ta yi murmushi tana cewa." An jima kadan zai ce da tsohuwar zuma ake magani ni ce uwargidansa. Hajja da tunda suke maganar ba ta sanya musu baki ba sai yanzu ta ce." Duk ku gama yin jigila dashi yace ni yake so ko Tabawa." Aka yi dariya gabad'aya cikin raha da barkwanci. Cikin wannan yanayin ya shigo tare da Kamalu dama a tare nake ganinsu duk lokacin da suka tashi daga kar'bar ta'aziyyar. Ya tsaya suka gaisa da su Hajja kafin ya haye sama. Shi kuma Kamalu ya zauna a cikinmu Hajja ta ce Baba Tabawa ta zuba masa abinci. Saman na bi shi ina shiga d'akin na same shi ringine a gado. Na k'Γ rasa na zauna gefan kafafunsa. Ya tashi zaune yana sauke ajiyar zuciya." Na gaji tubis Amina ga'bobina ciwo suke yi mini wallahi na jima ban yi gajiya irin ta wannan lokacin ba." Na sauke ajiyar zuciya Ina fad'in." Ya za a yi abu ne da aka asassa shi amma da yawa wasu ba sa yin wannan zaman." Ya ce." K'warai kuwa gobe idan an yi addu'ar uku zan sanya a cire rumfunan da aka kafa kowa ya tafi kuma haka ya isa ranar bakwai zan sanya masallatai a yi mata addu'a." Shiru na yi ban ce komai ba. Gabad'aya tunanina na kan yaranmu. Amma har yanzu ban ji yace komai ba akansu. Ba ni son na yi magana ta zama fitina zan d'an jira shi daga nan zuwa ranar da za ta cika kwanaki bakwai duk wacce za mu yi sai mu yi. Ya yun'kura zai tashi sai ya koma ya zauna. Na ri'ko hannunsa cikin mamaki ina kallonsa lallai da gaske ya gaji. Hannunsa da na ri'ke na ji d'umi ba kamar koyaushe ba. Sai kawai na ta'ba wuyansa zafi rad'au zazza'bi ne. Na ce." Zazza'bi kake yi fa Baba?" Ya ce." Zazza'bi ne ko?'' Wai tambaya yake yi. Na ce." K'warai kuwa zazza'bi ne ya kawo maka sagewar gabobi da ciwon jiki, ya kamata ka samu hutu fa." Ya sake yun'kurawa a karo na biyu yana fad'in." Bari na yi wanka zan kira likitana yanzu ya duba ni tun wajan sha biyu na rana na ji yanayin jikina ya canza ina dan jin ciwon kai ma." Na kama hannunsa muka nufi bandakin tare na hada masa ruwan wankan ina fad'in.'" Wankan ma da ka bar shi tunda ka yi da safe. " Ya ce." Ai ba zan iya bacci ba idan ban yi shi ba Amina, kada ki damu bari na yi na fito ki kawo mini abinci." Na ce." To a sanyaye na fito na bar shi a toilet din na sau'ka kasa cikin 'yar damuwa ya jima kuwa bai kwanta ciwo ba tun bayan zazzafar murar da ya yi a gidana sakamakon ruwan saman da ya dake shi a shekarun baya.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book 2k complete on telegram what'sapp Gruop Kuma 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank.* *07084653262* *120* Yusi Ya fito daga toilet ya same su a zaune shiru. Ganin Nusaiba a d'akin ya sanya shi d'an sakin fuska ya gaisheta cikin girmamawa ta amsa da yanayi na damuwar da take ciki ta tashi ta fita. Adam ya mike babu kuzari ya shiga toilet din domin yin wanka. Shi kuma Salim ya tashi ya fita daga d'akin. Daga lokacin ya fahimci cewa bayan damuwar da suke ciki ta rashin mahaifiyarsu akwai wadda ta k'aru duk da bai ji komai ba ya san abinda suke tattaunawa a kai ba mai dad'i ba ne. Yana nan zaune cikin zullumi da nazarin yadda rayuwar 'ya'ya take sauyawa idan suka rasa wani jigo Adam din ya fito a gurguje ya shirya suka fito falon tare wanda ya yi daidai da lokacin da Mairo ta fito tare kaf da yaran kowanne cikin tsafta. Suka nufi masaukin Hajiya Ayya mahaifiyar Alhaji Amadu kenan wadda take tare da jama'arta. Bayan sun gaisa anan wajenta yaran suka zauna twins da Minal tunda Mairo tana can suna hidimar d'orawa da saukewa kamar yadda al'ada ta zama a gidan mutuwa. Yusi ya ri'ke hannun Khalil suka fita tare domin duk zaman da ake yi na makoki da yaron suke zaune gabad'aya gaban babansu suna kar'bar gaisuwar tare. Shi ma bai jima da zama a wurin ba suka fito can suka hange shi yana kar'bar gaisuwa daga jama'ar da suka yi dafifi domin jiran fitowarsa. Muna zaune a falo gabad'aya har da su Hajja duk sun yi wanka sun fito ina ta kallon yadda inna Uwani take nan nan da Hajja har goya Sultan a bayanta tana ta jijjigashi duk da ba kuka yake yi ba. Sai ta ba ni tausayi sosai domin duk tana yin hakan ne domin dakushe lefin 'yarta amma ai ba haushe yace tun ran gini ran zane Hauwa ta bata goma daya bata gyaru ba, duk da gaskiyarta babu wanda zai gani saboda abinda tayi a yanzu ya dusashe lefin da take ji an yi mata. Suka shigo a tare su uku har da Khali da ya d'an fara tasawa abinda yake burgeni da yaron nutsuwa sam bashi da hayaniya ba za ka ta'ba cewa Tajo da Hauwa ne suka haife shi ba. Har suka 'karaso wurin da muke zaune ban d'auke idona daga kansu ba, wannan abota da soyayyar ta Yusi da Adamu sai Allah had'uwar jini babu dangantaka ko kad'an sai ta addinin islama. Duka muka gaisa a tsanake don d'aya bayan daya suka bi suka gaisa da kowa. Na kasa janye idona daga kan Yusi ganin yadda ya kara zama saurayi wannan jikin da ake yi masa tsiya a kai duk ya rairaye da akwai dai amma ba kamar lokacin da yake tashar kuruciya ba. Ganin kallon da nake yi masa ya yi yawa ya sanya ya sunkuyar da kansa yana d'an kalato murmushi ya sake fad'in ." Mama ya karin hakuri." A tak'aice na ce." Ai ku zan yi wa ta'aziyya ko Adamu." Ya d'an saki fuska kad'an amma bai ce komai ba sai tausayinsa ya sake kama ni. Na ce." Allah Ya yi mata rahama Annabi ya san da zuwanta. " Gabad'aya muka amsa da Amin har ni da na yi. Addu'ar. Sun d'an jima a tare damu kafin su fita Adam yana tambayar Kamalu na ce ai shi tun sassafe ya fita don ya riga ma maigidan zama a wajen. Gabansa suka je suka zauna gabad'aya har Salim ya dube shi yana fad'in." Ku kunna wayarta ku sanar da rasuwar duk da nasan da yawa wasu daga cikin abokan nan kasuwancinta sun san ta rasu tunda an yi jana'iza da wasu amma dai a tambayi idan da wanda yake bin ta bashi ya fad'a a sauke mata nauyi daga nan zuwa ranar da za a yi addu'ar bakwai. Sannan ka nemi yaranta ina nufin wad'anda suke yi mata hidima ta kasuwanci idan da wanda yake da hakki a kanta ya fad'i a biya shi. Sanin da na yi ita mai bayarwa ce amma hakan ba zai hana a bibiyi abubuwan da ta wanzar a lokacin da take rayuwa ba, wannan shine gatan da ni daku zamu yi mata bayan addu'a." Ya amsa cikin ladabi tare da tashi da sauri can rumfar da ya hangi yaranta sun zauna jiya ya nufa wasu sun zo daga ciki wasu kuma ba su zo ba kawai sai ya nufi cikin gidan domin kar'bo wayarta dake hannun Nusaiba tunda Allah Ya taimaka har da manyan wayoyinta masu tsada ta kwashe a lokacin da ta had'a da katin cire kudinta. Yana nan zaune jama'a na 'barkowa ta ko'ina abokanansa wasu daga cikin abokanan tsohon mijinta da 'yan uwansa dama wasu sam da bai san daga ina suke ba sukan tsuguna gabansa da tafka tafka rawaninsu a kan su suna yi masa gaisuwa. Wani daga cikin masu rawanin ya sake komawa wajansa ya gurfana Yana fad'in." Allah Ya taimake yanzu yaron mai rasuwar na ji yana magana a wajan da muke zaune cewa idan da wanda yake bin marigiyar bashi ya fad'a, to ina daya daga cikin wad'anda ta sanya a aiki." Ya dube shi a tsanake kafin ya furta.'' Wane aiki ka yi mata, kuma nawa ne hakkin naka?" Ya gyad'a kansa tare da dan juyawa yana waiwaye akwai jama'a sosai don dai hayaniya tayi yawa amma duk da hakan ko da suke maganar bai fasa kar'bar gaisuwa ba tunda har yanzu shigowa ake yi. Cikin nazari ya ce." Ko akwai buk'atar sirri ne?" Da sauri ya d'aga kansa yana fad'in."E, kwarai kuwa Yallabai." Sai ya ce." To babu damuwa fita waje ka tsaya jikin gate zan fito yanzu na same ka." Ya kuwa tashi da sauri yana sa'be babbar riga ya kama hanyar fita. Ya bi shi da kallon nazari kamar akwai rashin gaskiya a tare da shi. Yaran duk suna gefensa a zaune ya tashi ya bi bayansa. Ya zuba hannuwansa duka biyun cikin aljihun tazarcen dake jikinsa tare da fad'in." To ina jin ka Allah Ya gafarta Malam." Ya risinar da kansa yana fad'in." Hakika Maryam ta sanya ni aiki babba a wannan tsukin da Ubangiji Allah Ya d'auki rayuwata. Mun gama magana da ita akan kudin kayan aiki da duk abinda za a buk'ata wurin biyan buk'ata dubu dari bakwai da ashirin to sai ta kwanta ciwon nan da bata tashi ba daga shi kuma ba ta turo mini kudin ba ni kuma na juya dana hannuna na fara aiki domin nasan bata da wasa akan samun biyan bukatarta wallahi yanzu haka daf nake da kammala aikin kwatsam sai rasuwarta na ji kuma dama a satikan da suka wuce ba ni samun wayarta hankali ya tashi wallahi domin na riga na juya mata kuma kaf abinda yake hannuna kenan." A tsanake ya ce." Wane aiki ne? kuma nawa ne kudinka." Ya yi dan Jim kafin ya ce ." Duka dubu dari bakwai ne da ashirin kamar yadda na gaya maka da farko abinda ya ja kud'i shine rago mai tozali da muka nema akan aikin. Sai fatar karsana sannan mun nemo zuciyar jemage, akwai kuma kaji da muka saya jan zakara, wake-wake ba'kar kaza da kuma turarukan da muka saya wurin yin aikin." Shiru ya ratsa wajan bayan gama maganarsa. Ya ce." To, na ji wane aiki aka yi akan hakan." Ya yi shiru tare da yin kasa da kansa sai da ya kara maimaita tambayarsa tukkuna ya ce." Alhaji a zahirin gaskiya ni ina daya daga cikin manyan Malam Hajiya Maryam kuma duk lokacin da ta buk'aci wani aiki muna ko'karin ganin mun gudanar dashi duk rintsi domin samun biyan buk'ata. Wannan sirri ne tsakani na da ita amma yanzu ta ta 'kare sai dai mu ro'ka mata gafara wurin Ubangiji. Dole ta sanya ni neman ha'kkina domin dai aiki gaf nake da kammala shi rasuwarta ta katse na taho. Kuma kudin hannuna sun yanke Hajiya Maryam aiki ta sanya ni na yi akan wata baiwar Allah mai suna Hauwa. Yadda take gaya mini cewa tunda take a duniya ba a ta'ba yi mata tozarcin da matar ta yi mata ba shine dalilin da ya sanya take so a d'ora mata jinyya mai tsanani ko kuma a shafe ji da ganinta ta yi mutuwar tsaye babu ji babu gani cikin biyu tace ayi daya. Duk abinda na lissafo maka da farko na saya na kuma fara aikin sai dai ban kammala ba, Allah ya yi mata rasuwa. K'warai da gaske ya tsorata tun lokacin da mutumin ya fara magana. Mazantaka kawai ya nuna tare da gogewa ta fannin mu'amula bai nuna masa razani ba. Ya ce." Yanzu ya ake ciki idan ka koma za ka kammala aikin ko kuwa?" Sai ya gyad'a kansa yana fad'in." Zan dakata gaskiya tunda Allah ya yi ikonsa akan wadda ta sanya ni sai dai da iska (jinnu) muke yi su kuma ba alkawari ne da su ba, idan na gaya musu mu tsaya da yin aikin bai zama lallai su tsaya kai tsaye sai sun gindaya abinda suke buk'ata amma ba zai wuce yanka ba." Ya girgiza kansa cikin d'an karan mamaki da al'ajabi cikin zuciyarsa tana nanata istigifari. Ya dube shi kafin ya ce." Ka kyauta da ka d'auki aniyyar dakatawa zan kuma biya ka hakkinka. Amma ba yau ba ina so ka dawo bayan sadakar bakwai kud'i hannu da hannu." Ya risinar da kansa yana ta godiya. Shi kuma ya yi ta nazarinsa cike da madaukakin mamaki gashi cikakken mutum cikin manyan kaya da kamala har da rawani ashe mushiriki ne ta'babbe ne, wato iskokan da suke yi musu aiki sune masu biyan buk'ata ba Allah ba. Ya sanya hannu cikin aljihu dubu ashirin ya bashi kafin ya ce ." Ka yi kudin motar komawa gida amma kamar yadda na gaya maka bayan an yi addu'ar bakwai ka zo ka kar'bi kudinka." Ya kar'ba da sauri yasa a aljihu yana ta godiya ya mika masa hannu wai su yi sallama bai kar'ba ba kawai sai ya daga masa hannu yana fad'in "A sauka lafiya." Daga haka ya koma cikin gidan cike da tunani da nazari.. Ya samu Bashir tare da su Salim da Yusi a zaune. Kallo guda ya yi wa yaron ya hangi kama sosai da Maryam domin duk irin fuskarsu daya sai dai shi fuskarsa ta yi duhu sosai da lebensa tabbacin wiwi ta ratsa shi. Ya dinga sunkuyar da kansa kasa kamar munafiki ya fara gaishe shi cikin ladabi irin wanda suka saba. Ya amsa yana dubansa tare da fad'in." Ko kaine Bashir din ne?'' Da sauri ya ce." Ni ne, eh ni ne?'' Ya fad'a yana wata dariya da sosa kansa. Shigowar Alhaji Sulaiman gidan da iyalinsa ya d'auke masa hankali, da kansa ya tafi domin tar'barsa tun kafin ya karaso rumfar da suke zaune. Tare muka yini da Hajiya azizi da abokiyar zamanta mai suna Hajiya Salamatu da Halisa 'kanwarta da ta ba ni labarinta kwanakin baya. Muka yini dasu a gidan sai wajan uku na rana bayan sun ci abinci sun yi salla muka yi sallama da su kan cewa za su shiga can gidan Maryam din domin yi wa danginta ta'aziyya na yi ta mamaki ashe ba su shiga ba sai yanzu da suka tashi tafiya. Alhaji Sulaiman ya shigo har gida ya yi mana gaisuwa ni da Hajja ya d'an jima a tare da Hajja suna hira kafin ya yi mana sallama ya fita. Daf da magriba mun d'an samu sau'ki shige da fice na mutane domin duk wanda ya je can gidanta ya yi gaisuwa sai ya shigo mini mussaman mak'otanmu dama wad'anda muke cikin estate din a tare. Na shiga d'aki sallah na samu Anti Yagana har ta idar ta kashingida tana fad'in." Gobe ana yin addu'a da safe zan d'auki hanya da wuri Amina." Na ce" Ba za ki ta ya ni zama ba anti Yagana kina ji su Hajja ma fa gobe suke cewa za su tafi." Ta furta." Na so hakan Amina Amma hankalina ya yi gida saboda Fadila ban san a wane yanayi take ciki ba tunda an ce har da karin ruwa." Na ce." Hakane kuma to shikkenan Allah ya kaimu zan gayawa maigidan idan ya shigo in sha Allahu." Ba tace komai ba. Na shige band'akin domin d'aura alwalar sallar magriba. Har bayan isha'i muna tare da anti Yagana a d'aki muna tattauna mas'aloli masu yawa. Hajja ta shigo d'akin da kanta tana fad'in." Yagana tun safe da ki ka fito mu ka gaisa ki ka auri zaman d'aki ko ba kya jin dadi ne." Ta mike zaune tana yar dariya kafin tace." Wallahi lafiyata lau Hajja kawai gajiyar tafiya ce bata sake ni ba." Itama da murmushi da kulawa ta ce." To ku fito mu ci abinci, ke Amina kema tun d'azu nake hankalce dake kowa ya ci abincin rana babu ke, maza ku fito mu had'u mu ci abinci yanzu nan Tabawa ta kammala har ta fito mana dashi." Na ce." To shikkenan Hajja.'' Anti Yagana ta yi murmushi bayan fitarta daga d'akin tana fad'in."Baiwar Allah nan tana sona Amina, ko da yake k'aunar da take yi miki ne ta shafe ni." Na ce." K'warai kuwa na sheda soyayyata da Hajja ta daban ce, amma shekarun baya anti Yagana an so a juyar mata da hankali wallahi na d'an fuskanci gizago daga wurinta da na ri'ke addu'a kuma sai abin ya shud'e kamar ba a yi ba." Ta ce." Muddin baka nufi kowa da sharri ba Amina to ko shi ya nufe ka dashi ba zai yi tasiri ba, addu'ar nan dai da ki ka rike ki ajiye a ranki cewa itace makaminki." Na ce." In sha Allahu anti Yagana." Tare muka fito falon duk suna zaune wannan karon Sultan yana hannun gwaggo tana d'an jijjigashi. Kafin na zauna na ce." Gwaggo yau kece ki ke auran kenan." Tana dariya take fad'in.'' E, ai yau yace da ni yake auran." Ina Uwani ta yi murmushi tana cewa." An jima kadan zai ce da tsohuwar zuma ake magani ni ce uwargidansa. Hajja da tunda suke maganar ba ta sanya musu baki ba sai yanzu ta ce." Duk ku gama yin jigila dashi yace ni yake so ko Tabawa." Aka yi dariya gabad'aya cikin raha da barkwanci. Cikin wannan yanayin ya shigo tare da Kamalu dama a tare nake ganinsu duk lokacin da suka tashi daga kar'bar ta'aziyyar. Ya tsaya suka gaisa da su Hajja kafin ya haye sama. Shi kuma Kamalu ya zauna a cikinmu Hajja ta ce Baba Tabawa ta zuba masa abinci. Saman na bi shi ina shiga d'akin na same shi ringine a gado. Na k'Γ rasa na zauna gefan kafafunsa. Ya tashi zaune yana sauke ajiyar zuciya." Na gaji tubis Amina ga'bobina ciwo suke yi mini wallahi na jima ban yi gajiya irin ta wannan lokacin ba." Na sauke ajiyar zuciya Ina fad'in." Ya za a yi abu ne da aka asassa shi amma da yawa wasu ba sa yin wannan zaman." Ya ce." K'warai kuwa gobe idan an yi addu'ar uku zan sanya a cire rumfunan da aka kafa kowa ya tafi kuma haka ya isa ranar bakwai zan sanya masallatai a yi mata addu'a." Shiru na yi ban ce komai ba. Gabad'aya tunanina na kan yaranmu. Amma har yanzu ban ji yace komai ba akansu. Ba ni son na yi magana ta zama fitina zan d'an jira shi daga nan zuwa ranar da za ta cika kwanaki bakwai duk wacce za mu yi sai mu yi. Ya yun'kura zai tashi sai ya koma ya zauna. Na ri'ko hannunsa cikin mamaki ina kallonsa lallai da gaske ya gaji. Hannunsa da na ri'ke na ji d'umi ba kamar koyaushe ba. Sai kawai na ta'ba wuyansa zafi rad'au zazza'bi ne. Na ce." Zazza'bi kake yi fa Baba?" Ya ce." Zazza'bi ne ko?'' Wai tambaya yake yi. Na ce." K'warai kuwa zazza'bi ne ya kawo maka sagewar gabobi da ciwon jiki, ya kamata ka samu hutu fa." Ya sake yun'kurawa a karo na biyu yana fad'in." Bari na yi wanka zan kira likitana yanzu ya duba ni tun wajan sha biyu na rana na ji yanayin jikina ya canza ina dan jin ciwon kai ma." Na kama hannunsa muka nufi bandakin tare na hada masa ruwan wankan ina fad'in.'" Wankan ma da ka bar shi tunda ka yi da safe. " Ya ce." Ai ba zan iya bacci ba idan ban yi shi ba Amina, kada ki damu bari na yi na fito ki kawo mini abinci." Na ce." To a sanyaye na fito na bar shi a toilet din na sau'ka kasa cikin 'yar damuwa ya jima kuwa bai kwanta ciwo ba tun bayan zazzafar murar da ya yi a gidana sakamakon ruwan saman da ya dake shi a shekarun baya.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book. 2k complete on telegram. What'sappa Gruop 1k Via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *121* Lokacin da na koma d'akin bai fito ba na zauna ina jiransa ya fito a rikice da d'ari irin na zazzabin ya sake ninkuwa kaya masu d'an kauri na d'auko masa ya kar'ba yana ko'karin sanyawa ya ce na d'auko masa hular sanyi duk a cikin kayan nasa ina fad'in." Abinda nake ta gudu kenan. Ya gama sanya kayan jikinsa ya zauna gefan gado cikin yanayi na ciwo da kaina na shafa masa basiline a jikinsa gabad'aya. Ya sanya hular har ta rufe kunnuwansa. Kafin na fara zuba masa abincin ya d'auki wayarsa ina jin ya kira likitansa ya yi masa bayani ya bashi tabbacin cewa gashi nan zuwa yanzu. Cokali biyu ya iya ci na abincin ya dakata. Gabad'aya ni ma sai na ji zazzabin yana nema ya rufe ni. Babu zato ba tare da tsammani ba na ji yana fad'in." Kira mini Hauwa a wayarki Amina." Da mamaki mai yawa nake dubansa. Ya d'an lumshe idonsa kafin ya bud'e yana gyad'a mini kai. Ban iya cewa komai ba na tashi a hankali na sauka kasa da nazari a k'wanyata. To ko dai an daidaitasu ne ban sani ba wata'kila kafin mu fito daga d'aki ni da Sahura mahaifiyarsa ta zauna dashi akan hakan zuciyata ta dinga yi mini sa'ke-sa'ke. Na koma d'akin na same shi a takure a gado ga blanket din bai rufa ba. Na zauna tare da rufe masa k'afafunsa har zuwa saman kirjinsa sannan a tsanake na fara neman layin Hauwa. Bugun farko ta daga ta kama sunana. Na amsa kafin mu gaisa ban ji ta sake yin gaisuwa ba kawai ta yi shiru sai na daure na ce." Maigidan ne yake son magana dake?" A yatsine tace." Kamar yaya menene a tsakanina da shi, kuma ai yana da lambata mai ya sanya sai kece za ki kira ni.'' Na danne b'acin ran da nake ji yana taso mini na furta." Haka dai ya ce ni na kira ki Hauwa." Ta ja siririn tsaki wanda ya yi mini ciwo sosai a rai amma ban katse wayar ba na mik'a masa yana daga kwance don bai tashi ba ya kar'bi wayar yasa a kunnansa. Sunanta ya kira ta amsa a dakile. Ya d'an yi jim ban sani ba ko yana jiran gaisuwarta ne ko kuma yana jiran ta yi masa ta'aziyya ko daya dai ba ta yi ba. Ya furta." Kina lafiya ko?'' "Umm" Ta ce cikin basarwa. Ya yi shiru na d'an wani lokaci kafin ya furta." Idan kin ji wani canji ko yaya ne a jikinki kada ki yi shiru." Na yi zugum ina kallonsa da mamaki wai yau Hauwa yake rarrashi har yana fad'in idan ta ji canji na ciwo a jikinta kada ta yi shiru ta sanar da shi. Duk ina k'iyayyar da yake fadin yana yi mata. Mamaki ya kasa bari na janye idona daga kansa har sai da suka yi sallama ya miko mini tare da lumshe idonsa. Na daure ina fad'in." Alhamdulillahi na ji dadin wannan abin da ya faru, Ina fatan Allah Ya sa ya zama na karshe." Ya yi shiru bai ce mini komai ba. Ni ma na yi shiru ina d'an duba wayata sai dai can kasan zuciyata wani takaici ne na dinga tunanin daga ina yake ai ni nake so Hauwa ta dawo mu cigaba da zama to mai zai sanya don ya yi waya daya da ita yau na ji haushi idan hakane kuwa gaskiya zuciyata bata kyauta mini ba. Ban iya tashi na fita daga d'akin ba har sai da likitansa ya zo ya duba shi sosai ya yi masa BF domin yana kuka da ciwon kai sosai jininsa ya haura amma ba sosai ba, dama kuma yana da hawan jinin sai dai ba kasafai yake tashi ba sai da damuwa kamar shakarun baya da ya motsa masa lokacin ina amarya yana neman hanyar da zai samu kaina ni kuma na'ki bada fuskar hakan tun zamana na farko Legos kenan a iya sanina tun daga lokacin bai kara motsa masa ba sai yanzu. Suka yi sallama yana fad'in " Za su tafi da Sukairaju yanzun domin ya bashi magunguΓ±a. Ya ce mini lallai ya ci abinci sosai kafin ace ya sha maganin. Da kyar da jibin goshi kamar wani yaro ko d'an yayen da yake rigima ya ci cokali biyar bayan biyun da ya ci da farko yana fad'in bakinsa babu dad'i, ba zai iya ci da yawa ba. Haka nan na ha'kura na kyale shi tunda iya naci da magiya na yi masa akan ya kara yace a a. Sukairaju ya kawo magunguΓ±an ya tsaya ya yi masa sannu kafin ya fita. Na duba kowanne akwai yadda za a ba shi. Na dube shi idonsa biyu rufe idon kawai Yayi kamar mai bacci. Na ce." Ka tashi kasha maganin to." Bai yi mini jayayya ba ya tashi na d'auki ruwa na tsiyaya a cup na mik'a masa ina ciro maganin ina bashi yana sha tsaf ya gama ya ajiye zai kwanta na ce." Ka dan bari ya fad'a maka." Bai ji ba ya yi kwanciyarsa minti biyu kuwa sai yun'kurin amai. Ya tashi da azama ya nufi toilet ya fara watso shi duk abincin da yaci da maganin da sha suka yo waje. Na rasa yadda zan yi gabad'aya damuwa ta dabaibayi ni. Haka nan na tarairayo shi muka fito ya je ya kwanta ya nishi. Na lura baya son ciwo kuma bashi da wani dauriya idan bashi da lafiya haka ya yi mini lokacin da ya kwanta ciwon mura a gidana na kuntau na sha dawaniya. Toilet na gyara na fito na same shi bacci ya d'auke shi sosai. Aikuwa ba zai yiwu ba, tashinsa na shiga yi ya bude idonsa na ce." Dole fa sai ka tashi ka sake cin wani abincin da maganin idan yaso sai ka yi baccin." Bai ce komai ba ya gyara kwanciyarsa ya rufe Ido. Na ce." Ka tashi don Allah ka ji.'' Ya yi mini shiru bai motsa ba. Kawai sai na zuba masa ido tsabar takaici da damuwa na ce." Shikkenan gaskiya zan sanar da Hajja an ta'ba yin ciwo ba cin abinci da magani." Ya bude idon yana kallona yace." Wai ba na ci ba ne?". Na ce." To nawa yake wanda ka ci, kuma duk ka amayar dashi da maganin." Ya tashi zaune tare da tallafe ha'barsa. Sosai na zura masa ido ina nazarinsa sai nake ganin kamar bayan ciwon da yake damunsa akwai wata damuwar. Zuciyata ta fara raya mini ko ya fara kewar matarsa ne da ta rasu. Wani sashe na daban yake ce mini 'Anya kuwa' ai an yi masa mace-mace da yawa ya ha'kura kuma bai ta'ba yin wani ciwo ba, kawai dai ciwon ne ya zo masa akan ga'ba ne. Nasa hannu na cire hannunsa da ya tallefe ha'barsa da shi a d'an sanyaye na ce." Wai menene don Allah, kada ka jefe ni cikin tashin hankali, yau kana tallafe ha'ba ko akwai wani abu da yake damunka?" Ya dube ni. Muka tsirawa juna ido sosai mun jima a haka bai ce komai ba sai ni na janye idona na sake zubo masa abincin da kaina na dinga bashi cikin ikon Allah kuwa ya ci da yawa da kamar minti goma tukkuna na sake bashi maganin a karo na biyu, ban yarda ya kwanta ba sai da muka yi zaman kimanin minti ashirin har ya fara gyangyadi sannan ya kwanta ni kuma na sauka k'asa. Na samu anti Yagana ta jima da yin bacci. wanka na yi a gurguje na sanya kayan bacci tare da a turare a jikina na koma saman. Lokacin baccinsa ya yi nisa sosai, na shiga cikin bargon kusa dashi sosai na kwanta kafin na fara yin addu'ar kwanciya bacci. Da asuba da d'an kuzari ya tashi domin ya riga ni ma tashi motsinsa na ji a bandaki na yun'kura da sauri na dira daga gadon domin ina tsoron ya ce zai watsawa jikinsa ruwa. Na same shi yana alwala sai na sauke ajiyar zuciya na tsaya har ya kammala tukkuna ya fita zuwa massalaci sannan shiga toilet din sosai domin yin nawa uzurin. Tun bayan da ya fita da asuban bai dawo ba sai wajejan goma da arba'in na safe. Na d'an shiga yar damuwa saboda yanayin jikinsa. Amma nasan abinda ya zaunar dashi bai wuce yin addu'a ba kamar yadda aka yi duk ranar da mamaci ya cika kwanaki uku da rasuwa. Anti Yagana Hajja da inna Uwani Gwaggo sun shirya tsaf da Shirin tafiya muna falo da su gabad'aya domin jiran shigowarsa Kamalu ya riga shi shigowa da kusan minti goma kafin ya shigo. idan kin karanta ba ki biya ni ba ina bin ki bashi. Cikinmu ya zo ya zauna kujera kusa da ni. Suka gaisa sosai. Hajja ta gaya masa tafiya za su yi. Na d'auka zai ce su yi hakuri su bari ayi bakwai sai bai nuna damuwarsa akan hakan ba ya ce ." Ita anti Yagana ta bari zuwa an jima kadan Sukairaju ya dawo sai ya d'auketa a mota ya kaita har gida. Hajja kuwa dama a babbar mota suka zo da direbanta duk zai kwashe su har Hajiya Saratu Kamalu da Yusi da Shima shigowarsa kenan yanzu a lokacin da suke maganar cikin shiri tunda ya san da tafiyar tun jiya 'dan uwansa ya gaya masa Cike da damuwa muka yi sallama na kasa daurewa sai da na yi kwalla na d'auko hijabi muka bi bayansu harbar gidan ni da anti Yagana har sai da suka shiga mota suka tafi tukkuna muka koma cikin gidan. Anti Yagana ta koma d'aki ta kwanta jiran dawowar Sukairaju kamar yadda maigidan ya fad'a. Na bi shi saman na same shi a kwance. Na zauna a d'an sanyaye ina fad'in." Ina kwana?'' Ya tashi zaune yana amsa da kulawa tare da tsira mini ido. Tun jiya yawan kallon nan da yake yi mini ya fara damuna." Na ce." Ji ki ya yi sau'ki ko?" Ya gyad'a kansa yana fadin." Alhamdulillahi, na ji sau'ki ina godiya." A tak'aice na furta." Me za ka ci yanzu?" "Shayi kawai zan sha idan da hali a yi mini farfesun kifi bakina babu test ko daya." Na ce." Da hali mana da kaina ma zan yi maka sai ka had'a da bread ko?" A tak'aice ya ce." Amma fara had'a mini tea din." Na tashi na sauka kasa kicin na nufa Baba Tabawa tana ta gyare-gyare tare da wanke kwanunan da aka yi karin kummalo na hada duk abinda zai buk'ata na kai masa. Na sake komawa kicin din Baba tana fad'in na bari ta yi na ce mata a a kawai ta bari ta huta jiki da jini tun asuba take tashi tunda aka yi rasuwar nan ga hidima da Sultan dama wani lokacin yana hannun inna uwani ko Gwaggo. Farfensun ya yi masa dad'i sosai kuma ya sha da yawa ya hada da bread har da gyasa Yana fad'in." Ya yi mini dad'i sosai na gode." Na ce." Sai shan magani?" Ya gyad'a kansa yana dan murmushi na dinga cirowa ina bashi daya bayan d'aya ya sha. Sannan ya kwanta yana. yi mini godiya. Sai wajan sha biyu muka yi sallama da anti Yagana wai ita da ta zo gaisuwa har sai da ya bata kudi bayan sanyawa da ya yi a kaita. Tare muka fito har da shi muka yi mata rakiya Sukairaju ya d'auketa a mota tana d'ago mana hannu. Gidan ya kasance shiru kowa ya watse gabad'aya ma area ta yi tsit kamar ba a yi wata hada-hada ta jama'a ba tunda zahirin gaskiya ta samu mutane wannan kuma yana da ala'ka da su waye mazajen da ta aura da kuma fannin kasuwancinta sai danginsu daga can jos din da suka dinga zuwa. Tun da ya yi sallar azuhur ya kwanta sai daf da la'asar tukkuna na tashe shi. Ya tashi kuwa da kuzari sosai ya ce zai yi wanka na ce a a tunda la'asar ce babu kyau haka annabi ya ce. Kuma gashi ba shi da lafiya. Yana d'an murmushi ya ce." Ban ta'ba jin wannan hadisin ba Amina, sannan a ina aka ce idan mutum ba shi da lafiya ya daina wanka, ba zan iya ba gaskiya." Na b'ata rai ina fad'in." Wallahi haka aka ce babu kyΓ u wankan daf da la'asar da bacci. Sannan kuma duk mai zazza'bi bayan son ruwa sai ka ga ciwon ya sake tsananta ka manta jiya kana zubawa jikinka ruwa ya rikice." Ya ce." Kwarai kuwa hakane amma ai yau gabad'aya ban yi wankan ba fa tun safe kin ga kuwa babu lefi don na yi yanzu, tunda na ji sau'ki gaskiya." Na ce." Kadai bari sai da daddare idan za ka kwanta." Bai ce komai ba ya nufi toilet din ba bi shi a baya sai naga yana burush ina tsaye ina kallonsa ya gama ya daura alwala ya fito. To a daran ranar can gidan Hajiya Maryam dai ba su rintsa ba duk da an cire rumfuna kuma maigidan ya sallami kowa amma su anti Yabi ba su tafi ba. Ita Nabila dama ta ci alwashin zama domin ta cigaba da kula da yaran. Anti Yabi Saliha da Rukky da shi Bashir din suka zauna wai sai an yi bakwai sai gidan ya kasance sai su kadai da masu aiki Taburni da Mairo sai yara Khalil Twins da Minal da suke hannun Mairo domin itace jigon kula da su shi Khalil yana tare da Adam tare suke kwana dakinsu daya itama Nusaiba tana nan ba ta tafi ba tukkuna. Talatainin dare wajan biyu da yan mintina duk sun yi bacci Bashir ya kusa kansa d'akin da suke kwance wanda ya kasance nan ne bedroom din Maryam din matattarar sirrinta anan suke ta dabdalarsu. Anti Yabi da Saliha sun yi washar da su a makad'ed'an gadonta suna ta bacci yayin da Nabila ke kwance kasan kafet ita kuma Rukky na can kan wata shirgegiyar kujera dake can gefa bacci ya shammceta ta bar wayarta a kunne tana yi kallo take yi wata'kila baccin ya cimmata. A kan Nabila ya tsaya yana fad'in." Ta shi, ke anti Nabila." Ta tashi zumbur ta ganshi a tsaye dogare a kanta ta ce." Baka da hankali za ka shigo mana a wannan daran wai Bashir me yake damunka ne?" Ya ce." Na gaya miki tun muna sheda juna ku sallame ni na ware, idan ba haka ba wallahi sai na yi muku illah." Ta mutsika idonta sosai tana fad'in.'' Dame zan sallama ka Bashir na rantse da girman Allah zan yi magan..... Ba ta kΓ rasa ba ya fille 'yar k'aramar askar da take hannunsa mai bala'in kaifi ya yi mata bille a kumatu gefan idonta. Cikin tsananin kid'ima da tashin hankali ta kurma ihu! jini ya mamayeta fuska tunda askar ta shiga sosai kuma ta samu tsokar kumatu. Gabad'aya suka tashi zaune. Ya dinga bin su daya bayan d'aya yana fad'in." Illa zan yi muku na rantse da girman Allah idan ba ku fito da abinda yake rabo na ba kun ba ni, shegu yan iska taron tsintsiya babu shara, wallahi zan tsinke miki yatsun hannunki anti Yabi." Ya dumfareta a zabure yana rangaji da askar a hannunsa mai la'kanin gayawa jini na wuce.... Suka yi tsuru-tsuru ganin yadda fuskar Nabila ta yi gaja-gaja da jini tana ta kuka. Anti Yabi ta nuna masa kusa da ita tana fad'in." Zo ka zauna nan kusa da ni Bashir mu yi magana ka ji ko, kada ka sake illata kowa a cikinmu mu din 'yan uwanka ne.'' Ya yi rangaji yana wani abu da hannu kafin ya dumfareta a karo na biyu yana fad'in." Ku ba ni abinda yake hakkina kawai na tafi tunda dama kun sallamawa duniya ni.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* **Gudun aure paid book complete 2k akan telegram. Normal Gruop wsp 1k via 0542382124... Binta Umar gtbank.* *07084653262* *122* Da farko har ya zauna kusa da ita kamar yadda ta buk'ata sai kuma ya tashi zumbur ya fara d'urawa Rukky ashariya yana fad'in ta daina kallonsa. Anti Yabi ta dinga jan hannunsa tana zaunar dashi yana fizgewa tare da ko'karin zuwa inda Rukky take domin dama can sakuwarsa ce kuma abokiyar fadansa. Da azama ta d'auki wayarta ta fice daga d'akin cikin tashin hankali don ganin kamar itama yana so ya yi mata lahani. Yabi ta fara fadin." Babu komai na kudi a d'akin nan Bashir tun daran jiya mun binceke komai sai sutturunta kai kuma namiji ne me za ka yi da kayan mata. 'Yar ta Nusaiba ce ta kwashe duk abinda muke hankoro ta boye sai waccan munafukar Nabila itama tana daya daga cikin wad'anda suka san sirrinta amma saboda ba'kar mugunta ta'ki ba mu goyon baya. Da tun farko ta amince mana da duk haka ba ta faru ba ni kaina a cikin wannan nazarin nake ace an watse ba mu tashi da komai ba." Nabila na kuka take fad'in." Anti Yabi ba kya ganin abinda ya yi mini lefi ma ki ke ba ni, kina ganin yadda ya yanka min kumatu amma duka baku da damuwa." Saliha tace." Ke ma kin so haka ta faru Nabila tuntuni muke miki magana kina nuna ke ba ki san komai ba bayan na tabbatar da cewar mukkulin dirowar can yana hannunki mugunta ce ta sanya ki boyewa tunda gashi kina fad'in za ki zauna a gidan. Ina yaran suke da za ki ce zaki kula dasu duk sun zama samari. Su wad'anan 'kananun dole ubansu ya mayarwa da iyayensu Nusaiba kuma ba zama za ta yi ba itama gidanta zata koma, kina so mu tafi sai ki yi wad'aka da dukiya ko to ai duk cikinmu babu yaro mun fahimci me ki ke nufi ." Yabi ta ce." Tunda abin ya fara zama haka Nabila ki fito da key din dirowar nan nasan anti Maryam a cike take ajiye sirrikanta wata'kila zamu samu gwalagwalanta a ciki da takardun shagunanta da ta mallaka sai mu d'auki wani abu daga ciki mu kasafta a tsakaninmu.." Cike da damuwa da jin rad'adi ta furta." Ban san inda key din nan yake ba anti Yabi ko ku yarda ko kada ku yarda wallahi ni ma ban d'auka ba. Wayoyinta da ATM dinta suna hannun Nusaiba to key din ma yana wurinta ku je ku binkiceta. Ya tashi yana rangaji da d'ura ashariya ya fita falon ya ritsa Ruky a zaune domin d'akinsu Mairo ma a rufe yake zage-zagen da yake yi ne ya tashe kaf har da yaran abinda ba su saba ji ba sai kuka. Adam da Salim suka tashi a firgice yayin da Bashir ya dinga bugun kofar d'akin da Nusaiba take kwance da yaranta. Itama a gigice ta tashi tana bud'e kofar ya yi ciki da ita ya ritsata. Salim da Adam suka bi shi d'akin. Itama Rukky ta koma d'aki a guje tana gaya musu gabad'aya suka fito a gigice Lokacin har ya sa mata wu'ka a wuya wai ta bashi kud'i da mukkulin dirowa an ce komai yana hannunta. Salim ya yi tsalle ya buga masa duka a bayansa tunda yana tsakiyar Nusaiban ya raba kafufunsa a kanta ya saita ta da wuka. Gidan ya cika da koke-koke a guje-guje. Mairo da gudu ta ja yaran suka koma d'akin suka rufe. Salim ya d'agata ta shi da gaske ya gilla mata wukar a wuya har ya yi sheda ta matsa gefe tare da ri'ke ma'kogwaronta da ya fara d'an fitar da jini kad'an. D gaske yankar rago ya yi shirin yi mata. Jama'a 'kwaya bala'i ce. Yaranta ihu kawai suke yi. Nabila ce kad'ai ta iya zuwa wurin da take amma su anti Yabi suna can sun rirri'ke Salim da ya shemar da Bashir din a kasa yana dukan hancinsa. Da yake ba sosai yake kashe wayoyinsa idan zai kwanta ba. Cikin bacci muka ji kiran waya gabad'aya kusan a tare muka tashi zaune ni dashi ya d'auka da sauri yana sanyawa a kunnansa muka ji muryar Adam cikin rud'u da tsananin tashin hankali yana fad'in." Baba ka zo babu lafiya ka zo yanzu Bashir ne zai kashe anti Nusaiba." Da wani irin hanzari ya sauka daga gadon na taso na biyo shi ya ce na koma. Har ga Allah na tsorata duk da gidansa cike da tsaro ina jin tsoro ya fita jin ana maganar kisa. Na koma na zauna cikin tsananin tashin hankali da damuwa wace irin masifa ce wannan kuma. Lokacin da ya shige gidan Bashir din ya samu nasarar ta shi yana ta kai wa Salim suka da wu'kar da take hannunsa 'karama ce amma kisa da illa take yi nan take. Ihu da koke ya cika gidan ita Nabila ga yanka a kumatu ga iskokai. Da hanzari ya nufe shi duk da ya hangi abinda yake hannunsa. Amma da ya gama fahimtar bashi da wani kuzarin kirki irin na maza dalilin shaye-shayen da yake ya dakusar da garkuwar jikinsa sai ya nemi ma'karfafansa ya kai masa duka a k'irji kafin ya falla masa mari ya murd'e hannunsa da kyau ya k'wace wu'kar ya mi'kawa Salim ita ya kar'ba duk ya yi wujiga-wujiga ai yayi namijin kokari ma wai aka ce ranar naka sai naka tabbas da da tsautsayi yau Nusaiba zata ba'kunci lahira itama. Ya ce da Adam maza ya fita ya kira masa Sukairaju da 'Dahuru sune majiya k'arfi sosai fadi yake kisan kai za ka yi mana a gida Bashir dama dan ta'adda ne." Ya yi shiru yana ciccije baki. Ya dubi Nusaiba dake zaune a gefe yaranta biyu a kusa da ita tana share hawaye sai ya girgiza kansa cike da tsananin damuwa ya kalli Anti Yabi yana jin kamar itama ya falla mata mari, tuntuni ya fahimci bata da hankali gabad'ayansu babu na za'be itama Maryam din da yake shedarta ashe ba'kar macijiya ce. Tun a d'akin Sukairaju da 'Dahuru suka fara tafkar Bashir ya hana su ya ce dai su caje jikinsa tsaf idan da wani makamin su fito dashi haka kuwa aka yi irin wannan wu'kar uku ce a soke a jikinsa sai daurikan wiwi da ganye ya ce su fita da shi. Ya juya yana kallon Saliha ita din ya tambaya menene abinda ya faru. Ta fara kame-kame. Nusaiba tana kuka ta ce." Ba haka ba ne wallahi baba tunda Momi ta rasu suke yi mata bincike d'aki wai tunda sun ji an ce ba su da gadonta. Sun 'ki tafiya ne tunda sun shirya halaka ni, anti Yabi duk abinda Momi ta yi muku da irin abinda za ku saka mata dashi kenan yau kwana uku da rasuwarta kuna rigima har da zubar da jini akan dukiyarta. Ba mu da iyaye wallahi domin ba zamu ta'ba nuna ku a matsayin iyayenmu ba." Suka yi shiru anti Yabi ta yi kasa da kanta tana fad'in." Ba haka ba ne Nusaiba wallahi kada ki zarge mu domin rashin Maryam na kowane. Ba mu da yadda za mu yi da Bashir tunda ya zo yake daga mana hankali wai a raba gado a bashi rabonsa, amma mu ai mun fi buk'atar Maryam akan abinda ta tafi ta bari na dukiya." Babu wanda ya ce mata komai, ya sake duban Nusaiba a karo na uku yana fadin." Ya aka yi har ya shigo ya yi miki Illa abinda nake so na ji kenan. Tana kuka ta ce." Wai sai na bashi wayoyin Momi da atm din da kuma mukullin dirowar da take ajiye muhimman abubuwanta." Ya gyad'a kansa cike da tsananin al'ajabi da mamaki, shi kaddararsa kenan abokinsa ya rasu ya bar shi da rikicin iyalinsa in ba haka ba shi a tarihin rayuwarsa da family dinsu wani abu na tashin hankali makamancin wannan bai ta'ba faruwa ba. Ya kama hanyar fita yana fad'in." Zo mu je d'akin ki nuna mini dirowar. Ta tashi da sauri tare da sanya yaranta a gaba ta bi bayansa su kuma suna tsaye cikin jin kunya Ruky ce kawai take tsugune gaban Nabila tana yi mata tofi. Madaidaiciyar dirowa ce ta mussaman domin ba irin ta gado ba ce wannan maybe daban ta sanya aka yi mata. Ya d'an ta'ba ya ji yanayin katakon yana da nauyi. Sukairaju ya kira a waya ya ce ya dawo. Ya fito falon Salim da Adam suna tsaye suna magana ya a kira Mairo. Adam ya dinga bubbuga kofar dakinsu tana fad'in." Wanene a cikin tsoro." Sai da ta yi muryar Adam din tukkuna ta bude ta fito Taburni ta biyo bayanta duk sun gigice kuma a tsorace suke. Ya ce su had'o kan yaran kaf su biyo bayansa. Haka akayi kuwa yaran duk suka fito ganin Babansu ya sanya suka ruga wajansa suna kuka tunda a gabansu abin ya faru lokacin da Bashir din ke ko'karin kai wa Nusaiba duka ga fuskar Nabila da ta'bon yanka da jini." Duk da Bashir din baya gidan Nusaiba kasa zama ta yi a gidan dalili ta tsorata ainun da 'yan uwan momin nasu. Salim da Adam ne kawai suka koma dakinsu ita kuma ta bi bayansa da yaranta tana kuka cikin tashin hankali ga wuyanta yana d'an yi mata zugi kad'an dole sai ta je asibiti. littafin gudun aure na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Haka muka kΓ rasa kwana cikin alhini da damuwa mai tsananin gaske. Da safe da wuri Salim ya shigo ya biyo ni har d'aki ya gaishe ni amma bai yarda mun had'a ido ba ya ce mini asibiti za su je yanzu da Nusaiba na biyo shi falon sai na same su tare da maigidan a tsaye suna magana itama ta gaishe ni cikin jin nauyi na amsa tare da tambayarta jikin ta ce da sau'ki. Sai bayan da suka fita ne tukkuna ya juyo yana kallona tare da cewa." Ina yaran suke?" Na ce." Suna tare da Mairo a can d'akin Baba Tabawa." Ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce." Sun dawo gidansu daga yau." Cike da godiyar Allah na furta." Allah Ya taya mu riko ya kuma albarkace su." Sama ya nufa yana amsawa. Ban bi bayansa ba sai da na kintsa jikina tukkuna na hau na same shi shima ya yi wanka yana dan duba wayarsa. Na ce." A kawo maka abin kari ko?" Ya ce." Bari zuwa an jima kad'an, abin nan da ya faru ya daga mini hankali Amina, wai me wasu suka mayar da zumunci ne, mutane idonsu ya rufe akan abinda duniya. Yar uwar nan ta su sanin da na yi mata lokacin da take raye ta wahalta musu kwarai da gaske domin ko kafin rasuwar iyayensu itace jigon kula da su Alhaji Amadu na yin nasa ko'karin. Ina daya daga cikin mutanan da suka dinga bashi Sha'awar bata goyon baya tare da ha'baka kasuwancinta tunda iyayenta ba su da k'arfi kuma itace babba. Ta yi musu zumunci k'warai ta kuma dinga ko'karin halakar da kanta duk akan su rayu yanzu ta fad'i ta mutu suna rigima akan abinda ta bari, abinda ya fi ba ni tsoro Bashir da yake ko'karin halaka yarinyar nan Nusaiba akan abinda bashi da hakki." Ajiyar zuciya na sauke tare da fad'in." Gaskiya da tsoratarwa a cikin wannan lamarin. Jiya da daddare na ji ita Nusaiban tana cewa shi Bashir din ya gudu an neme shi an rasa amma yana jin rasuwar ya dawo wai a bashi hakkinsa." Dariya ya yi irin ta takaici kafin ya ce." Ba shi da hankali ai da alama shaye-shayen da yake ya fara ta'ba masa kwakwalwa wannan barin irinsu ai babbar masifa ce, yana can hannun hukuma ai dama nemansa suke yi d'an iska." Na kalle shi jin ya yi zagi tabbacin abin ya yi masa ciwo sosai na furta." Allah Ya rufa asiri yasa mu fi karfin zukatanmu." A tak'aice ya amsa da "Amin." Idona ya sauka kan bakuwar dirowar da na ga Sukairaju ya shigo da ita a tun jiya da daddaran. Ganin inda nake kallo ya sanya ya ce." Sun ce wai muhimman abubuwanta na ciki an rasa mukkulin kuma dalilin da ya sanya na ce a d'auko mini ita gabad'aya idan na samu nutsuwa zan sanya a bud'e a gaban yaran domin su tabbatar da abinda yake ciki na game da dukiyar uwarsu." Na ce." Hakan ya yi, Allah Ya kawo musu sau'ki ya kuma takaita." Ya sake amsawa da Amin Yana fad'in." Kafin na shigo yanzu ai na sake shiga gidan tare da ba su umarni kan cewa duk su had'a kayansu su tafi basu da amfani sam gida kuma ba na Maryam ba ne ballantana su yi magana na Alhaji Amadu ne da y'a'yansa, ba su da gurin zama a cikinsa." murmushi kawai na yi irin na takaici ina mamakin karfin halin wasu mutanan, a ce akan kudi mutum sai ya sarayar da mutumcinsa. Duk kawaici irin na mutumin nan sun 'kure shi yana korarsu Allah na gode maka daka sanyawa iyayena wadatar zucci shima Baba Sule Allah ya taimake ni ya daina ya kama kan sa ganin yana tara surukai. Da yamma can kira ya shigo wayata da sabuwar number. Da mamaki na daga tare da sallama. Nusaiba na ji tan fad'in." Anti Amina Ina yini." Na amsa da kulawa ina sauraranta tana fad'in." Na kar'bi lambarki ne a wurin Adam dama zan gaya miki cewa Salim ya wuce da ni gidana bayan mun dawo daga asibiti ana I gobe addu'ar bakwai zan zo sai na kwana idan an yi addu'a sai na tafi." Cikin nutsuwa da kulawa na ce." To shikkenan hakan ya yi, Allah Ya huta gajiya ya kuma kiyaye faruwar hakan anan gaba. Ita kuma Mominku Allah Ya yi mata rahama." Ta amsa da "Amin cikin sanyin jiki muka yi sallama. Koda na gayawa maigidan yadda muka yi da ita yace ai ta sanar da shi. A daran ranar Mairo da Taburni suka had'o kan kayansu da na yaran gabad'aya kayansu na sanyawa da kayan wasansu irin wanda Momin take saya musu Minal ta dinga bin Mairo tana kuka wai sai ta tashi sun koma gida a daran. Ta'ki jin rarrashi Hassana da Husaina dama babu fuska domin ba su ganta ba a wajena suna zaune dai suna kallonta duk sun yi shiru kamar a tsorace suke da ni. Sun 'ki sakin jikinsu rigima take yi sosai lallai sai Mairo ta tashi sun tafi na kamo ta ina fad'in." Za ki je wurin Baba?" Ta d'aga kanta. Na dubi Mairo tare da fad'in." Ta ja su d'akinsu da na ware musu a falon su ci abinci. Baba Tabawa ta samu mataimakiya Taburni tare suka shiga kicin a yammacin ranar. Na ce su yi sallah isha'i tukkuna kafin su ci abincin." Ta amsa da "To." Wanda ya yi daidai da lokacin da ya sauko ya dubi Khalil yana fad'in." Yi maza ka dauro alwala mu je massalaci." Ya tashi da sauri. Ya dube Minal din dake saman cinyata tana kuka. Hannu ya mik'a mata ta sauko daga jikina ta nufe shi ya sunkuya ya d'auketa ya sanyata a k'ugunsa irin d'aukar dai ake yi yaran da ba su wuce shekara biyu zuwa uku ba. Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya ya dube ni yana fad'in." Me aka yi mata ne?" Na tashi tsaye ina fad'in." Wai sai Mairo ta tashi sun tafi gida." Ya yi murmushi yana cewa." Amina rigima ai a gidan kike." Na ce." Gidan Momi fa take nufi." Ya dire ta a kasa ganin Khalil din ya fito ya ce." Momi ai tana can gidanta na gaskiya Amina, ita kuma Minal nan ne gidansu." Ya kama hanyar fita Khalil ya bi shi a baya da sauri. Kaina na girgiza kawai na shige d'akina domin gabatar da tawa ibadar. *** To ranar sadakar bakwai din kamar yadda ya fad'a abinda ya faru kenan bai ma zauna balle a zo a taya shi zaman. Addu'a kawai ya sanya aka yi mata a massalatai. Nusaiba anan wurina ta kwana duk da Nabila tana can gidansu ita bata tafi tana tare da su Salim don bala'i har da kukanta tana fad'in ba zata iya tafiya ta bar su su kadai ba, kuma mamansu kafin ta rasu ta ce ko bayan ranta ta tsaya ta kula mata da yaranta. Haka suka ha'kura suka kyaleta shima Yallabai din da ya ji cewar ba ta tafi ba sai da abin ya bashi haushi sosai ya k:yaleta ne kawai domin ya ga iya gudun ruwanta. Duk da Nusaiba ta san tana gidan hakan bai sanya ta shiga ba nan su Salim din suka same ta. Ta shiga cikinsu Mairo suka yi aikin funkaso da fanke manyan kuloli aka fita da su domin sadaka. Tun bayan azahar ya shirya ya fita. Muka kasance da Nusaiba da yaranta har bayan la'asar kafin ta yi shirin tafiya gidanta. Yana shigowa estate din Sukairaju da 'Dahuru suka yi ram da shi Malam Isiyaku ne Malamin Hajiya Maryam da ya zo kar'bar kudinsa kamar yadda aka al'kawaranta masa. A mota suka zura shi tare da zuge gilashin motar sai ya fara zare ido na k'aduwa da tashin hankali. Sukairaju ya ce." Maigidanmu ne ya ce mu kai masa kai can gidan hutawarsa za ku tattauna wasu batutuwa ko ba kaine malam Isiyaku ba." Ya gyad'a kansa da saurin baki ya furta." E, ni ne, Malam Isiyaku." D'ahuru da yake driving ya ce." To kada ka damu lafiya za ka fito in sha Allahu." Ya yi shiru yana zazzare Ido. To ai shi ba haka ake yi da shi ba me yasa za a yi masa kamun kazar kuku magana aka yi akan mai hakki ya fito ya fadi hakkinsa a ganinsa hakan da aka yi masa tozarci ne tunda shi ba 'barawo ba ne. Gabansa suka dire Malam Isiyaku da tunda suka isa guesthouse din suka sanya shi a tsakiya babu wata hanya da zai samu ya fece.. Suka fita cike da bin umarni. Ya dube shi a nutse Yana fad'in." Nutsu sosai ka kwantar da hankalinka. Na buk'aci ke'bewa da kai anan ne saboda muhimmanan batutuwan da zamu tattauna da kai, ai komai yana buk'atar sirri ko." Ya gyad'a kansa kamar k'adangare kana ganinsa za ka gane a tsorace yake ko ina aljanun nasa suke oho. Wato ashe duk karyar banza ce." Ya gyara zamansa a gabansa kamar wani mai d'aukar darasi ba malamin da yake da 'kumaji da dulmiyar da al'ummar annabi ba." Ya ce.'' Tun sanda ka ba ni labarin abinda yake tsakaninka da Maryam mai rasuwa na gaza samun nutsuwa da kwanciyar hankali, a takaice nake sanar da kai har ciwo na kwanta saboda tsananin tashin hankali da damuwa. Malam Isiyaku shin za ka gaya mini irin bak'aken ayyukan da aka yi wa Maryam domin zalinci. Kada ka kuskura ka 'boye mini komai nasan ni ma da nake zaune nan a gabanka ka yi aikina ai asiri da tsafi gaskiya ne tunda ya ci annabinmu fad'in gaskiya shine abinda zai k'waceka bayan haka kuma ina so muje da ni da kai a gabana duk inda kayi binne a kaina ko akan wani na ka tone shi da hannunka." Ya ki'dime sosai da sosai ya kasa zama Yana fad'in." Yallabai Wani aikin kaikayi ne wallahi idan na karya shi zai dawo kaina, zan iya kwanciya ciwo ko abin ya shafi iyalina don girman Allah ka gafarce ni." Ya dube shi cike da tsantsar mamaki ya ce." Abin zalinci ne kenan, me yasa gabad'ayanku baku da imani ne, kai kanka kana gudun kada abinda ka yi ya shafi iyalinka to me yasa ka yi. Okey shikkenan tunda duk ina da bayanai a kan ka zan had'a ka da hukuma su za su yi maka tonan asiri duniya ta sheda wannan rawanin daka nad'a a kanka na zalinci ne furfurar dake gemunka kuma ta banza ce, daga nan 'yayanka da kake gudun su damu lahani su yi tur da kai da nadamar fitowa daga tsatsonka." Ya ce." Duk ba za mu kai ga haka ba ranka ya dad'e za mu je duk inda na yi haka da binne a kanka zan tone da hannuna in sha Allahu ko da hakan zai zama barazana ga rayuwata." Ya gyad'a kansa yana kallonsa cikin nazari kafin ya ce." Maryam ta yi aiki a kaina da iyalina kenan.'' Ya rusanar da kansa yana fad'in." K'warai kuwa na yi mata aiki akanka da kuma tsohon mijinta Alhaji Amadu akwai wanda na yi binne a kasan bishiyar kuka akwai wanda na yi a bishiyar tsamiya da kuma d'aurin baki da aka yi maka shima yana can za mu je ka gani domin laya ce aka 'dora mata gungumen dutse a can cikin wani daji.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book 2k complete on telegram what'sapp Gruop 1k via 0542382124...... Binta Umar gtbank* *07084653262* *123* Wato a duk lokacin da Ubangiji ya so bawansa da rahama ya kan wanke shi ya daidaita tunani da tafarkinsa zuwa hanyar tsira ya kuma yafe dukkunanin kuraransa. Allah," Ya ce kada ku hada ni da wani bawa na wurin neman biyan buk'ata ni ne da Ubangijin talikai mai jin kai, mai kuma bayarwa da hanawa. Ni ne d'aya wanda ba ni da farko da kuma k'arshe. Ku ro'ke ni da kowane irin yare ina jinku zan kuma amsa muku. Had'a Ubangiji da waninsa babban zunubi ne da yake tabbatar da cewa babu afuwa da yafiya daga wajensa. Domin Allah yakan iya yafe kowane irin zunubi ne mutukar bawa ya yi tabbaccen tuba. 'Kwarai da gaske ya girgiza ya kuma shiga razani da nadamar rayuwa a lokacin da suka dinga haurawa kan dutse tare da Malam Isiyaku da yaransa biyu Sukairaju da D'ahuru. Duk gwagwarmayar rayuwar da ya yi ta duniya k'afarsa bata zuwa ire iren wannan wurin ba. Karamin gari ne a cikin jos din kuma mafi akasarinsu maguzawane. A wannan 'kauyen da mahukunta suka manta dashi nan Malam Isiyaku ke zuwa ya gudanar da ayyukansa. Tunda a bayan gari yake kuma gari ne da ba su san menene addini ba. Suka dinga tsallake koguna da dutsina suna wuce manyan bishiyun kuka masu tsananin firgitarwa da bada tsoro. Wata narkekiyar bishiyar kuka suka nufi mai manyan koguna kuma babu ganye a jikinta. Suka tsaye gabad'aya wurin tsit sai kukan tsinye-tsinye ne ke tashi. Da alama bishiyar ta zama sansani wurin ajiye kayan asiri domin ga layu nan birjiki wasu a cikin kwalabe wasu kuma an nad'e su da jan zare da kwalaban tururukan da iska ke so. Ya tsuguna ya fara wasu zantuka kimanin minti goma ya gama can daga gefe ya fara hak'a da zurfi sosai ya d'auko wata doguwar kwalba da ta fara rinewa cikinta cike da allurai da bakin yadi mai kama da likkafani a ciki. Daga 'kasan wurin da ya yi hak'an ya cire yadin likkafani shima ya dan rine da kasar wajan Amma hakan bai hana ganin sa'kandamin da yake zane ba. Ya taso da kayan a hannunsa yana fad'in." Na ha'ko nan." Ya tambaye shi nasa ne ko na Alhaji Amadu. Cike da nadama da tsoron abinda zai biyo baya ya ce." Na ka ne Yallabai." Ya ce ya warware a wurin. Sukairaju da ba shi da tsoro ya kar'bi likkafanin da sa'kandamin yake hannunsa suka fara dubuwa. Zanen hotonsa ne tsaf kowace ga'ba da kusurwa ta jikinsa rubuce da sunan Allah da kuma wani irin jagwalgwalon rubutu mai ri'ke ta kwakwalwa. Abin mamaki yadin likkafin yana ta 'kamshin wani irin turare mai masifar karfi. Ya dube shi yana fad'in." Menene makarin aikin." Ya ce." An karya ai tunda an ha'ko." Suka yi gaba bishiyar tsamiya ce itama turgijejeya kana kallon wannan bishiyasa zaka tan ta tara 'kwan'kwamai masu illa gashinan ma da kanta take kamawa da wuta tsabar sansanin bak'aken aljanune. Itama dai kamar daya bishiyar kukan aikin mutane ne birjik a k'asanta da sassan reshenta tunda akwai ragowar ganye a jikinta ga layu nan murtuka murtuka suna ta reto wasu daban wasu a cikin kwalabe." Ya shiga mamaki sosai da ya ga ya d'ane bishiyasar can k'ololuwa ya kamo wani reshe ya d'auko wata doguwar kwalba da aka d'aureta sosai a jikin reshen an nannad'eta da jan yadi ya daddafo ya sauko da ita a hannunsa. Sukairaju ya mika masa babbar rigarsa yasa yana fad'in." Wannan shine na alhaj Amadu mai rasuwa." Ya buda kwalbar a wurin ta fashe. Layu k'ananu ne soke da allurai suka fito da wani irin warin turare mai gigitarwa.. A wurin ya sanya shi ya warware layun gabad'aya sunan Allah ne gashinan muraran Maliki yaumiddin mimun din da sunan Alhaji Amadu da Hajiya Ayya babarsa da kuma mahaifinsa. Duk ya warware guda ukun. Ya bawa Sukairaju umarnin tattarawa ya zuba a leda domin babu damar barin su a wurin da sunan Ubangiji. Suka yi gaba sosai suka riski wani shuri zungurere ya tsaya a sanyaye yana fad'in" Sati uku da suka wuce na zo na yi aikin wata mata a nan itama akan abokiyar zamanta ne farra'ku zan cire." Ya fad'a a sanyaye da alamar nadama a tare da shi. Suka tsaya kuwa ya tsuguna ga rana ta kwalle a wurin tururuwai masu yawa sun fito har suna bin kafafunsu. Ko alama bai sare ba, kuma bai tsorota duk da akwai razanarwa saboda ya san jahadi ya yi shiyasa ya fi yarda su je ya gani da idonsa domin tabbatar da duk ya warware kullin da ya yi." Ya haka gefen shurin inda ya san ya yi ajiyar ya d'auko wata yar tukunya ta 'kasa nan nad'e da likkafani ya kwance layu ne uku masu kauri ya warware cikinsu gashi ne da barkono tsidigu a hade da kuma d'anyan nama wanda kwance layun ke da wuya wari ya game hancinsu. Daga kansa ya yi musu bayani cewar naman na ja'ba ne sai gashin matar da aka yi wa asirin tsidigun (barkono) kuma shi zai dinga zafafawa ma'auratan zuciyoyinsu su ji sun tsani kansu da zama da juna. Suka gama da wannan suka sake nausawa sosai wannan karon tafiyar da suka yi tafi ta baya can suka riski murgujejen dutsan. Suka tsaya cikin ransa yana raya da wannan aka danne masa baki kenan. Gudun aure paid book ne kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba Daga can gefe Malam Isiyakun ya tsaya ya takarkare yana ture dutsen D'ahuru ya taimaka masa. Aikuwa sai ga wata laya mai fad'i a kwance tsabar nauyin dutsin ya sanya ta tamushe duk tudunta da nannad'ar da aka yi mata. Suka d'auko tare da fara kiciniyar kwanceta yana tsaye yana kallonsu jikinsa duk ya yi sanyi wato nan aka kawo bakinsa aka daure to akan me wai? Annabi ya yi gaskiya da yake cewa mata za su kasance da yawa a wuta, shi kam bai ga abinda ya yi wa Maryam ba da za ta yi masa haka. Aka warware laya itama mai cike da sa'kandamai guda uku daga kowane sashe sunan da labaraci ya fito radau Tajudden!. Suka had'a kan komai suka juya da baya domin fita cikin gari. Sukairaju da D'ahuru suna bayansu shi da Malam Isiyaku suna gaba. Ya d'an dube shi da gefan Ido gabad'aya ya yi sanyi mutumin fargaba ta mamaye shi. Tausayi ya bashi kad'an domin dai babu yadda za a yi ya sake shi ba tare da ya sanya hukuma a ciki ba. Mutumin banza ne wanda zuwansa duniya bai amfanar da kowa ba. Abin jajantawa da tausayawa iyalinsa da ya jefa rayuwarsa cikin gagari da 'kyama ta jama'a duk da akwai ire-irensa da yawa a gari masu ci da addini da halakar da mutane amma a ganinsa wannan nasa ya yi muni sosai. Ya ce." Ranar da ka fara yi mini bayani akan za ka yi aiki akan matata Hauwa ita dayar ba ka ta'ba wani aiki a kanta ba?'' Ya yi shiru na d'an wani lokaci kafin ya furta." Idan itace Amina gaskiya marigayiya bata ta'ba sanya ni aiki a kanta ba, abinda na sani shine ta ta'ba ce mini tana so a had'a taurarinta dana Amina din saboda nata suna da haske sosai kuma iyayen makarai ne a tare da ita tana da jalabi sosai bayan haka ma ba kasafai jifa ya ke kaita kasa ba tunda ba raguwa ba ce wurin addu'a. Taurarinta suna da tsananin haske dalilin da ya sanya kenan itama ta buk'aci da su yi musharaka wurin haduwar taurarin. Ya jima yana girgiza kansa da mamakin abin. Ya jima da sanin cewa ana iya amfani da haske da taurarin mutum domin cimma wata manufa wasu lukutan mutum na zaune kaf sai a kwashe masa taurari bai sani ba. Wato malam ka ji tsoron Malaman yanzu da suka kwashe kayansu daga gaban ma'aki. Kwana da yini suka yi a garin jos duk yadda Malam Isiyaku yake karyar da kai da nuna ya yi nadama bai saurare shi ba. Yana da jama'a sosai duk da wata mu'amula ba ta ta'ba had'a shi da shugaban jami'an tsoron garin ba. Dalilin suna da shahararsa a duniya ya sanya a daran ya gana da commissioner yan'sanda suka cika hannu da Malam Isiyaku zuwa sansaninsu. Gajiya kam sun kwaso ta daga shi har yaran nasa ga tafiyar mota sai gefen asubahi suka shiga garin abuja ana ta kiran sallar farko. Ban san ya dawo ba sai da gari ya waye tukkuna na fito na same shi da yaran gabad'aya a falo a zaune. Sun zagaye shi yana ta sauraransu yana murmushi Minal yar lelanshi tana kan cinyarsa. Twins kuma na gefansa a tsaye suna ta tsalle Khalil na saman kujera a zaune. Dukkaninsu cikin tsafta Mairo ta kintsa su. Suna ta 'kamshi. Na yi murmushi ina kallonsu gwanin ban sha'awa na ce." Cikin dare ka dawo ne?" Suka juyo gabad'aya suna kallona har da shi ba su lura da fitowata ba sai da na yi magana. Ya gyad'a kansa a nutse ya ce." Gefin asuba na shigo Amina. Ya kuke na same ku lafiya." Na ce." Alhamdulillahi ya su Hajja?" Domin ni ce mini yayi kano za shi kuma zai kwana daya." A tak'aice ya furta suna gaishe ku." Ya sauke Minal kasa Yana fadin." Zan kwanta zuwa an jima ki tashe ni." Na ce." To shikkenan." Ya haye sama da dan sauri. Na dube su Usai ta yi saurin janye idonta daga kaina. Na sassauta fuska tare da mika mata hannuna ina fad'in." Zo." Tun ranar da na mur'de mata kunne take ja baya dani. Hassana ce ke iya zuwa kusa da ni har ta yi mini hira. Minal kuwa yar d'akina ce tunda ita dama can akwai ta da saurin sabo." Ta zo din kamar yadda na buk'ata amma bata kalle ni ba. "Na ce." Menene?" "Babu komai." Na ri'ko hannunta a nutse na furta." Kina jin tsorona ne?" Ta girgiza kanta. Na d'ora ta saman cinyata ta ai kuwa sai tasa dariya tana kallona abin ya zo mata daban. Hassana ta taho itama tana bata rai. Na dauketa na sanya a daya gefan suka dinga dariya suna yi wa Minal gwalo ita kuwa mai neman jiran kiris ta fashe da kuka. Khalil yana yin dariya ya ce ni zo na goya ki." Na ce." Zo nan goyo kike so ko?" Ta daga kanta. Na ce." To ta kwana gidan sau'ki je ki ce Mairo ta bada abin goyo." Ta kuwa ta fi da sauri. Na dire su a kasa ina fad'in." Idan ba ku sanyata kuka ba bakwa jin dadi, kun yi girman banza." Ina shiga d'aki ta shigo da towel din Sultan tana mika mini na ce." Aiki ya same ni kenan, gashi wanka zan yi yanzu Minal amma muje." Ta biyo bayana na samu Taburni da yaran tana had'a musu tea na ce." To zauna ki ci abinci idan na yi wanka na fito zan goya ki." Mairo da ke goge musu kayan makaranta ta ce." ashe da gaske goyon za a yi Hajiya." Na ce." K'warai kuwa Mairo na juya na fita daga d'akin ina jinsu suna yi mata dariya. Na sami Adam a falon a tsaye wanda shigowarsa kenan. Muka gaisa yana tambayata Baba ya dawo?" Na ce masa ya dawo amma ya kwanta sai zuwa an jima ya dawo lokacin ya tashi. Ya ce to cikin sanyin jiki kafin ya juya ya fita na bi shi da kallo gwanin ban tausayi. Wajan daya da rabi na tashe shi domin yin sallah. Ya tashi zaune yana kallona goye da Minal a baya. Ya ce "Wacece a bayanki?" A tak'aice na ce." Name sake dina ce." Sai ya yi murmushi ya ta shi ya shiga bandaki ina zaune ya fito d'aure da alwala na ce." Adam kuwa ya shigo nemanka d'azu." Ya ce." Zuwa an jima zan nema shi. Sallah zan yi yanzu ki kawo mini abinci.". Na tashi na sauka kasa na had'o masa abincin da abinda zai buk'ata na koma na same shi ya idar amma yana gyangyadi a saman daddumar hakan kuma ba dabi'arsa ba ce. Na ajiye tiran ina tashinsa ya tashi ya nufi bed yana fad'in." Baccin zan sake komawa. Da mamaki na ce." Abincin fa.'' Ya rufa da bargo yana fad'in." Sai na tashi tukkuna. To wasa-wasa haka ya wanzu tsayin kwanaki hud'u yana wannan baccin gabad'aya yin ibada ne kawai yake tashinsa idan ya gabatar ya ce zai koma ya kwanta da rigima sosai yake cikin abinci ya zama kamar wani sususu jikinsa babu kuzari sai bacci sai kace wani rik'akken d'an 'kwaya. Hankalina ya fara tashi domin na ce masa ya kira likitansa ya duba shi bashi da lafiya ya ce na kyale shi a hankali zai warware kawai dai na cigaba da kunnansa karatun al'kurani. Ganin abin nasa ya'ki sau'ki na fara kuka domin tunda ya yi tafiyar nan ya dawo bai kwanta da ni mun yi sunna ba kwana biyar yanzu wanda a tarihin rayuwarmu hakan bai ta'ba faruwa ba. Muka dinga rigima akan na ce zan gayawa Hajja ba shi da lafiya a ganina ai mai matsalar aljanu da farfadiya ya kamata ace ana kunnawa akaratun al'kur'ani a saitin kunne, ga yanayin jikinsa ya nune babu kuzari amma ya ce shi lafiyarsa lau wace irin gajiyace wannan da zata mayar da shi d'an maye kullum bacci....✍️ *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book 2k complete on telegram what'sapp Gruop 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *124* A cikin kwanakin da ya kasance cikin wannan yanayin ki'ba ya yi ta fuska sosai ban sani ba ko baccin da yake yi ne ya janyo faruwar hakan oho! tunda gaskiya ba abincin kirki yake ci ba ballantana na ce tun asali ma mutum ne shi da bai fiye tasa abinci a gaba ya yi ta narka ba, kuma ba shi da irin ciye-ciyen nan na masu kudi. Cikin dare na tashi na yi sallah raka'a biyu na tsananta addu'a sosai domin abin ya fara daga mini hankali yanzu kuma na gano babu shakka akwai abinda ya faru wanda yake b'oye mini. Gefan kansa na zauna na bud'e alk'uranin izifi sittin din da yake hannuna daga sama na fara a cikin nutsuwa har aka fara kiran sallar farko wanda ya yi daidai da lokacin ya motsa. Ya tashi zaune yana kallona na rufe al'kur'anin muka dubi juna na dan wani lokaci kafin ya kira sunana na amsa. Sai ya zura k'afafunsa kasa domin sauka yana fad'in." An yi kiran sallah ko?'' Na ce." Za a yi yanzu dai." Toilet din ya nufa na bishi da kallon nazari kafin na tashi na bi bayansa na ga yana had'a ruwan zafi dana sanyi wanka zai yi ban hana shi ba kawai na ja masa k'ofar na fito na zauna har ya kammala ya fito d'aure da towel ashe ba iya fuska ya murmure ba har jikin gabad'aya. Ga mamakina da kuzarinsa ya kintsa ya fita massalaci wanda ya d'auki kimanin kwanaki biyar rabon da ya sanya kafarsa a waje duka sallolinsa a gida yake yin su ya koma ya lafke a gado. Kasa sauka 'kasa na yi har sai da gari ya yi haske ya dawo. Ya gan ni a zaune bai nuna mamaki ba na zuba masa ido har ya zo ya zauna kusa da ni wanda na yi zaton kwanciyar zai sake yi sai naga akasin haka muka gaisa ya ce mini na d'auko masa Loptop dinsa dake ajiye can wurin da yake zama. Cike da jin dad'in ganinsa a haka na tashi da azama na je na d'auko masa har ya bud'e ya kunnanta sai kuma ya kashe ya janyo ni jikinsa. Ga mamakina na ga yana ko'karin cire mini hijabin dake wuyana. Muka kalli juna ya kanne mini ido cikin wata kalar murya ya ce." Mu 'dan yi wani abu ko." Kasa ce masa komai na yi domin ni hakan ma jefe ni ya yi a farinciki ganin ya fara dawowa hayyacinsa. Na biye masa kimanin minti talatin muka d'auka kafin komai ya kammala. Ya riga ni yin wanka ko da na fito sai na same shi yana yin waya na ji yana kiran sunan wani Malam Rabi'u akan zai tura masa da abin sadaka a sake yin saukar al'kur'anin da aka yi a watannin baya. Sai da suka gama tukkuna na sake gaya masa Adam ya shigo jiya da shekaran jiya wurinsa. Yana sake ko'karin kunna Loptop din a karo na biyu ya ce." To zan neme shi na ji menene nasan ba zai wuce maganar Nabila ba ita take turo shi wai zata zauna tare da su." A tak'aice na ce." Hakan yana da kyau ai." Na tashi na sauka kasa domin had'a masa abin kari. Kafin na shiga kicin din d'akin yaran na fara dubawa duk sun yi shirin tahafiz yau asabar da lahadi tun takwas na safe suke tafiya sai shida. Ranakun da suke da boko kuma suna shiga k'arfe uku. Dukkaninsu cikin uniform a tsaftace kamar yadda dai suke yi musu hidima a gidan Momin Taburni da Mairo kowanne da lunchbooks dinsa. Ganinsu ya saukar mini da wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali a raina na tsinci kaina cikin nishadi da annashuwa suka fara gaishe ni ina amsawa tare da tsokanar Minal yau sai makaranta. Falon muka fito tare na ce." Mairo ta kira mini Masa'udu. Kamar yadda suka bar gidan Maryam ba ni son abinda zai sake dangantasu da gidan duk kuwa da cewa direban da yake jigila dasu yana nan tare da masu gadin amma ba ni son abinda zai sake kai yaran gidan ina so su fara gina sabuwar rayuwa mai cike da nutsuwa da kwanciyar hankali. Ya shigo tare da risinawa yana gaishe ni na amsa na ce.'' Daga yau za ka cigaba da kai yara makaranta kafin Babansu ya samar musu da sabon direba." Ya amsa da "To shikkenan in sha Allahu Hajiya." Ya tasa kan su gabad'aya har Khalil suka fita suna yi mini bye-bye Mairo ta bi su da jakkunansu da kayan abincinsu. Na leka d'akinsu Baba Tabawa muka gaisa sosai suna tare da Taburni da alama ta su ta zo daya tunda duk dattijai ne. Sultan na ta bacci cikin net din shi sun shirya shi tsaf. Har na juya zan fita Baba Tabawa ta ce." Hajiya Amina kina jin mu da Taburni ko wai tafiya gida za ta yi." Na juyo da sauri ina fad'in." Me yasa Taburni ko an yi miki wani abin ne? ko kuma ba ki jin dadin zama da mu." Ta girgiza kanta tana fad'in." Ko daya wallahi Hajiya ina so na je na ga yarana da iyalinsu idan hali ya yi zan dawo suna can suna jirana tunda sun san uwar rikon nawa ta rasu wasu daga cikin iyalina ma sun zo gaisuwa." Na ce." A a gaskiya ba za ki saki aikinki ba Taburni za ki zauna da mu in sha Allahu a madadin marigayya kuma za mu ninka miki albashinki, zuwa ganin gida wannan ba lefi ba ne, amma ina jin dad'in ganinku a tare ga yara sun saba daku." Kwalla ta cika kwarmin idonta tana fad'in." Shikkenan Hajiya Amina na gode sosai Ubangiji Allah ya saka muku da alheri cikin satin nan zan je na dawo." Na ce." Zan sanar da maigidan in sha Allahu nasan zai sanya a aiki kuma aje a dauko ki." Na fita daga d'akin cikin nazari. Idan Taburni ta tafi baba Tabawa ba zata ji dad'i ba sun saba ga yaran ma idan Mairo na wani uzuri wajanta suke zuwa kuma macace mai hankali. da kaina na shirya masa abinda zai ci farfensun kifin na sake yi masa tunda na ga ya yi masa dadi kwanaki na hada masa da funkaso da tea wanda nasan dole zai bukace shi domin dumama cikinsa. Ya kuwa ji dad'i sosai kuma ya ci da yawa ya dinga yi mini godiya ina jin dadi a raina ganinsa ya fara nutsuwa har ma yana ta rage ayyukan da ya jima bai yi ba. To shi din ma da na gaya masa cewa Taburni za ta koma garinsu bai bada goyon baya ba ya ce yara sun saba da ita sosai idan har ba a takura mata ba to na gaya mata ta zauna zai dinga biyanta fiye da yadda tsohuwar uward'akinta take biyanta. Yinin ranar haka na yi shi babu komai a cikina domin duk abinda na tunkara da zumar kaiwa bakina zan ji zuciyata na tashi abu mai tsami tsami shi na fi sha'awa tun da na fara jin haka kuwa akwai matsala daf nake da yin al'ada idan ba ta zo ba kuwa ciki ne. Duk yadda na kai ga daurewa kuwa kasawa na yi domin da daddare amai na dinga kyalayawa Allah ya sa a d'akina ne na yi na gama na gyara toilet din na fito na kwanta lamo cikin kasala sallar Isha'i ma a zaune nayi ta saboda yadda jikina ya mace lokaci k'an'kani. Sai wajan goma da arba'in na dare na iya fitowa falon shiru yaran duk sun shiga sun kwanta. Na nufi saman abin mamaki hawa daya biyu zuwa uku sai da na zauna na huta. A haka na kΓ rasa hayewa zuwa d'akin nasa. A bud'e yake tunda dama yana tsammanin shigowata na same shi yana waya da harshen larabaci karo na biyu kenan da na ji shi yana magana da harshen. Ranar da aka d'aura auranmu a makka da kuma yau. Ban jima da zama a gefansa ba ya gama wayar ya dube ni yana fad'in." Hajiya yau mantawa ki ka yi da ni ne?" A tak'aice na ce." A a gani na yi ka ji sauki ai." Ya ce." Sai ba ni da lafiya za ki zo wajena har ki d'ora kaina anan." Ya fad'a tare da dora hannunsa saman kirjina. Murmushi kawai na yi ban ce masa komai ba kaina ne ma yake yi mini ciwo. Ya ce." Tunda magriba da ki ka kawo mini abinci ki ka sauka ba ki dawo ba ko na yi wani abin ne?" Ya fad'a cikin rausayar da kai." Na ce." Babu abinda ka yi kawai na ga kana aiki ne shine na ce bari na dan baka wuri ka kammala." Kira ya shigo wayarsa ya d'auka na ji yana fad'in." Lafiya ya kike ina Uwani." Daga nan na fahimci Hauwa ce. Sai na juyar da kaina gefe to da yake hands free wayar take na ji tana fad'in." Yau kwana uku Ina neman wayoyinka bata shiga." A tak'aice ya ce." "Ba ki da number Amina?" Ya bata amsa da haka. Ta ce." Itama ba ta shiga." Da mamaki na kalle shi wayata kullum a kunne take wannan ba gaskiya ba ne ba ta kira ni ba. Ya ce mata." Ok Ina fatan lafiya ko?" "Ba ni da lafiya ne?" Ta fad'a cikin 'yar k'aramar murya." Babu wani gigita a tare da shi ya ce. Sannu idan kin je asibiti sai ki sanar da ni abinda ya kasance na sayan magani zan sa miki." Daga haka bai jira jin abinda za ta sake cewa ba ya datse wayarsa ya ajiye. Ya dube ni muka had'a Ido sai ya kanne mini idonsa yana fad'in." Ina labari?" Gudun aure paid book ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Na ce." Kai zan tambaya domin cikin kwanakin nan ka jefa ni cikin rudani" Ya sauke ajiyar zuciya bai ce komai ba sai ya d'ora kansa saman tudun kirjina. Ni ma da taya 'bera 'bari na tallafe masa kan ina shafa shi. Ai sai na kunna shi ya sake ma'kale ni tare da zura hannuwansa duka biyun ya kewaye 'kuguna. Mun jima haka Ina ta shafa saman kansa a hankali yana ta sauke ajiyar zuciya babu wanda ya sake yin magana a cikinmu. Hauwa ta sake kiran waya a karo na biyu ba tare da ya d'auke kansa daga kirjina ba ya d'auki wayar yasa a kunnansa. Ta fara maganar da karamin sauti ban ji komai ba, ni kuma daman ban so na jin ba na ji yana fad'in." Babu halin hakan." A tak'aice ya gaya mata haka duk kuwa da cewa doguwar magana ta yi masa ya sake dai kashe mata wayar a karo na biyu na ji shi can kasa yana fadin." Na d'auka mutuwa zan yi a cikin kwanakin nan ban zaci zan sake moruwa ba wallahi saboda tsabar yadda ga'bobin jikina suka mutu." Na ce." Ni ma na tsorata gaskiya amma dai duk da haka yana da kyau likitanka ya dubaka sosai baka da lafiya." Ya ce." Hakan za a yi in sha Allahu." Ya d'auke yana gyara zamansa na ce.'' Kasan yaran nan sun koma makaranta yau ko?'' Ya ce." K'warai kuwa mun yi magana da Masa'udu d'azu dana fita sallar la'asar zai maye gurbin Dauda direbansu na can gidan Maryam." Na ce." Hakan ya fi." A daran ranar ma sai da ya yi auratayya da ni, na dinga daurewa domin akwai buk'atar hutu da samun bacci a tare da ni ga jikin babu kuzari. Sai da ya gane kuwa ya d'an saurara mini da asuba da yawo daga massalaci bai sake nema na ba. Nima tunda na koma bacci bayan sallar asubahin ban tashi ba sai wajan sha biyu da kwata sai da na yi wanka tsaf na kintsa jikina sannan na fito yaran suna makaranta a falon na samu Mairo da Nusaiba suna hira Taburni da Baba Tabawa suna kicin suna aiki. Cike da girmamawa duka suka yi mini barka da fitowa na nemi wuri na zauna cikina na hautsinawa yunwa da tashin zuciya bakina salam. Ina fad'in." Yaushe ki ka zo ne?" Da murmushi a fuskarta take fad'in." Wajan sha daya da rabi Baba ya kira ni yana sama amma bai sauko ba mun dai yi magana a waya ya ce mu jira shi." Na ce." Allah sarki Ina yaran na gan ki ke kadai." Ta ce." Suna makaranta anti." Salim da Adam suka shigo cikin kaya iri daya gabad'aya yaran daga lokacin rasuwar Mamansu zuwa yanzu sun ladabtu sosai ba kamar Salim da yadda yake risina mini ke ba ni mamaki yaron da ya d'auki mummunan gaba da ni. Itama Nusaiban har yanzu bata iya had'a Ido da ni. Adam kuwa dama d'an d'akina ne tunda suna tare da Yusi. Muka gaisa cikin kulawa na tashi ina fad'in." Bari ina zuwa." saman na nufa domin sake sanar dashi zuwan yaran. Sai na same shi shi da Sukairaju suna ta kicin-kicin bud'e wannan dirowa da aka shigo da ita kwanakin da suka shige. Da kyar suka samu nasarar bud'eta da dabaru da kuma wasu mukkulai da na gansu a hannun Sukairaju... Na ce." Nusaiba da 'yan uwanta sun zo wajenka." Bai ce mini komai ba sai da Sukairaju ya fita tukkuna ya fura." E, wannan ma'ajiyar ta Mamansu zan bud'e a gabansu. Ya d'auki wayarsa ya kira Nusaiban ya ce mata su haho saman. Muna zaune suka shigo gabad'aya suka gaishe shi ya amsa cikin kulawa yana tambayarta yara da yanayin jikinta. Ta nuna masa wuyan nata tana fad'in." Wurin ya warke alhamdulillahi. Ya ce." To alhamdulillahi kamar yadda na gaya muku cewa idan na samu nutsuwa sosai zan bude wannan ma'ajiyar domin ni daku muga abinda yake ciki ma sha Allah cikin ikon Allah yanzu Sukairaju ya samu nasarar bud'eta don haka ku ba ni hankalinku gabad'aya. Ya sanya hannu a nutse zai bud'e na fara ko'karin tashi domin ba su waje ya ce na zauna. Ba don raina ya so ba na zauna din Tana da d'an zurfi amma ni da nake zaune kusa da shi na gama ganin duk abinda yake ciki. Da saurin gaske na d'auke kaina gabana na wani irin fad'uwa. Daga b'angaransa ban hangi wani razani ba da hannunsa ma ya shiga fito da abubuwan da suke ciki. Farko dalar amurka ce ta fi bandur ashirin ya gama fito da su sannan ya kwaso tarin akwatinan gold's dinta kusan set biyar manya ba k'ananu ba bayan zobuna na tsayun hannu dake cikin akwatinansu. Ya debo wasu takardu ya mi'kawa Salim yana fad'in " Duba nan ka ga menene. Ya kar'ba da sauri ya fara dubawa. Abubuwa biyu da suka yi saura cikin dirowar ya d'auko Mutumin-mutumi ne mai d'auke da suffarsa da suffarta tsirara kammaninsa sak haka zalika itama kammaninta sak an had'e su waje daya an matse sosai da farin likkafani da jan zare aka nannad'e sannan 'kasa da sama duk an kulle da ko'ina da kwa'do. (Key) Sai wata kwalba doguwa mai kama da ta lemo cike da turare mai maiko da k'ananun layu a ciki kimanin takwas kowacce soke da allura. Ya dubi Nusaiba da ta gama kidimewa ganin abinda ya biyo bayan dukiyarsu da Mamansu ta boye musu ya nuna mata yana fad'in." Wannan shine abinda ya rage cikin wannan dirowa Nusaiba." Sai ta rushe da kuka tana 'kunshe bakinta da hannu hawaye suka fara kasa tsere a kumatunta. Adam kuwa sunkuyar da kansa kasa ya yi yana cike da damuwa mai yawa. Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un kawai take fad'in tana kuka. Shi kuma Salim sakato kawai ya yi da takardu a hannu ya tsirawa abubuwan ido yana kallo cikin jin nauyi da kunya. Ganin yadda duk suka ki'dime ya sanya ya fara rarrashinsu yana fad'in su nutsu Nusaiba dai fadi take yi don Allah Baba ka rufa mana asiri ka ce ka yafe mata ko zata samu rahama. Anti Amina kuma don Allah ku yafe mata ban sani ba ko ta yi muku wani abin na cutarwa ni dai wallahi ban san Momi tana bin wannan hanyar ba domin kullum idan mun zauna da ita cikin yi mana fad'a da nasiha take bantaba sanin abinda take yi ba." Ya ce." Babu komai ku nutsu kowane dan Adam yana tare da jarrabawarsa a duniya mai kyau ko mara kyau ni daku duka ba mu san abinda yake lullube ba domin alherinta muka sani shi kuma muka dinga fad'a bayan mutuwarta. Ba ni da masaniyar cewa ta tuba kafin Allah Ya d'auki rayuwarta tunda zuciyarta a kirjinta take kuma ba a bud'e mini na gani ba. Na yafe mata Ina kuma roka mata sasaauci daga mahallicinta. Wannan abin da kuka ga ni zai zama sirri in sha Allahu, abinda nake so daku gabad'aya shine ku samu nutsuwa kada cikinku wani ya sanya damuwa a ransa. Ina nan har yanzu a madadin mahaifinku kamar yadda ya ba ni amanarku in sha Allah......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Paid book ne 2k complete on telegram WhatsApp Gruop 1k 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* Kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Mu kiyaye mu kula da hakkin junanmu. Kukan da Nusaiba take yi shi ya fara ta'ba mini zuciya na ji hawaye ya cika kwarmin mini idona. A hankali na janye idona daga kanta gabana na fad'uwa cikin raina ina ta kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Yadda yaran nan suka ki'dime ganin abinda Mamansu ta mutu ta bari na sa'bawa Allah shine ya tabbatar mini da cewa duk zargin da ake yi mata na cewa mushirikiya ce ba su gazgata ba sai yanzu da mutuwa ta yi mata tonan silili. Babu kama ko d'aya a zahirance da kuma mu'amularta domin ni kaina ban ta'ba gazgata maganar dake yawo a kanta ba saboda ban ga ni da idona ba a wasu lukutan dai idan abin ya yi tsanani nakan ji a raina anya babu k'amshin gaskiya akan abinda ake fadi akanta. Tun farkon neman auranta Sahura ta gaya mini har nake kwa'barta kan tabbatar da abinda baka da sheda a kansa. Na sanya hannu na d'an share guntun hawayen da ya sauka saman kumatuna sun gama karya mini zuciya yaran yayin da tausayinsu ya zauna a zuciyata me ya fi wannan takaici ace ana binciken sirrin uwarka bayan ta rasu a gano wani abu na takaici wanda ta aikata. Ban ankara ba kawai na ganta a kusa dani gwiwa a kasa ta kamo hannuna tana fad'in." Anti Amina don Allah ku rufa mana asiri don Allah anti Amina." Na ri'ke hannunta har na ji yana karkarwa na gane akan abinda take yi wa kuka da tashin hankali kada maganar nan ta fita mutane su gazgata zarginsu. Sosai na ri'ke ta ina fad'in." Ki kwantar da hankalinki Nusaiba, yadda Ubangijin da ya hallice ta ya rufa mata asiri a lokacin da take raye ya amince da jama'a su ambaci alherinta da kyakykyawan fata har ta rasu to ban ga dalilin da zai sanya don ganin wani sirrinta da ya kasance tsakaninta da Allah ya sanya ni fad'i a gari ba. Na yi miki alkawari kan cewa ni dai babu wanda zai ji haka daga b'angarena, muna ro'kon Allah Ya yafe mata, mu kuma rayuwarmu ta yi kyau a duniya da lahira ." Ta dinga godiya cikin rawar murya da tashin hankali. Na ji maganar Salim yana fad'in." Wannan takardun gidan da ta saya ne a kano da filaye uku sai na shagunanta biyu dai na san haya ta kar'ba amma watannin baya kafin ta kwanta ciwo ta ce mini sun gama magana tana so ta biya kudin duka su zama mallakinta." Ya ce." To tunda ka ga baka ga shedar mallaka ba a cikin wannan takardun da suke hannunka wata'kila ba ta biya su ba, amma dai ka bincika mana wanda suka bata hayar wajan mu ji daga gare su kafin nan sai a had'a kan komai a zauna domin sauke mata nauyi." Ya amsa a sanyaye yana had'a kan takardun ya mik'a masa ya kar'ba ya mayar cikin dirowar da kudin da sarkokin. Sauran biyun da suka zama na karshen fitowa kama bai mayar da su ba. Tsabar fargaba da tashin hankali a duk lokacin da na dubi mutum-mutimin da ya sha d'auri tamau sai gabana ya fad'i lallai bokan da ya sassa'ka suffofinsu ba 'karamin hatsabibi ba ne. Fuskar Baba sak da yanayin jikin itama suffarta sak rai ne kawai babu a tare da su amma an had'e su waje daya an nannad'e da likkafani da jan zare sai da na k'ura ido ma tukkuna na hangi da wasu 'yan mici-micin layu sun saje da jan zaren ne shiyasa ban gansu ba ga wasu manyan mukullai an had'a an kulle. Ina can cikin tunani na ji maganarta tana fad'in." Anti mun tafi." Da sauri na daga kaina ina fad'in." Ki gaishe mini da yaran Nusaiba." Ta amsa da in sha Allahu kafin su fita da sanyin jiki. D'akin ya kasance shiru bayan fitarsa. Ya juyo yana kallona muka zubawa juna ido na dan wani lokaci. Ji na yi zuciyata ta tsinke haka kawai sai na ji ina tausayinsa wace irin masifa ce wannan ni Amina matar nan ashe d'aure mutumin nan ta yi sai ta yi aikin akan ga'ba dama aka ce asiri yana tasiri sosai mussaman idan ya tarar da hali. Ya d'auki abin zai kwance da sauri na ce." Ka ajiye kada ka ta'ba" Ya kuwa ajiye da sauri a tsorace yana kallona. Na ji hawaye sun zubo mini wannan d'aurin ba k'arami ba ne tunda har ta yi masa wannan boyon ina jin tsoron duk ranar da aka warware d'aurin ya fadi ya mutu ko kuma ya kwanta jinyyya mai tsanani mafiakasari irin wannan mugun aikin wad'anda suka yi sune suke da makarinsa. Kuka kawai na dinga yi hankalina ya yi bala'in tashi ainun muna cikin masifa ni da yara Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ya zo ya rirrike ni hankalinsa a tashe yana fad'in." Menene abin kuka Amina na amince Maryam ta cutar da ni ta mini illah a rayuwata amma godiyar da nake yi ga Allah yadda ya zaunar mini dake ba ki bar ni ba. Har kullum idan na daga kaina na dube ki sai na ce alhamdulillahi a zuciyata na kuma yi alfahari da kasantuwarki matsayin matata abokiyar rayuwata. Na gode Amina, Na gode kin so ni kin zauna da ni a lokacin da mata suka guje ni, kin yi mini biyayya bisa abinda ranki ba ya so, kin daraja mahaifiyata kin kyautata mata a yau ina gaya miki bayan mahaifiyata ke ce ta biyu a cikin matan da nake alfahari da su, ina so mu kasance tare anan gidan duniya da kuma na lahira." Kuka na ya sake tsananta jin irin zantukan da suke fitowa daga bakinsa. Gabana ya cigaba da bugawa tsigar jikina na tashi na sanya duka hannuwana biyu na matse shi sosai a jikina ina fad'in." Rayuwarmu da ni da yara za ta shiga garari idan babu kai a cikinta Maryam ta illata mu muddin warware wannan d'aurin da yake tsakaninku ya haddasa masa maka mummunan ciwo. Ko ba ka gaya mini ba kwanciya ciwon da ka yi a kwanakin baya yana da ala'ka da irin ayyukan da ta yi a kanka a jikina na ji hakan mutuwarta abubuwa suka fara lalacewa. Ya ki'dime sosai yana d'an jijjigani da rawar murya yake fad'in." Ba abinda zai faru, na yarda Maryam ta yi mini illah Amina amma bata samu nasarar kai ni k'asa ba, ga ni ina raye tare dake ta jefe ni sosai ta ko'ina ta dabaibayi ni da d'aurin baki domin kada na hangi lefinta amma ni jin dadina da bata nemi hanyar da zata illata mini ke ba Amina kamar yadda ta ci laya akan Hauwa Allah Ya d'auki ranta kudirinta bai cika ba. Ba ki da hakkinmu da ni da ita shiyasa bata ma yi tunanin cutar da ke ba. Tsafi gaskiyar mai shi na gazgata hakan ne a kwanakin nan da suka wuce da muka je da wani malaminta ya warware ayyukan da ta sanya shi ya yi aikana wannan shine dalilin da ya sanya ni wannan kwanciyar na dinga bacci da ciwon jiki. Ban zalinceta ba amma ni ta zalince ni ta hanyar d'addaureni ta ko'ina babu gaira babu dalili tare da haddasa mini rikici da husuma ta karkashin kasa a gidana. Tunda har ki ka ga na tashi yanzu bayan warware wancen makarun da ta yi mini to warware wannan ma ba zai zama cutarwa a gare ni ba in sha Allahu." Na dago ina dubansa tare da cewa." Da bakinka fa ka ce tare ku ka je da malamin da ya yi aikin ya warware da hannunsa. To shi wannan din kana da makarin warware shi, ka dubi abubuwan da suke jikinku kai da ita kuma likkafani ne ya yi muku sansani da kai da ita. Wata'kila ta yi aikin ne akan idan ta riga ka mutuwa duk ranar da aka kwance d'aurin da yake tsakaninku kaima ka bi bayanta, idan hakan ba ta samu ka kwanta ciwo mai tsananin gaske." Ya yi shiru yana kallona a d'an tsorace! sai ya sake matseni gam a kirjinsa yana kiran sunan Allah tare da sake duban idan gunkin mutumin-mutumin na su yake ajiye. Muka kasance cikin shiru da zullumi jikinsa ya yi bala'in mutuwa ya yi mini wata matsa tsam kamar yana jin tsoron a k'wace ni. Minti goma a haka muka wanzu babu magana ya cika ni tare da zuwa ya d'auko wayarsa. Ya zauna yana fad'in." Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Kimanin minti biyar yana waya da Malam Rabi'u kafin su yi sallama ya dube ni yana fad'in." Akwai gaskiya a cikin maganarki Amina. Ba ni da masaniyar akan malamin da ya yi wannan aikin don haka dole zuwa kano ya kama ni can kauyen Bunkure wajan Malam D'aha abokin mahaifina ne in sha Allahu ina da yakinin shi zai warware mini wannan d'aurin kuma babu abinda zai same ni da izinin Allah." Na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." To ita fa waccan kwalbar mai layu a ciki." Ya ce." Har da ita za mu je gaban Malam din duk abinda yake da akwai Allah zai bayyana shi." A daran ranar ban iya rintsawa ba har ya ma fi ni tawakkali a wannan ga'bar hawayen idona kuwa ya kasa tsayuwa domin sai nake ganin kwance wannan tsatstsauran d'aurin da yake tsakaninsu zai kassara masa rayuwa idan bai fadi ya mutu ba to ya yi mutuwar tsaye tunda bata raye a duniya to kowace mace ta yi asara. Abinda na ke ji a raina kenan shine kuma ya hana ni sukuni don daga zarar na tuna irin wahalar da ya sha kwanakin da suka wuce sai hankalina ya sake tashi zuciyata tana ta raya mini cewa wannan likkafanin da yake d'aure a jikinsu ita dashi akwai alamar tambaya a kansa tunda duk inda aka ce an yi wa mutum asiri da likkafani ko an binne a makabarta abu ne mai munin gaske. Tsakanin d'azu da safe da yanzu da muke cikin talatanin dare dana juya na kalle shi zan ji wani bala'in tsoro da tausayi da kaunarsa a cikin zuciyata idan ya mutu ni da yara mun shiga masifa wace rayuwa ce za ta biyo bayan faruwar hakan, me zai faru? Maryam ta so zuciyarta ta cuce ni ta cutar mana da yaranmu. Na jima a sujjada ina kuka ina ro'kon Allah har sheshshekar kukana ya tashe shi ya kira sunana na juya na dube shi yana fad'in." Me yasa wai kike wannan kukan ne? Na gaya miki ba ni so ni shine kadai yafi damuna ki zo ki kwanta babu abinda zai same ni." Kasa tashi na yi daga saman daddumar na cigaba da jan hanci ina share hawayen da nake ta ko'karin tsayar da shi amma ya'ki yatsuwa. Ya sauko ya zo ya zauna gabana har da tankwashe kafa. Na kalleshi baccinsa ma yake yi shi kamar abin bai dame shi ba. Ya ri'ko hannayena cikin kulawa yana fad'in." Ban san haka kike sona da yawa ba Amina, Maryam ashe k'aryar so take yi mini tunda har za ta iya cutar da ni ta hanyar yi mini mugun k'ulli mai razanarwa. Ha'kikanin so shine irin wannan wanda ki ke yi mini. Kuma na tabbatar da hakan ba tun yau ba daga wajenki Amina, abu daya za ki yi mini yanzu shine ki ji maganata ki share hawayenki ki tashi mu je mu kwanta." Ya sanya tafin hannunsa ya goge mini fuska kafin ya ri'ke hannuna na tashi da kansa ya cire mini hijab din wuyana muka nufi gadon yana ri'ke da ni sosai a gefansa....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Paid book ne 2k complete on telegram WhatsApp Gruop 1k 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* Kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Mu kiyaye mu kula da hakkin junanmu. Kukan da Nusaiba take yi shi ya fara ta'ba mini zuciya na ji hawaye ya cika kwarmin mini idona. A hankali na janye idona daga kanta gabana na fad'uwa cikin raina ina ta kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Yadda yaran nan suka ki'dime ganin abinda Mamansu ta mutu ta bari na sa'bawa Allah shine ya tabbatar mini da cewa duk zargin da ake yi mata na cewa mushirikiya ce ba su gazgata ba sai yanzu da mutuwa ta yi mata tonan silili. Babu kama ko d'aya a zahirance da kuma mu'amularta domin ni kaina ban ta'ba gazgata maganar dake yawo a kanta ba saboda ban ga ni da idona ba a wasu lukutan dai idan abin ya yi tsanani nakan ji a raina anya babu k'amshin gaskiya akan abinda ake fadi akanta. Tun farkon neman auranta Sahura ta gaya mini har nake kwa'barta kan tabbatar da abinda baka da sheda a kansa. Na sanya hannu na d'an share guntun hawayen da ya sauka saman kumatuna sun gama karya mini zuciya yaran yayin da tausayinsu ya zauna a zuciyata me ya fi wannan takaici ace ana binciken sirrin uwarka bayan ta rasu a gano wani abu na takaici wanda ta aikata. Ban ankara ba kawai na ganta a kusa dani gwiwa a kasa ta kamo hannuna tana fad'in." Anti Amina don Allah ku rufa mana asiri don Allah anti Amina." Na ri'ke hannunta har na ji yana karkarwa na gane akan abinda take yi wa kuka da tashin hankali kada maganar nan ta fita mutane su gazgata zarginsu. Sosai na ri'ke ta ina fad'in." Ki kwantar da hankalinki Nusaiba, yadda Ubangijin da ya hallice ta ya rufa mata asiri a lokacin da take raye ya amince da jama'a su ambaci alherinta da kyakykyawan fata har ta rasu to ban ga dalilin da zai sanya don ganin wani sirrinta da ya kasance tsakaninta da Allah ya sanya ni fad'i a gari ba. Na yi miki alkawari kan cewa ni dai babu wanda zai ji haka daga b'angarena, muna ro'kon Allah Ya yafe mata, mu kuma rayuwarmu ta yi kyau a duniya da lahira ." Ta dinga godiya cikin rawar murya da tashin hankali. Na ji maganar Salim yana fad'in." Wannan takardun gidan da ta saya ne a kano da filaye uku sai na shagunanta biyu dai na san haya ta kar'ba amma watannin baya kafin ta kwanta ciwo ta ce mini sun gama magana tana so ta biya kudin duka su zama mallakinta." Ya ce." To tunda ka ga baka ga shedar mallaka ba a cikin wannan takardun da suke hannunka wata'kila ba ta biya su ba, amma dai ka bincika mana wanda suka bata hayar wajan mu ji daga gare su kafin nan sai a had'a kan komai a zauna domin sauke mata nauyi." Ya amsa a sanyaye yana had'a kan takardun ya mik'a masa ya kar'ba ya mayar cikin dirowar da kudin da sarkokin. Sauran biyun da suka zama na karshen fitowa kama bai mayar da su ba. Tsabar fargaba da tashin hankali a duk lokacin da na dubi mutum-mutimin da ya sha d'auri tamau sai gabana ya fad'i lallai bokan da ya sassa'ka suffofinsu ba 'karamin hatsabibi ba ne. Fuskar Baba sak da yanayin jikin itama suffarta sak rai ne kawai babu a tare da su amma an had'e su waje daya an nannad'e da likkafani da jan zare sai da na k'ura ido ma tukkuna na hangi da wasu 'yan mici-micin layu sun saje da jan zaren ne shiyasa ban gansu ba ga wasu manyan mukullai an had'a an kulle. Ina can cikin tunani na ji maganarta tana fad'in." Anti mun tafi." Da sauri na daga kaina ina fad'in." Ki gaishe mini da yaran Nusaiba." Ta amsa da in sha Allahu kafin su fita da sanyin jiki. D'akin ya kasance shiru bayan fitarsa. Ya juyo yana kallona muka zubawa juna ido na dan wani lokaci. Ji na yi zuciyata ta tsinke haka kawai sai na ji ina tausayinsa wace irin masifa ce wannan ni Amina matar nan ashe d'aure mutumin nan ta yi sai ta yi aikin akan ga'ba dama aka ce asiri yana tasiri sosai mussaman idan ya tarar da hali. Ya d'auki abin zai kwance da sauri na ce." Ka ajiye kada ka ta'ba" Ya kuwa ajiye da sauri a tsorace yana kallona. Na ji hawaye sun zubo mini wannan d'aurin ba k'arami ba ne tunda har ta yi masa wannan boyon ina jin tsoron duk ranar da aka warware d'aurin ya fadi ya mutu ko kuma ya kwanta jinyyya mai tsanani mafiakasari irin wannan mugun aikin wad'anda suka yi sune suke da makarinsa. Kuka kawai na dinga yi hankalina ya yi bala'in tashi ainun muna cikin masifa ni da yara Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ya zo ya rirrike ni hankalinsa a tashe yana fad'in." Menene abin kuka Amina na amince Maryam ta cutar da ni ta mini illah a rayuwata amma godiyar da nake yi ga Allah yadda ya zaunar mini dake ba ki bar ni ba. Har kullum idan na daga kaina na dube ki sai na ce alhamdulillahi a zuciyata na kuma yi alfahari da kasantuwarki matsayin matata abokiyar rayuwata. Na gode Amina, Na gode kin so ni kin zauna da ni a lokacin da mata suka guje ni, kin yi mini biyayya bisa abinda ranki ba ya so, kin daraja mahaifiyata kin kyautata mata a yau ina gaya miki bayan mahaifiyata ke ce ta biyu a cikin matan da nake alfahari da su, ina so mu kasance tare anan gidan duniya da kuma na lahira." Kuka na ya sake tsananta jin irin zantukan da suke fitowa daga bakinsa. Gabana ya cigaba da bugawa tsigar jikina na tashi na sanya duka hannuwana biyu na matse shi sosai a jikina ina fad'in." Rayuwarmu da ni da yara za ta shiga garari idan babu kai a cikinta Maryam ta illata mu muddin warware wannan d'aurin da yake tsakaninku ya haddasa masa maka mummunan ciwo. Ko ba ka gaya mini ba kwanciya ciwon da ka yi a kwanakin baya yana da ala'ka da irin ayyukan da ta yi a kanka a jikina na ji hakan mutuwarta abubuwa suka fara lalacewa. Ya ki'dime sosai yana d'an jijjigani da rawar murya yake fad'in." Ba abinda zai faru, na yarda Maryam ta yi mini illah Amina amma bata samu nasarar kai ni k'asa ba, ga ni ina raye tare dake ta jefe ni sosai ta ko'ina ta dabaibayi ni da d'aurin baki domin kada na hangi lefinta amma ni jin dadina da bata nemi hanyar da zata illata mini ke ba Amina kamar yadda ta ci laya akan Hauwa Allah Ya d'auki ranta kudirinta bai cika ba. Ba ki da hakkinmu da ni da ita shiyasa bata ma yi tunanin cutar da ke ba. Tsafi gaskiyar mai shi na gazgata hakan ne a kwanakin nan da suka wuce da muka je da wani malaminta ya warware ayyukan da ta sanya shi ya yi aikana wannan shine dalilin da ya sanya ni wannan kwanciyar na dinga bacci da ciwon jiki. Ban zalinceta ba amma ni ta zalince ni ta hanyar d'addaureni ta ko'ina babu gaira babu dalili tare da haddasa mini rikici da husuma ta karkashin kasa a gidana. Tunda har ki ka ga na tashi yanzu bayan warware wancen makarun da ta yi mini to warware wannan ma ba zai zama cutarwa a gare ni ba in sha Allahu." Na dago ina dubansa tare da cewa." Da bakinka fa ka ce tare ku ka je da malamin da ya yi aikin ya warware da hannunsa. To shi wannan din kana da makarin warware shi, ka dubi abubuwan da suke jikinku kai da ita kuma likkafani ne ya yi muku sansani da kai da ita. Wata'kila ta yi aikin ne akan idan ta riga ka mutuwa duk ranar da aka kwance d'aurin da yake tsakaninku kaima ka bi bayanta, idan hakan ba ta samu ka kwanta ciwo mai tsananin gaske." Ya yi shiru yana kallona a d'an tsorace! sai ya sake matseni gam a kirjinsa yana kiran sunan Allah tare da sake duban idan gunkin mutumin-mutumin na su yake ajiye. Muka kasance cikin shiru da zullumi jikinsa ya yi bala'in mutuwa ya yi mini wata matsa tsam kamar yana jin tsoron a k'wace ni. Minti goma a haka muka wanzu babu magana ya cika ni tare da zuwa ya d'auko wayarsa. Ya zauna yana fad'in." Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Kimanin minti biyar yana waya da Malam Rabi'u kafin su yi sallama ya dube ni yana fad'in." Akwai gaskiya a cikin maganarki Amina. Ba ni da masaniyar akan malamin da ya yi wannan aikin don haka dole zuwa kano ya kama ni can kauyen Bunkure wajan Malam D'aha abokin mahaifina ne in sha Allahu ina da yakinin shi zai warware mini wannan d'aurin kuma babu abinda zai same ni da izinin Allah." Na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." To ita fa waccan kwalbar mai layu a ciki." Ya ce." Har da ita za mu je gaban Malam din duk abinda yake da akwai Allah zai bayyana shi." A daran ranar ban iya rintsawa ba har ya ma fi ni tawakkali a wannan ga'bar hawayen idona kuwa ya kasa tsayuwa domin sai nake ganin kwance wannan tsatstsauran d'aurin da yake tsakaninsu zai kassara masa rayuwa idan bai fadi ya mutu ba to ya yi mutuwar tsaye tunda bata raye a duniya to kowace mace ta yi asara. Abinda na ke ji a raina kenan shine kuma ya hana ni sukuni don daga zarar na tuna irin wahalar da ya sha kwanakin da suka wuce sai hankalina ya sake tashi zuciyata tana ta raya mini cewa wannan likkafanin da yake d'aure a jikinsu ita dashi akwai alamar tambaya a kansa tunda duk inda aka ce an yi wa mutum asiri da likkafani ko an binne a makabarta abu ne mai munin gaske. Tsakanin d'azu da safe da yanzu da muke cikin talatanin dare dana juya na kalle shi zan ji wani bala'in tsoro da tausayi da kaunarsa a cikin zuciyata idan ya mutu ni da yara mun shiga masifa wace rayuwa ce za ta biyo bayan faruwar hakan, me zai faru? Maryam ta so zuciyarta ta cuce ni ta cutar mana da yaranmu. Na jima a sujjada ina kuka ina ro'kon Allah har sheshshekar kukana ya tashe shi ya kira sunana na juya na dube shi yana fad'in." Me yasa wai kike wannan kukan ne? Na gaya miki ba ni so ni shine kadai yafi damuna ki zo ki kwanta babu abinda zai same ni." Kasa tashi na yi daga saman daddumar na cigaba da jan hanci ina share hawayen da nake ta ko'karin tsayar da shi amma ya'ki yatsuwa. Ya sauko ya zo ya zauna gabana har da tankwashe kafa. Na kalleshi baccinsa ma yake yi shi kamar abin bai dame shi ba. Ya ri'ko hannayena cikin kulawa yana fad'in." Ban san haka kike sona da yawa ba Amina, Maryam ashe k'aryar so take yi mini tunda har za ta iya cutar da ni ta hanyar yi mini mugun k'ulli mai razanarwa. Ha'kikanin so shine irin wannan wanda ki ke yi mini. Kuma na tabbatar da hakan ba tun yau ba daga wajenki Amina, abu daya za ki yi mini yanzu shine ki ji maganata ki share hawayenki ki tashi mu je mu kwanta." Ya sanya tafin hannunsa ya goge mini fuska kafin ya ri'ke hannuna na tashi da kansa ya cire mini hijab din wuyana muka nufi gadon yana ri'ke da ni sosai a gefansa....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book complete 2k akan telegram. Wshap Gruop 1k via 0542382124....Binta Umar gtbank.* *07084653262* *126* Kwanciya muka yi a tare a gadon ya d'auki kaina ya d'ora saman kirjinsa sannan ya d'ora hannunsa a jikina a hankali ya ja bargo ya rufe mu gabad'aya. Rufe idona kawai na yi ba da niyyar bacci ba domin kuwa babu shi a idona wanda nake da tabbacin shi din bai sake komawa ba har aka kira sallah. A tunaninsa bacci nake yi ina ji ya sauke kaina a hankali ya mike ya nufi toilet na tashi zaune ina kallonsa har ya gama abinda yake yi ya fito. Ya d'an tsaya yana kallona na d'an wani lokaci sai kuma ya girgiza kansa kafin ya kama hanyar fita ba tare da ya yi magana. Sauka k'asa na yi a d'akina na yi wanka na yi sallah a gurguje na kimtsa jikina don babu yadda za a yi ayi wannan tafiyar babu ni. Na sake komawa saman na shi sai na same shi har ya yi wanka ya shirya yana zaune gefan gado cikin kaftani gilas da hularsa a gefe yana waya dai da Rabi'un da suka yi magana jiya yana sanar da shi gasu nan zuwa. Sai da ya gama tukkuna ya dube ni na zauna gefansa tare da gaishe ya amsa cikin kulawa ya dago fuskata muka kurawa juna ido. Kallon da yake yi mini ya kara karya mini zuciya hawaye suka zubo. Ya fara fadin." Kash! menene haka kuma? ki dubi idanunki sun kumbura Amina ni kam na tsanani wannan kukan wallahi." Ya fad'a cike da yanayi na damuwa da tashin hankali." Sosai na fashe da kukan da karfin gaske ina fad'in." Ni fa wallahi tare za mu tafi." Ya ce." Akan wane dalili, ai nima ba kwana zan yi ba kuma in sha Allahu da k'afafuna zan dawo gidana, kada ki yarda da abinda zuciyarki take raya miki Amina tunda har na riga na tsallake na baya to wannan ma zan tsallake in sha Allahu." Na girgiza kaina ina fad'in." Ban yarda ba kawai dai mu je tare na raka ka hankalina zai fi kwanciya." Ya ce." To yaran fa?'' Ya fad'a yana goge mini kumatu. Na ce." Su zauna wurin su Mairo ai da mutane a gidan ba za su ci karo da wata matsala ba in sha Allahu tunda dama babu wani sabo mai yawa a tsakaninmu." Ya girgiza kansa yana cewa." To ai so nake ku saba yanzu ki zauna cikinsu sosai ki kula mini da su hankalina zai fi kwanciya ki zauna a gida na je na dawo Amina irin wannan rigimar taki ce fa ta sanya ban sanar dake na farko ba." Na ce." Sai ka jefa zuciyata cikin damuwa ba, menene abin boyewa." "To in banda abinki ai abin alheri shi ake shela, sharri kuwa ba abin fad'i ba ne." Ya ri'ke hannuna yana duba zoben azurfan da ya sanya mini a yatsana." A d'an sanyaye ya ce." Kin amince na je na dawo ko matata?" Girgiza kaina na yi tare da fad'in." Wallahi ban amince ba tare za mu je gashi ma na shirya." Ya yi jim na dan wani lokaci kafin ya furta." Tunda dai har kin rantse ba zan karya miki ita ba." Na sauke ajiyar zuciya Ina fad'in." Na kawo maka abinda za ka ci ko?" Ya ce." Ke 'din kin ci?" girgiza kaina na yi. Ya furta." To je ki kawo sai mu yi breakfast din tare." Na tashi da azama na sauka k'asa ina jin dad'in yadda ya amince tafiyar da ni. To ba mu isa 'kauyen Bunkure ba sai gefin la'asar tafiyar mota ce K kuma ta samu k'wararran direba Ade wannan karon tare aka tafi da shi su uku da Amintattun yaransa Sukairaju da D'ahuru. Ko da nake cikin a garin kano kafata bata ta'ba taka garin ba sai a wannan karon. Yadda dama muka shirya shine idan har abin ya zo da sauki mun kammala abinda ya kawo mu gidan malamin sai mu wuce can gidana na sharad'a mu kwana idan ya so idan mun gaisa da Hajja zuwa jibi sai mu tafi. Mun samu tar'ba ta mussaman a gidan Malam D'aha. Na ga kara da karamaci irin na mutanan kauye domin kuwa ina idan da sallar magriba aka cika gabana da kwanukan abinci har daga ma'kota. Mafiakasari towo ne na masara dana dawa sai wata langa da aka kawo mini ita daga baya cike da dambu na tsaki wanda ya ji zogale da gyad'a yana ta k'amshin mangyad'a zuryan da yajin barkono a gefe. Ya ba ni sha'awa sosai na kuma yi masa cin yaushe gamo na toshe cikina da shi duk tarin yunwar dana nad'a a tsukin nan sai da na rasa yadda zan yi da cikina. A daddafe na yi sallar Isha'i. Ina idarwa wata matashiyar budurwa ta shigo doguwa mai duhun fara ba ta da jiki sosai akwai yarinta a tare da ita ta sake gaishe ni na amsa ina fad'in ta kwashe kwanukan abincin da ta dinga kawo mini gasu nan shida a jere. Ta tsuguna tana bubbud'awa ta dube ni tana fad'in." Ai d'aya kawai ki ka ci Hajiya." Na ce.'' Ina zan kai wannan abincin yar uwa wannan ma na gode sosai kuma wallahi ya yi mini dadi 'kwarai da gaske." Ta yi murmushi ba tace komai ba ta fara had'a kan kwanukan tana fita da su. Na d'auki wayata dake gefena na duba na ga network dina ya d'auke gabad'aya wata'kila yana da ala'ka da yanayin d'akin da nake ciki tunda na 'kasa ne kuma a k'asa yake sosai. Gabad'aya hankalina yana can b'angaran malamin tun zuwanmu da muka shiga tare na gaishe shi na fito ban sake jin wani motsi ba sai ta hayaniyar iyalin gidan da shige da fice da ake ta yi na d'aukar abinci daga almajiran malamin. Gajiya na yi da zaman d'akin na fito tsakar gidan na samu jama'a a cike da yake mai yalwa ne kwarai matan gidan su hud'u suna can daga gefe suna cin abinci a tare wasu daga cikin yaran kuma sun ci sun gama wasu na cin na su. Kwanuka gasunan birjik a bakin manyan tukwanansu. 'Yar budurwar nan da har yanzu ban san sunanta ba na ji tana fad'in." Bandaki za ki shiga.'' Kafin na ce komai daya daga cikin matan gidan ta ce." Hajara zuba mata ruwa maza a buta Hajiya alwala za ki yi ne?" Na ce." A ai na yi sallah na fito na sha iska ne." Yarinyar da aka kira sunanta da Hajara ta d'auko tabarma da sauri ta shimfida mini can gefe na je na zauna ina yi mata godiya cikin ikon Allah zamana ke da wuya network din duka layukana ya dawo. Na fara neman number Sahura muka gaisa sosai ta sake yi mini gaisuwa nan nake sanar da ita cewar na shigo garin zan kira ta zo gida ta same ni zuwa gobe. Muna sallama na nemi number Hajja da ta shiga sai ta katse na kira ya kai sau biyar nan na gane network din yake hawa da sauka wai ina so na gaya mata cewar za mu shigo gobe. Na dauki kimanin minti talatin da zama a tsakargidan wanda ya yi daidai da lokacin tara na dare da minti biyar. Daga can b'angaran malamin na ji maganarsa alamun zai fito na sauke ajiyar zuciya a hankali idona a kan hanyar suka fito tare da wannan Rabi'u da yake yawan kiransa a waya wanda shine ya kan gaba wurin tararmu lokacin da muka sauka a garin. littafin gudun aure na kudi kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Suka fito tare da kuzarinsa ya tsaya cikin kulawa yana yi wa matan gidan sallama na tashi ina gyara mayafina na d'auki jakata can inda suke zaune na nufa ina fad'in." Za mu tafi, na gode sosai da karamaci Allah Ya saka da alheri, na dubi Hajara dake zaune cikin 'yan uwanta na ce." 'Yar uwa sai Wani lokacin ko na gode da kulawa." Ta washe bakinta tana fad'in." Ku gaida gida Allah Ya tsare hanya." Na ce." Amin Ya Allah tare da yin gaba ganin ya riga ni fita ina jin matan da yaransu suna ta yi mini fatan alheri. Ina fita daga can wajen motar da mu ka zo Sukairaju nake hange da D'ahuru sai Rabi'un suna taga-taga kafin na hangi Baban ya yi wata irin fad'uwa irin ta ruf da ciki da kirji. Ade ya fito daga mota a ki'dime! yayin da gabad'aya suka rufu a kansa duk da yake dare ne amma ai irin na karkara ne da suke da wadatar kwanciyar hankali ba irin cikin gari ba hakan ya sanya mutane fara tsayuwa a wajen. Ban san inda nake jefa k'afafuna ba kawai dai na tsinci kaina a tsakiyarsu lokacin da suke ko'karin ciccib'arsa. Rabi'u yana fad'in da k'afafunsa ya fito kuna dai kallo magana ma muke yi da shi ya yanke jiki ya fadi." Jikina ya dinga kyarma na tsuguna ina d'ago kansa yana karyewa ganin haka ya sanya ni ihu! ina Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Baba Baba, na dubi Sukairaju a gigice ina fad'in." Ku d'auke shi mu tafi asibiti." Rabi'u ya ce." Cikin gidan za mu mayar da shi Hajiya ." Daga haka suka fara kici-kicin ciccib'arsa Sukairaju ya cire gilashin idonsa da wayoyinsa tare da wallet dinsa ya sanya cikin aljihunsa su biyu shi da D'ahuru suka kama saman shi ta wajen kansa. Rabi'u da Ade suka rirrike k'afafunsa a haka ina kallo suka taitayeshi suka koma dashi cikin gidan suna ta Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Na bi bayansu k'afata na karkarwa shikkenan kuma tunda har kansa ya karye ya mutu. Kai tsaye d'akin malamin suka nufa da shi gidan ya rud'e sosai da hayaniya duk kowa a tsaye na bi su ina kuka na fitar hankali. Babar yarinyar nan Hajara ta zo ta ri'ke ni ta baya ina cire hannunta tana sake ri'ke ni fadi take yi "Yi hakuri ki yi masa addu'a kin ji, Allah ya ba shi lafiya." Na dube ta ina cewa." Ya mutu ko?" Sai ta girgiza kanta cikin ko'karin kwantar mini da hankali ta ce." Bai mutu ba ke waye ya gaya miki." Hawaye ya sake tsinke mini na ce." Kansa na ga ya karye ko'ina na jikinsa ya shika. Kin ga ai lafiya lau ya fito har muka yi muku sallama ko?'' Ta daga kanta cikin alhini ta ce." E, kwarai kuwa amma hakan ba shi yake nuna cewar bashi da rai ba zai tashi in sha Allahu." Na ri'ke hannunta tamau ina fad'in.'' Ta cutar da ni, ta cutar da yaranmu ta zalince shi, ya yi mata alheri ta saka masa da sharri. Ta gigita mini rayuwata." Kawai sai itama ta fara kuka ta rungume ni a jikinta tana cewa." Ki yi hakuri ki samu nutsuwa mu je can wajenmu ki zauna ki nutsu kin ji ko, ki yi wa mijinki addu'a." Hajja ta fad'o mini a rai. Na sake fashewa da kuka mai gunji! Ta kama ni sosai muka nufi d'an wajenmu a hankali take ta fad'in." Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Na kama ni ma idan ta ajiye na d'auka. Ta zaunar da ni saman tabarma tana cewa Hajara ta d'auko mata mafici. Ta kar'ba ta fara fifita mini har yanzu ba ta cika ni ba domin ni kaina nasan ba a hayyacina nake ba gabana duf-duf kawai yake yi mini daga zarar na yun'kura zan tashi sai ta riko ni. Gabad'aya yaransu da manya sun yi cirko cirko a gaba. Da wani irin sauti na ce." Wayyo Allah anti Yagana kina ina?" Na silale saman tabarmar na kwanta hawaye suka dinga biyo gefan idona. Na riga fa nasan mutumin nan ya mutu kawai a fito a gaya mini ne ba za a yi ba. Na riko hannunta ina sake tambayarta a karo na biyu ta girkiza kanta tana cewa." Na gaya miki fa bai mutu ba Hajiya yana da rai in sha Allahu." Na zuba mata Idona kafin na ce." Wuyansa ya karye ana gane alamun rashin rai a jikin dan adam tana nan fa kada ku yaudare ni." Ta ri'ke ni da kyau a hannunta sai ta dubi yaran tana fad'in." Ku tafi ku yi alwala kowa ya d'auko al'kur'aninsa a yi karatu. Jin haka ya sanya ni k'ara gazgata abinda zuciyata take gaya mini me yasa ba su yi karatun tun d'azu ba sai yanzu k'wa:kwalwata ta dinga gaya mini cewa a gidan mutuwa ne kad'ai ake yin karatun al'kurani. Jakata na d'auka da take ajiye a gefena na d'auko wayata a karo na shida number Hajja na kira ta yi ringing sau biyu a na ukun ta d'aga. Tana magana na yi shiru hannuna yana ta rawa kiran sunana take yi Amina, Amina, bakina ya yi nauyin gaske hawaye ya ziraro daga idona cikin 'karamin sauti na ce." Ya mutu Hajja ta kashe mana Babanmu Hajiya Maryam ta cuce ni......✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book complete 1k akan telegram via 0542382124.... Binta Umar Opey bank* *127* Da tsananin damuwa nake jin ta tana kiran sunana na ajiye wayar ba tare da na kashe ba jikina na rawa sosai na 'kunshe bakina da hannu jin yadda wani mahaukacin kuka ke ko'karin kufce mini. Mahaifiyar Hajara da na ji suna kiranta da Inno ta d'auki wayar tana fad'in. Hajiya halima ce. Daga daya bangaran ita hajjan tana ta fad'in." Ko Baba Sulen ya rasu Amina domin shekaran jiya Kamalu ya ce mini ya je ya duba shi a can asibitin Murtala an kwantar da shi. Amina, Amina kina ji na." Ta ce." Ni ce Inno uwargidan Malam D'aha nan Bunkure." Hajja ta ce." Inno me yake faruwa ne, wanene ya rasu ina Amina take?" Duka ta jero mata wad'an nan tambayoyin. Cikin sigar kwantar da hankali ta ce." Babu wanda ya rasu Hajiya Halima gigitace dai kawai ta sanya har ta gaya miki haka." Ta ce." Inno ki gaya mini gaskiya kin san dai ni ba yarinya ba ce?" Sai ta dabarbarce ta kasa gaya mata komai. Zuciyata ta sake karyewa tabbas bata da abinda za ta fad'a kuma da bakinta take cewa bai mutu ba gashi yanzu an tambayeta ta yi shiru. Ina jin Hajjan tana ta magana Inno ki gaya mini menene, ki bawa Amina wayar mu yi magana na ji ta a kusa dake tana kuka." Ta miko mini wayar jikinta a sanyaye. Na kar'ba nasa a kunnena na ji tana fad'in." Yi shiru ki kwantar da hankalinki Amina ki gaya mini abinda yake faruwa kin ji ko, ki gaya mini ko menene ina sauraranki." Da kyar na daidaita kaina na ce." Muna nan Bunkure ni da Baba amma ban san halin da yake ciki ba yanzu Hajja ki zo don Allah." Ta ce." Yi shiru zamu zo in sha Allahu, yanzu dare ya yi amma da asuba zamu d'auko hanya dukkan tsanani yana tare da sauki." Ban iya cewa komai ba sai jan hanci na ji ta kashe wayar sai ni ma na ajiye tawa na matsa jikin bango na takure can 'kasan zuciyata ina ta ambaton Allah akan ya kawo mana d'auki. Dare ya tsala sosai muna zaune a tsakargidan ni da Inno mu biyu kacal ta yi ta yi da ni na shiga na kwanta na ce mata ta barni ko na kwanta din ba bacci zan yi ba gabad'aya hankalina na sashen malamin shiru ya hana kowa shiga Sukairaju da yan uwansu su Dahuru tunda suka shiga dashi ban sake ganin gilmawarsu a hanyar ba Rabi'u ne ya shiga sau d'aya kafin ya fito ya nufi bangaransa dake cikin gidan bai sake fitowa ba. Muna zaune har aka kira sallar asubahi. Kowa ya fito ya yi alwala yara da manya na yi na shiga d'akin da suka sauke ni a tun farkon zuwanmu gidan na yi sallah ina kuka sosai ina yi wa rayuwarmu addu'a. Karatun al'kurani tun daga almajiransa na waje da cikin gidan iyaye da yaransu. Na kar'bi al'kur'ani wurin Hajara na bude nima ina karantawa a hankali a hankali na ji zuciyata tana sanyi. Gari ya fara haske Hajja suka shigo gidan ita da Hajiya Saratu da kanin mahaifinsa alh Sa'idu. jin maganarsu ya sanya na rufe al'kur'anin da sauri na fito tsakargidan. Inno ta sauke su tare da shimfida musu tabarma suka zauna yanayinsu ya nuna tsantsar tashin hankali a haka suka dinga gaisawa da jama'a. Ba su wani jima da zama ba. Rabi'u ya fito daga wurinsa suka gaisa a gurguje ya nufi sashen malamin minti biyar a tsakani ya fito tare da fad'in." Hajja Malam yana magana." Kusan a tare muka tashi gabad'aya ya shige mana gaba kowanne mu zuciyarsa na dokawa. Yana zaune saman buzu da al'kur'ani warshu mai falle-falle a hannunsa d'akin tsaf Y yana ta k'amshin turaran wuta. Can muka hange shi kan wata katifa madaidaiciya da shimfidar bargo a samanta. Yana kwance sambal sun cire masa rigar jikinsa daga shi sai singileti da dogon wandon rigar da suka cire hannayensa nade a k'irji ido a rufe. Kafafuna suka fara kyarma Hajja kuwa kuka ta sanya tana fad'in." Me ya faru Malam ma'kiyane suka jefe shi ko, Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ta nufe shi tana kuka sosai ta tsaya a kansa tana fad'in." Ni kuwa me ka yi wa jama'a ne Tajo daidai gwargwado kana alheri da kyauta da yawa wasu na ta ganin wautarka akan dukiyar da Allah Ya baka. Ka yi kyautar hajji ka yi ta umara, ka yi kyautar kud'i ka yi ta gida da mota da jari, duk hakan bai yi musu ba sai sun kwantar mini da kai." Shiru d'akin ya yi tana kuka da sambatu Hajiya Saratu na kusa da ni tana goge hawaye ta ma kasa zuwa inda yake kwance. Gabad'aya ta gigice sai kuka take yi na kasan zucciya. Ni kam idona bushewa ya yi k'amas ban yi mamakin hakan ba wata'kila hawayen idona ne ya 'kare sai dai wani kutittiran abu da nake jin sa ya tokare mini a wuya. Da na d'aga kaina na dubi wurin da yake kwance sai gabana ya yanke ya fadi. Alhaji Sa'idu ya tashi a hankali ya je ya kamo hannun Hajja ya zaunar da ita a gaban malamin wanda tunda take koke-koken bai ce komai ba. A nutse ya had'a al'kur'anin da yake hannunsa ya mayar da shi ma'adanarsa ya kalli Hajja da har yanzu ta kasa nutsuwa ya ce." Hajiya Halima kukan ya isa haka, mu godewa Allah da ya takaita lamarin kuma aka samu hanyar warware shi cikin sau'ki. Littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Kamar yadda ki ka sani dai ni malamin zaure ne mai almajiran mai kuma hidima da al'kur'ani. Na ji dad'i sosai da Allah ya tsawaita mini nisan kwana wannan al'amarin ya kasance ya kuma ba ni iko da damar warware shi. Ba ni cutarwa ta hanyar sanin da Ubangiji ya ba ni kamar yadda wasu malaman suka d'auki wannan hanyar ta zalinci domin neman abinci da cutar da hallitar Allah. Hakika a wani zuwa da Alhaji Tajo ya yi gare ni wattanin baya na karanci akwai rikici da makaru a tattare da shi. Wannan dalilin ne ya sanya ni gaya masa cewar ya dage da addu'a akan shi da kuma yaransa idan ban manta ba na tambaye shi iyali da adadin yaransa ya sanar da ni. Na bashi adduoi sosai na kuma yi masa da kaina domin samun mafita da warware wa. jiya suka zo nan da matarsa ya yi mini bayanin dukkanin abinda ya faru bayan rasuwar matarsa Maryam wadda itace musabbabin kwantar da shi tunda aikin da ta sanya aka yi akansa ni kaina ya tsorata ni ba don komai ba sai don ganin irin d'aurin da aka yi masa bayan lokacin da Ubangiji ya d'iba masa bai cika ba. Na jima ina aikin warware asiri iri iri wannan ya ba ni mamaki ya kuma tsoratar da ni k'warai da gaske, kuma an cire tsoron Allah wajen aikata shi. Ya yi shiru yana duban inda yake kwance tare da girgiza kansa tabbacin da gaske abin ya bashi tsoro da mamaki kamar yadda ya fad'a.. Hajja ta ce.'' Ni ai a zatona abokan kasuwanci ne ko wasu da ba sa kaunarsa suka jefe shi tunda kasan yadda duniyar take." Ya girgiza kansa yana cewa iyalinsa ce Hajiya halima kin san ku mata wani lokacin da son kai kuke da kuma mugunta. Ba dai a tara sani da Allah wata'kila ta ji a jikinta za ta riga shi mutuwa ne sai ta yanke shawarar yi masa d'aurin rai da ajali idan ta rasu a cikin biyu ko ya bi bayanta ko kuma ya kwanta kamar dai yadda yake a haka yana numfashi amma bai san a duniya yake ko a lahira ba." Shiru ya ratsa kafin ya cigaba da cewa jiya na kwanta bacci bayan na yi sallar istahara akan lamarin domin kara tabbatarwa Ubangiji Allah Ya nuna mini ita ko ba ita ce 'yar fara mai karamin jiki ba da doguwar fuska?" Hajiya Saratu da sauri ta ce." K'warai itace malam suffarta kenan." Ya gyad'a kansa cikin jajantawa yana fad'in." Rahama sai ta Allah a wajen da take domin irin shirkar da take yi Allah Ya la'ancesu. Ba za mu yanke hukunci kai tsaye a kanta ba amma tunda har son zuciya da mugunta ya sanya ta kafurta kanta ta iya yadda da juya zancen Allah wurin neman biyan buk'atarta tabbas alkawarin Allah baya ta shi." Ya nisa kafin ya cigaba da cewa." Na warware duk d'aurin da ta yi a kansa da yaransa zai tashi da izinin mai buwaya. A yadda ta so shine ko ya tashin ya zama mutumin-mutumin kamar gunki tunda da ayar nan ta (Summunbukkum!) aka yi aiki akansa bayan ita suka had'a (Makisinafiyiabada) ayoyi ne masu zafi wurin dakusar da duk wani karsashin dan adam idan aka juya su ta gefan zalinci. Ita kuma wannan kwalbar ya fad'a yana nuna musu ita ya cigaba da cewa." Kowacce laya akwai sunan mutum guda a ciki. Amina Hauwa Kamalu Yusuf Khalil Hassana Usaina da kuma Minal. Mallaka ce aka yi akan wad'annan sunayen da na zayyano da kuma jefa soyayya a zuk'atansu. Hajja na kuka tace fad'in." To me ya yi mata ni Halimatu na ga da iyalinsa ta same shi. Tsananin abotar da take tsakaninsa da Alhaji Amadu ya sanya da ya rasu ya aureta ni ma na bashi goyon bayan yin hakan tunda ya gaya mini a rubuce aminin nasa ya bar masa wasiyyar yin hakan. Me ya yi mata da zafi irin haka da za ta yi masa wannan mugun asirin." Ya ce." Son shi take ainun kuma macace mai zafin kishi abinda na fahimta kenan." Hajiya Saratu ta ce." Mun gode sosai Malam Ubangiji Allah saka da alheri, yanzu ya yanayin jikin nasa." Ta fad'a tana kallon wajen da yake. Ya ce." A nan za ku bar mini shi daga nan zuwa sati guda zai warware in sha Allahu rabbi zai tashi ya cigaba da gudanar da al'amuransa." Alhaji Sa'idu ya ce." Malam abin nan ya jefe ni a rud'ani ba kad'an ba. Ashe akwai irin wad'annan matan marasa Imani da tsoron Allah wallahi idan ana fad'a ba ni gazgatawa." Ya ce." Akwai su da yawa muna ta fama da su. Ita wannan nata akwai razani k'warai domin tana iya bada jinin adam akan biyan buk'atarta tana aiki da ba'kar iska kuma suna iya neman jinin kowacce irin hallita. Kuma suna nan da yawa. Abinda dai na fahimta ga sha'aninta shine macace mai zafin kishi da mugunta. Kamar yadda na gaya muku da farko ni ba na bugun 'kasa akan neman sanin abinda Allah rufe bai bayyana ba. Istahara irin wadda Annabi ya koyar ita nake a duk dare kan wata mas'ala da aka kawo ta gabana idan na kwanta bacci Allah Ya akan nuna mini abinda yake faruwa. Iya fahimtata soyayyar da take masa ne ya sanya ta aikata masa haka saboda kishin ko bayan ranta kada wata mace ta more shi wannan shine abinda ya halakar da ita har ta k'etare iyakar Ubangiji." Hajja na girgiza kai tana fad'in." Kin yi kyawun dan maciji Maryam kin ci amanar mijinki, kin ci amanarmu da muka so ki muka kaunace ki, kuma duk inda muka zauna muke fad'in alherinki. Kin zalinci Tajo da iyalinsa kin mutu ba ki nemi gafara ba zahiri ba mu yafe miki ba maryam " Tasa gefan mayafi ta goge hawayenta cikin damuwa. Ya ce." Matarsa ta zauna nan har tashon kwanakin dana d'auka in sha Allahu komai zai wuce kamar ba a yi ba." Hajiya Saratu ta ce." To shikkenan Malam yadda ka ce haka za a yi Allah Ya saka da alheri amma za mu dinga zagayowa muna duba shi ko?" Ya ce." Hakan yana da kyau in sha Allahu." Muka fito daga d'akin a tare da d'an sasaauci ba kamar lokacin da muka shiga ba cikin tsananin tashin hankali. Hajja ta fara rigima wai itama sai ta zauna. Da kyar da jibin goshi Alh Sa'idu suka rarrasheta kan cewa ta yi hakuri su tafi idan ya so duk bayan kwanaki biyu sai su dinga zuwa. Sai da suka yi sallar Azhar suka ci abincin suka yi shirin tafiya lokacin malamin ya yi b'aki ba su samu damar yin sallama da shi ba. Tunda ba kasafai ake shiga wurinsa ba sai ya yi izini. Da magriba yarinyar nan Hajara ta sake kawo mini dambu cikin langa tana fad'in.Matar yayansu ce ta ce a kawo mini tunda na jiya ya yi mini dadi. Godiya na yi mata sosai na daure na ci ba don yana yi mini dadi irin na jiya ba sai don korar yunwa. Ba ni son na kwanta ban sake ganinsa ba. Na fito tsakargidan suna zaune iyayen da yaran. Ban san ina su Sukairaju suke ba nasan dai tunda gidan karamci ne za a kula da su. Ina so ya je ya d'an yi mini sayayyar cikin kasuwa ko dogwayen riguna ne na yi na yi na kira Sahura a waya ta'ki shiga ina so na ce mata ta je can gidana ina da kaya ta debo mini sai ta kawo mini ba a samu network mai karfi a gidan sai an fita waje a tsakargidan kuma idan ya hau sai ya sauka haka yake yi. Ina tsaye da waya a hannu Malam Rabi'u ya zo yana gaishe ni na amsa cikin dan jin nauyi domin yanayin yadda yake risina mini na sanya ni jin kuny. Ya tambaye ni ko ina da buk'atar eani na ce masa ina son na yi magana da Sukairaju. Tare muka nufi wajan da aka sauke su. Ya fito ganina a tsaye ya risina na ce." Garin nan babu network mai karfi kasan gidan Sahura ko?'' Ya ce." E, na sani." Na d'an yi shiru ina kallonsa gabad'aya shima baya nutsuwarsa botiran rigarsa duk sun zube idonsa ya yi ja da alamun bai samu bacci ba.. Na ce." Gidana na can kuntau can ta koma da zama." Ya gyad'a kansa yana kallona na ce." Ku je tare da ita can gidana na sharad'a za ta debo mini kaya sai ka kawo mini akwai mukkuli a hannunta." Ya ce." In sha Allahu zan yi wanka yanzu na tafi amma ya jikin oga, mun tambayi Malam Rabi'u ya ce mana da sau'ki ." Na ce." Da sauki alhamdulillahi amma ku taya shi da addu'a domin ita ya fi buk'ata a yanzu." Ya ce." In sha Allahu Hajiya amma a wane hali yake ciki yanzu ya tashi ne muna ta so mu shiga mu duba shi ba a ba mu dama ba ." Na ce." Yana dai kwance har yanzu yadda kuka d'auke shi Sukairaju." Sai ya yi shiru yana kallona cikin damuwa. Na juya ina fad'in.'' idan ka je ka dawo sai ka sanar da ni." Na samu Rabi'u a soro a tsaye na ce." Ko za a yi mini iso wurin Malam zan shiga." Da sauri ya ce. Eh amma yana d'an wani aiki yanzu zuwa an jima idan ya kammala zan sanar da shi sai ki shiga ko" Na ce." To shikkenan na gode sosai. Ciki na shige gabad'aya jikina a sab'ule har in dai Hajiya Maryam ta samu nasarar nakasta mutumin nan ya tashi da wata tawaya ta cuci mutane da yawa wad'anda suka dogara da Allah suka kuma dogara da shi, halin da Sukairaju ya shiga yanzu abin jajantawa ne da tausayawa, to balle kuma yaransa da wad'anda suke makusantansa....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book complete 2k akan telegram normal What'sapp group kuma 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *128* Haka na yi ta zaman jiran ganin Malam Rabi'u ya yi mini izinin shiga d'akin malamin shiru har dare ya yi nisa ban ji daga gare shi ba hakan nan na ha'kura na kwanta a wannan daran ma bacci sai dai b'arawo domin da ya d'auke ni na 'yan mintina zan bud'e ido har dai asubahi ta yi motsin iyalin gidan ya sanya ni tashi na fito da buta cike da ruwa wadda Hajara jiya ta ajiye mini kafin ta je ta kwanta. Na jima saman abin sallah ina jan carbi bacci ya fara shammatata tunda dama shi ba a cin bashinsa. Na ji maganarsa yarinyar tana fad'in." Ina kwana." Na bude idona da sauri tare da shi zaune ashe har na kai ga kwanciya kan daddumar ta ajiye mini dogon kofi na kunu da silbar k'osai a gabana ta juya ta fita minti biyar a tsakani ta dawo da wata langa ta ajiye mini da ruwan pure water guda biyu. Na bude langar dumamen towo ne na masara miyar kuka tana ta k'amshin daddawa da zafinsΓ  nan da nan yawuna ya tsinke na mike na fita. Yaran gidan da alama sun shiga makaranta domin shiru babu hayaniya kamar koyaushe. Inno na bakin tukunya da kwanuka a gabanta ta juyo tana kallona sai ta saki fuskarta tana fad'in." Hajiya kin fito. Na daure sosai ganin yadda matar ke ko'karin ganin lallai sai ta faranta mini da kwantar mini da hankali na ce." Eh ina kwana ya hidima na gode sosai Allah Ya saka da alheri.". Ta amsa cikin dadi tana fadin." Ai na ce Hajara ta kawo miki dumame nasan zai yi miki dadi." Na ce." Sosai ma kuwa wallahi Allah Ya saka da alheri." Ta amsa da Amin ya rabbi." Bakina na wanke na koma d'akin zuciyata cike da zullumi haka na ci towon nasha ruwa d'aya na fito tsakargidan shiru matan gidan na d'akunansu. Can bakin 'kofar fita na nufa na lura wajen akwai network sosai na kira Sahura muka gaisa na ce." Sukairaju ya zo jiya ne?" Ta ce." A a sai yanzu dai ya zo kin ga ina shiryawa wai me yake faruwa ne ya ce mini Yallabai ne bashi da lafiya kuna kauyen Bunkure." Na ce." Sahura abubuwa da yawa sun faru masu muni ba zan iya ba ki labari a waya ba amma ina cikin tashin hankali mai tsanani" Ta ce." Idan babu damuwa zan iya biyo Sukairaju ko Amina wallahi hankalina ya tashi ban san a wane hali ki ke ciki ba." Cikin rauni take maganar. Na ji zuciyata ta yi nauyi lallai Sahura masoyiyace ta hakika duk lokacin da na shiga matsanancin hali takan rasa sukuni tun muna 'yan mata haka muke idan daya ya shiga wani yanayi duk sai mu rasa sukuni." Na daure na ce." Me zai hana ki biyo shi amma bai zama lallai ki samu ganin Yallaban ba tunda ni ma sau daya na ganshi malamin baya bari." A sanyaye ta furta." Zan dai biyo shi Amina domin ganin halin da ki ke ciki idan kuma ina da sa'a sai Allah yasa a bar ni na shiga na duba shi din." Na ce." Shikkenan duk abinda ki ka san zan buk'ata ki kawo mini Sahura zama ya kama ni dole." Ta ce." In sha Allahu." Na kira layin Anti Yagana cikin sa'a ta shiga na sauke ajiyar zuciya ina jiran ta daga na ji maganarta tana kiran sunana na amsa a sanyaye. Ta ce." Ya aka yi Amina ya kuke ya yaran fatan kowa lafiya, ki yi hakuri sosai domin ke nauyi ya hau a yanzu ki yi kokarin ganin kin ri'ke yaran nan na Maryam tsakani da Allah domin ki rabauta da lada." Na ce." In sha Allahu anti Yagana amma akwai matsala fa." Ta ce." Menene kuma?" Shiru na yi domin ban ma san ta yadda za a yi na fara yi mata bayani ba. Ta sake maimaita tambayarta murya na rawa na furta." Maigidan ne ba shi da lafiya anti Yagana ina nan kano wani gari Bunkure ana yi masa magani." A dan tsorace ta furta." mai ya same shi Amina amma tun yaushe me yasa ba ki gaya mini ba?" Na ce." Anti Yagana duk yadda za a yi na yi miki bayani ba za ki fahimta sosai ba tunda a waya ne, abinda zan iya ce miki anan shine matarsa ce da ta rasu ta yi masa asirin rai da rayuwa yanzu haka yana kwance sai dai a kwantar a tayar bai ma san a ina yake ba." Sosai ta ki'dime tana fad'in." Maryam d'in Amina wane irin asiri ne wannan an ya kuwa babu sanya hannun magauta kin san fa ba zai rasa makiya na fili da boye ba don Allah ku daina amincewa da jita jita akan matar nan." Murmushin takaici na yi tare da fad'in." Ba za ki gane ba ne ai anti Yagana kawai idan da hali ki zo sai ki ji komai ba sharri ake yi mata ba wallahi da gaske ne ga zahiri ya bayyana bayan rasuwarta." A sanyaye ta ce." Zan zo in sha Allahu tunda jikin baba Sule babu dadi an ce yana kwance a asibiti sai na duba shi." Na ce." Haka na ji a wajen Hajja ban sani ba wallahi yaushe za ki zo." Ta ce." In sha Allahu cikin satin nan, zan dai kira ki." Na ce." To shikkenan anti Yagana" Sallama muka yi cike da yanayi na damuwa domin abin ya doke ta itama kwarai da gaske. Wajajen daya da minti goma Sahura ta shigo ina d'aki a kwance na yi muryarta suna gaisawa da matan gida yara suna ta gaisheta sannan suka nuna mata d'akin da nake. Ina kwance ban motsa ba ta shigo da k'aramar akwati a hannunta.. Na tashi zaune ina kallonta ta zo ta zauna kusa da ni hankalinta gabad'aya a kaina sai na ga ruwan hawaye ya ciko idonta ta ce." Amina ke ma jinyyar ki ka yi ne?" A tak'aice na ce." Me ki ka gani ne?" "Kin rame sosai wallahi kin yi wani iri?" Ban ce komai ba na zuba mata ido ina kallonta ta goge hawayen da ya d'an zubo ta riko hannuna a sanyaye tana fad'in." Menene yake faruwa don Allah ina Yallabai din Amina na ji tsoron ganinki a hargitse cikin k'unci da damuwa." Na yi ta ko'karin ganin na hana hawayen da yake dannowa zuba amma sai da ya fito ban goge ba na ce." Sahura ashe maganar nan da ki ka gaya mini farkon jin labarin auran Hajiya Maryam a wurin aikinku da gaske ne, ta asirce mini miji ta bi yaranmu daya bayan d'aya ta asirce ko na ce ta tsaface domin haka malamin ya fad'a tsafi take yi." littafin nan na kudi ne Hajiya kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Ta gyad'a kanta cikin al'ajabi tana kallona sannu a hankali na shiga warware mata tun daga farkon lamarin har zuwa yanzu da za a kira da fad'an k'arshe tunda komai ya bayyana. Ta jima shiru cikin tsananin tashin hankali da mamaki kafin ta ce." Anya matar nan mutum ce Amina wane irin zalinci ne wannan. Mutum ta aure shi da iyalinsa da yaransa saboda tsabar mugunta da son zuciya. Wallahi tunda labari ya fasu a wurin aiki nake ta jin ana magana akanta har na gaza ha'kuri na gaya miki amma kin san abinda hana a gazgata gaskiya ne ayyukan da take yi na alheri da suke a bayyane shine dalili da ya sanya da yawa wasu ba su yarda da wancan zargin ba. Wai akan namiji Amina ki ga mace ta yarda ta mutu a matsayin 'yar wuta domin dai Hajiya Maryam babu abinda zai hana Ubangiji bai hukuntata ba idan an yi duba da irin ayyukan zalincin da ta gudanar a lokacin da take raye." Na ce." K'warai kuwa Sahura a raina nake jin idan har mutumin nan bai tashi da lafiyarsa kamar da ba to har na koma ga mahallicina ba zan yafe mata ba zan ta yi mata addu'a har karshen numfashina. Ta ce." Don kin yi hakan ba lefi ba ne Amina ta cuceku wallahi kuma ta cuce mu domin duka hanyar abincinmu tana ga Allah tana hannunsa babu abinda za mu yi masa sai dai addu'a Allah ya saka masa." Hajara ta shigo da tire na silba jera da kwanukan abinci ta ajiye a gabanmu ta fita ta sake shigowa da ruwan pure water a leda ta dube ni tana fad'in." Hajiya ruwan da ki ka ce a dora miki ya yi har na kai miki bandaki." Da kulawa sosai na ce to na gode kwarai Hajara Allah Ya yi miki albarka." Ta juya ta fita da sauri. Na dubi Sahura ina fad'in." Akwai brush a kayan ko?" Da sauri ta ce." E a kwai na tsaya na sayo." Ta fito mini dashi tare da matsa mini abin goge bakin da sabon soso da sabulu na kar'ba na fita Sai da na fara wanke bakina tukkuna na shiga bandakin tsaf da shi cikin tsafta duk da na gargajiya ne ba zaka taba ce wa na had'aka ba ne suna da tsabta da kula sosai kuma sun horar da yaransu aiki da tarbiya." Sai bayan la'asar tukkuna Sahura ta yi shirin tafiya ba tare da ta samun ganin Yallabai din ba Sukairajun dai shine ya mayar da ita bai dawo ba sai bayan ishai. To a washe garin ranar da Sahura ta zo su Hajja suka sake zuwa tun safe haka muka yini tare da su a wannan karon ma ba su samu damar ganinsa ba haka suka hanya suka tafi cike da matsanaciyar damuwa. Kwanaki hud'u yana kwance shi ba mai rai ba shi ba matacce ba numfashi ne kadai ke nuna tabbacin da rai a gangar jikinsa na shiga na gan shi da safe amma ban iya zaman minti biyar a d'akin ba na fito 'kafafuna suna rawa a ranar kuwa yini na yi a kwance abinci bai samu shiga ba sai dai zubar hawaye da k'uncin zucci. Idan har mutuwarsa za ta sassauta masa wannan mawuyancin halin Allah Ya gaggauta yanke hukunci a kansa. Idan na rintse idona sai na dinga ganin kamar a mafarki na dinga tariyo irin rayuwar da muka dinga gudanarwa ni da shi daga lokacin da muka hadu har kaddarar aure ta ratsa tsakaninmu da irin rigingimun da muka dinga yi kamar za mu halaka juna da fushinsa da gabarsa da kuma tausayi da alherinsa sai uwa uba tsananin soyayyar da yake nuna mini. Na dubi zoben azurfan da ya sanya mini a yatsa ina tuna lokacin da ya sanya mini shine sai da ya gama tsokanata da wasa da dariya abu ne mai muhimmanci a gare shi dalili zoben mafiakasari an fi samunsa a hannun shahararrun Malamai yan siyasa masu kudi ko masu mulki azurfa ce ta mussaman a wajensa amma tsananin yadda yake k'aunata ya kama yatsana ya sanya mini shi. Na sa hannu na goge hawayen da suka zubo mini tare da jan hanci Ina tuna yadda muka dinga da k'ullatar juna rikicin da ya kaimu har gaban baban saude ashe akwai abinda Allah ya shirya shiyasa a duk lokacin da na samu ciki yake gaya mini yana so ko da za su kasance masu nakasu. Maryam ta yi wa rayuwata illah Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Nasa hannu tare da rufe bakina jin sautin kukan da nake yi na ko'karin fita. Ina cikin wannan yanayi na 'kunci da neman taimakon Allah na ji muryar Malam Rabi'u ban motsa ba amma hankalina na wajen domin in bayan malamin shine mutum na biyu da yake dawainiya da Yallabai din mahaifiyarsa Inno shi take tambaya halin da ake ciki. Na ji shi cike da annashuwa da kuma murna yana fad'in." Wallahi yanzu nan ya motsa Inno ya kuma fara da sunan Allah, ina alfahari da kasancewar Malam a matsayin mahaifina Ubangiji yakan taimake shi akan duk abinda ya sanya a gaba. Wallahi ban ta'ba tunanin Alhaji Tajuden zai tashi da nutsuwa da hayyacinsa ba Inno idan an yi duba da yanayin yadda muka shigo dashi a lokacin da ya fadi, cikin ikon Allah Ya yi magana har ya kira sunana a cikin hayyacinsa ya kuma sheda cewa a gidan Malam yake.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Gudun aure paid book 2k complete on telegram what'sapp Gruop 1k. via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *129* Da wani irin yanayi na godiyar Allah na tashi zaune na dubi gabas sujjudur-shukur ta godiya ga Allah na yi ina kara jadadda tasbihi a gare shi lallai Ubangiji mai ji ne da gani kuma maji ro'kon bayinsa ne. Na dago da tarin tahamidi a zuciyata inno ta leko fuskarta a washe tana fad'in . Hajiya Amina ko bacci ki ke yi ne alhamdulillahi maigidanki ya tashi yanzu nan wannan yaron yake gaya mini. Jin yadda ta kira shi da wannan yaron ya sanya ni gane cewar d'anta ne na fari. Ina murmushin da ni kaina ban san kalarsa ba dole sai mai kallona ne zai gane wane iri ne na ce." Na ji lokacin da yake yi miki bayani, Ubangiji mun gode maka, Inno Allah Ya karawa malam lafiya rabbi ya saka da alheri." Ta amsa da "Amin Ya Allah yanzu kam ai sai ki ci abinci ki dan fito cikin jama'a ko?" Na ce." In sha Allahu rabbi a kawo mini abincin." Ta saki laluban d'akin da sauri na ji muryarta tana kiran sunan Hajara. Na sake daga hannuna ina fad'in." Allah Ina sake godiya a gare ka, na gode Allah ka karawa Annabi daraja." Hajara ta ajiye kwano biyu na abinci da ruwa. Na bude na farko alala ne da manja da yaji da maggi d'unkule a gefe d'aya kwanon kuma shinkafa da wake ne yana ta k'amshin mangyada. Alalan ne ya ba ni sha'awa tunda harkar manja da yaji ne bakina kuma dama babu wani d'and'ano. Shida ne manya na ci hud'u cikina ya cika sosai na sha ruwa na fito tsakargidan. Yaran sun shiga makarantar dare sai iyayen suna ta hira akwai mutunta juna a tsakaninsu duk kwanakin da na yi a gidan har yanzu na kasa tantacce 'yayan kowacce dalili yaran kansu a hade yake kamar iyayen kuma suna mu'amularsu a kowane d'aki. Cikinsu na zauna muna hira daya daga cikinsu da na ji suna kiranta da Uwa ta fara tsokanata tana fad'in." Kuka yake 'kare Hajiya." Dariya kawai na yi na sunkuyar da kaina kasa ina jin nauyi tare da tuna abinda ya faru a tsakanin kwanakin.. Muna zaune Rabi'u ya shigo da wayoyinsa Yallabai din a hannunsa. Ganina cikin iyayensa ya sanya shi washe baki ya tsaya da kulawa muka gaisa kafin ya ce." Gashi har ya yi wanka Malam ya bashi daya daga cikin tufafinsa ya sanya ya ci abinci ya kuma buk'aci wayoyinsa ." Na ce." Ma sha Allah Ubangiji Allah Ya kara bashi lafiya." Ya nufi wurin malamin a gaggauce na kasa jurewa a hankali na ce." Za a iya sanar da mahaifiyarsa ko?" Ya ce." K'warai kuwa Hajiya." Na tashi na je na d'auko wayata na dawo na zauna. Cikin ikon Allah na samu network na kira layin Hajja ta katse ba a daga ba. Kira na biyu na ji muryar Kamalu ya gaishe ni na amsa ina tambayarsa Hajja ya ce." Tana d'aki a kwance tun safe da suka dawo daga asibiti. Da sauri na ce." Wanene lafiya?" "Itace yau ta tashi da jiri shine Hajiya Saratu ta zo ta d'auketa suka je asibitin Malam Aminu likitanta ya dubata amma dai alhamdulillahi tunda yadda ta fita da kafarta haka ta dawo da k'afafunta ta kuma ta ci abinci tasha magani shine bacci ya kwasheta." littafin nan na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Ajiyar zuciya na sauke da damuwa na ce." To Allah ya sawakke kada ka tasheta yanzu da safe dai kace mata na kira ta.'' Ya ce." To Mama amma ya jikin Baba?'' Na ce." Jiki alhamdulillahi Kamalu yanzu ma kiran da na yi mata kenan domin na gaya mata cewa ya tashi har ya ci abinci ana hira dashi." Ya dinga fad'in." Alhamdulillahi Ubangiji Allah mun gode maka." Na ce." Da safe zan kira in sha Allahu" Daga haka sai na datse kiran na nemi Hajiya Saratu bugun farko ta shiga ta daga na ji muryarta cikin tashin hankali tana fad'in." Amina Allah dai yasa lafiya." A tsanake na ce." Lafiya lau Mamana na kira ne domin na yi miki albashiri." Ina jin lokacin da ta saki ajiyar zuciya a kagauce ta furta." Ya tashi ne?" Na ce." E, wallahi cikin nutsuwa kuma yadda mai dawainiya dashi yake fadi har ya yi wanka ya ci abinci ya kuma buk'aci wayoyinsa." Ta dinga godiya ga Allah ina jinta muryarta har tana rawa take fad'in." Amina wallahi da na ga kiranki da farko sai da gabana ya yanke ya fadi haka kawai sai zuciyata take raya mini za ki ce mini Tajo ya rasu. Yau tun safe na kai Hajja asibiti saboda ta kasa nutsuwa bata bacci ba ta cin abinci hakan ya haddasa mata jiri da ciwon kai kuma kin san tana da hawan jini fadi take yi wai ta san ya rasu b'oye mata ake yi." Na ce." Na kira Kamalu yanzu ai yake yi mini bayani na ce to bari na sanar dake tunda yace bacci take yi." Ta furta." Ai yanzu zan sake komawa gidan in sha Allahu. Amina mun gode sosai lallai mata suna suka tare a gidan Tajo ina yi masa murna ya yi dace da mace tagari mai tausayi da kuma soyayya ta domin Allah. Abinda Maryam ta yi mana kuma mun barta da hasken rana fad'uwarta Ubangiji shi zai yi mana sakayya." Na ce." Amin Mamana, ai babu godiya a tsakaninmu mijina ne kuma shi ma ya yi mini tarin alheran da ba zan iya lissafasu ba ni ya kamata ace na tsaya kan gaba wurin bashi kulawa." Ta dinga fad'in." Hakane wannan Amina hakane." Na dan yi shiru ina jinta da kuma nazarin maganganun da na furta wata zuciyar tana gaya mini kamar na yi mata rashin kunya akan dan uwanta ina cewa ni ya kamata a kan gaba wurin kula dashi bayan suna raye da ita da mahaifiyarsu can kasan zuciyata kuma na gaya mini cewa babu rashin kunya sai tsage gaskiya domin duk cikinsu ke kin fi amfanarsa kuma abokanan rayuwa ne wanda idan babu daya a tsakani dole kowanne ya shiga yanayi na tashin hankali." To a daran duk wanda ya cancanta sai da na kira shi na sanar da shi har Babanmu sai da na gayawa ya ce da ni gobe zai zo ya duba shi tunda nan nan ne bunkure. Aikuwa sammako su Hajja suka buga a gidan Malam ni dai ina bacci na ji maganganunsu na tashi zaune wanda ya yi daidai da shigowar Hajiya Saratu na saki fuska sosai ta shigo tana fad'in." Bacci ki ke yi Amina." Na ce." Wallahi kwashe ni yayi ban yi tsammani ba Mamana ina kwana ya hanya." Ta amsa da kulawa sosai tana dan kallona da murmushi a fuskarta. Hijabina na zura a jikina muka fito tare Hajja ana ta hira da matan malam har da dariya abinda ban taba gani ba duk zuwan da suke yi. Muka gaisa sosai da ita ina ta mamakin ganin yadda ta watstsake har take ta magana haka. Rabi'u ya zo suka gaisa kafin ya ce Malam yana magana." A wannan karon ma tare muka shiga d'akin malamin yana ta k'amshin turaran wuta na tsinke kamar dai koyaushe tsaf ko'ina babu kazanta balle abubuwan da zai nuna malamin matsubbaci ne. Al'kur'anai ne gasu nan a jikin bango a rataye a cikin jaka gefan buzunsa kuwa tarin littafan addini ne masu yawa da irin carbin nan zabgege mai dubu. Yana zaune cikin tsafta da shiga ta Kamala yayin da majinyacin nasa yake can gefe zaune a kan shimfidar da aka yi masa amma sun dan sanya fillo sun tokare bayansa. Yana sanye da wata babbar riga ta shadda wadda take nuna alama ta malamin ce ita kadai ce a jikinsa sai dogon wando don daga cikin rigar ma ana gano fatar jikinsa sai dai fa gilashin nan nasa na bala'i yana idonsa wato komai d'an lafiya ne. Shi ma al'kur'anin ne a hannunsa lokacin da muka shiga har da shi wajan amsa sallamar mu gabad'aya hankalinmu na wajan da yake haka zalika shima idonsa na kanmu na yi kokarin daidaita nutsuwata sosai domin yadda zuciyata take ingizani zuwa wurinsa sai nake ganin hakan ba daidai ba ne kada za'kewata ta yi yawa. Amma zahiri Ubangiji ne kad'an yasan yadda nake jin wani mugun dad'i da k'aruwar sonsa a cikin zuciyata. Tunda muka had'a ido sau daya na yi k'asa da kaina smma na saki fuskata sosai a haka muka gaisa da Malamin na zauna gefan Hajja yayin da nake saurarar maganar da suke yi cikin jin dadin yadda Ubangiji ya sassauta lamarin ya kuma kawo sau'ki cikin dan kankanin lokaci har yana fad'in zuwa gobe ma za mu iya tafiya gida tunda jiki ya yi kyau domin ya cigaba da gudanar al'amuransa." Hajiya Saratu ta nufi wajansa ina jin suna magana ban dai ji komai ba smma yanayinsu gabad'aya ya ba ni tausayi kwarai da gaske kaina a kasa na ga Hajja ta tashi itama ta tafi wajensa. Na kasa tashi har sai da malamin ya ce mini malama Aminatu je ki duba maigidanki." Na yun'kura na tashi da tahamidi domin duk motsin da zan yi a yanzu godiyar Allah ce. Na d'an tsuguna gefan kafafunsa ina fad'in." Baba ya jikin Ubangiji Allah sanya kaffara ce, Allah Ya warware ya kara maka lafiya." Yana kallona ya ce." Amin Amin Ya hayyu ya 'kayyumu." Hira suke yi a tsakaninsu kaina a k'asa ba zato na ga ya kamo hannu na sai na dube shi da sauri muka had'a Ido sai ya saki hannun da sauri yana duban su Hajja to mantawa ya yi da suna wajan oho kuma sun ga ni da ri'ke hannun da sakin da ya yi kamar wanda ya kama wuta. A zuciyata na ajiye hakan da kewa da kuma yadda yake jina a ransa. Da yake kusa da k'afafunsa na zauna sai ya d'an dinga sanya k'afarsa daya yana ta'bo ni idan na kalleshi sai ya yi mini murmushi na d'an janye kad'an ina mamakin abinda yake yi gashi magana suke yi a junansu amma hankalinsa na kaina gabad'aya har sai da suka fahimta ganin hakan ya sanya ni saurin tashi ina fad'in." Hajja sai kun fito." Ta ce." To Amina ai yanzu za mu fito mu tafi gabad'aya domin Uwani tana kan hanya ba ni so ta zo ba ta same ni ba d'azu da wurwuri kafin mu fito ta kira waya tana gaya mini. Na ce." To Allah Ya kawo su lafiya." Kafin na fita sai da na d'an risina gaban malamin tukkuna sannan na fice zuciyata cike da tunanin abinda ya yi wato shi dai mai hali baya fasawa amma in ba haka ba a gaban mahaifiyarka ma ba za ka saurara ba kuma kai da kwana daya kacal da tashinka......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book 1k complete on telegram. Ko kuma arewaa arewa pen* *0542382124...... Binta Umar Opey bank* *07084653262* *130* Wayata na duba lokacin tara da arba'in da biyar na safiya Lallai yadda ya tashi garau din nan yana da kyau ya sanya sabbin kaya gobe idan Allah Ya kaimu da rai da lafiya. Muna harkar huluna da takalma sosai next target dina bude shagon yaduka da shaddodi in sha Allahu amma dai yanzu ya zama lallai a nemi k'wararran tela wanda ya iya d'inki sosai ya yi masa orgent akwai su k'wararru muddin da kudi yanzu za ka ga biyan buk'ata. Koda Hamusu ya d'aga wayar bayanin da nayi masa kenan ya ce in sha Allahu yanzu zai fita zuwa yamma zai kira ni na ce babu matsala. Wanka na yi na shirya sannan na zauna na karya da kunu da wainar gero na ji dad'inta sosai dalili na jima ban ci taba kwanciyar hankali da nutsuwar da na samu ya sanya d'andanon bakina ya d:an dawo har ina jin bambacin sukari da gishiri. Gama karin kummalona ke da wuya su Hajja suka fito da shirin tafiya kafin su tafi din mun d'an jima muna magana tukkuna suka yi sallama da iyalin malamin suka kama hanya suka tafi. Ashe anti Yagana tun jiya da daddare ta zo garin sai da ta kira ni a waya yanzu na sani tana gaya mini sun shirya tsaf yanzu za su taho su uku ita da Babanmu da kuma Ummansu Hadiza. Na ce kawai su bari idan mun dawo sai su zo gidan Hajja tunda nasan lallai nan za mu zauna kafin ya sake warware mu koma abuja. Na yi mata cikakken bayani sosai yadda za ta fahimta tunda Allah ya tashe shi to sau'ki ya zo ga kowa Kamalu ma ya ce mini suna so su zo hana su zuwa na yi na ce su bari gobe za mu dawo gabad'aya. Yinin ranar ana ta shige da fice d'akin malamin yau ya lamuncewa kowa tun daga kan matansa 'ya'yansa duka da surukansa babu wanda bai shiga ya duba shi ba. Da yamma na nemi Sukairaju domin mun yi waya da Hamusu cewa ya gama had'a mini komai saboda na sau'kaka masa tafiya nace ya bari Sukairaju ya zo ya kar'ba tunda shi da mota a hannunsa. Tsakanin k'waryar birnin kano da k'auye bunkure bai zai wuce awa daya da rabi zuwa biyu ba. Misalin biyar na yamma ya kama hanya ya tafi bayan magriba da kad'an ya dawo da sa'kon. Duk abinda na umarci Hamusu ya yi mini yakan yi kokarin yin iyakacin bakin kokarinsa kamar yadda na buk'ata din shadda ce kalar sararin samaniya dakakkiya zanenta irin na manyan mutane dinkin ma fitacce ne da hula zannar bukkar ta karshen tsada da takalmi daidai kafarsa maigidantsaya kamar dai yadda na gaya masa ga yadda nake so. Na ji dad'i sosai bayan isha'i dana nutsu na kira shi a waya ina sake yi masa godiya sai hakan ya bashi dariya da mamaki yana fad'in abinda ya yi bai kai na yi masa wannan godiyar ba nafi karfin haka a wajensa. Na yi murmushi kawai na kashe wayar cikin zuciyata nake fadin lallai da matasan samari irin Hamsu za su zama masu tsoron Allah da Amana da an rage masu zaman banza. Hamusu tun kafin na kai k'arfin haka yake tsaye akan dukiyata ban ta'ba kama shi da zamba cikin aminci ba ko ya danne mini kudi duk shekara muke buga lissafi a fitar da abinda aka zuba a fitar da ribar da aka samu a biya duk wanda yake da hakki hakkinsa. Yanzu da su Kamalu suka koma can al'amarin sai ya kara bunkusa Hamusu na kula da shagon zannuwa da ma'aikatan da suke yi mana d'inki shi kuma Usaini na kula da shagon da muke harkar huluna kala daban daban. Yayin da muka bude sabon shagon sayar da takalma cikin kasuwar kwari wanda Yusi da Saminu suke kula da shi Kamalu kuma hankalinsa ya fi karkata wajan yawon neman sani akan abinda ya shafi da'awa da hadisai Annabi s'aw shikkenan yawon bin malam sunnah yana kuma zuwa legal kwalejin addinin musulunci. Cikin matan gidan na zauna kamar jiyya muna ta hira sosai suna ba ni sha'awa ganin yadda suke gudanar da rayuwarsu a sau'kake ba kuma su zafafa kishi ainun irin na wasu matan k'auyen ba. Kayan suna kusa da ni Malam Rabiu yana shigowa na sanya Hajara ta yi mini magana da shi kafin ya shiga bangaransa ya zo muka gaisa sannan na bashi kayan tare da gaya masa na Yallabai ne. Bai jima ba a wurinsa ba kuwa ya fito da kayan a hannunnsa ya nufi sashen malamin da d'an sauri. A daran ranar na yi bacci sosai irin wanda na kwana biyu ban yi shi ba hakan kuwa baya rasa nasaba da nutsuwar da na samu da asuba da na yi sallah ban koma ba. Gari yana yin haske Hajara ta shigo da abin kari da kuma kayan makarantar boko a jikinta litiinin ce dama muka gaisa ta ce Inno ta dora mini ruwan wanka ita zata tafi makaranta. Na ce ." To na gode sosai Hajara sai dai za mu tafi baki nan kina makaranta ko?" tana murmushi ta ce." Eh shiyasa na shigo mu yi sallama wata'kila kafin na dawo kun tafi Allah ya tsare ya kiyaye hanya." Na amsa da Amin Ya Allah. Har ta juya zata fita na kirata ta dawo na ce." Ajinki nawa ne?'' ta ce." Aji na uku a sakandire." Na gyad'a kaina jakata da take saman katifar dake shimfide a d'akin na d'auka ina da kudi a ciki dubu biyar na mik'a mata ta nok'e wai ba zata kar'ba ba tana dariya ta juya zata fita na tashi da sauri na ri'ke hijabinta jakarta ta makaranta na saka kudin ni ma ina dariya na ce" Ki dinga sayan aya da rake a makaranta na gode sosai kin ji, Allah Ya ba ki miji nagari." Ta amsa da Amin tana jin kunya ta fita da sauri. Sai da na karya tukkuna na yi wanka na shirya tsaf na fita domin gaisawa da matan gidan da kuma bankawana. Malam Rabi'u ya zo yana gaya mini Malam na kira na. Na bi bayansa cikin nutsuwa dama kuma da hijabina a jikina. littafin nan na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Koda na shiga d'akin alamu ya nuna mini tare suka yi karin kummalo da malamin domin kayan karin na gani a gabansu sun gama suna magana. A nutse na zauna gefe d'aya na dubi malamin na gaishe shi ya amsa da kulawa kafin na juya shi ma na gaishe shi muka had'a ido. Sosai ya yi mini kyau cikin kayan ya yi fes dashi kamar sabon ango duk da shi din ma'abocin gayu da tsafta ne amma sai nake ganin yau ya fiye mini koyaushe kyau da kwarjini. Na ce." Baba ina kwana ya jikin." Ya amsa da sauki alhmdullhi." Na janye idona daga kansa don ganin shi bashi da niyyar janye nasa wasu lukutan idan yana yi mini irin wannan kallon nakan ji nauyi da kunya akan kaina balle kuma da mutane a wurin. Cikin nutsuwa ya fara yi mini bayanin rubutu da daurikan magunguΓ±an da suke gabansa. Rubutun cikin wata jarka ne yayin da daurikan maganin ya kasance uku daya asha da zuma kullum da safe daya kuma a tsiyayi rubutun kofi daya a zuba karamin cokali sai ya sha idan zai kwanta. dayan kuma a ruwan wankansa za a zuba duka tsayin sati hud'u. Ya sake d'auko wata madaidaiciyar jarka itama cike da rubutu shi kuma kullum da daddare idan zai kwanta za a shafe masa jikinsa da shi. Sosai ya yi mini bayani ya kuma ce mini na kula kada a tsallake rana d'aya. Godiya da ni dashi muka dinga yi wa malamin har sai da ya dakatar damu yana dubansa ya ce." Har yanzu a matsayin uba nake a wurinka shin ko ka manta ala'ka da dangantakar da take tsakanina da mahaifinka. Godiyata ga Allah da Ya sanya ina raye wannan kaddara ta same ka. Allah Ya lamunce mini da taimakonsa aka samu mafita don haka tsakanina da kai babu godiya Tajuden yadda zan tsaya akan matsalar yarana hakan nan zan tsaya akan matsalar yaran abokan k'uruciyata." Wannan kalaminsa ya kashe mana jiki gabad'aya muka yi sallama da shi muka fito Wannan karon ma ya tsaya tsakiyar tsakargidan kamar wancen lokacin da za mu tafi yana yi wa iyalin malamin sallama. Na shiga d'akin na fito da 'yar akwatina ina fad'in." Mun gode sosai Allah Ya saka da alheri Allah Ya biya ku da aljanna." Gabad'aya suka dinga amsawa suna yi mana fatan alheri kamar koyaushe ya riga ni fita na bi bayansa Inno har bakin soro na farko ta rako ni tana fad'in." Allah Ya tsare ya kuma kiyaye hanya Hajiya Amina." Yaransa suna jikin mota a tsaye sai suka ba ni tausayi ganinsu a jeme kwana biyar da tufafi daya a jikinsu ko sun yi wanka shi suke yi mayarwa abin ya ba ni tausayi ainun. Amma kuma kallo daya za ka yi musu ka ga annashuwa da farinciki a fuskokinsu sai washe baki suke yi suna sallama da Malam Rabi'u da ya biyo bayanmu. Sukairaju ya bud'e masa motar amma bai shiga ba ya tsaya suna magana da Rabi'un ganin haka ya sanya ni shiga na zauna kimanin minti biyar ya shigo da Bismillah a fuskarsa. Ajiyar zuciya na sauke bayan mun hau titi na dan lumshe idona ina ambaton sunan Allah Ubangiji Allah kada ka kara maimaita mini wannan tashin hankalin da shiga. Har muka isa gidan Hajja bai fi sau hud'u muka yi magana ba dalili akwai yaran shi don Sukairaju ma yana daf da shi shiyasa ya kama kansa ya dai gaya mini cewa shi ya hana su Hajja zuwa ayau din ita a yadda ta so su zo sai mu sake juyawa tare. Kawunansa biyu muka samu a gidan Hajja Alhaji Sa'idu da Alhaji Haruna wanda shi baya gari ma al'amuran suka faru sai da ya dawo tukkuna ya samu labari. sai kuma Inna Uwani ita kad'ai ce ban ga Hauwa ba sai 'yar uwarsa Hajiya Saratu. Sun d'an jima tare da shi suna tattauna mas'aloli da yawa kafin su tafi. Shi ma ba su jima da tafiya ba ya tashi yana fad'in zai shiga ya kwanta gidan tunda yana da wajensa na mussaman a gidan wanda ya shirya shi domin yin rayuwa da matarsa ta farko Samira Allah bai kaddara zama ba. Ina Uwani ta kasa yarda mu had'a Ido ban san dalili ba daga zarar na daga kaina ana hira sai ta yi saurin sunkuyar da kanta kasa na dinga tunani akan abinda yasa take yin haka. Har dai abin ya zo yana ba ni dariya babu mamaki tana jin kunyanta ne da tsoron kada na tona mata asiri a wurin yar uwata tunda yanzu an yi walkiyya asirin Hajiya Maryam ya tono to ita kuma tasan na ganta da idona tana yarfa masa ruwan rubutu mai d'auke da magani a hanyar wucewarsa a shekarun baya. Cikin zuciyata nace jininka ma yana yun'kurin cutar da kai ina ga kuma wani daga waje wanda yake karyar so. Ai soyayya ta gaskiya itace ka so mutum tsakani da Allah ka so abinda yake so, ka gaya masa gaskiya a duk lokacin da ya kauce hanya. Ka k'yamaci munanan ayyukan da yake yi kuma ka yi kokarin nuna masa hanyar daidai. Babu wata soyayya ta gaskiya da za ta sanya ka illatar da wanda kake so ta hanyar son rai wannan zalinci ne a so ba cikakkiyar k'auna ba. Muna nan zaune wajan daya da rabi Yusi ya dawo daga makaranta suna da lakca da sassafe ya fita ba don ya so ba. Muna gaisawa yana tambayata ina Baba. Hajja ta ce ya fita harabar gidan Sukairaju zai nuna masa inda yake. Aikuwa ya tashi ya fita da sauri anan ya bar tarkacensa na makaranta ya fita da sauri bai damu da tsokanar da ake yi masa ba. Ni hakan bai ba ni mamaki ba tunda na dade da sanin matsananciyar soyayyar da take tsakaninsu. Shi Kamalu baya ma garin gabad'aya a jiyan da yamma suka tafi Abuja wurin wannan malamin professor Ma'kari. Da yammacin ranar dai ya tura Sukairaju can gidanmu na sharad'a da kayan shi a can ya d'ebo masa duk abinda ya zama lallai zai buk'ata a son ransa mu tafi can mu biyu Hajja ta ce a a mu zauna anan din na tsayi sati tukkuna ko sati biyu idan ya so idan ma abujan za mu koma shikkenan. Ganin haka sanya ni sanar da Sahura tunda ni ma ina da kaya a can ta sake d'ebo mini. Na kira Hamusu na ce masa ya sayi yaduka masu matsakacin kudi kala bibbiyu ya bayar da d'inki Sukairaju da D'ahuru da kuma Ade ya san biyu Ade din ne bai sani ba na ce shi ma ba shi da tsayi sosai Amma dai duk ya fi su ki'ba da kad'an. Na tausaya musu da zama da kaya daya babu dadi kamar akwai cutarwa. A daran ranar na fara ko'karin yi masa amfani da rubutu da magunguΓ±an da malamin ya ba shi tunda ya jadadda mini sosai kuma a gabansa. Babu matsalar zuma ya had'a da ita gangariya ce farar sa'ka wannan da safe ya ce ya sha kafin ya ci komai. Da za mu kwanta ne a lokacin da za a shafa na shafawar a duk jiki na ga shegantaka ya cire jallabiya har da gajeran wandon ya zauna a haka na ce babu kyau kallon tsaraicin mutum ya ce ai yana jin lokacin da malamin ya ce sai babu komai a jikinsa za a shafa rubutun har yana kara jadaddawa ya ce ki shafe mini ko'ina na jikina. Ya kwanta abinsa babu kunya ba tsoron Allah da jin nauyin abinda ya yi. Na jima kaina a sunkuye da rubutun a hannuna. Ba wai shafawar ce matsala ba yadda zan kalle shi a haka shine damuwar na tashi na je na kashe fitila na dawo da lalube na zauna na fara shafa masa a haka a cikin duhun. Bai yi yun'kurin yi mini komai ba har na gama bai kuma yi magana ba a takaice na ce." Na gama.'' Ya lalubi wayarsa ya kunna hasken yana ko'karin tashi zaune na d'auki wandonsa na ciki na bashi ya sanya sannan yasa jallabiyar ya koma ya kwanta. Sai da na yi wanka da alwala tukkuna na kwanta gefansa wanda duk a tunanina bacci yake yi. Ya janyo ni sosai ya rungume tsam. Haka muka kwana bai yi yun'kurin yin wata mu'amula ta aure da ni ba sai dai duk juyi zai sake rike ni a jikinsa ya sanya bakinsa wuyana ya sumbuta da haka har asubahi ta yi muka tashi kusan a tare......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* *Littafin kudi ne akwai complete 2k a Telegram normal What'sapp group kuma 1k akwai a arewa pen domin biyan kudin karatu......0542382124....Binta Umar gtbank* *07084653262* *131* A ranar da muka wayi a gari a gidan Hajja muka dinga kar'bar mutane mabambamta ciki har da su anti Yagana Babanmu da Sahura wadda ta kawo mini kayan dana ce ta d'ebo mini. Babanmu dai bai wani dade sosai ba ya tafi babu yadda ban yi da shi ba akan ya zauna ya huta ya kuma ci abinci sai asa direba ya mayar dashi gida ya ce a a tafiya zai yi ba zai zauna ba. Ina jin dadin yadda yake ko'karin kama mutunci da kuma girmansa ba ya ta'ba yadda ya yi abinda zai zubar mana da mutunci gabad'aya. Yini muka yi tare da su anti Yagana Ummansu Hadiza da Sahura ana ta hirar duniya Ummansu Hadiza dai ta yi shiru kanta a kasa sai dai ta yi d'an murmushi yanayinta gabad'aya babu dad'i zantukan da su anti Yagana suke yi akan Hajiya Maryam da irin zagi da tofin alatsinen da suke yi mata shine ya dan dameta wata'kila tunda itama tana ta'ba harkar bin malaman yasa ta damu tana ganin kamar anti Yagana da gayya take zage-zagen tun muna yara muka tabbatar da hakan yanzu ne da duniya ta juya mata baya ta gane babu sarki sai Allah ta daina, to babu kudin yi ma a yanzu amma ba zan ta'ba mantawa ba ita har zannuwanta take sayarwa ta tafi wajen malami. Sai yamma Garba ya d'auke su a mota domin mayar da su gida ina jin anti Yagana tana gayawa Hajja za ta sake dawowa kafin ta tafi domin da Hajjan cewa ta yi wai su zauna su kwana. To ita Sahura da mijinta duk da har yanzu ba wai sun shirya ba ne ta dai koma amma a yadda take ba mu labari ta'ki sakin jiknta da shi har yanzu kuma shi bai fasa shirye-shiryen auransa ba da ya rage wata biyu a daura tunda budurwa ce yarinyar da zai aura. Shine fa take gaya mata cewa za ta dawo kafin ta tafi wanda ni nasan ta fadi hakane kawai amma ba dawowar za ta yi ba. Kwananmu hud'u a gidan Hajja mutumin ya warware sosai ya ma fara fita yana duba ma'aikutunsa nan yana kuma yin baki a kai-akai. Ranar da muka cika sati daya a gidan Hajja da sassafe ya tafi bunkure bayan la'asar ya dawo sai da ya yi wanka ya ci abinci tukkuna yake gaya mini wai an bashi sa'ko ya kawo mini. Na ce sakon menene ya ce bai sani ba yana mota wata yarinya ce wai Hajara dariya na yi ina fad'in." Ai k'awa na samu a gidan. Ya gyad'a kansa bai ce komai ba. Can kuma ya ce gobe za mu tafi Abuja Amina hankalina na kan yara. Na d'an yi shiru Ina kallonsa mun yi waya da Kamalu shekaran jiya tunda yana garin tare da ayarin abokansa masu neman da'awa. Ya ce mini ya je gidan domin duba yaran suna nan lafiya lau har Hauwa ta ba shi turare. Mamaki na yi sosai Hauwa ta koma kenan amma ba ni tsammanin iyayen sun sani da shi mai gayya da aikin da ko maganarta ma baya yi. Kenan idan tana gidan a ganina yaran ba za su yi kad'aici ba fad'in haka daga wajensa ya tabbatar mini da cewa bai san cewa ta koma ba. Yadda bai san lokacin da ta tafi ba haka zalika ta koma bata gaya masa ba ya makomar auran na su take ni dai har yanzu daga wajensa ban ji wata tartibiyar magana ba. Amma na tabbatar da cewa ba zata koma ba tare da sanin mahaifiyarta ba. Na ce masa hakan ya yi ni ma hankalina yana kan yaran yanzu duk da nasan ba su da wata matsala dalilin samun k'wararriyar mai raino. Tun bayan tashinsa yau sati daya kenan bai ta'ba neman yin sunna da ni ba sai dai yakan rungumeni ya tatta'ba abinda yake so a jikina har mu yi bacci a wanda ni kuma hakan ya kan jefa ni yanayi na damuwa da buk'ata dalili sha'awata takan motsa sosai na shiga wani yanayi na gigita. Ban ta'ba kawo cewa matsala ba ce sanin da na yi masa gwarzo ne sosai a wannan gefen jajurtacce ne wanda duk fitinar mace yakan k'ureta. Sai a yau da muka lula cikin shau'kin da muka kwana biyu ba mu riski kanmu ba a ciki ba. Sosai muka kai k'oli a lokacin ya yi ta ko'karin ganin mun yi kamar yadda muke yi amma abin ya ci tura ya fara da k'umaji da karsashi amma kash jim kad'an jikinsa ya mutu ya gaza tab'uka komai na yi iyakacin yina domin ganin mun cigaba da nemawa kanmu mafita amma hakan bai samu ba k'arshe ma kirif mirginawa ya yi ya kwanta gefena ya kama bacci abinda bai ta'ba faruwa ba kenan. Na tashi zaune tare da sanya rigata ina kallonsa gabana na faduwa. Me yake Shirin fad'uwa kuma. Tarihin rayuwata dashi babu ranar da ya ta'ba gaza mini a shimfida duk yadda nake ji da fitina ya fi ni, koyaushe ma cikin kirkiro abubuwa yake yi wanda yake jefe ni d'imauta da shau'ki. Kasa ha'kuri na yi sai da na tashe shi ya tsarkake jikinsa tunda ka'idarmu ce ni da shi ba ma kwanciya sai da tsarki. Da safe duk yadda ya so ya danne damuwarsa sai da fuskarsa ta nuna abin shima bai yi masa dad'i ba. Na yi ta nazari akan abinda ya faru a jiyan shin asirin ne bai sake shi ba ko kuwa wata sabuwar matsalar ce ta kunno mana. Da rana da kaina na bashi abinci a baki da yake towon shinkafa miyar taushe ne idan na gutsiro nasa masa baki sai ya had'a da yatsuna ya tsotse a haka ya rikita ni sosai ina daurewa har sai da yanayina ya canza gabad'aya kwanciyar nan tasa ta sanya shi k'aro fitintinu fannin romance. Amma kuma kamar wanda aka dasa wa tsoron yin auratayya da ni. Haka muka ciyar da juna abincin kamar sababbin amare muna ta soyayya muka sake hawa gado nan ma abinda ya faru jiya da daddare ya sake kasancewa. Da mazantakar sosai irin ta d'a namiji yake dumfarata amma jim kad'an da farawa sai ya yi realizing jikinsa ya mutu! Gudun aure littafin kudi ne Hajiya kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Ni dai kamar zan yi dan k'aramin hauka na fashe da kuka ina kallonsa a kwance gabad'aya hankali ya tashi ban ta'ba cikin da ya sanya ni masifar son jima'i ba tun yana karaminsa sai wannan. Ya tashi ya kamo ni ya riga ya gane akan abinda nake yi wa kuka na kasa daurewa domin abin sabo ya zo mini abinda nake ci na ture amma yanzu ana dan sammi ni kad'an wanda yake tayar mini da kwad'ayina. Ya fara kici-kicin ko'karin sake jarrabawa babu ma mazantakar kamar ta farko ban kuma ji abin yaje can har inda ya cancanta ba. Hawayen takaici ya dinga ziraro mini ta gefen ido. Ya gama jagwalgwalani babu biyan buk'ata ya sauka shima kamar ya d'ora hannu aka ya kurma iho ya shiga bandaki. Na tashi zaune rungume da bargo a jikina na kasa danne kukan yin sa nake yi tukuru domin gabad'aya jikina ya riga ya nuna ga abinda yake buk'ata kuma bai samu ba. Ina da sha'awa daidai misali amma abin ya kara tu'azzara sakamakon cikin da nake d'auke dashi wanda shi bai ma san da shi ba. Ya fito ya same ni a haka ya sanya kayansa ina zaune yana fad'in."Kin ga halin da na tsinci kaina a ciki ko Amina." Na dube shi ina jan hanci ban ji haushinsa ba sanin da na yi ai da ba haka yake yi ba tabbas akwai matsala ko asirin ne har yanzu bai gama rabuwa da shi ko kuma dai wata matsala daban. Na ce." Kai me kake tunani da hakan?" Ya d'an yi jim kafin ya furta." Jiya zuwan da na yi bunkure yana da ala'ka da hakan Amina aikin da Maryam ta yi wata'kila har da wanda zai hana ni mazantaka da gamsar da iyalina wace irin masifa ce wannan Amina? Maryam ba sona take yi ba wannan mugunta ce." Ya kΓ rasa maganar kamar zai rushe da kuka har da 'yar kwalla a idonsa. Na ce." To yanzu me malamin ya ce? Ya gyad'a kansa yana fad'in." Zan cigaba da amfani da magunguΓ±an da ya had'a mini da farko ai yau kwana takwas kenan kuma na sati biyu ne idan na kammala ya ce sai na yi magana da shi domin tabbatar masa da cigaban da aka samu. Amina na fi ki shiga tashin hankali domin ban shirya rabuwa dake ba" Ya riko hannuna ya matse sosai yana fad'in." Ko mu k'ara jarrabawa yanzu?" Da sauri na girgiza kaina na ce." A a mu bari ka gama amfani da maganin da rubutun sai mu sake gwadawa amma ka daina maganar rabuwa ba zan iya ba ni ma." Ya d'an rungomo kafadata yana fad'in." Ji bi kukan da ki ke yi fa Amina nasan wacece ke tsakanin jiya da yau ke kadai ki ka san halin da kike ciki tun d'azu da muna cin abinci na fahimci damuwarki." Na sanya hannu da sauri na goge kumatuna ina fad'in." Ka daina fad'in haka ni ba wannan ne damuwata ba yadda abubuwa suke ta faruwa da rayuwarka shine abinda ya fi daga mini hankali." Ya yi murmushi yana cewa." Kin fadi hakane kawai Amina ko da wannan to ba shine musabbabin sanya ki kuka tuk'uru ba. Idan ba kya samun gamsuwa da ni ai akwai cutarwa ko?" Yafad'a cikin rauni wanda ban ta'ba ganinsa a ciki ba. Hawaye ya sake ciko mini ido na ce." A a fa na gaya maka ba haka ba ne." Shiru kawai ya yi bai ce komai ba yana dai ta murza hannuna da ya rike. Na dago na dube shi a tsanake ina fad'in." Wannan matar ba sonka take yi ba idan har haka aka so to Allah ya wadaransa ba zan yafe mata ba." Ya ce." Idan ta karya karsashina na d'a miji za mu tsaya a gaban Allah da ita Amina wallahi tallahi ba zan yafe mata ba ni ma." Ya fad'a da masifar damuwa. Cikin wannan yanayin kira ya shigo wayarsa ya cika ni ya tashi. Ni ma na d'auki rigata na sanya na nufi toilet na ji yana fad'in.'' E, gobe nake so na tafi Abuja a alhamdulillahi fa jiki da sauki wallahi, amma tunda ka ce za ka zo za mu jira ka in sha Allahu." Na shige na je na tsarkake kaina ina fitowa yake gaya mini da Baban Saude suka gama waya yana tafe. Na ce." Ka gaya masa baka da lafiya ne?" Ya ce." Ya kira wayoyina lokacin da nake kwance a bunkure Bai same ni ba sai shekaran jiya ya sake kira yake gaya mini yana ta neman wayata bata shiga har taki ma ya kira bata tafiya a lokacin na ce masa na kwanta jinyya ne wallahi, ya yi fad'a sosai wai da mutuwa na yi ashe sai dai ya ji labari ba za a gaya masa ba.'' Na ce." Gidan malamin fa akwai matsalar network sosai ni kaina sai na yi da gaske wataran nake samun damar kiran waya amma idan ya zo sai a ba shi ha'kuri ko?" Ya ce." Haka za a yi domin wannan Baban namu rigimamme ne, koda yake ai ya fara tsufa ba za a rasa shi da rikici ba." 'Dan hararsa na yi na ce." Zan kuwa gaya masa idan ya zo to dame kwado ya fi gaya kaima ai ka fara tsufan Baba." Yana dariya ya ce." Ke ma haka malama kin tsufa kawai gaya miki ne da ban yi ba." Ta'be bakina na yi ina cewa." To menene a ciki tsufa dole ne fa kowa ya tsufa kuma darasi ne." Ya gyad'a kansa tare da janyo hannuna na zauna a gefensa ya ce." Ina kallon ki a matsayin matata har a cikin aljanna. Abokiyata makusanciyata da babu wani shamaki a tsakaninmu Amina me ki ke ganin ya cancanta da Malam 'Daha umara dai na bashi shi da Rabi'u in sha Allahu da azimin nan da za mu shiga amma bayan wannan ina so na yi masa alheri wanda zai nuna masa cewar na yi alfahari da taimakon da ya yi mini a ganina kudi sun yi kad'an wajan biyansa wannan hidimar." Shiru na yi Ina nazari lallai Malam D'aha ya cancanta da ayi masa komai dalilin namijin ko'karin da ya yi har yanzu ma yana kan yi. Na ce." Ka sanya a rushe gidansa tsaf tunda na ga na kasa ne ginin da a zamanantar dashi a gyara masa tsangarsa sannan ka samawa wasu daga cikin yaransa maza aikin yi ko da a karkashinka ne duk da zaman da muka yi a gidan na fahimci ba su da yunwa dalili duka yaransu suna fita gona amma yana da kyau a ce sun fito cikin gari sun waye sun dan yi karatun zamani da hurd'a da jama'a da kasuwanci." Ya dinga gyada kansa yana saurarena har na gama maganata ya ce." Haka za a yi my love shawarar nan taki ta yi mini sosai za a yi duk yadda ki ka ce in sha.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t 🌲🌳🌿☘️ *TALLAH!* *DA MAGANI A GONAR YARO!!* *08089965176* *07084653262* *Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.* *Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.* *07084653262 ko* *08089965176* *SIYAN NAGARI!!!!!!* *A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH* Masu buk'atar a tallata musu hajarsu kofa a bud'e take za a yi akan farashi mai sau'ki in sha Allahu rabbi *Gudun aure paid book ne 2k complete on Telegram normal What'sapp group kuma 1k ko AREWAPEN via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *132* Baban Saude dai lokacin da ya ji abinda matar da yake yabawa ko'kari da bajintarta ta fannin kula da miji har ma yana bada misali da ita tare da jaddada goyon bayansa akan abinda a gaya masa a kanta sai da ya ki'dime sosai. Mutum ne shi jarumi jajurtacce wanda ko rasuwa aka yi bata gigita shi ainun domin ko lokacin da Mamanmu ta rasu ya nuna jarumta da dakiya a cikin 'yan uwanta ko yanzu a ka tashi zancenta yana tsawatarwa da masu yi mata kuka cewa ba daidai ba ne sai ga shi jin irin mugayen ayyukan da maccen da yake misali da ita tare da ko'karin tabbatar mata da aljanna ta aikata ya yi shiru yana zare ido har abin ya so ya ba ni dariya na danne ban yi ba. Da farkon da abokin nasa ya fara bashi labarin ya dinga dakatar da shi yana nuna babu yadda za a yi ta aikata haka tunda shi kansa ya sheda soyayyar da take masa a ganinsa babu dalilin da zai sanya so ya sanya ka nakasta wanda kake so. Ganin yadda yake rantse masa da girman Allah da buwayarsa ya sanya jikinsa saduda ya yi tsuru kawai yana sauraran bayanin da yake yi masa da yadda ya ci tsananin wahala kafin ya samu kansa a yanzu da yake zaune suna magana. Ya jima yana girgiza kai da tu'ajibi da mamaki kafin ya bud'e bakinsa yana fad'in an yi shed'aniya amma mai suffar munafukai tana sunkuyar da kai kamar mutuniyar arziki ashe macijiya ce mai mugun dafi Allah Ubangiji ya saka muku da mu kanmu da ta jefe cikin zullumi da tashin hankali da damuwa. Da k'yar da jibin goshi ya yarda ya kwana a gidan Hajja a cewarsa zai je ya kama hotel idan ya duba Baba Sule a asibiti sai ya d'auki hanya da sassafe tunda jibi zai komai bakin sana'arsa. Da 'kyar ya lalla'be shi ya amince. Da daddare gabad'aya har da ni muka je asibitin domin duba jikin Baban Sule kamar dai yadda ya fad'a. Alhamdulillahi jikinsa da sauki wai ashe basir ne yake damunsa irin mai daure cikin nan. Ya yi tsiro kuma yana fitar da jini sai da aka yi aiki duk ya rame kuwa ya zabge kamar ba Baba Sule ba Sunusi babban d'an sa shine yake jinyarsa. Na tausaya masa sosai kuma ban san haka ciwo ya ci karfinsa ba duk da ba ni cikin hayyacina amma ina da hakki a sanar mini domin na bada taimakona asibitin gwamnati ne amma dole ai za a sayi magani shi kuma bashi da k'arfi asalin ubangidansa Alhaji Muntari ne kuma ya rasu don ma yaransa maza sun tashi sune suke ta dawainiya da shi da taimakon Babanmu tunda alhamdulillahi yanzu shine yake da rufin asirin da ba su dashi tun farkon samun d'aukakata dana bude masa shagon huluna yake cigaba da gudanar da kasuwancinsa. Bacci yake yi har muka gama zamanmu a d'akin da yake bai farka ba da za mu tafi Baban Saude ya bawa Sunisu dubu goma ya ce a sayi magani shi kuma Yallabai din ya ce zuwa gobe zai ga sa'ko. Jin haka ya sanya ni kar'bar lambar wayar Sunusin da ta asusun ajiyarsa nasan lallai tunda ya fadi haka zai buk'aci da na bashi details din da zai saka kudin. Duk da dare ne ashe da yawa wasu sun ankara da shigowarsa asibitin muna fitowa kuwa jama'a suka rufe shi ni da Baban Saude muka ja gefe muna kallon ikon Allah uwar zuma kenan ki tashi a biki idan har za ka bayar to babu shakka za ka ga tarin masoya da yawa. Sukairaju da yake bayansa ganin abin ya yi yawa ya sanya ya fara ko'karin korar mutane muka nufi mota suka biyo mu har da mata masu zaman jinyya. Mota muka shiga gabad'aya har da shi ya bude ma'ajiyar kudinsa ya fito da kudi da d'an yawa ya mik'awa Sukairaju wani dattijo ya bawa daga ciki ya ce su kasftaa. Ya zo ya shiga motar da saurin gaske domin ganin jama'a na sake k'aruwa a wajan. Baban Saude tun a mota yake tsokanarsa wai zai yi kyau da siyasa ya nemi kujera gwaman Kano. Ya dinga dariya yana fad'in abinda bai taba sha'awa ba kenan siyasa ya yarda dai ya yi gwagwarmayar ta neman kudi a ko'ina ya tara ta hanyar halak amma mafiakasari 'yan siyasar nan da suka ci suka tada kai suna bushasha da dukiyar jama'a suna mutuwa da nauyin al'umma a kan su. B'angaran ba'ki na cikin gidan Hajja ya sanya Sukairaju ya gyarawa Baban Saude ya kwana anan da sassafe kuwa ya kira shi a waya yana fad'in shifa ya shirya. Ba shiri muka fito harabar gidan ni da shi sai a lokacin ma muka gaisa aka yi aka yi dashi ya jira aka kawo masa abin kari ya ce a a. Sai da ya yi masa dubara kan cewa yana da kyau ya yi wa Hajja sallama kafin ya tafi sannan ya yarda muka shiga ciki a tare anan Hajja ta sanya aka kawo masa abinci funkaso da miya da kuma kayan shayi ya sha ruwan shayin babu madara sannan na zuba masa funkason manya guda biyar zan zuba miya ya ce na cire biyu na bar masa uku ya isa. Na yi yadda ya ce din ya sake sosai da Hajja ana hira da shi har aka ta shi labarin abinda ya faru ya kara jadadda mata mamakin da ya yi da aka ce masa Hajiya Maryam mashirika ce duk nagartar da ta nuna masa a farkon ganinta da shi bai taba tsammanin haka daga gare ta ba. To bayan tafiyar Baban Saude da kad'an ni ina tare da su Hajja a falo muna hira har da ita inna Uwanin shi kuma ya bi bayan Baban Saude amma bai dawo ba. Littafin kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Na ji maganar Hajja cikin nutsuwa tana kiran sunana. Na amsa tare da mayar da hankalina gare ta ta ce. "Amina." Na ce." Naam Hajja." Ta ce." Hauwa ta koma dakinta tun Tajo yana bunkure a kwance." Na d'an saki fuskata ban nuna mata cewa na sani ba na ce." Ma sha Allah Hajja ai haka ya fi Allah ya kiyaye gaba." Ta amsa da Amin Ya Allah. Ta cigaba da cewa ita da mahaifiyarta suka buk'aci hakan ga ta a zaune hakane Uwani?" Ta amsa "Hakane Hajja." Sa ta cigaba da cewa." Hauwa a cewarta tana jin kunyarku ke da Tajo bisa abinda ta yi na rashin kyautawa a baya ta yi nadama ta kuma gane ba daidai ba ne. Ta ji labarin ibtila'in da ya samu mijinku shine ta ce tunda ke kina tare dashi kina jinyarsa ita sai ta koma ta kula da yaran. Jin hakan ya sanya na bada goyon baya domin yaran za su samu kulawa sosai kuma za su ji dad'i akan ace suna tare da masu aiki." Falon ya yi shiru ina sauraran ta cigaba da magana domin nasan ba ta gama ba. Can kasan zuciyata kuma ina mamakin ta hanyar da suka b'ullo wato dama mafaka suke so su samu tunda ta fara gane kuranta tana bibiyarsa yana shareta da ya kwanta ciwo kuma ta tabbatar ina tare da shi ta san yara sun dawo hannuna sai ta lallaba ta koma ta fake da cewa za ta kula da yara da haka suka tsara Hajja har ta amince take kuma ganin sun kyauta sun yi tunani mai kyau. Babu wata sha'kuwa tsakanin Hauwa da yara har na cikinta domin ba da ita suka rayu ba abinda yake tsakaninsu tsawa ce da hantara wataran har da duka. Khalil dai yana shan rank'washi ko ta kwashe fuskarsa da mari na gani kusan sau biyu. To balle Minal ma da bata son zuwa wajenta. A ganina babu wata mafificiyar kulawar da za su samu a wajenta baya ga ta Mairo da Taburni tunda da su suka saba kuma duk wata nau'in kulawa suna samu a tare da su. Ta cigaba da cewa." A wani zuwa da Tajo ya yi nan farkon rikicinsu ya ce mini ya mayar da ita kusan wata hud'u kenan har yanzu tana a matsayin matarsa a yadda na sani dai ban san kuma shi abinda yake zuciyarsa ba sai ya shigo sai na tambaye shi." Ta Nisa kafin ta cigaba da cewa." Shekaran jiya mun jima da ita a waya sosai na ja mata kunne kada na ji kada na gani ba ni son wata matsala ta sake faruwa idan ta shure maganata zan cire hannuna a kanta kuma zan bawa Tajo za'bi zama da ita ko rabuwa." Inna Uwani ta yi k'asa da kanta cikin damuwa Amma ba tofa ba. Na ce." In sha Allahu ma babu abinda zai sake faruwa Hajja, ni da ma tsakanina da Hauwa ai girmamawa ce wallahi kuma na ji dadin wannan sulhu wanda da tun farko ta yi aiki da shawarata hakan ba za ta faru ba, ina yi musu fatan alheri." Ta ce." Ba wai ina goyon bayan Tajo ba Uwani ki zauna ki yi nazari da tsinkaye anan Hauwa ta yi daidai na yi shiru ne kawai ba wai don abin bai yi mini ciwo ba. Ban isa na bata umarni ta bi ba na sha gaya masu daga ita har abokiyar zamanta a duk lokacin da suka samu sa'bani da magidansu su sanar da ni, amma saboda ta raina kowa ta haihu da d'anyen jego ta tafi ke kuma ki ka bata wajan kwana har kina aiko mini da sa'ko iyayen Hauwa sun ce a ba su takarda domin su ga sheda." Inna Uwani tasa kuka tana fad'in." Hajja ni kaina Hauwa taurin kanta ya ishe ni wallahi nasan bata kyauta ba kuma b'acin rai ne ya sanya na fadi haka abinda ya kara dagula mini lissafi yadda ta ce mini yana dukanta kuma ya mayar da ita koma baya a gidansa har hakkinta na aure baya bata shine hankalina ya tashi." Hajja ta harareta tana fad'in." Baya bata hakkinta na aure a ina ta samu wannan cikin da ta haife wad'ancan yaran biyu Khalil da Minal a ina ta same su?" Inna Uwani ta yi shiru tana jan hanci tare da goge ragowar hawayen idonta. Ta gyad'a kanta tana fad'in. "Ai ban 'ki komawar ba domin ban san abinda Allah ya lullube ba, shiyasa tun da farkon faruwar lamarin na tura shi can bauchin domin a samu sasanci ba ni da niyyar raba uwa da yaranta tunda ni ma babu wanda ya yi mini haka. Nasan soyayyar da take tsakanin iyaye da yaransu me yasa na yi masa fad'a sosai a lokacin da ya kwashe musu yara ya kaiwa Hajiya Maryam. Ba daidai ba ne amma dole a wannan ga'bar mu yi masa uzuri tunda ba a hayyacinsa yake ba har yaran gabad'aya nasan yanzu ko giyar wake ya sha ba zai k'ara yarda ya d'auki d'ansa da'ya ya kai wani wajen ba sai dai idan ya zama dole." Ta girgiza kanta tana fad'in." Hakane wannan hakane." Ta ce." Ki ja mata kunne kwarai idan za ta ji tunda ta fi karfin ki ba tun yau ba na fahimci haka wannan ya zama na farko ya zama na k'arshe ta zauna ta kula da yaranta." Ta ce." Ai tun a gida na yi mata fad'a sosai Hajja ai abinda ya fi alheri shine ta koma cikin yaranta domin duk wanda zai rike maka yara ba kamar uwa ba." Hajja ba ta ce mata komai ba ta juyo gare ni tana fad'in." Ya gaya mini cewa gobe za ku tafi hakan ya yi ba zan dakatar da shi ba domin nasan yana da hurd'odi da yawa. Ki yi hakuri ki 'kara akan wanda ki ke yi Amina ni dai babu abinda zan yi domin na saka miki alherin da ki ka yi mini sai da na ce Allah Ya yi miki albarka ya albarkaci zuri'arki ya sa su zama abin koyi da kwatance a duniya." Na ce." Wannan addu'ar ita kad'ai ta isa Hajja ai ban yi domin a gode mini ba ni ma kaina na yi wa kuma in sha Allahu ni dai daga bangarena zan yi iyakacin bakin kokarina wurin ganin mun samu zaman lafiya da juna." Ta saki fuskarta sosai tana fad'in." Na gode sosai Amina Allah Ya yi miki albarka na gode." To a daran ranar ta kira shi ya je ya same ta nasan dai ba zai wuce maganar da za ta yi masa ba kenan. Ko da ya dawo ya same ni tare da Yusi muna bankawana ban ga wani can ji a fuskarsa ba ya zauna cikinmu ana hirar da shi har yana tsokanar Yusi ya zama saurayi ko yana da budurwa ne shima. Abinda ya assasawa yaron tashi ya fita kenan yana sinne kai shi kuma sai dariya yake masa yana fad'in." Ta'b wa ya ga su wa'e da suruka humm tsufa ya zo garinsu wata mata." Na gane da ni yake na share shi ban tanka masa ba ya cigaba da cewa ni kuwa kin ga ko yanzu zan iya auran budurwa ba ni da matsala. Ban kula shi ba na tashi na shige band'aki ina murmushi wani sa'in idan yana barkwacin har mamaki yake ba ni. A wannan daran kafin mu kwanta ya kar'bi details din Sunusi dubu dari da hamsin ya sanya masa ni kuma na sa hamsin a kai ya zama dubu dari biyu ta What'sapp na yi masa magana na ce ya duba sako an tura masa. Ya kuwa kira ni a waya ya yi ta godiya kamar zai ari baki. To duk yadda na kai ga nok'ewa a wannan daran kasawa na yi domin ha'din kai na bashi zuciyata na dokawa muka jima cikin wassanin soyayya ya yi kokari kwarai ta wannan hanyar ya samar mini da nutsuwa kafin ya nemi hanyar biyan tashi buk'atar cikin k'ankanin lokaci yana farawa ya kammala. Akwai sha'awar sosai da mazantakar amma karfin da za a jima ana yi ne babu wannan kuwa babbar matsala ce. Da sassafe muka d'auki hanyar abuja bayan duka mun yi sallama da wad'anda suka dace....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *GUDUN AURE PAID BOOK 1K ON TALGRAM KO KU GARZAYA AREWA PEN.* *0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *133* Yadda yaran suka dinga tsalle da murnar ganin Babansu haka ni ma suka yi mini kamar dama can akwai tsananin sabo a tsakanina da su. Minal dama can 'yar gidana ce kai tsaye wajena ta taho da dan gudunta tana tsalle da dariya na kuwa sunkuya na sunkuceta duk nauyinta ni ma ina dariyar murnar ganinsu tsaf cikin annashuwa. twins kuwa dama wajan Babansu suka nufa ya rirri'ke hannayensu shima fuskarsa kamar gonar addu'a Allah ne kad'an yasan yadda yake ji a cikin ransa ganin ya dawo cikin ktoshin lafiya domin cigaba da rayuwa da su. uwa uba kuma samun iyayen rainon da suke tsananin kula da su tamkar suna rayuwa da iyayensu. Yarinyar ta dabaibayeni sosai ta sa'kalo wuyana da hannayenta tana ta dariya duk acikin farincikin ganin mun dawo. Ina nishi sosai gajiyar tafiya da yanayin jikina ga kuma nauyinta na fara ko'karin sauketa k'asa ina kallonsu Mairo da suke tsaye suna ta dΓ riya na ce." Minal ta kara girma da nauyi a 'yan kwanakin nan Mairo me kike bata?'' Cike da kulawa ta sinne kai ta furta. " AbiΓ±ci take ci ta k'oshi Hajiya bayan haka babu komai tunda ita dama can ba gwanar ciye ciye ba ce." Shiru na yi ban ce komai ba na sauke yarinyar a k'asa tana riko gefan hijabina ina jin Mairo da Taburni suna yi masa sannu da zuwa. Baba Tabawa ta fito daga cikin fuskarta a washe take fad'in." Sannunku da zuwa Alhaji sannuku da dawowa." Ya tsaya suka gaisa sosai kafin ya kama hanyar samansa yaran suka bi shi a baya Khalil da twins ita Minal tana tare da ni ta ri'ke mini hannu tamau. Muna magana da Mairo Hauwa ta fito daga d'aki muka kalli juna babu yabo babu fallasa ta furta." Kun dawo kenan?" A tak'aice na ce." E, mun same ku lafiya?'' Ta amsa da 'Kalau.' Ta nemi kujera ta zauna na d'an dubeta ta gefan ido ta k'ara ramewa abinka da mara jiki dama ai zaman gida sai dole ta so ta yi wa kanta ganganci. Ta yi kwalliya sosai wata'kila ta tar'bar angon nata ne naga har da lalle ja da ba'ki irin wanda yake so ya yi kyau sosai a farar fatar 'kafafu da hannayenta. Na kama hanyar d'akina jikina a galabace Minal tana take mini bayana. Ban yi wanka ba tukkuna sai da na yi sallar magriba na fito na sami yarinyar ta bingire a gado bacci ya d'auketa. Ba ta yi wani murnar ganin uban ba kamar sauran sau daya ta je wajensa ya d'an ri'ke ta kamar yadda ya yi wa sauran ta dawo wurina. Kamar yadda twins din suka yi mini. Sai da na shirya tukkuna na tashe ta muka fita a tare babu kowa a falon. Kai tsaye d'akin ya yaran na nufa Mairo tana ta fama da su Khali na can gefe yana rubutu a littafi. Ta burni kuma tana gyara musu wardrobe. Na ce." Mairo a bawa Minal abinci." Da sauri ta ce." To ta janyo hannunta zuwa ciki. Usai ta biyo bayana muka zaune kujera a tare jim kad'an itama Hassanar ta fito na daga kai na dube su a nutse tare da fad'in." Kun yi sallah ko?" Suka daga mini kai a tare na ce." AbiΓ±ci fa?'' Girgiza kansu suka yi. Na d'an 'bata fuska ina fad'in.'' Bebaye ne ku?'' Usai ta ce." Menene Bebaye Mama?" Sai na fara gwada mata maganar kurame da hannuna da bakina." Aikuwa sai dariya gabad'ayansu suna kallon bakina yadda nake yi. Ni ma na kama dariyar ina fad'in." Bebaye ne masu magana da hannu da kuma gyada kai, ku kam ai kuna da baki ko?" Da sauri Hassana ta ce." E, wanda muke magana da shi muna cin abinci." Na ce." K'warai kuwa daga yau idan na yi muku magana ku daina yi mini ta kurame ku bude baki ku ba ni amsa." Suka ce "to Mama." Na ce." Aje a ci abinci idan da aikin gida na makaranta a d'auko a yi." Suka ce "To" a tare da sauri suka ruke hannun juna. Na sauke ajiyar zuciya tare da fad'in." Hassana duba d'akina ki d'auko mini wayata saman gado." A tare suka nufi d'akin jim kad'an suka fito na kar'bi wayar suke wuce dakinsu. Ina dubawa na ga miss call Hamusu ya kira ni jim kad'an da fitowa daga d'akin. Na kira shi bugun farko ya daga muka gaisa yana fad'in." Anti Amina Gwaggo tana ta fad'a wai ba ki sanar da ita cewa Yallabai bashi da lafiya ba. Yau a gidan Hajja ta yini ta sanya ni na kaita muka je muka tarar kun tafi." Na ce." Wallahi Hamusu ku yi mini uzuri ka bawa Gwaggo hakuri ko kuma idan ka je gidan sai ka kira ni a waya abubuwan ne sai a hankali amma ka ce mata ya ji sau'ki sosai ya warware." Ya furta." In sha Allahu rabbi." Muna yin sallama na hangi Hauwa na saukowa daga benansa. Na yi gaggawar janye idona daga hanyar har ta sauko ta iso tsakiyar falon na daga kaina na kalleta duk yadda take ko'karin kalato annashuwa ta ya'ba a fuskarta sai da na gane karfin hali ne kawai ta kira sunana na amsa za ta shiga d'akinta na ce." Ni kuwa akawai maganin maigidan da ake yi masa kullum da daddare Hauwa bari na d'auko miki shi zai yi miki bayani yadda ake yi masa." Ta ce." To tare da tsayawa na tashi na shiga d'akina na d'auko mata sauran maganin da ya yi ragowa da rubutun ina fad'in zai gaya miki yadda za a yi." Ta sake cewa ." To." Kamar mai koyon magana ta kar'ba ta shige d'akinta. Baba Tabawa ta fito da Sultan a hannunta ya yi wayo sosai yana ta furzar da yawu alamun hak'ori na kar'be shi Ina dariya tare da cewa" Yaro ya sake wayo duka bai fi sati biyu ba rabona da ku amma kowa ya canza mini a gidan na ji dadin ganinku cikin koshin lafiya." Ta zaune tana fad'in." Alhamdulillahi kam sai godiyar Allah." 'Daga shi sama na yi na cafe ya dinga b'angala baki yana d'igo mini da yawu a fuska. Baba na murmushi ta ce." Ai ya yi wa uwarsa yankan k'auna a gidan nan Hajiya wallahi kamar al'amara ko wanda aka rad'awa a kunne koda ta dawo ya ga 'bakuwar fuska idan ya kalleta sai ya tsalla ihu duk ya sheda fuskokinmu amma ban da tata 'kiri-'kiri ya'ki yarda ta d'auke shi, da ta tsananta a washe garin ranar da ta dawo don kuka sai da ya kusan shid'iwa ya yini yana baccin wahala daga lokacin tace kada a kara fitowa falo da shi falo. Idan kuma ana canza uwa sai ya canza. Wai ta ji haushin abinda ya yi mata." Murmushi kawai na yi ina d'an cire hannunsa da yake janyo mini d'ankunne a takaice na ce." A hankali zai saba da ita dama ai mussaman yaro mai 'kuiya yake." Ba na so maganar ta yi tsayi a tsakaninmu don ban san abinda za ta haifar ba. Nan falon na zauna na ci abinci muka yi hira ta yaushe gamo da Baba Tabawa wajan yara da arba'in Hauwa tun da ta shiga d'aki bata fito ba shima maigidan tunda ya sauko wajejan Isha'i ya fita bai shigo ba har na yi sallama da Baba ba shige d'aki. Isha'i na yi kawai na sanya kayan bacci na kwanta amma raina gabad'aya babu dad'i ba na son wannan matsalar ta su ta shafi lafiyarsa Malam D'aha ya jadadda mini cewa kada a tsallake rana d'aya wajan aiki da abinda ya bayar. Ban hangi wani sasanci da d'okin juna a tsakaninsu ba. Hauwa ta kar'bi maganin ne kawai domin kada ta nuna mini akwai matsala tunda abinda na karanta kenan a fuskarta amma ai ni ba yarinya ba ce tun saukowarta na karanci tsananin damuwa da tashin hankali. Yadda na yi wa Hajja alkawarin kawo zaman lafiya a tsakaninmu hakan ne ya sanya ni bata damarta a matsayinta na wadda ta yi kome gidan mijinta dole ita zata shiga turaka idan magana ta gaskiya za a yi. Na d'auki wayata domin kiransa. Ko da ta shiga bai yi jinkirin d'agawa ba. Na ce." Allah Ya taimake zan ce dama sai da safe domin na yi ta jiran ka shigo mu yi magana shiru ragowar maganinka na wajen Malam D'aha na bawa Hauwa na ce sai ka yi mata bayanin yadda ake yi maka ko?" Ya ce." Akan wane dalili Amina?'' Shiru na d'an yi ina mamakin maganarsa. Dalili saboda matarsa ce ya yarda ta dawo su cigaba da rayuwa an yi musu sulhu iyaye sun shiga yanzu zaman aure za mu yi babu cin amanar juna da zalintar wani. Ya sake maimaita maganarsa da b'acin uana fad'in." Sai ki je ki kar'bo mini maganina idan ba za ki zo ki yi yadda ki ke yi kullum ba ki kawo mini na yi abina." A dan daburce na ce." Ai ba da gangan na'ki zuwa ba sanin da na yi cewa dole ne itama a bata damarta hakkinta ne kuma..... Ya katse ni "Ni na ce ta dawo?" Shiru na yi ina sauraransa. Ya cigaba da cewa." Ki je ki ce ta baki magani na ki kawo mini ina da lafiya Allah ya hore mini ba ni da nakasa a hannu zan gudanar da komai." A tak'aice na ce." Gaskiya ba zan iya ba ai na riga na bata." Ya datse wayar ba tare da ya sake magana ba. Na kashe na nemi gado na kwanta ina fad'in" Ban da rigima ai da tun a can sai ka gayawa mahaifiyar taka baka amince ba, haba a yi ta abu daya sai kace 'kananun yara." Jin yawu ya d'an ciko bakina ya sanya ni tashi na bud'e dirowa nan na sanya ledar da Hajara ta aiko mini da ita na ji dad'i sosai kuwa tun a gidan Hajja dana bud'e na gani magarya da kurna taura da aduwa har da tsamiyar biri irin kayan motsa baki na gargajiya. Aduwa na d'iba na zauna gefan gado ina tsotsa a tsanake ina duba wayata What'sapp na shiga na ga sa'kon Nusaiba ya shigo voice note ko da na bude sai na ji muryarta har tana rawa tana gaishe tana fad'in ta zo gidan ba na nan har sau biyu zuwanta na k'arshe Hauwa ta ce kada ta 'kara zuwa domin ita najasa ce da mahaifiyarsu. Voice na biyu kuwa kuka take yi tukuru tana fad'in. Anti Amina don Allah kada kema ki k'yamace mu don Allah kada lefin da mahaifiyarmu ta yi ya shafe mu wallahi tallahi ba mu ta'ba sanin abinda take aikatawa ba kenan, ta rasu ta dasa mana tsangwama da k'yama a wajan mutane ba mu da lefi kada ke ma ki tsane mu antina......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure littafin kudi ne complete 1k akan telegram via 0542382124.... Binta Umar gtbank* *07084653262* *134* Ina tsaka da mamakin abinda Hauwa ta aikata ya shigo dakin ransa a 'bace ganin haka ya sanya ni daidaita yanayin fuskata. Fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba duk akan na d'auki magani na bawa Hauwa kamar zai mangareni da duka. Na yi shiru kawai ina jinsa ban tanka masa ba ya gama da fad'in na tashi na je na kar'bo masa maganinsa. Nan fa d'aya na ce ba zan je ba na nemi waje na kwanta raina gabad'aya a b'ace wai shin yaushe za mu samu zaman lafiya ne a gidan nan. Ni a ganina abinda na yi shine daidai da adalci ban d'auka cewa zai zama lefi tunda ai shima yana son lafiyarsa Me yasa ya amsawa mahaifiyarsa ya san bai shirya cigaba da zama da ita ba. Ba ni so daidai da kwayar zarra hakkinta ya kama ni. A yanayinta dai sulhu da sasanci take nema tunda har ta iya yin ado da kwalliya dominsa ta kuma bi shi dakinsa to ai sai ya yi hakuri ya yafe tunda zahiri shi ma yana yi mana lefin kuma ha'kuri yake yi da ita. Ina kallonsa ya shiga toilet dina ya yi uzurinsa ya fito d'aure da alwala ya zauna saman dadduma ya bude Al'kur'ani mai girma yana karantawa daga tsakiya suratul-kahfi sai da ya kammala ya rufe al'kur'anin bai nade daddumar ba ya kwanta a samanta tare da takurewa kamar wani maraya. Na tashi zaune ina duban bayansa da mamakin abinda ya yi akan ya yi wa Hauwa magana ko ya kwana d'aki daya da ita gwara ya kwanta a kasa bisa dadduma wace irin zuciya ce wannan ta riko da gaba mai tsanani. Ina ta yi masa magana ya yi mini shiru kuma idonsa biyu tunda ina ganin haske wayarsa yana dubawa. Na sauko daga gadon hijabina na sanya na bude d'akin na fita dole na kar'bo maganin na shafa masa tunda na lura shi akan hakan sai dai duk abinda zai faru ya faru ga lafiyarsa amma ba zai kwanar mini a d'aki ba balle ta fahimci haka ta ji haushi ko ta zarge ni. Na bubbuga kofar d'akin nata ta zo ta bude mini ta yi sabon wanka cikin kayan bacci tana kamshi na ce." Maganin nan za ki ba ni." Sai ta yi kasa'ke tana kallona cikin nazari na yi kasa da kaina ina jinta tana fad'in." Yanzu nan fa na gama shiri zuwa saman ya dawo ne?'' A tak'aice na ce." E, shine ya ce a bashi." Ta juya jikinta a sanyaye ta d'auko mini na kar'ba na ja mata kofar. A zaune na same shi yana waya ya gama ya koma ya kwanta bai dube ni ba. Na daura tare da furta." Ga maganin na kar'bo." Ya yi mini shiru bai ce komai ba. Shiru d'akin ya d'auka kusan minti goma sha biyar ba shi da niyyar tashi ya d'auki maganinsa ya fita. Na ce." Ni fa wallahi ba zan yadda da wannan rayuwar ba. Ba zan ta'ba amincewa na zalinci wata ba mu yi maganar gaskiya a tsakaninmu kada ka so zuciyarka akan duk abubuwa da suka faru Hauwa matarka ce kuma 'yar uwarka ni kuma na dauketa abokiyar zamana tunda ka ce na kar'bo maka maganinka gashi ka tashi ka tafi wajenka ta sameka a can shi yafi alheri." Uffan bai ce mini ba sai ya mika hannu ma ya d'auko fillo daya daga cikin wad'anda suke jere a saman gadona ya gyara kwanciyarsa. raina ya b'aci sosai na kwanta jikina a sanyaye ina kallon bayansa da tarin mamakin abinda yake yi. Ni dai anan ban ga lefin da na yi ba kuma da zai tsiri jin haushina. Damuwa ta cunkushe mini da fargaba domin yadda ya yi zuciya da kallon inda nake haka yake so ya yi wa lafiyarsa mugunta. Kaina ya fara sarawa tsabar takaici na rintse idona domin kirkiro bacci amma nasan ba zai ta'ba zuwa ba. Can na fara jin saukar numfashinsa alamar bacci ya d'auke shi. Na tashi zaune da sauri da mamaki da gaske yake yi Na zuro 'kafata kasa ina le'ka fuskarsa bacci yake sosai kuma cikin kwanciyar hankali. Na tashi na je na d'auko kayan maganin na zauna kusa da shi tare da d'an bubbuga fillon da yake kwance ya bud'e Ido yana kallona da yanayin bacci. Na ce." Ka tashi na shafa maka." Ya tashi kamar yadda na umarce shi da kansa ya cire kayan jikinsa. Ban ce komai ba na fara shafa masa yana ta bina da kallo har na gama bai yi magana ba ya mayar da rigarsa da wandonsa na ciki ya koma ya kwanta. A haka muka kwana a d'akin kai da gindi. Sai da asuba ya fita bai kuma kula ni ba. Na kasance cikin mamaki sosai shikkenan daga gyara kayanka Allah Ya sawwa'ke. A haka kwana biyun da Hauwa ya kamata ta yi da shi suka shud'e a banza ba ma ya yarda ya kwanta a dakinsa balle ta biyo shi sai ya taho nawa ya kwanta kuma ba zai mini magana sai dai idan na gaji na yi masa idan na zo na shafa masa maganin sannan yake amsa mini amma bai ri'ke mini hannu ba balle ya ce zai nemi wani abu. ranar da na kar'bi girki da yamma na shiga kicin domin hada masa fruit-salad kamar yadda ya buk'ata. Baba Tabawa da Taburni suna ta hidimar abinda za a ci daddare. Muka gaisa kafin na ji maganar Baba tana fad'in. " Ban da abinki Taburni ai ba ita ta d'auke ki aiki ba to me zai sanya ki damu da abinda ta ce don Allah ki yi hakuri me yasa za a yi ta maimaita magana d'aya." Na ce." Menene kuma?'' Murmushi ta yi tana fad'in." Ita da Hajiya Hauwa da alama jininsu bai hadu ba tun bayan dawowarta kafin ku dawo ke da maigidan su ka d'an yi sa'insa abin dai babu arziki da b'angaran Hajiya Hauwa kamar yadda ki ka san halinta na cin mutunci wallahi har da zagi wai zamansu ba shi da amfani mun had'u har da ni munafurcin banza. daga lokacin ko Taburni ta gaisheta ba ta amsaw.........." To me zai sanya ni amsawa Tabawa" Muryar Hauwa ta katse maganar Baba Tabawa gabad'aya muka juya muna kallonta. Ni mamaki ne ma ya kama ni yadda yau ta kira Tabawa kai tsaye babu ma Baba dukkaninsu dattijai ne cikinsu babu wadda ba ta haife mu ba ai rashi ba hauka ba ne don suna masu aiki sai su zama wulakantattu." Ta shigo kicin din sosai tana fad'in." Baba Tabawa tunda Amina ta dawo ki 'kara kuzarin gulma da munafurci yanzu don Allah ba ki ji nauyi da kunya ba da girmanki da shekarunki? saboda ni ba ni da kudi ba na baki toshiyar hanci shiyasa ba ki d'auke ni a matsayin matar gida ba. Matsiyaciyar matar can wadda ta yi mutuwar wulakanci tun tana raye kike maula da yi mata fadanci kada ki ce na manta duk abinda zai faru ba ki ta'ba goyon bayana ba Amina da Maryam sune mutane tunda suna sinna miki. To a shirye na dawo na gaya miki kowane sakarai da sha'kiyyi zan daidaita masa zama wallahi na kuma fad'a Mairo da Taburni sai kun bar gidan nan domin duk wani abu da ya danganci matsafiyar matar can najasa ne ba za ku hana mala'ikun rahama shigo mana gida ba." Baba Tabawa duk yadda ta kai ga daurewa sai da ta fashe da kuka ta sanya tafin hannunta ta 'kunshe bakinta hawaye share-share a kumatunta. Tunda na d'auki baiwar Allah nan aiki tsayin shekaru kusan biyar tsakanina da ita alheri ne da kyautatawa da wasa da dariya amma yau Hauwa ta dubi tsabar idonta tana kiranta da munafukai shakiyya sakarai. Taburni ta jingina a jikin wardrobe din kicin din tare da sunkuyar da kanta. Bakincikin da nake ciki ya sake hauhawa ai na d'auka ta yi sanyi ta dawo ne domin ta gyara kuskuran da ta yi mu zauna lafiya ashe ba haka ba ne a zuciyarta da wani shirin ta zo. Na dube ta sosai ina fad'in." A matsayinki na wa za ki sanya su barin gidan ko ke ce ki ka d'auke su aiki ki ke biyansu?" Ta gyad'a kanta tana cewa." A matsayina na matar gida kamar yadda ki ke matar gida ko da bambanci ne a tsakaninmu." Na ce." Da bambanci kwarai da gaske Hauwa Ina so na gaya miki ki gyara kalamanki akan wad'an nan dattijan Annabi Muhammadu s.a.w ya ce ka girmama furfura ko ta wacece ke yanzu don Allah ba ki ji kunyar duban tsabar idon Baba Tabawa kin gaya mata wannan maganganun ba." Ta ta'be baki tana fad'in." Ita ba ta ji kunyar abinda take yi ba ai munafukar tsohuwa ce." Na buga mata tsawa sosai ina fad'in." Wallahi tallahi Hauwa za mu yi ta dake gidan nan akan wad'an nan da suke tsaye na gaya miki." Ta girgiza kanta tana fad'in.'' Na ji duka to Amina na ce ki rufe ni da duka." Na ja tsaki kawai ban sake wata magana ba na juya bangaransu ina ba su ha'kuri zuwa lokacin itama Taburni kukan take yi tana fad'in." Shiyasa na ce fa tafiya zan yi cikin iyalina na yi abinda na yi Hajiya Amina ba na so a kaskantani ki yi hakuri ni ba ki yi mini komai ba amma don girman Allah ki sanya a mayar da ni k'auyenmu. Na ji 'kwalla ta ciko kwarmin idona na dubi Baba Tabawa da take goye da Sultan a bayanta yana ta bacci idonta duk ya kumbura tsabar kukan da ta jima ba ta yi irinsa ba. Na gyad'a kaina in banda rashin mutuncin Hauwa matar da ta rungumi d'anki da ki ka dangwarar ki ka tafi take yi masa wahala itace abar zagi da aibatawa. Lallai da gaskiyar Hajja Hauwa ba ta da kunya yau na sake gasgazatawa tunda ita duk girma da shekarun mutum furfurasa ba ta hana ta yi masa diban albarka. Da kyar na iya had'a fruit-salad din ina yi ina basu baki Hauwa ba su kadai ta ci mutunci ba har da ni da maigidan gabad'aya ta tsinka. Na had'a masa abinci tsaf tunda lokacin su ma sun kammala na kai samansa na jere inda yake zama. Na yi wanka da sallar magriba na shirya na zauna kaina ya kulle gabad'aya na rasa ta yadda za a yi na fara yi masa bayanin abin nan da yake faruwa wanda na tabbatar da cewar wani sabon tashin hankalin ne zai sake faruwa a tsakaninsu tunda haushinta yake ji dama. Ya kira ni a waya na tashi na je na same shi ya sake sosai ya daina gabar yana ba ni labarin Bashir kanin marigayiya cewa an yanke masa hukuncin zaman gidan kaso na shekara goma sha biyar tare da horo mai tsanani babu kuma biyan tare tunda dama tsohon mai lefi ne nemansa ake yi ruwa a jallo dilan wiwi da 'kwaya ne ga 'yan sace-sace yana ta'bawa. Jin sa kawai nake yi hankalina baya kansa amma dai na yi kokarin aro jarumta ban bari ya fahimci cewa akwai rikici ba. Da asuba yana fita salla na sauka kasa. Kai tsaye d'akin yaran na leka tare suke da Mairo dama har ta yi musu wanka tana shiryasu da kayan makaranta. Khalil da yake ya girma shi da kansa yake shiryawa. Muka gaisa da su na wuce wajansu Baba Tabawa na same su suna dambarwa Taburni ta had'a kan kayanta ta 'kulle a d'ankwali tamau wai tafiya za ta yi rarrashinta ya hana Baba Tabawa shiga kicin kamar dai koyaushe. Ganin da gaske take ya sanya hankalina ya tashi ba ni son rabuwa da matar gabad'aya ita kuma yadda ta yi fushi koda an bar ta tafi garin nasu ba lallai ta dawo ba. Gabad'aya muka fito fallo na yi na yi da ita ta yi hakuri ta'ki Mairo da yaran gabad'aya duka suka fito aka yi cirko-cirko. Minal ganin Taburnin tana kuka sai itama ta fashe da kuka da kar'fi don da alama hayaniyar da ake yi da kukan da suke yi su biyu ya tsorata kukan ta ya yi daidai da lokacin da ya shigo ya fara fadin." Lafiya a d'an ki'dime yana kallona domin neman karin bayani." A tak'aice na ce." Taburni ce za ta tafi." Ya sunkuya ya d'auki Minal din yana rarrashinta da yanayi na damuwa ya furta.'' Taburni ke da na ce miki muna buk'atar zama tare dake yara sun yi sabo daku yanzu ki duba ki ga yadda Minal ke kuka ganin kina yi, ki yi hakuri ki zauna tare da mu duk abinda ya kamata na kulawa za a yi miki daidai gwargwado." Ta sa gefan mayafinta tana fad'in." Dole ce ta sanya ni tafiya Alhji amma ni ma ina son zama daku." Ya ce." To shikkenan ki gaya mini me aka yi nasan lallai ruwa baya tsami banza." Shiru falon ya d'auka babu wanda ya yi magana. Sai da ya sake maimaita maganarsa tukkuna a sanyaye ta furta." Amaryaka da ta dawo ita ce bata buk'atar zamana a gidan." A dan daburce ya ce." wace amaryar tawa kuma Taburni?" Ta yi shiru tana jan hanci. Can kuma da ya gane Hauwa take nufi sai ya ja tsaki bai ce komai ba ya nufi dakinta da d'an karfi ya buga kofar d'akin ta yi magana ya ce." Bud'e malama." Minti biyu ta bud'e ta fito da yanayi na bacci a idonta wato duk wannan dambarwar da take faruwa a gidan ita baccinta ma take yi. Na tausaya mata k'warai da aniya yadda ya fara yi mata tijara da kausasan kalamai wanda ke nu ni da cewa ya fi buk'atar zaman Taburni a gidan a kan zamanta idan ba za ta iya zama ba hanya a bud'e take ta 'kara gaba. Ta muzanta ainun domin ya yi bala'in tsinkata ya kuma nuna mata cewa masu aikinsa sun fiye masa ita tsit! falon ya d'auka na yi 'kasa da kaina ina jajanta mata ina kuma jin wani iri a raina yanzu me ya fi wannan takaici. Babu abinda ya fi zaman lafiya dad'i a gidan aure Hauwa da za ta d'auki shawara sam tashin hankali bai kar'be ta ba bata ta cin riba ko kad'an sai fad'uwa a gigice da borin kunya ta nufi dakinta tana kuka mai cin rai......✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK 1K ON TALGRAM VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK.* *07084653262* *V-VIP AREWAPEN* *135* Ya wuce mu ya hau samansa da tsananin 'bacin rai a fuskarsa wannan ya sake nuna mini cewa dama kiris yake jira da ita a gidan don dai haka siddan ba zai yi mata rashin mutunci ba ne sai da dalili amma yanzu da ya samu mafaka ya yi da hujja! ita aka yi wa amma ni nake jin kunya da nauyi wai hausawa suka ce sandar da ta daki uwargida da ita ake dukan amarya. A ranar kuwa yini ya yi yana 'kuncin rai tabbacin ta gama 'kona masa rai da kuma damuwoyin mas'aloli masu yawa a tare da shi har ni da nake ta ko'karin sasanta al'amarin haushina yake ji. Hakan ya sanya ni rabuwa da shi na sauko na yi kwanciyata a d'akina gidan ya kasance shiru tunda ranar makaranta ce yara tun safe idan sun tafi sai yamma likis za su dawo. Da k'yar dai muka rarrashi Taburni ta janye k'udirinta ta ha'kura da tafiyar har suka shiga kicin da Baba Tabawa a tare. Sai da daddare tukkuna wajan sha d'aya na yi shirin kwanciya na sake komawa saman. Na same shi zaune kan dadduma yana ta karatun al'kurani abincin da na jere masa bana tsammanin ya ci. Sai da ya kammala tukkuna ya juyo yana kallona muka had'a Ido. Ya d'auke kansa yana fad'in." Zuba mini abinci kad'an amma." Ban ce komai ba na tashi na isa wurin abincin kamar yadda ya buk'ata shinkafa ce da taliya da miyar kifi masu girma. Ya zo ya zauna da babbar wayarsa a hannu ya d'auki flat din abincin ya tallafe a hannunsa kamar yadda yake yi wasu lukutan ya fara da Bismillah sai da ya kusa cinyewa ya ajiye flat din ban ce komai na sanya a hannu cikin abincin na fara gyara masa kifin da bai ci ba duk da manya ne marasa k'aya amma dai ba a rasata ko yaya ne. Ya ci kifin sosai don da alama ya fi bukatarsa a kan nama idan shine ba zai yi masa irin wannan cin ba. Na tsinci maganarsa yana fad'in.'' Amina Hauwa tana ganin tana da wani matsayi mai girma a gidan nan ko?' Na yi shiru ban ce komai ba domin ni gabad'aya ma al'amarinsu ya ishe ni. Ya cigaba da cewa." Yara da suka ratsa tsakani na da ita ne kadai suke ri'ke da ita amma wallahi zan fad'a miki gaskiya ba ni son na bud'e idona na ganta cikin gidan nan nawa sai dole akan wad'an nan dabi'un da ta fara za ta sake fita domin ba ni had'a kowa da masu aikin nan mussaman Mairo da Taburni ina ganin 'kima da mutuncinsu duk wanda zai tsaya tsayin daka akan abinka ai masoyi ne." Na ce." K'warai kuwa amma ita Baba Tabawa saboda ni na kawo ta bata da muhimmanci da zamanta da babu a gidan duk daya ne a wajenka ko." Ya dube ni yana fad'in." Ban ce ba Amina ai ban ware ba har da ita na ke nufi." Ya mutsa fuskata na yi ban ce komai ba. Ya gama cikin kifin na tattara kayan abincin na sauka da su k'asa na wanko hannuna tsaf na sake komawa saman na same shi zaune a wajen bai tashi ba. Na dube shi sosai ina fad'in" Yau bacci ne a idona sosai za a shafa maganin yanzu ko sai na kwanta." Ya lumshe idonsa tare da bud'e su a kaina yana fad'in.'' E, amma mu dan yi wani abu kafin wannan ." Na gane abinda yake nufi na dan 'bata fuskata kadan ban shirya kwanan tashin hankali da damuwa da kewa ba domin dai tsakani da Allah duk yadda yake ko'karin ganin ya samar mini da nutsuwa ba ta gamsar da ni ha'kuri nake yi kawai sai nake ganin idan bai ta'ba ni ya tsokano ni ba hankalina zai fi kwanciya. Cikin rarrashi da kwantar da kai har sai da ya ba ni tausayi ya samu ya hillace ni a daran muka yi soyayya sosai ya samu biyan buk'atarta kwarai daga nawa bangaran kuwa abin sai a hankali har sai da na yi kukan b'akinciki a toilet anya rayuwa za ta tafi a haka kuwa gashi maganin da malamin nan ya bayar ya kusa k'arewa saura na kwana biyu kacal babu wani canji. Sai da na yi kwana uku ban sanya Hauwa a idona ba tana d'aki a kwance na fi tunanin sai ta ji sahu ya d'auke take fitowa ta yi abinda za ta yi a kicin din ta dibi abinda take so ta koma. Ai dole kunya ma yanzu ta fara har in dai ba za ta daidaita tunaninta ba ta zauna lafiya da kowa. Kuma har yanzu duk ranar girkinta wajena yake kwana idan na shafa masa magani sai ya yi kwanciyarsa idan ina yi masa nasiha da rarrashi kamar da kurma nake magana sai ya juya mini baya kawai sai na zubawa sarautar Allah ido. Tunda duk abinda ya kamata na yi na yi wannan shine alkawarin dana daukawarwa mahaifiyarsa. Yau ne zai je bunkure kamar yadda muka gama maganar jiya magungunansa sun kare malamin ya ce ya je ya same shi gobe Kuma Hajiya Maryam za ta cika kwana arba'in da rasuwa mun yi waya da Nusaiba kan cewa tana so ta zo gidan su yi aikin funkaso da fanke duk na gaya masa bai ce kada ta zo ba. Da assubaha ya fita daga d'akina don haka gari yana d'an yi haske kad'an na bi shi nasan ya dawo daga massalaci yana shirin tafiya tunda ya ce su biyu kadai za su tafi da Sukairaju kuma ta jirgi ce yau din yake so su je su dawo idan lokaci ya bada damar hakan. Na ji maganganunsu tun kafin na murda kofar d'akin sai na yi saurin cire hannuna daga handline din. Ina jinta cikin kuka mai ta'ba zuciya da 'kas'kantar da kanta tana cewa." Hajja cewa ta yi na zo na cigaba da kula da yarana to me zai sanya ka had'a kai da matarka har da masu aiki ku dasa musu tsoro da k'yamata. Tun da kuka dawo nake bin ka ina baka ha'kuri don girman Allah ka yafe mini na yi kuskure ba zan kara ba amma ka daina tozarta ni da nuna mini iyakata a gaban Amina, ban cancanci wannan wulakancin daga wurinka ba tun da ka aure ni kake nuna fifiko akan matayenka Maryam da Amina idan ka amince da cewa Hajiya Maryam tana yi maka asiri akan ta samu soyayya da d'aukaka a wajenka to wallahi ya zama dole ka amince da cewa Amina ma tana yi maka asiri domin ko makaho ne ya duba ya san kana yi mata makauniyar soyayya irin wadda hankali ba zai d'auka ba sai an bi mutum ta k'arkashin kasa. Ni da kai iyayenmu daya cikinsu daya ba zan ta'ba cutar da kai ba domin kai dan uwana ne mijina kuma uban yarana b'acin rai ne kawai ya sanya ni ajiye yaron nan na tafi gidanmu saboda jingine ni da ka yi baka kula ni naga ai babu amfanin zamana a gidan. Amma don girman Allah ka yi hakuri ka yafe mini kuma yarana su dawo hannuna don gaskiya ban yarda da tarbiyar da ake ba su ba. Na ji shi yana fad'in." Ke a ganinki tarbiya ce dake Hauwa. Ko kin d'auka wata fitacciya ce ke a zuciyata ne? ki kiyaye ni wallahi idan za ki yi sakarcinki kada na kiara jin kin ambaci sunan Amina. Idan kin danganta Maryam dake bai dame ni ba, amma Amina ba ta da zunubi na itace matar da take rufa mini asiri cikin kowane yanayi. Babu ke a cikin zuciyata Hauwa kuma ba na tsammanin za ki ta'ba samun gurbi a cikinta. Kin yi abinda ya kamata ace hukunciki ya fi haka muni amma arzikin yara da zumunci ya hana hakan don haka ni ban ri'ke ki ba idan kin ga ba za ki iya zama ba ki tafi kawai hankalina ma zai fi kwanciya yara kuwa ai za su rayu tunda ba ke ce mai rayawa ba." Tana kuka take fad'in." Idan kuwa aka yi mini haka ba a yi min adalci ba anzalince ni kuma wallahi sai Allah Ya saka mini." gudun aure littafin kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina bam Ya furta." Ki ka zalinci kanki dai Hajiya hakkin Sultan kadai ba zai bari ki samu sau'kin zuciya ba, ni dai ba zan sake rayuwar aure dake ba balle ki samu ciki ki haihu ki ajiye mini yaro ki tafi. Ki zauna dai a gida gashinan babu wannan alak'ar a tsakanina dake yanzu." Da tashin hankali mai tsanani na ji tana fad'in ." Wallahi abinda ba zai yiwu ba kenan ai zalinci ne wannan kuma ni mutum ce ina da bukata a koyaushe me yasa za ka yi mini haka ina kallo kana mu'amula da matarka ni kuma ka ce ba za ka yi da ni ba, zan gayawa Hajja domin wannan abin ya ishe ni ko da can ma ai sai na nema kake kula ni ba ka zuwa wajena don ra'ayin kanka sai na yi ta bin ka, da haka duka muka tara wannan yaran da ake yi mini gadara a kansu, wallahi ba zan iya jurar wannan wulakancin ba." Ya ce." Kada Allah Ya sa ki jure din ko ni ne na ce miki ki dawo da zan damu kaina tafiyarki kwanciyar hankali da nutsuwa ta haifar mini a gidana ai ke ce ba ki sani ba." Da gunjin kuka da jan hanci na ji tana cewa." Shikkenan na ji to ka rubuta takardata ka ba ni zan tafi har abada kuma ba zan sake sha'awar sake zama da kai ba ai ko Allah ma ana yi masa lefi ya yafe." Hankalinsa a kwance ya furta." Idan na sake sakin ki a yanzu na zama sakarai kenan. Ki zauna dai ki ga ikon Allah aure ma zan k'ara bayan Aminata na yi rayuwata da iyalina cikin hayyaci da samun nutsuwa. Na fi ki mugunta da d'anyan kai Hauwa ko kin d'auka cewa ke kadai ce mara ji ne?" Ta yi shiru tana jan hanci. A hankali na ri'ke karfen baranda gabana na dokawa na fara sauka maganarsa na yi mini kud'a a tsakiyar kunnena 'aure ma zan k'ara na yi rayuwa da iyalina.' Shin da gaske ne ko kuma barazana ce kawai yake yi mata domin ya gigitata. Zuciyata take rada mini aure a ina mutumin da ba shi da lafiya babu karfi irin na jarumar maza. Daya sashen ta na ce mini duk da haka ai akwai da dama mazan da ba su gama kawar da matsalar iyalinsu ba amma suke rakito auran. Na zauna jigum da mamaki a cikin raina. A amma dai bari mu gani lokaci shi zai nuna. Ina kwance ya shigo ya shirya tsaf cikin manyan kaya ya kuma yi kyau ainun kamshinsa yana ta sirnanowa hancina muka gaisa dama na ware kayan da nake so ya tafi da su turmin atamafa ne biyu da mayafi sai takalma guda biyu duka sawa ta daya sun yi mini tsayi duk da nake gajeriya ba kasafai nake son takalmi mai tudu ba na ce masa sa'kon Hajara ne a ce mata na gode da abin arzi'ki. tare muka fito falon shiru yaran ba su fito ba suna ciki ana shirin skull. Ya d'an tsaya yana kallona kafin ya janyo ni ya matse tsam a kirjinsa na dan wani lokaci ya cika ni tare da juyawa da sauri ya kama hanyar fita na sauke ajiyar zuciya a kasalance na ce." A gaishe mini da Hajja sosai Allah Ya tsare." Ya amsa da "Amin kafin ya fita. Ina juyawa da zummar komawa d'aki na ga Hauwa a tsaye a bakin kofar dakinta. Na yi kasa da kaina ba tare da na sake kallonta ba na wuce sai ta zo ta sha gabana muka dubi juna. Murya a dashe alamun ta ci kuka ta k'oshi ta furta." Kin yi nasara a kan Hajiya Maryam Amina kin dawo kaina ko, kin rantse dai sai kin rayu ke kadai a gidan nan to bari ki ji abinda ba ki sani ba ko kin yi nasarar fitar da ni daga cikin yarana tana jika domin da bakinsa ya fadi cewa aure yake nema kuma in sha Allahu rabbi duk wadda za ta shigo itace za ta karya alkadarinki." Na jima ina kallonta sosai ina kuma tunano irin zaman da muka yi da ita a baya a lokacin da ta dinga nuna mini k'auna da kara akan rigingimun da suka dinga faruwa. Har ga Allah a lokacin na ya ba da kokarinta kwarai duk da ina cikin kokwanto tunda bata buda mini zuciyarta na ga zahiri ba a aikace take yi komai da ita muka dinga ya'ki a gidan nan akan Maryam da d'anta Salim ta yi mini mubaya'a domin jajanta mini abubuwan da suke faruwa. Wannan shine dalilin da ya sanya ni nake iyakacin bakin kokarina akan lamarinta an ce duk dan halak baya manta alheri a lokacin tare muka dinga fafutukar kwatar 'yancinmu a wajan gidan Amma cikin wad'an nan kwanakin gabad'aya kaina ya kulle a kanta na rasa da wane ma'auni zan auna al'amuranta. Hakan ya nuna mini cewa dama can tana ya'ki ne a kan kanta domin ta cimma wata manufa tata. Lallai Ubangiji baya bacci kuma yana tare da mai gaskiya. Na dube ta sosai ina fad'in." In ban da abinki Hauwa ai ni ban isa na kore ki a gidan nan ba. Ni a suwa kuma ke da ki ka d'auki tudu biyu ai ke ya kamata a ce kin yi nasara a kaina na fita na bar miki gidan. Amma bari ji ki sirrin nasarata a kanki da zuciya daya nake zaune dake kuma ban zalinceki ba, ban nemi kai ki kasa ta k'arkashin 'kasa ba sai ko'karin ma ganin mijinki ya duba halin da ki ke ciki na kad'aici da damuwa. Amma idan kina ganin za ki iya had'a kafadarki da tawa to bisimillah sai mu fara buga wasan daga yau ni dake. Amarya kuma ai a shirye nake da zuwanta ko kin d'auka ina tsoro ne? ta shigo mu zauna namiji mijin mace hud'u ne a ciki kuwa dole daya ta yi zarra nasan kuma na cinye wasan tuntuni. Don haka tunda kin biyo ta wannan hanyar mu zuba ni dake shege ka fasa.'' Na wuce a gaggauce na shige d'akina domin bana buk'atar sake jin komai daga bakinta. Tunda ta ce za ta iya to mu zuba daga yau na daina d'aga mata 'kafa wallahi........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *V-VIP AREWAPEN* *136* Zama na yi gefan gado tare da d'umbun mamaki da al'ajabi wai yau Hauwa ce take jingina mutuwar Hajiya Maryam da ni saboda tsananin kishina da yake damunta. Kafin kowa ya san da cewa Maryam mashirika ce ita ta fara fad'in haka a bakinta na ji har nake nuna mata kuskuranta akan tabbatar da abinda ba ta gani da idonta ba. Yanzu da rasuwarta ta tona duka ayyukanta na sa'bon Allah kowa ya sheda hakan amma a yau saboda sharri da k'iyayya tana alak'anta mutuwarta da ni. Wani irin sanyi (d'ari) ya mamaye ni a take a lokacin tsabar k'aduwa da mamaki da kuma tsoron duniya. Ni dai duk yadda na kai ga kishi da nuna k'iyayyata akan kishiya ba zan iya neman hanyar da zan halakar da ita ba kamar dai yadda Maryam ta yi ba kuma zan 'kir'kiri karya ko da sharri na ya'ba mata ba. Ina da kishi sosai mussaman akan abinda nake so amma a duk lokacin da ya taso mini nakan iya sarrafa kaina zuciyata bata ta'ba kissima mini na bi wata hanyar domin cutar da kowa ba. Zazzabi ne mai zafi ya rufe ni da ciwon kai abubuwa da yawa sun yi mini dabaibayi haka na yi wani irin bacci mara dad'i da mafarkai irin na mai mashashshara. Biyu da minti ashirin na tashi kaina ya tsananta da ciwo na daddafa na shiga toilet alwala na yi na fito na yi salla kafin na fita falon. Shiru na d'an harari kofar d'akinta a garkame kamar koyaushe tsaki na yi na wuce dakin su Baba Tabawa nan na tarar da Nusaiba ashe tun d'azu ta zo tana cikinsu suna ta hira muka gaisa sosai na tambayeta yara tace mini suna can gidan kakarsu da ta haifi Babansu. Kamar wancan lokacin ranar addu'ar uku yau ma da shirin kwana ta zo. Na ce hakan ya yi ka fi na dubi Baba Tabawa da take ta fama da Sultan yana ta rigima ta ce tana tsammanin zazza'bi ne a jikinsa don ya yi zafi. Na shiga d'akin sosai na sunkuya na ta'ba wuyansa rau zazza'bi yake da gaske kamar ni dole ne kam Dr Sailuba ta zo gidan nan ta duba mu. Goya shi ta yi tana jijjigashi har ya yi bacci muka fito falon ni da ita ta shiga kicin ni kuma na zauna saman kujera cikin nauyin kai da bugawa. AbiΓ±ci ta kawo mini alkubus suka yi da rana da miyar agushi ya yi mini dadi sosai na ci hud'u nasha ruwa na sake komawa d'aki na kwanta ashe tana hankalce da ni ta biyo ni dakin tana fad'in.'' Hajiya ba kya jin dadi ne tunda ki ka fito na karanci yanayinki." Na ce." Wallahi zazzabi ni ma nake yi Baba har ma da ciwon kai." Ta dinga yi mini sannu cikin damuwa. Na daure na tashi zaune tare da d'aukar wayata na lalubi number Dr Sailuba bugun farko ta daga muka gaisa na ce mata idan babu damuwa ko za ki zo gida ki duba ni da yaron nan Sultan nasan yau babu aiki gashi weakened muke babu matsala ko." Ta ce." Babu komai zan shigo bayan la'asar maigidan ma baya gari ai." A tak'aice na ce." Na gode sosai." Na kashe wayar na ajiye Baba Tabawa ta ce." Ko da akwai abinda ki ke buk'ata na game da abinci tun da naga baki ciki alkubus din nan da yawa ba." Na ce." Da daddare ku yi mana towo a yi kuka maigidan ita yake so amma a yi mini miyata daban ta d'an yi yaji." Ta ce." An gama in sha Allahu ta juya ta fita da sauri.'' Ledar kayan motsa bakin da Hajara ta ba ni na d'auko na tsinci tsamiyar biri na sanya a bakina saboda galmi-galmi nake jinsa na sake kwanciya da wayata a hannu. Na rasa wanda zan kira na gayawa tsakanin anti Yagana da Sahura abinda yake damuna a game da abinda Hauwa ta ce mini d'azu abin ya tsaya mini a raina. Anti Yagana na kira muka gaisa jin maganata da kasala ya sanya ta fara jero mini tambayoyi na ce."lafiyata lau amma ina zargin ciki ne da ni.' Ta ce." Ba ki na zargi ba kin tabbatar kuma kin gayawa mai shi ko?" Yar dariya na yi domin nasan dalilin da ya sanyata ta fad'i haka tunda artabun da aka sha a baya na ce.'' Na tabbatar gaskiya shi din ne smma yanayi bai barni na sanar masa ba amma zan gaya masa yau idan ya dawo ya je bunkure wajan Malam D'aha." Babu tsammanin kawai na ji ta rufe ni da fad'a. Sai da na bari ta gama na ce." Lokacin da na samu cikin nan fa yana kwance anti Yagana bai ma san a inda yake ba yanzu ne ya dan fara dawowa hayyacinsa babu abinda zai faru in sha Allahu." Ta sauke ajiyar zuciya kad'an tana fad'in.'' Duk da haka dai Amina tunda kin san halin mijinki da zargi mussaman idan kin samu ciki kamata ya yi ace yanzu ya sani tunda ai ya jima da dawowa nutsuwa ba ki da wata hujja anan." Na ce." Ki yi hakuri zan gaya masa in sha Allahu anti Yagana ni akwai dalilin da ya sanya ma na kira ki yanzu." Ta ce." Menene kuma?'' Hanci na dan ja a sanyaye na furta." Hauwa ce take jingina rasuwar Hajiya Maryam da ni." Duk na kwashe sa'insar da muka yi da ita na gaya mata . Ta ja tsaki tana fad'in." Ta dawo ashe?'' Na ce.''kwarai ta dawo amma ta ki yadda mu zauna lafiya fitinar yau daban ta gobe ma daban tana daga mini hankali wallahi domin ni yanzu anti Yagana babu abinda na fi buk'ata face zaman lafiya duniyar nan tsoro take ba ni." Ta furta." Kin ga Amina idan za ki kwantar da hankalinki ki kwantar ina abin yake me yasa Hauwa zata razanaki har ki dinga jin fargaba a kanta. Ban yarda ki zalinceta ta kowace siga ba amma ki daina raga mata balle ta hangi lagonki ta raina ki tunda ita Yar iska ce mara mutunci to sai kema ki sanya rigar rashin mutuncin ku buga aga wanda zai ci riba ina dalilin wannan masifar." Na ce." Anti Yagana ai na riga na yi wa Hajja alkawari ba na so na biye mata wata matsalar ta faru wadda Hajja za ta ji haka kawai dattijiwar take ba ni tausayi wallahi a ganina idan nima na biyewa Hauwa kin ga mun zama sakarkaru gabad'aya kuma maigidan ba zai samu nutsuwa ba.'' Ta ce." Ai ba cewa na yi ki biye mata ba Amina ki fita daga harkarta ki daina raga mata ko ki nuna mata kina son zaman lafiya da ita. Kuma ki yi duk yadda za ki yi wajan ganin kin sake samun gurbi a zuciyar mijinki abinda nake nufi kenan." Na ce." Ni ma shawarar dana yanke kenan wallahi." Ta furta." Dada kuwa ba ta da lafiya sosai Amina har sai da ta kwanta a asibiti kwananta biyu jiya aka sallamota." Da damuwa mai yawa na furta." Mai yake damunta ne?" Ta ce." Lalura ce kawai irin ta girma da shekarun yau ta ce kafafunta na ciwo gobe ta ce bayanta ya 'kage abinda dai ya tsananta a ciwon har ta kwanta a asibiti ciwon wuya da ta yi eanda ta kai ta kawo ma ba ta iya motsa wuyan ya 'kage amma yanzu alhamdulillahi da sauki." Cike da tausayinta na ce.'" Allah Ya sawwa'ke idan ya dawo zan gaya masa wata'kila mu zo dubata. Anti Yagana ina labarin Ya falmata ne ko a Whasap na jima ban gan ta ba kuma mun jima ba mu yi waya ba. Ta ce." Ai Ya falmata tana saudia neman kud'i Baban Saude ya shige mata gaba wajan mahukunta sai da Alhaji Bana ya sake ta." Na ce.'' To kin ga wannan shine adalci ai ko banza ana samun jajurtatun iyaye a family kamar irinsu Baban Saude da yawa mazan da suke zalintar matayensu za su shiga hankalinsu. Abinda ya faru shine kowa ya san da cewar Ya falmata macace mai zafin nema domin ni kaina itace madubina kuma sai da na takata tukkuna na tashi. Harkokinta sun bukasa sosai a lokacin da muka had'a karfi da k'arfe domin gina gobenmu muka tashi a tare. Tun bayan da na yi auran nan sai kasuwancin da muka yi da ita ya raunana dalili duka ta nuna mini hanyoyin yadda zan dogara da kaina da kuma yadda kayana za su cigaba da zaga 'kasashen waje irinsu sinigal nijar mali kamaru da chadi har ma da saudiya dama kusan sune suke sayan kayanmu a lokacin da muke fafutar ganin mun tashi manyan matan abuja ma suna saye amma duka ta hanyarta tunda ni ce mai aikin dinkawa na yi mata odarsu zuwa maiduguri ta rarraba a sassasa daban-daban. Ta cigaba da kujiba-kujibarta ni ma na cigaba da yin tawa har Allah ya sanya ta bude katafaran shago ta zuba iyayen kekunan d'inki manyan kai da k'ananu ya yara suna aiki. Shekara daya ta sake bude wani a takaice dai sai da shagunanta na d'inki suka kai biyar kuma shago bai wai karami ba wanda yake iya cin sama da keken d'inki goma sha biyu. Mijinta Alhaji Bana shine silar karyata domin had'a ba ki ya yi wasu daga cikin yaranta suka dinga kwashe mata kaya cikin dare suna fita da su a baggo. Idan suka sayar su raba kudin kashi uku shi ya d'auki kashi biyu yaran su d'auki kashi daya. Wataran rigima ta shiga tsakanin yaran nata da suke aikata mata haka har da makami abinda ya assasa musu zuwa gaban hukuma kenan daga nan sai suka fara tonawa junansu asiri dama kuma gefe guda ta sanya Malamai ana ta yi mata ro'kon Allah itama ta tsananta da addu'a. Suka fadi mijinta ne me sanya su da ya ji duka da matsa ya tabbatar da sanya hannunsa wanda da da farko ya fara gardama da jayayya yana fad'in yaushe zai kai matarsa k'asa uwar yaransu har biyu. Daga lokacin ne ta yi tsalle ta dire ta ce sai ya saketa har suka shiga kotu alkali ya yanke musu hukunci daidai da abinda suka aikata ya kuma tilastashi sakinta tunda gaskiya ba namijin da kowace mace za ta yi sha'awar zama da shi ba ne. Anti Yagana ta cigaba da cewa." Ai tana fita idda ta lallaba Dada ta tafi makka wata shida fa yanzu tun bikin Fadila Na ce." Allah sarki Ya falmata zuciyarta a tsaye take irin ta Baban Saude ba ta son zama koyaushe tunaninta ya za a yi ta juya biyar ta koma goma. Amma ni da ta yi shawara da ni zan ce mata ta yi zamanta anan ta cigaba da sana'arta kamar zai fi alheri." Ta ce." To ta dai ce shekara uku kacal za ta yi ta dawo sai dai mu yi mata fatan alheri kawai." Na ce." Ubangiji Allah Ya taimake mu bakidaya anti Yagana ke kuma me ki ke sayarwa?" Na tambayeta cikin sigar tsokana." Ta ce." Babu komai hankalinta a kwance har sai da na yi dariya na furta.'' Babansu Fadila ne ya tsaya miki anti Yagana shiyasa kike wanke goma ki tsoma biyar ba ki da matsala." Ta ja tsaki tana fad'in." Amina ai sai mutum ma ya rasa wace sana'ar zai yi wallahi maza daga waje duk sun k'wace mana abin yi." Na kudi ne littafin don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Na ce." Anti Yagana ba ni so ki kasance daya daga cikin matan nan da barmani coge take yi wa wa'ka (Sakarai baki da wayo) na yi dariya ina fad'in." Ki yi nazarin abinda za ki sayar na baki jari don Allah." A tak'aice ta furta."Aikuwa na gode sosai ai ba ki ga yadda Fadila take cinikin ruwan sanyi ba cikin nan da take d'auke da shi ya hanata fara zuwa koyan d'inki don har mijin nata ya sayo mata form na makarantar." Na ce." Ai ni ya burge ni sosai da ya ke so ta yi Sana'a dalili kuwa rayuwa juyawa take yi ga kuma yadda duniyar ta zama komai ya yi tsada tunda karamin ma'aikaci ne za su taimake ki kan su anan gaba" Ta ce." K'warai kuwa hakane ni ma in sha Allahu zan yi nazarin abinda zan sayar idan na yanke shawara zan sanar da ke." Da jin dad'i sosai na furta.'' Yawwa anti Yaganata ko ke fa" Dariya ta yi kawai muka yi sallama cike da barkwanci da k'aunar juna irin ta jini. Wayar mu da anti Yagana ta kara mini karsashi da kuzari na tashi na je na dauro alwalar la'asar ganin uku da rabi har da minti biyar jim kad'an bayan idar da sallata Dr Sailuba ta kira ni ta iso tana falo na ce mata ta shigo d'aki ta same ni mun saba sosai da ita tuntuni. Ta shigo kamar yadda na buk'ata ta zauna can kujerar dake gefe a d'akin. Na tashi na same ta muka gaisa cikin kulawa na ji dad'i kuwa da ta zo da abin gwajin bf ta yi mini jinina normal bayan ta gama kai tsaye ta tambaye ni ina da ciki na ce mata eh. Cikin raina ina tunanin fa ranar da Hajiya Maryam ta rasu na same shi tunda mun yi kwanciyar aure a daran ranar idan kuwa hasashena daidai ne bai fi kwana arba'in ba tunda itama gobe za ta cika arba'in da rasuwa. Bayan magriba ta aiko mana da magunguΓ±ana kamar yadda ta fad'a mini kafin ta tafi muka sake yin waya tana yi mini bayanin yadda zan yi amfani da nawa maganin da kuma bayanin na Sultan tunda shi ma ta duba shi kafin ta tafi zazza'bin hak'ori ne yake damunsa magunguΓ±a ta had'a masa masu kyau tana fad'in daga zarar an bashi maganin zazzabin zai sauka don haka muka yin sallama a wayar na tashi na fita da ledar maganin nasa hannuna. Suna kicin ba su fito ba tunda na duba d'akin babu kowa har ita Nusaiban na same a kacame suna ta aikin kwa'ba fulawa har da Mairo dama yaran gabad'aya ganin Nusaiba ya sanyasu zuwa wajenta tunda akwai sabo kuma yadda take hira da yaran ya tabbatar mini da cewa ko a can baya da suke tare da mahaifiyarta bata tsangwame su ba hakan ya nuna sun yi sabo domin da babu kulawa da ja a jiki nasan babu yadda za a yi su je wajenta za su guje ta ne da kallon rashin sani kamar yadda suke yi wa Hauwa. Da yake kicin ne mai girma mai d'auke da na'urorin sarrafe-sarrafe hakan bai sanya sun takura ba. Baba Tabawa da Taburni suna ta aikin towon dare kamar yadda na umarta. Mairo da Nusaiba suna kwa'be-kwaben fulawa. Na saki fuskata sosai Ina kallonsu suna cikin nishadi lallai d'an adam rahama ne a ko'ina sai na rasa ma gaisuwar wanda zan amsa manyan na yi haka zalika ma yaran na yi na bi duka na amsa ina fad'in." Nusaiba wannan funkason zai yi dad'i har miyau na ya tsinke." Ta kuwa sanya dariya tana fad'in." Kai anti." Na dubi Baba Tabawa ina fad'in. " Ga maganin Sultan Dr Sailuba ta aiko da shi a bashi abincinsa sai ba shi yanzu." Rufe bakina ke wuya Hauwa ta shigo kicin din ta fara bin ko'ina da kallo babu wanda ya yi yun'kurin gaisheta Baba Tabawa ta zo zata kar'bi maganin tana fad'in." Jikin nasa da zafi har yanzu." Ta juya da sauri tana fad'in ko dai bari na fara dama masa kamun nasa. Da yake kamu ake yi masa na nikakkiyar gyad'a ya fi son sa akan duk sauran abubuwan da ake bashi kuma shine yake kara masa kuzari da lafiya babu kuma rama a tare da shi. Na ji maganarta a cushe tana fad'in." Ba shi da lafiya ne?'' Ba tare da na dube ta ba na ce." Eh.'' A takaice na mi'kawa Baba Tabawa ledar magungan kafin ta kar'ba sai ta yi gaggawar warce ledar daga hannuna. Duka muka bi ta da kallo da mamaki. Ta fito da magunguΓ±an tana duba su. Na zura mata ido da tsananin takaicinta kamar na mangareta haka nake ji a raina wai ita likita amma mara tunani da kangado . Ta gama duba magunguΓ±an tsaf ta miko mini na kar'ba ina girgiza kaina duk abinda zan yi a yanzu wallahi ba don ita nake yi ba. Baba Tabawa ta kar'bi maganin daga hannuna. Hauwan ta dube ta tana fad'in." Ba ni shi na duba shi." Sai ta dan dube ni a tsorace wata'kila tana fargabar ta bata shi ya bude ido ya ga fuskarta tunda ta gaya mini ya ta'ba shid'ewa a kwanakin baya. Na daga mata kai alamar ta kwanto shi daga bayanta ta bata shi kamar yadda ta buk'ata. Na ji tsakinta tana fad'in." Sai kin nemi izininta za ki ba ni d'ana na gani Baba Tabawa ko kin manta ni ce na haife shi ne ikon Allah sai kallo ni Hauwa" Babu wanda ya tanka mata Baba Tabawa ta kwanto yaron daga baya wanda ya yi daidai da lokacin da ya bude ido ya fara kusurkusur sai kuma ya sa kuka. Nasa hannuna a wuyansa da zafi. Itama ta mika hannunta domin kar'barsa kukansa ya tsananta kuwa ta rike shi yana fizga irin ta yara yana mika hannu domin komawa wajan Baba Tabawa. Kukan da yake yi ya tsorata ni sosai ita kuma ta'ki ba bawa Baban shi gashi dai ta fahimci so yake ya koma hannunta. 'Dif!! kamar an yi ruwa an d'auke ya yi shiru jikinsa ya shika lakaf! Idanunsa suka kakkafe. Suma ya yi.... Ta gigice ainun da sai ta fashe da kuka tana kallonmu na yi gaggawar kar'bar shi daga hannunta muka yi tiri-tiri a kicin din har muna bangazar juna ni da ita Baba Tabawa kuwa tuni ta fara hawaye tana fad'in.'' Suma ya yi. Kafin mu yi wani yun'kurin Taburni ta nufi friji ruwa mai sanyi gaske ta d'auko ta gumtsa a bakinta ta fesa masa da karfin a gaske a fuskarsa ya saki nishi! Numfashinsa ya fara hawa da sauka. Ya motsa kafafunsa. Muka fita daga kicin din a gaggauce ni da su gabad'aya rasa inda zan nufa na yi da yaron a hannuna d'akinsu Baba Tabawa na nufa hankalina a tashe yaron nan ya mutu ko ya samu wata matsalar mun shiga uku a gidan nan gabad'aya..... Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *137* "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wannan kalmar ita na dinga nanatawa a cikin raina ina zaune gefan gadon da Baba Tabawa take kwanciya da yaron hannuna. Duka sun yi cirko-cirko a kaina yayin da ita Hauwan take bakin kofar d'akin a tsaye ta gagara shigowa amma kallo daya za ka yi mata ka tabbatar da cewa a cikin tashin hankali take. Numfashinsa yana ta hawa da sauka kafin a hankali ya bud'e idonsa yana juya kansa ya ga Baba Tabawa sai ya fara mik'a mata hannu alamar ta d'auke shi. Wata nannauyar ajiyar zuciya na sauke cikin raina ina tasbihi da godiyar Allah. Ta kar'be shi a gaggauce ta sanya shi a kafadarta tana dan jijjigashi sai lokacin hankalin kowa ya kwanta ganin yadda yanayin yaron ya daidaita na juya babu Hauwa babu dalilinta dama kuma ba ta iya shigowa ba a bakin kofar d'akin ta tsaya. Minal ta je tana jan zanin baba Tabawa tana fad'in." Mutawa ya yi Sultan din shikkenan ya mutu ko?" Da sauri na janyota ina girgiza mata kaina alamar a a gabad'aya yaran duk sun yi tsuru-tsuru ganin yadda muka ki'dime don shi Khalil har da yin kuka kuma bai biyo mu d'akin ba. Na ce Baba Tabawa ta zauna dashi a d'akin ta bashi abincinsa gabad'aya muka fita. Smma ko da na koma dakina kasa zama na yi minti goma a tsakani na sake fitowa Hauwa na samu a tsaye a jikin kujera ita kad'ai don duk sun koma kicin din domin cigaba da ayyukan da suke yi. Muka dubi juna na wuce ta ban ce komai ba na ji ta kira sunana cikin damuwa na juya amma ban amsa ba ta zo ta tsaya daf da ni tana fad'in" Don Allah Amina kada ki gayawa maigidan ina neman wannan alfarma a wajenki." Na zura mata ido cikin nazartar maganarta ashe mara kunyar 'karya ce. Na ce." To akan me zan gaya masa Hauwa da dai Allah Ya d'auki rayuwarsa ne wannan zama dole ya san dalili yanzu kam tunda Allah Ya sa ya dawo hayyacinsa sai ayi ko'karin kiyaye gaba." Ta gyad'a kanta tana fad'in na gode. Ban saurareta ba na shige dakinsu Baba Tabawa tana ta kici-kicin bashi kamun data dama masa yana cinyarta a zaune yana kamo hannunta. Na sake sauke ajiyar zuciya ta jin dadi ganinsa kalau har ma yana d'an wasansa. Na zauna har sai da ta gama bashi ta gyara masa jikinsa da bakinsa tukkuna na bude maganin na fara nuna mata yadda za ta bashi koda ta kammala sai ta sanya shi a kafad'a ya yi gyatsa sannan ta d'auki towel dinsa ta goya shi. Yana ta gwalantu irin na yara. Fitowata daga d'akin ya yi daidai da lokacin shigowarsa. Dama ya ce da wahala ya kwana. Na yi kokari sosai wajan daidaita yanayina na yi masa barka da zuwa ya amsa da kulawa yana fad'in.'' A kawo mini abinci Amina." Ya kama hanya zai hau samansa da wata leda viva a hannunsa. Yaran gabad'aya suka fito daga kicin har da Mairo jin maganarsu ya sanya ya dakata ya tsaya aikuwa suka nufe shi da sauri ya rirri'kesu yana dariya suna ta jero masa sannu da zuwa. Ina kallo ya dubi Khalil cikin nazari ya riko hannunsa yana fad'in." Kai matsalata da kai zurfin ciki da miskilanci ko akwai abinda yake damunka?" Ya yi shiru yana sunkuyar da kansa. Karaf muka ji Minal na ce." Sultan ne ya mutu ko Hassana, shikkenan ya mutu, shikkenan ya mutu." Ta dinga fad'a tana tafa hannunta. Na ji kamar an rad'e mini guiwata da tar'barya. Nusaiba ta fito daga kicin din ganinmu a tsaye ya sanya ta d'an daidaita yanayinta ta dan risina tana fad'in.''Baba sannu da zuwa?" Ba a hayyacinsa ya amsa ba saboda maganar Minal ta dake mu gabad'aya sai Khalil ya fara hawaye. A lokacin ne ya kara kid'imewa yana fad'in." Sultan ne ya rasu Amina?". Na ce." A a lafiyarsa lau me yasa za ka yarda da maganar yara." Ni kaina na fad'i maganar ne wadda nake da tabbacin cewa ba zai yadda da ita ba amma don ya gazagata na ce da Mairo ta kira Baba Tabawa. Ta kuwa fito da yaron goye a bayanta na ce." Kwanto mini shi." Ta yi yadda na umarta tana gaishe shi ya amsa babu sukuni. Inda yake na nufa da yaron a hannuna yana ta bacci. Na ce da yaran su je su yi sallar Isha'i su ci abinci da sauri suka bar wajan shi kuma ya kar'bi yaron muka haura saman a tare. Leda viva dana kar'ba a hannunsa a lokacin da zai kar'bi yaron a hannuna na ajiye can gefa ya zauna da shi a hannunsa yana dudduba shi yake fad'in na dawo da farinciki sakamakon albishir din da Dr Sailuba ta yi mini Amina amma kuma me yasa za a yi mini a haka har yanzu a cikin gigita nake wallahi dalili ta yi mini bayani shima bai ji dad'i ba yana zazzabi hak'ori hakane ko?" Na ce." E, yau tun safe ya tashi da zazzabin dalilin da ya sanya ni kiran Dr Sailuba kenan amma tsakani da Allah me yasa zaka yarda da maganar yara?" Ya furta." Me yasa ba zan yarda ba lallai ne fa akwai abinda ya samu yaron nan ko ga yanayin yadda na ga tsoro da firgici a idon Khalil yarinyar nan Minal ba za ta yi karya ba." Na ce." Ai ga yaron nan a hannunka ka duba shi sosai ka gani." Ya kuwa fara duba shi har da cire masa kayan jikinsa ya bar shi da pampas yana jujjuyashi shi kuma sai dariya yake yi cikin ikon Allah zazza'bin ya sauka don dana ta'ba jikinsa babu zafi. Na yi murmushi ina kallonsa na furta." Me ka gani a tattare da shi." Ya saki ajiyar zuciya yana fad'in." Ban ga komai ba amma har yanzu ban yarda ba akwai abinda ake b'oye mini." Na ce." Don Allah mu bar maganar nan mu yi wata ka ji." Ya tsira mini ido na dan wani lokaci kafin na ji yana fad'in." Kin kyauta Amina ke ba za ki daina abinda ki ke yi ba ko?'' Nasan akan abinda yasa ya fadi haka na ce." Ka yi hakuri don Allah ina da ciki Dr Sailuba ta gaya maka ko?'' Ya gyad'a kansa yana cewa ta gaya mini amina amma mai yasa ki ke yi mini haka ba na fa jin dad'i tuntuni na gaya miki mai zai sanya abin alheri ya same ni a dinga b'oye mini wannan zalinci ne da d'aukar hakki wallahi." Na ce." Ka yi hakuri ba zan sake ba." Yaron na kar'ba ina mayar masa da kayansa. Shi kuma ya cire agogon hannunsa ya zare gilas din da hular kansa ya tashi tsaye tare da cire babbar rigar ya ajiye saman gado. Toilet ya nufa bai sake ce mini komai ba na sauka kasa da yaron na mayar dashi wajen mai rainonsa. Kicin din na nufa sun kammala komai na shirya masa abincin kamar yadda ya buk'ata da ya shigo Na same shi yana sallar Isha'i na ajiye tiren a wurin da yake zama sai da ya jima saman daddumar yana addu'a kafin ya shafa ya taso yazo ya zauna na fara ko'karin zuba masa abincin yana ta kallona. yana ci muna hira gidan Malam 'Daha da irin sallahun gaisuwa da godiyar da suka bashi zuwa gare ni. Nan yake yi mini bayanin abinda yake cikin leda viva da take ajiye gefe naje na daukota kayan dake ciki na fito dasu sassa'ken gargajiya ne da saiwowi gasunan kala daban daban. Ya fara yi mini bayanin yadda za a yi da ruwan rubutun dake d'aure a waya farar leda irin mai zurfin nan za a dafa maganin a tace a sha tsayin sati daya kullum karamin kofi d'aya. Babu maganar sauran asiri a tattare dashi kamar yadda malamin ya yi masa bayani matsalar dai aka samu har ta ta'ba masa lafiyarsa wannan mummunan d'aurin da aka yi masa tunda dama an yi shine akan manufofi da yawa. Idan har an dage da magani da kuma addu'a karfi da mazantakarsa zai dawo fiye ma dana baya. Sai dai ya ce kada wata mu'amula irin ta aure ta wanzu har sai an gama shan maganin tukkuna. Ai a daran ban bari gari ya waye ba na dafa maganin na tace shi sosai na zuba cikin wani dogon jug guda biyu na kai saman nasa na ajiye kullum da safe za a sha kofi d'aya idan ya yi karin kummalo. Da safe kafin na fita falo Sahura ta kira ni a waya cikin annashuwa da farinciki take fad'in." Amina don girman Allah ki taya ni da godiya wurin Yallabai jiya na kar'bi takardar gidan da ya yi mini alkawari zai ba ni anan hotoro wajan ma'aikatarmu gida mai kyau Amina ginin zamani gashi ya sanya an zuba mini komai tarewa kawai zan yi." Sai ta rushe da kuka.' har sai da na ji wani iri a raina na ce." Haba Sahura menene kuma na kuka don Allah ai kin wuce haka a wajenmu don girman Allah ki daina wannan kukan ba na so." Na ji ta tana fad'in." Ya zama dole na yi kuka Amina na dad'i ne wallahi na rasa inda zan tsoma raina ba ki ga gidan ba mai yalwa da wadatattun d'akuna ga ababen more rayuwa kuma wai gidana ne mallakina." Na ce." To menene a ciki ai komai rabo ne, ki godewa Allah kawai." Ta ce." Shine abin godiya a koyaushe amma dai ya zama tilas na godewa wanda ya zama sanadi." Sallama muka yi da ita ban kuma yi kasa a guiwa ba yanzu zan je na sake jadadda masa godiyata. na kudi ne littafin don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Sai da na leka su Baba Tabawa tukkuna na duba Sultan ta yi masa wanka yana ta bacci cikin net dinsa muka gaisa sosai da su ina tambayar jikinsa ta ce ai ya warware sosai don jiya ma kwata kwata bai kwana da zazzabin ba har gari ya waye. Na godewa Allah a cikin raina na fito saman zan nufa na samu Hauwa a kan kujera ita kadai a falo a zaune muka kalli juna na ganta a hargitse duk ta muzanta na janye idona da sauri daga kanta ai hausawa suna cewa.' Duk wanda ya hana uwarsa bacci to shi ma watarana bai zai rintsa ba kana ganinta kaga wadda take cikin tashin hankali da damuwa ashe tana son yaron ta cillar dashi ta tafi gashi yanzu 'kiri-'kiri tana kuka da nadama 'ya'yanta suna gudunta har dai mai suma saboda ta daukeshi Khalil da Minal kuwa ba na tsammanin ma suna yi mata magana domin duk gidan kamar mujiya haka ta zama. Ina hawa saman ya ce na had'o masa shayi haka na sake sakkowa na shiga kicin na had'o kayan shayin na fito still dai tana zaune a kujera shiru ta d'an ba ni tausayi amma kadan ban kalleta ba na ji ta kira sunana na tsaya tare da dubanta. Maganar dai jiya ta sake maimaita mini kada na gaya masa don ta d'auki sultan ya suma." Na b'ata Raina ina fad'in." Wai me zai sanya na gaya masa ne Hauwa? me ki ka d'auke ni ne?" idan har ya san abinda ya faru to ki tabbatar babu yawuna smma ai kin san a gaban yara aka yi kuma irin wannan lamarin da wahala ya 'buya." Ta yi shiru tana gyad'a kanta ba ta ce komai ba. Na kad'a kaina kawai na haura saman da mamakin yadda ta yi sanyi ta zama wata Saliha bana tsammanin ma jiya ta rintsa saboda yadda na hangi tashin hankali a idonta. Sai da na bari ya kammala shan shayin tukkuna na tsiyaya masa maganin a madaidaicin Kofi da kamar minti ashirin da biyar a tsakani ya sha maganin har yana yin gyatsa yana fad'in." Na gode uwar biyu.' Na janye kayan tea din daga gabansa ina murmushi na ce." A madadina da Sahura muna kara godiya zuwa gare ka Ubangiji Allah Ya kara suttura da rufin asiri Allah Ya sa a mizani na gode sosai Allah Ya saka maka da alheri." A tak'aice ya furta." Ni ma na gode sosai Allah Ya saka miki da alheri Ubangiji Allah Ya sa mu rayu tare har karshen numfashina." Amin na furta. Ina kallonsa zuciyata na d'an dokawa kan zuciyata na sa'ko mini wani lamari na ji maganarsa yana fad'in." Yau Maryam ta cika kwanaki arbarin da rasuwa ko?" Na ce." K'warai kuwa Nusaiba sun yi abin sadaka da sassafe su Masa'udu suka fita da shi zuwa bakin titi tana can tana baccin gajiya dakinsu baba Tabawa." Ya gyada kansa a nutse Yana fad'in." Babu wani Abu da nake buk'ata a game da dukiyar matar nan Amina amma ya zama dole mahukunta suka shiga ciki tunda duka mun gama harhad'a abubuwan da ta mallaka ni da yaronta Salim sutturanta kuma na gayawa Nabila tunda har yanzu tana gidan a zaune tare da yaran Salim da Adam na ce su raba a tsakaninsu abinda ya danganci furniture na d'akunan gidan da na'urorin dake kicin dinta yaran sun ce a bar musu a gidan abinda na gada daga ciki na bar mu su. Wad'annan manyan kadarorin nata da kudin da muka gani cikin wannan dirowar tata sune alkali zai kasafta ba ni buk'atar komai na bar musu abinda dai nasan ba zan ta'ba yafe mata ba shine ko'karin mayar da ni rago mai rauni da ta yi. Idan har lafiyata da mazantakata irin ta d'a namiji ba ta dawo daidai ba Allah Ya isa ban yafe ba wallahi." Na yi gaggawar danne dariyar da take so ta kufce mini sosai na daidaita yanayina don ganin yadda yake magana cike da alhini da saduda da damuwa. Na daure na ce." Maryam ba kai kadai ta cutar ba my love har da ni fa." Ya yi saurin kallona kafin ya gyara zamansa ya riko hannuna yana murzawa ya furta." Shiyasa ai kullum idan na yi sallah nake neman sakayya a wajan Ubangiji ta cuce ni Amina idan na gaza miki ta wannan fannin zan k'wareki kawaici da hak'urinki zai k'are nasan watarana za ki nemi hanyar rabuwa da ni saboda rashin samun wani babban lamari wanda ya tasirantu da gangar jikinki." Na ce." Haba dai ka daina yin wannan tunanin in sha Allahu rabbi zaka samu lafiya ka ma fi da k'arfi da mazantaka kamar yadda malamin nan ya fad'a kai dai mu cigaba da yin maganin sau'ki zai zo in sha Allahu." Rungume ni ya yi sosai a jikinsa yana fad'in." Na gode sosai matata tuntuni na gama sheda cewa soyayyar gaskiya ki ke yi mini amma ba na jin dad'i a cikin raina a duk lokacin da na nemi ki na gaza kawar miki da bukatarki hankalina na tashi ina kuma tausaya miki a cikin zuciyata." Cikin dauriya na ce." Babu komai fa kada ka tayar da hankalinka ina tare da kai duk rintsi in sha Allahu." Ya sake matse ni tsam-tsam yana sauke ajiyar zuciya tare da sumbatar wuyana kamar dai koyaushe. Yana d'an yamutsa wasu wuraran na jikina. Na janye a hankali Ina kallonsa yanayinsa ya canza sosai wanda yake nuna zallar buk'ata. Ya dinga sauke nishi a hankali a hankali Ina kallonsa ya mike babu wani karsashi a tare da shi ya tafi ya je ya kwanta a gado. Yadda alamu suka nuna wannan shara'din da aka gindaya ya yi masa tsauri Allah kuma ya sanya ya iya jurewa zuwa sati dayan........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK.* *07084653262* *V-VIP AREWAPEN* *138* To a daddafe dai ya iya bari wa'adin da Malam 'Daha ya gindaya ya cika. Ranar da maganin ya k'are kamar ya zuba a ruwa a k'asa ya sha saboda murna abin ya dinga ba ni da dariya da mamakin yadda gabad'aya ya manta da cewar ba ni kadai ba ce matarsa akwai wata wadda son rai da rashin hakuri ya sanya yake take mata hakkinta. Yanzu tun ina jin haushin Hauwa wallahi ta fara ba ni tausayi domin kuwa tun daga ranar da yaron nan Sultan ya suma ta yi bala'in sanyi take neman shiri da ni kuma yanzu takan fito falo ta zauna idan ta ji motsinmu da yara da masu aikin ana wasa da dariya sai ta fito ta zauna tana bin mu da kallo tana d'an murmushi har idan an yi magana ta tsoma baki amma dai duk da hakan yaran nahiyar da take zaune basa kallo balle ma su je wurinta ta dinga jan Usai kenan da wasa ita kuma tana nok'ewa tare da zum'bura baki nata yaran Khalil da Minal bata yi musu magana balle kuma Sultan da baya son ganinta ko zama ta yi idan yana wasa sai ya rarrafa ya nufi wajen uwar rainonsa abin yana yi mata ciwo sosai. Amma babu yadda za ta yi haka gobe ma idan ta ji mu da yaran za ta sake fitowa. A yau din ne da wa'adin ya cika kwanan turaka ya dawo hannunta duk da na lura duk ranar girkinta bata hawa saman yau kuma tun safe naga tana kai wa da kawo wa a falon ta hau saman har sau biyu. Sai na ji dadin hakan a cikin raina duk dai har yanzu ina jin tsoron kaidinta amma dai zan fi so su shirya su daina zaman gaba da k'ullatar juna tunda tuntuni sun riga sun zama abu daya. Ban sani ba ko sun sasanta bai nuna mini alamar hakan ba tunda ai namiji ne yau zai ce baya son abu gobe kuma ya canza ya ce yana so kuma itama macace tana da nata dabarun na janyo hankali. Na so dai a ce a yau din da yake ta gand'okin yin jima'i ya jarraba a kaina domin fita daga kokwanto da samun kwanciyar hankali dan gaskiya damuwarsa ce kawai ta fito fili sai nake ganin na fi shi damuwa kawai ina dannewa ne. Kwalliya ta yi sosai da yamma nuna tare da yaran a falo da yake Juma'a ce suna hutun makaranta ta fito ta dan zauna cikin mu na kamar minti talatin wajan biyar da arba'in ta haye saman tun daga lokacin ba ta sakko ba har da dare ya shigo na tashi na nufi d'akina domin gabatar da sallar magriba. Na gama lazimina na dan jingina jikin gado zuciyata na d'an harbawa kad'an sai na tsinci kaina da shiga damuwa. Na sake rintse idona da k'arfi ina kiran sunan Allah ba ni so kishi ya jefa mini son rai a zuciyata idan har da adalci ya kamata a ce na bashi goyon baya wajan ganin ya yi hakuri sun sasanta junansu. kuma daidai gwargwado ta yi hakuri ta jure kuma alamu ya nuna ta zubar da makaman ya'kinta neman shiri take yi ta sigogi da yawa. Amma dai duk da haka na so a ce yau din a yi gwajin a kaina ko don samun nutsuwar zuciya. Sai da na yi sallar Isha'i tukkuna na ci abinci. Na samu waje na kwanta da wayata a hannu Ina d'an duba What'sapp dina amma dai still can kasan zuciyata sai dokawa yake yi ina mamakin ganin bai kira ni a waya ya nemi abinci ba kamar yadda yake yi idan ya dawo daga sallar isha'i wata zuciyar ta ce mini wata'kila bai shigo ba har yanzu shiyasa. Na girgiza kai ba na tsammanin hakan domin da ya yi sallar Isha'i yake shigowa sai da babban dalili yake sake fita idan ya ci abinci yakan dan duba Loptop din shi har zuwa goma na dare ko sha daya gaskiya ya shigo. Ko dama murnar da yake yi kenan tunda sun jima ba su had'u ba dole ya yi marmarinta ya nuna gandoki. Idan kuma na tuna irin lugwigwitar da jikina ya sha a hannunsa a tsukin kwanakin da suka kasance na shara'din sai jikina ya yi sanyi na kasa gazgata kowane sashe na zuciya. "Na gaya miki fa Hauwa na daina kwanciya dake saboda wannan dalilin na ji dad'i dake na dare daya ki dasa mini b'akinciki na shekara goma. Ban had'a shimfida dake ba balle ki d'auki ciki ki haife mu yi fad'a ki dire mini yaro ko yarinya ki tafi gidanku wannan shine hujjata." Ya yi maganar cikin kwanciyar hankali A raunane ta ce." To yanzu ya kake so na yi na kai geji na rantse da zatin Allah ji nake yi kamar zan yi hauka a tsananin buk'ace nake rayuwata za ta shiga matsala." A nutse ya furta." Ba ki yarda da hujjata ba kenan. Ba fa zan yi ba na gaya miki ki tashi ki fita kina 'bata mini lokaci zan yi aiki." "Dan girman Allah ka yi hakuri kada ka jefa rayuwata a wani hali." Ya dubeta sosai yana fad'in." Kin ga na yi miki kama da wanda zaki karyawa rantsuwa Hauwa?" Ta girgiza kanta cike da damuwa." Ya ce." Ba zan yi kaffara akan ki ba, ki tashi ki ba ni waje idan kuma za ki iya yi mini fyade Bismillah." Tana kuka sosai ta furta." Allah mai ji ne da gani, kana zalintata kana tauye mini hakkina na rayuwar yau da gobe ba zan yi maka fyade ba amma sai Allah Ya saka mini tunda ni ba mazinaciya ba ce balle na je na nemi wani kai kuma kana yi da matarka kuna gamsar da juna hakkina ba zai barku ba wallahi." Dariya ya kama yi yana kallonta kafin ya ce." Ke ni fa ba wata lafiya na cika ba yanzu idan ma za ki daina shiga 'kunci akan ban kwanta dake ba itama Amina ha'kuri take yi Maryam ta kassara ni da asirinta. Cikin rashin yarda da maganarsa ta furta." Wallahi ban yarda ba ai dama can haka ka ke yi mini ka jima kana zalintata sai Allah Ya saka mini." A gajarce ya ce." Ni ma Allah Ya saka mini." Ta tashi tare da kama hanyar fita ya bi ta da kallo ko daya bai tausaya mata ba domin ji yake yi har yanzu bai gama goge takaicin da ta cusa masa ba a baya. Da asubahi ban kai ga tashi daga dadduma ba ya shigo da jallabiya da carbi tabbacin daga massalaci ya fito. Muka gaisa ya nemi gefan gadona ya zauna har da cire jallabiyar ya ajiye. Na ninke dadduma na ajiyeta a wajenta na zauna ina kallonsa a nutse na ce." Kwana biyu da suka wuce mun yi waya da anti Yagana tana gaya mini Dada bata da lafiya don har kwanciya ta yi a asibiti." Da alhini ya ce." Me ya same ta?" Na ce." Ciwon wuya ta yi amma dai da sauki an sallamota daga asibiti ina son zuwa dubata." Ya gyad'a kansa yana fad'in." Ban 'ki zuwan ba amma legos nake so ki shirya mu tafi cikin satin nan da zamu shiga." Na ce." Da dai ka d'auke mini zuwa legos din nan tun da kaga a halin da nake ciki ya kamata na zauna waje d'aya na samu nutsuwa ku je da Hauwa kawai." Ya d'an Harare ni kafin ya ce." Dake zan je Hajiya ba wani dadewa za mu yi ba in sha Allahu mu dawo cikin yaranmu mu je mu huta ni dake na wata d'aya sannan akwai ayyukan da nake so na gabatar a can din." Shiru na yi ina kallonsa tare da raya abubuwa da yawa na yi masa maganar Hauwa yana hararata kuma bayan tare suka kwana nuna mini yake yi har yanzu ba su daidaita ba. Ya ri'ke hannuna yana d'an janyo ni jikinsa yana cewa." Jiya me yasa ba ki zo ba?" Na ce."Me yasa zan zo? Don girman Allah ka daina wasa da tunaninmu yanzu don ka sasanta da Hauwa shine abin yi mini boye-boye na fi kowa farincikin hakan wallahi." Ya fara ko'karin cire mini hijabin jikina yana fad'in." Ni na gaya miki haka Amina kada ki yi mini rigima a irin wannan lokacin da nake tsananin kewa da bukatarki kada ki yi abinda zai dakusar da farinciki da karsashina my love.." Ya fara sumbatar sasssan jikina a mutukar dimauce yana yin wani irin numfashi bakina ya mutu murus domin abinda jikina yake marari ne ya samu da na yi yun'kurin yin magana da turjiya sai na ji bakina ya yi nauyi bayan sa'kkonin soyayyar da yake aika mini ta kowace ga'ba. Bakinsa ma amayarwa yake yi tare da wata irin sheshsheka haka muka kasance cikin ru'kun'kumar juna zuciyata na ta tsalle ido a lumshe can kasan zuciyata ina ta kiran sunan Allah da ro'kon Allah wanzar da alheri akan abinda za mu yi Ubangiji maji ro'kon bayinsa wata iriyar rayuwa muka yi wadda ta ki'dimar da mu. Kuzuri da nagarta da mazantaka abin sai godiyar Allah da sake jaddada addu'a ga Malam D'aha da zuri'arsa kamar yadda ya fad'a mun ga zahiri domin kuwa ni zan tabbatar da cewa karfinsa na d'a namiji ya ninka na baya kafin a yi masa d'aurin goro. Muna gamawa ya dinga godiya ga Allah har sai da ya ba ni tausayi a d'akina ya tsarkake jikinsa yana fad'in." Amina zan iya mallakawa Malam D'aha rabin dukiyata domin wallahi ya taka muhimmiyar rawa ga rayuwata na riga na sare fa ban ta'ba tsammanin mazantaka zata dawo ba sai gani rass da ni ki gaya mini ya ki ka ji don Allah." Ya fad'a yana kanne idonsa daya. Ni ma cikin tsokana na ce." A wallahi ras da kai Baba gaskiya ka yi bajinta Allah Ya sakawa da Malam 'Daha da alheri ya cancanci komai daga wajenka Ya riko ni yana fad'in." A hankali duk zan biya ki bashin da na ci miki ko?" Cikin nuna ya yi kokari na ce." Haba ai tun jiya ka biya ni Allah Ya taimake ka, a ai sai da na ce alhamdulillahi." Ya kuwa fashe da dariya yana sake rungume ni a jikinsa. Na kudi ne littafin nan kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. To a haka na yi kwana biyu na muna morar juna da nishadi ranar da Hauwa ta kar'bi girki kuwa ya rasa gane inda ba dosa tunda na hau na gaishe da safe ban yadda mun sake had'uwa ba marigaba na yi na shige d'akina na kuma kulle kofata duk da nasan aikin banza na yi yana da mukkulin d'akin amma dai hakan zai fi mini kwanciyar hankali ya kwana shi kadai idan ma ba zai kwanta da ita ba. Babu kalar rarrashin da bai yi mini ba ta waya na ce ba da ni ba wallahi duk yadda nake jin zafinta a raina ba zan yadda ya had'a kai da ni a zalinceta ba to ballantana ma yanzu da da ta sauko take neman shiri ba na jin haushinta amma fa na ki sakin jikina da ita. A haka muka cigaba da rayuwar a gidan har ya ha'kura ma duk ranar girkinta baya nema na ban san dai ya suke 'karkewa ba tunda nakan dan ganta jefi jefi ta hau saman a ranakun da take da girkin ta kara ramewa kwarai da gaske ta zama silent ma kamar ba Hauwan da na sani ba mai neman fitina da son kin zaman lafiya. Kuma har yanzu jiya I yau tsakaninta da 'ya'yanta sai dai ido idan ma ta kira su wajenta Minal dai ba ta zuwa Khalil ne koda zai je a cikin fargaba da shakku yake zuwa saboda ta saba dukansa." "Hauwa Legos za mu tafi ni da matata ban hana ki zama ba tunda kina ganin za ki iya amma wallahi tallahi kada na ji kada na gani akan yarana da wanda ki ka haifa da wanda ma ba ki haifa ba lafiya lau za mu tafi mu bar basu da masu yi musu hidima duk abinda ya faru a gidan nan zan yi kuka dake kuma zan yi miki hukunci mai tsananin gaske." Ta ce." Hukunci ya wuce wanda kake yi mini a yanzu. Ni ina ruwana da yara kuma abinda ya dame ni daban me zan yi musu ai ni ba azzalima ba ce." "Na dai gaya miki domin na san halinka ba ki da mutunci babu ruwanki da kowa." Ta fashe da kuka tana fad'in." To na ji, yanzu sai ka gaya mini menene makomata ai ba maigadi ba ce ni. Wane irin zalinci ne wannan kake yi mini 'kiri-'kiri an raba da ni da yarana suna k'yamatata ai duk tsiya ba za su canza ni ba." Shiru ya yi mata. Ta cigaba da cewa." Ka gaya mini menene matsayina gaskiya na gaji wallahi, Allah kuma yana ji yana gani." Ya dube ta sosai tare da cewa." Na yi na yi na ga na ha'kura na yafe miki na kuma sanyawa zuciyata sonki da kaunarki amma kin san Allah babu waje a cikin zuciyata da farfajiyarta Amina ta shimfida mashinfidinta ta zauna daram da can Samira tana da waje amma yanzu Amina ta mayaye ko'ina ita kadai ce a ciki ba kuma na tsammanin har abada wata maccan za ta samu irin wannan sararin." Ta dinga wani irin kuka mai tsuma zuciya da sosai rai wanda duk wanda ya ji sautinsa sai ya tausaya mata amma a wajensa ma damunsa take yi so yake ta tashi ta fita ta bar masa d'akinsa. "Ni ba zan ta'ba yi maka irin wannan 'kiyayyar ba domin ko banza mun had'a jini kuma na haihu da kai yara uku duk irin cin fuskar da za ka yi mini da tozarcin da za ka yi mini ba zai dame ni ba, hakkina dai da yake rataye a wuyanka wallahi ba zan yafe maka ba, ka zalince ni kana k'untata mini kuma ba zaka sawwa'ke mini ba idan an yi duniya don manzon rahama ba zan sake nemanka ba." Ya ce." Hakan ya fi miki Hajiya ai ban hana ki ba idan kina da kwanjin da za ki kwaci hakkin na ki bismillah ai ga ni a zaune." Ta tashi jiki a sab'ule ta kama hanyar fita kamar zata mutu saboda b'akinciki. Har ga Allah ba na jin dad'in fuskar gizagon da yake yi wa Hauwa gabad'aya duka kowa ya gane Hauwa bora ce a gidan zaman ha'kuri take yi masu aiki duk sun gane irin zaman da suke yi da ita da maigidan. Abin ya dinga damuna a ganina ai shi ne namiji kuma jagora ce ya ci ace ya tsahirta da wannan tsatstsauran hukuncin da yake yi mata ta dahu lugub ta yi mugun laushi ta kuma tsunduma a cikin nadamar abinda da ta aikata. Shine bai sani ba ko kuma na ce ya sani yana takewa amma mugun zunubi yake nannagawa kansa domin wannan fad'in Annabi Muhammadu S.a.w ne. Wannan dalilin ya sanya ni ranar da za mu tafi Legos din da daddare na shiga d'akinta na sameta a zaune ita kadai kan gado ta kunna tivi amma gabad'aya hankalinta ma baya kanta kuka take yi tana waya ganin shigowata ta katse wayar tana share hawaye na yi kamar ban lura ba. Na zauna gefenta muka gaisa na ce." Ya gaya miki Legos za mu tafi gobe ko?'' Ta ce." E, ai jiya mun d'an jima muna magana da shi akan tafiyar taku.". Na d'an yi shiru Ina nazarin maganarta wadda na tabbatar da cewa 'karya ce kawai wai ita dole sai ta nuna mini suna shiri bayan komai a bayyane yake. Na ce." Ai da so na yi ku tafi tare idan kun dawo zai sake komawa sai mu je kamar hakan zai fi." Ta yi ya'ke tana cewa." Duk daya ne Amina ku je tare ni zan kula da yara kamar yadda jiya ya gaya mini cewa ya ba ni amanarsu za ku dawo ku same su lafiya in sha Allahu." Kamar zararriya haka take magana a tsorace tunda tasan duk abinda zata fad'a ba gaskiya ba ne shiyasa ta kasa had'a ido da ni.'' Na ce." Hakan ya yi Hauwa dama na ce bari na shigo mu yi sallama tunda da wuri za mu tafi wata'kila kina bacci a lokacin." Kanta a 'kasa ta ce." Hakan ya yi na gode sosai Amina sai kun dawo din.'' Na mike tsaye ina fad'in." To saduwar alheri Hauwa sai mun yi waya." Daga haka ban sake cewa komai ba na kama hanyar fita zuciyata da damuwar halin da take ciki kada fa mutumin nan ya zautata da bak'incikinsa domin duk ta shiririce wallahi........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK.* *V-VIP AREWA PEN* *07084653262* *139* Ba na tsammanin ya yi sallama da Hauwa da za mu tafi haka na bi shi ba don zuciyata ta so abinda yake aikatawa ba sai don sanin rashin yadda zan yi da shi. Tunda tsakani da Allah daidai gwargwado yana da ilimin addini ya kuma san abinda yake yi din ba daidai ba ne. Na zura masa Ido kawai domin nasan muddin bai gyara ba Hauwa za ta sake tafiya gidansu mahaifiyarsa kuma ta samu labari anan sai ta gane cewa shima ya fi kyarfinta ba Hauwa ba ce kad'ai mara ji shima lamba d'aya ne. Zuwanmu legos ya sake haifar mana da nutsuwa da kula da juna da kuma bud'e babin soyayya kamar sabbin aure duk da 'karamin cikin da nake d'auke da shi bai hana mun mori juna ba a duk lokacin da ya zo wajena da buk'ata irin ta d'abia. Daga lokacin na gama gazgata k'aunar da yake mini cewa babu algus ko almundahana domin duk wani nau'in kulawa ina samu da tarairaya har da kyautar kud'i miliyan biyar ya yi mini yana gaya mini na kara akan kasuwancin da nake yi domin yana hankalce da irin nauyi da d'awainiyar da nake yi a b'angarena. Na yi godiya sosai da addu'ar k'ara samun budi da fatahi ya ce babu godiya a tsakaninmu a duk lokacin da nake da buk'atar kudi domin yin wani abu da zai kawo mini cigaba zai tallafa mini saboda yana girmama duk wani wanda yake tsaye don dogaro da kansa karin abin kuma ina ko'karin ganin na yi alheri da taimakawa wad'anda na fi su wadata. Na ji dad'i sosai da sosai dama kuma mun yi magana da anti Yagana akan jari da zan bata ta yi sana'a ta ce mini tana so ta bude shagon jikin gidanta ta fara harkar provision da awo na ce mata harka ce mai kyau sosai kuma za ta samu alheri domin yanzu masu sayar da abinci kayan masarufi sune suke da kudi a hannu. Abinda na yanke a raina cewa ita zan turawa kudin gabad'aya ta fara idan Allah ya sanyawa kasuwancin albarka sai ta zama babbar dila ta bud'e manyan shaguna. Sai dai abinda yake dan damuna shine shin kudin da ya ba ni zai bawa Hauwa ko kuwa. Ina sonsa ba kuma zan yi farinciki da cewa ranar lahira ya tashi a cikin sahun mazan da za a yi musu azaba dalilin fifita bangare daya na daga cikin matansu. Kuma daidai gwargwado Hauwa ta kar'bi kuskuranta yau satin mu uku a Legos idan ba ta kira ni a waya yau ba to gobe za ta kira ni mu gaisa a sati sai mu yi waya biyar ko hud'u mun yi vidiyo call sau d'aya da ita kuma ban hangi nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ita ba. Abinda na fahimta shine kamar tana kamun kafa da ni akan mijin nata wanda ni kuma nasan ban isa na sanya shi ko na hana shi ba tunda ga abinda ya yi wa mahaifiyarsa na yaudara ya nuna mata kamar ya ha'kura ashe akwai abinda ya ajiye a ransa na ramuwar gayya. Na dinga nanata masa kan cewa yadda ya ba ni kudin nan Hauwa ya bata hakkinta ne. Na farko da na gaya masa shiru ya yi mini bai ce komai ba ya cigaba da sabogoginsa tunda ya ce mini yana shirye-shiryen bud'e sabon kamfanin na suminti ne wanda suka yi tarayya da yaran Alhaji Amadu abokinsa Salim da Adam da Nusaiba. Yana so ya fara sanya Salim din cikin harkokin da yake gudanarwa domin ya tsaya da kafarsa a matsayinsa na namiji babba da ake sanya rai a nan gaba zai zama wani abu. Mahaifinsa Alhaji Amadu harkarsa kenan sayar da siminti da sauran abinda ya danganci gini gidaje to shine yake so ya d'ora yaronsa a kai. A k'alla dai sai da na yi masa maganar Hauwa ya kai sau shida tukkuna ya tanka mini da tashin hankali ya rintse idonsa yana gaya mini babu ruwa da duk abinda yake yi na dawo masa da kudinsa idan ba na so tunda bai isa ya yi mini kyauta na ce na gode ba sai na yi masa gyara saboda na mayar dashi jahili Wanda ba shi da addini. Na kuwa bud'e wuta ni ma na ce ai gaskiya ce kuma d'aci ne da ita ban iya munafurci ba kuma zan yi masa shiru ya danne mini baki da kudi mu zalinci wata ba domin ba ni so na mutu da hakkin kowa. Ya ce idan akan Hauwa nake yi masa rashin kunya sai ya saketa kowa ya huta. Na ce masa dama hakan ya yi shi zai kara tabbatar mini da cewa babu wanda ya isa. Magana ce mai harshen damo ya tsargu sosai daga ranar da muka yi haka ya daina kula ni tsayin kwana uku muka yi ba ma magana gashi Muna kwana a d'aki daya a gado daya sai da ya juya baya ni ma na juya nawa. A ranar na hud'u ne muna bidiyo call da Hauwa na ce mata ta had'a ni da yaran mu gaisa na yi hakane domin na daidaita alakar da take tsakaninsu.. Aikuwa da azama ta tashi ta fita falo alhamis ce babu islamiyya ta yamma ina zaune ina kallonta ta shiga dakinsu tana Kiran sunan Khalil. Ya zo ya zauna a gefena ban ce masa komai ba shi ma bai ce mini komai ba amma dai tun shekaran jiya na fahimci jikinsa ya d'an yi sanyi ya rasa yadda zai yi ya rarrashe ni ya kuma nuna zai gyara kuskuransa. Daya bayan d'aya muka dinga gaisawa suna ta tsalle da dariya mussaman Minal sai washe baki take yi. Ya yi gyaran murya yana fad'in." Ni ba bu wanda yake nema ko?" Jin muryarsa ya sanya suka dinga kiran sunansa." Baba" Baba.'' Ya kar'bi wayar ya haska musu fuskarsa sai dariya suna kiran sunansa yana amsawa cikin nishadi yana cewa ni babu wanda yake nema na ko?" Usai ta ce." Baba yaushe za ku dawo?" Ya ce." Mun kusa in sha Allahu ana zuwa makaranta ko?" Suka ce "Eh.'' Ya gyad'a kansa yana fad'in." Muna nan dawowa in Allah Ya yarda." Hauwa ta kar'bi wayar daga hannun Khalil tana hasko fuskarta ta ce masa "Ina yini?'' Ya amsa da sakin fuska har yana tambayarta yara." Cike da jin dadi ta ce." Gasu nan ai suna ta kewa" a Takaice ya ce." Mun kusa dawowa amma ke ba ki yi kewar ba." 'Yar dariya ta yi kamar an yi mata dole ta ce.'' Sosai na yi kewar ku gabad'aya." Ya yi murmushi a hankali ya ce." Duk ranar da na yanke mana dawowar zan sanar dake." Da jin dadi ta furta." To shikkenan." Ya mik'o mini wayata na kar'ba muka d'an yi magana da ita akan yaran sannan muka yi sallama tare da bata sakon gaisuwa wajan masu aikin gidan. Na kashe wayata na ajiye ban dube shi ba na sake hade raina sosai domin har yanzu ina jin haushin bala'in da ya yi mini sai kace 'yar cikinsa daga kawai an ce gaya kayanka.'' Ya riko hannayena duka biyun na dube shi amma ban saki fuskata ba. Sai ya sanya hannunsa d'aya a kumatuna yana ta'be mini fuska da hanci yana d'an murza mini fatar le'be. Tankwa'be hannunsa na yi ya sake mayarwa ya cigaba da ta'bule mini kumatuna da hanci na sake cire hannunsa a karo na biyu. Ya sauke ajiyar zuciya a 'dan sanyaye ya ce." To ki yi dariya mana tunda na yi magana da ita?'' Juyar da kaina na yi gefe ban ce masa komai ba. Ya matso sosai yana fad'in. Ki yi dariya my love menene haka umm! Na ce." Wallahi ka ba ni haushi sosai wai me kake ji idan kana gaba da mutum ne babu kyau fa kuma ba abin burgewa ba ne saboda kawai na baka shawara ka gyara sai ki dinga fad'a mini magana zagi na ne fa kawai ba ka yi ba." Ya d'an yi shiru na wani lokaci kafin ya furta." Na gyara daga yau idan hakan zai kasance farincikinki shikkenan ko?" Shiru na yi tare da ta'be bakina ya juyo da fuskata yana fad'in." Mu yi soyayya ko?'' Ban ce masa uffan ba ya d'ora kansa a saman kirjina tare da zagaye k'unguna da hannayensa yana sakin ajiyar zuciya. Tun daga ranar Hauwa take yi mini vidiyo call a ranakun da yaran suke gida ta had'a ni da su mu jima muna hira. Wannan dabarar ta kara mata kusanci da su kwarai da gaske na ji dad'i sosai kuma ina sa ran nan gaba duka za su manta da abinda ya faru su d'auketa a matsayin uwarsu kamar ni. Ranar litinin da daddare muka yi waya da ita take gaya mini ai maigidan ya sanar da ita cewa za mu dawo alhamis nan da kwana uku kenan. Na ce mata eh haka ya gaya mini ni ma. Mun jima muna magana akan yara tana labari yanzu Sultan na yarda ta d'auke shi yaran kuwa gabad'aya sun daina gudunta. Cike da jin dad'in hakan na ce dama ai sakarci ne irin na yara cikin ko'karin nuna mata kuskuranta na baya na ce ai shi yaro baya son hantara da kyara duk inda ake dukansa ko aka nuna masa tsana zai guji wajen kuma kwakwalwarsa bata saurin mance abu. To a daran ranar da za mu tafi sai ga wayar Idiris mijin Sahura muka gaisa da shi sosai ya fara gaya mini dalilin da ya sanya ya kira ni cewa Sahura ta tare a sabon gidanta kuma ya sanya kwa'do ya kulle tsohon wanda na mallaka mata ya yi-ya yi da ita ta bashi aron gidan ya sanya amaryarsa ta ce 'yan haya zata zuba. Da farko ya kama hayar d'aki daya da rumfa mutum biyu ne a gidan da ya kama hayar to dakunan k'ananu ne gashi iyayen amaryatasa sun yi mata kayan d'aki a matse suke a gidan. Shine yake neman alfarma a wajena na yi mata magana ta d'an ba shi aron gidan su zauna shi da amaryar tasa na d'an wani lokaci. Na yi dariya sosai har sai da jikinsa ya yi sanyi ya dinga fad'in.'' Amina dariya ki ke yi mini tsakani da Allah daidai ne abinda Sahura ta yi mini ai mun zama daya ni da ita kuma ban auri yarinyar nan domin na wulakantata ba Allah Ya kaddara ne kawai." Na ce." To Idiris gida dai na mallakawa Sahura shi tuntuni ka ga ba ni da hurumin da zan ce mata ga yadda za ta yi da shi tunda yanzu mallakinta ne ai daidai ne idan ta zuba 'yan haya ba wata matsala ba ce." Ya furta." Ai na buk'aci cewar ta ba ni hayar gidan ta ce wai ita na waje za ta bawa domin tana zargi kada shekara ta zagayo na 'ki biyan ta wanda ni babu hakan a cikin raina wallahi zan biya ta kud'inta dalilin da ya sanya kenan na kira ki idan ba za ta sanya ni domin Allah ba to ki rarrasheta ta ba ni haya ta fad'i abinda ta yanke da shedu da komai a tsakani duk shekara na biya ta kud'inta.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *140* Na yi 'kokarin danne dariyar da yake ba ni na ce." Idiris a yanzu dai ba ni da wata hujja mai karfi da zan ce da Sahura ta baka gidanta ka sanya amaryarka a ciki. Akwai gidajen haya da yawa a unguwanni mai zai hana ka sanya dillalai su cigita maka sai ka biya hankali kwance ka sanya matarka a ciki ina ganin kamar hakan zai fi kwanciyar hankali." Ya yi d'an jim kafin ciki kame-kame ya fara cewa" To shikkenan zan sanya a nemo mini din amma tunda ita ta ce haya zata bayar da gidan mai zai hana ni ta ba ni akan dai ta bawa wani na waje kuma tsakanina da Sahura ai mun zama dayai shekaranmu kusan ashirin da aure yana da kyau a ce ta gane yadda take da matsayi a cikin raina. Karin auran nan na gaya mata nufin Allah ne amma ta ki kwantar da hankali koyaushe idan na je gidanta da rigima muke rabuwa abubuwan nan da take yi mini bana jin dadi wallahi." Na furta." Sai a hankali za ka ga komai ya wuce amma ni dai a shawarce kawai ka bar mata gidanta ka nemi wani." Ya amsa da "To a sanyaye muka yi sallama na kashe wayata na ci dariya na koshi lallai Idiris ba shi da kunya wato shi gani yake yi abinda ya yi wa Sahura 'karamin abu ne da bai kamaci ace ta daga hankalinta ba ana sa tunanin kenan kuma yanzu Allah Ya dube ta ya kawo mata d'auki ya lallabo su ci tare har yana so su samu sakewa da walwala da matar da ya auro a kuma cikin gidanta. Shi dai kawai ta bashi ya sanya matarsa a ciki amma babu maganar biyan kudin haya fad'e kawai yake yi mahaukaci ne shi ya d'auki kudi ya bata bayan yana ganin gidajen duka samunsu ta yi a sama ba kudinta ne ya saya mata ba. Ni kaina ba ni goyon bayan hakan domin yadda yake munafikin nan ta sanya shi a gidan watarana sai dai mu ji labari ya sayar mussaman idan ya sake tara yara wahala ta sake yi masa yawa. Kuma dole ta ha'kura ta kyaleshi dalilin yaran da suka ratsa a tsakaninsu . Daga na yi juyi sai abin ya fado mini nasa dariya har sai da shigo gidan ya fahimci Ina dariya jefi jefi ya fara tambayata menene na bashi labari yadda muka yi da Idiris din. Tsaki ya ja yana fad'in shima baya goyon bayan hakan tun daga farkon fara neman auran da rikicin da suka dinga yi ya gama fahimtar shine bashi da gaskiya kuma ai duk matar da za a yi wa kishi miji yakan ru'banya kulawa da ita domin dakushe mata damuwa da takaicin abokiyar zamar da za a kawo mata amma shi bai yi ko daya ba ya kuma nuna abinsa nasa ne shi kadai abinta kuma nasu ne gabad'aya mugunta ce tsantsa irin ta wasu mazan. To alhamdulillahi cikin hukuncin Allah muka isa abuja muka samu gida da jama'ar dake cikinsa cikin farinciki da murnar dawowarmu tun daga kan Hauwa zuwa yaran da masu aiki kowa bakinsa har kunne . Sosai na ga can ji mai kyau tsakaninta da su Taburni da akwai girmamawa da kuma mutunta juna. Na ji dadin hakan na yi addu'a a cikin zuciyata Allah ya sanya hakan ya d'ore. Kwana biyu ita take dawainiya dashi ya d'an sake da ita babu kallon kyama ballantana hantara kuma bai nemi da na zo na yi masa wani abin ba har sai da ta yi kwana biyunta tukkuna sannan na kar'bi hidimar tasa. Ranar da muka cika sati daya da dawowa Sahura ta kira ni a waya muka gaisa jin muryarta a cunshe ya sanya ni saurin tambayarta nan take gaya mini Idiris ya sanya an 'balle k'wadon da ta kulle gidanta sun tare da matarsa a ciki itama d'aya daga cikin yaran shagona ne yake gaya mata shine take gaya mini zata d'auko masa 'yan hizba.' K'warai na yi mamakin da jin haka wane irin karfin hali ne da Idiris ne shin ina kudin da ya samu to ai ba zai ce duka miliyan takwas din ce ta kare gabad'aya wajen neman auran matarsa ba. Lallai bai so zaman lafiya ba domin duk da take matarsa tana da 'yancin da za ta nemi hakkinta wace irin gadara ce wannan da son rai." Ta fashe da kuka tana fad'in." Amina wallahi saboda yara nake zaune da Idiris ba na so na kunyata Yallabai dan ganin irin tagomashin da ya yi mini amma wallahi na gaji da guma mini takaicin da yake yi hizba zan kai shi kwanaki fa haka ya kira baban yayanmu Alhaji Rufa'i yana gaya masa wai gaba nake yi dashi saboda ya k'ara aure na daina bashi hakkinsa na auratayya sannan ina fita ba tare da izininsa ba idan na yi abinci bana zuba masa idan ya zo gidan wallahi kuma sharri ya yi mini. AbiΓ±ci wataran ba shi yake yin cefane ba ni nake yin abina aiki kuma dole na fita tunda dama tuntuni shine yake ri'ke da ni da yara a gidan da bana fita aiki da ba mu kai labari ba. Maganar kwanciyar aure kuwa tuntuni na ajiye a gefe bana kaunarsa wallahi shiyasa ko sha'awar ya zo kusa da ni bana yi." Na ce." Lallai Idiris ashe bai d'auki shawarar da na bashi ba kenan. Kwanaki fa ya kira ni yake gaya mini kin hana shi gida kin sa kwa'do kin rufe wai na yi miki magana ki bashi hayarsa domin kayan d'akin da aka yi wa amaryarsa suna da yawa can inda ya kama mata haya ya yi matsatsi ya ce ki yanke kudin da zai biya wai na zama sheda duk shekara zai dinga biyanki." Ta ce." 'Karya yake yi wallahi ta 'karfi da ya ji yake so na bashi gidan akan ban bashi ba ya ce sai dai na ajiye aiki ni kuma na ki ajiyewa shine fa ya gaya yayanmu wai ina fita yawon ma'kota da zuwa kasuwa cefane bada yawunsa ba. Sannan ya bi dare da rana ya buge kwadon da na sanya ya shiga gidan da matarsa suna zaune yau kwana hud'u kenan." Dariya kamar cikina zai ciwo bakina ya mace na kasa ce mata komai saboda dariyar da nake yi ta hana ni maganar har sai da na ji maganarta a fusace tana auno mini zagi! Na danne dariyar sosai ina fad'in." Sahura Idiris takadirin mutum ne wallahi malam bahaushe tsantsa to ki kai shi hizba ki kai wa Sahura an zama daya fa ba zan baki shawarar kai shi hukuma ba don Allah ki rabu dashi wallahi muddin yana zalintarki Allah zai saka miki." Ta ja hanci tana fad'in." Sai fa hukuma ta shiga cikin lamarin nan Amina na rantse da Allah ba zan lamumci wannan rashin mutuncin ba." Na ce." Idan kin kai shi hizba suka tura ku kotu ai kin ga duniya ta ji kuma akwai manema labarai ko babu komai mu kyale shi ya ci darajar su Yusra mana Sahura. Kuma a jikina nake jin idan kin kai shi hukuma zai kara fusata ya ce dole ki ajiye aiki kin ga an biyu babu ko?" Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya irin ta b'akinciki da takaici can kuma na ji kittt ta kashe wayar na shiga duba wayata da mamakin abinda ta yi wato bata ji shawarar da na bata ba kenan. To Allah Ya rufa asiri. *** Wata uku a tsakanin dawowarmu daga Legos cikin da yake jikina ya d'an tasa zuwa yanzu wad'anda muke tare da su a cikin gidan sun fahimci ina d'auke da juna biyu tunda har ya huda zani ya yi kurcici wata biyar kenan ba wasu kwanaki. K'warai da gaske na yi mutukar mamaki ganin sauyin fuska da mu'amula daga Hauwa sabanin lokacin da muka dawo tana masifar haba-haba da ni da son shiga lamarina da kuma yawan yi mini hira idan muna falon gabad'aya amma tun sa'ilin da ta lura da cikin da nake d'auke shi ta sauya fuska ta kuma rage shiga jikina. Ba mu yin gaba dai tunda tana gaisheni kullum da safe ko da ban fito falo ba ta kan biyo ni dakina mu gaisa amma ba ta zama daga tsaye idan mun gaisa sai ta fita. Ta rage zaman falon sosai ta tsiri na d'aki tunda dama da'biarta ce idan tana nukufurci da jin haushi sai ta rufe kanta a d'aki sai ta ga dama take fitowa. Jikina ya yi sanyi sosai ganin halin k'uncin da ta shiga duk saboda ina da ciki menene abin damuwa ga matar da take da cikin haihuwa kuma take da mijinta a hannu. Don na d'auki ciki itama rabo yana rantsewa za ta d'auki nata abinda dama maigidan yake buk'ata kenan ni da ita har yanzu ba mu wuce haihuwar ba to ban ga abinda zai sanya ta daga hankali ba a ganina ni zan yi wannan damuwar tunda ta d'ara ni da 'daya har da namiji a ciki ni kuwa nawa duka mata ne kuma ban yi mata ganin kyashi da kishi ba. Ana haka maigidan ya tafi bunkure dalili an fara gudanar da aikin rushe gidan Malam D'aha kamar yadda ya yi alkawari zai sabunta masa gidan da gini na zamani kuma zai gyara masa tsangayunsa. Ya ce mana zai yi kwana uku ko hud'u domin bayan ya gama da gidan Malam D'aha zai gudanar da wasu al'amuran da duba ma'aikutunsa da suke jahar. Washe garin ranar da ya tafi ta yi bakuwa. Kallo d'aya na yi mata na sheda ta 'yar uwar nan ta ta ce da muka yi wani zuwa garin nasu domin gaisuwar mutuwa wadda ta dinga shige da fice tana kallona a lokacin har sai da ta magantu. A falo ta zauna tunda lokacin da ta shigo duk muna zaune a falon gabad'aya muka gaisa sosai da ita ban nuna mata komai a fuska ba take fad'in wai Seminar suka zo garin shine ta ce bari ta zo mu gaisa.. Cikin raina na ce ki gaisa dai da 'yar uwarki. Anan falon ta ci abincin da na sanya Baba Tabawa ta kawo mata sai da la'asar ta yi tukkuna suka tashi suka shiga d'akinta tare. Ni ma a lokacin na tashi na shiga d'akina domin yin alwala. Ina idar da sallah da kamar minti biyar kira ya shigo wayata na daga a nutse na gaishe shi ya amsa yana fad'in." An ce mini kun yi ba'kuwa ko?'" Na ce." E, bak'uwar Hauwa ce daga bauchi ta zo wata Seminar ne nan." Ya furta ya sunanta?" jim na yi kamar Sadiya na ji tana kiran sunanta. Ya ce." Ba ni son shige da fice ya yawaita idan ba na gari ku kula sosai." Na ce." In sha Allahu rabbi ranka ya dad'e." Ya d'an saki ajiyar zuciya yana fad'in." Idan na gama abinda nake yi anan zan wuce maiduguri domin duba Dada ba ki da sa'ko?" Na ce." Kash! amma ba ka kyauta mini ba wallahi tare fa muka yi da kai za mu je shine zaka zame ka yi tafiyarka kai kadai." Ya furta." Ki bari ki haihu ki samu lafiya sosai sai ki je in sha Allahu." Na ce." Shikkenan yaushe za mu yi tsammanin ganinka ?" Ya d'an yi jim kafin ya furta nan da kwana uku in sha Allahu." Na ce." To shikkenan Allah ya dawo mana da kai lafiya." Ya amsa da Amin ki shafa mini kan yarana gabad'aya a ce ina gaishe su." Ina dariya na furta." Zan gaya musu in sha Allahu rabbi." Sallama muka yi na ajiye wayar ina murmushi wanda na kasa tantance ko na menene. Yau su Baba Tabawa Jallof suka yi na shinkafa da tafiya sai suka yi amfani da bushashan kifi ta ji alayyahu da albasa ta yi kyau ainun a ido kuma na tabbatar da cewa za ta yi dadi amma bata ni sha'awa babdon ko da ta kawo ta ajiye mini ita a gabana sai na ji tana tashin karnin kifi wanda na tabbatar da cewa hancina ne kawai da kuma tsagunaguni na mai juna biyu. Ko loma daya ban iya ba na ce ta d'auke plate din ta yi yadda nace din ta zo tana tambayata ko akwai abinda nake buk'ata tunda da sauran dare sai ta yi mini." Na dube ta tausayi suke ba ni dattijan kwarai da gaske har gwara Taburni ta haihu har da jikoki ita kuwa Baba Tabawa bata ta'ba haihuwa ba sai jigila take yi da mu da yaranmu ga shekaru jiki da jini don ma jikin ya horu da aiki ni dai sai nace tunda nake da ita ban ta'ba ganin ta kwanta ciwo mai tsanani ba hana karya lokacin da muke kano ba ta jima da zuwa ba ta ta'ba wani ciwon kai wanda ya d'auketa tsayin kwana uku a kwance tunda na kaita asibiti aka duba ta da maganguna ta warware daga lokacin ban sake jin ta ce mini ba ta da lafiya ba. Paid book ne wannan littafin kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Na ce kawai ta bar shi idan zan kwanta zan sha tea wannan ba shi da matsala da kaina ma zan hada abina. Ta amsa da to kafin ta juya domin komawa dakinsu. Hauwa ta fito ganina a falon ni kadai sai ta tsaya tana fad'in." Ni kuwa Amina wanene ya gayawa maigidan Sadiya ta zo?" Na dube ta a tsanake kafin na furta. Kya tambaye ni Hauwa ko kuwa ni kadai nake rayuwa a gidan kin manta tun daga bakin gate gidan cike yake da masu tsaro saboda kin yi bakuwa sai na kira shi na gaya masa kenan?' Ta fara dariya irin ta kare kai tana fad'in." Haba Amina ni ban tambayeki domin na fusataki ba ya kira ni ne da fad'a yana cewa mu kula da masu shigowa sai naga tunda na zo gidan nan babu wani d'an uwana da ya ta'ba zuwa sai yanzu Sadiya ai ba bare ba ce 'yar uwata ce da babanta da mahaifina uwa daya uba daya suke." Na ce.'' Wannan kuma damuwarki ce Hauwa kina so ki gaya mini cewa ni nawa 'yan uwan tarewa suka yi a gidan kenan ko?" Ta girgiza kanta tana cewa." Na ga kin hasala daga tambaya sai cibi ya zama 'kari Amina ko dama haushina ki ke ji ne ban sani ba ko kuwa zuwan Sadiya ne bai yi miki dadi ba." Na ce." Me yasa zan ji haushin Sadiya me ta yi mini Hauwa wai ke don Allah an gaya miki kowa yana da tsatsar zuciya ne. Bayan Sadiya ki kawo wasu gidan nan su zauna bai dame ni ba Hauwa." Murmushi ta yi bata sake ce mini komai ba ta nufi kicin. Ina nan zaune ta fito da wasu madaidaitan mazuban abinci ta wuce ni. Tsaki na ja can k'asa na tashi na shige d'akina. Wai tambayata take yi wanene ya gaya masa ta yi bakuwa saboda raninin hankali yadda ya kira ta a waya yana tuhumarta ni ma haka ya kira ni ita dai har yanzu ta'ki zama da ni da zuciya daya. Can wajan sha d'aya na ji yunwa ta yun'kuro mini tabbacin tea din da na sha ba zai d'auke ni ba. Na tashi da azama na nufi kicin din fatan doya nake sha'wa wanda ya ji attaruhu. Daf da zan shiga kicin din na ji kamshin wainar k'wai. Na ji muryarta tana fad'in." Kina nan da cin dad'i dai Sadiya ba kya gajiya da ciye-ciye tsakani da Allah cikin daren nan kin tashe ni da soya kwai " Na ji maganar ita Sadiyan tana fad'in." Laulayi ne ya sanya ni a gaba Hauwa dama ya ya lafiyar kura da kwad'ayi tunda na samu cikin nan yake cin kudi wallahi kullum sai Babansu Haidar ya sayo mini balangu." Ta ce." Wai ba wani sirri da za ki ba ni ne Sadiya wani lamari ne yake damuna wallahi na rasa yadda zan yi na shawo kan matsalar nan ina cikin damuwa mai tsanani. Na ji tana cewa." Menene kuma ke dai kullum cikin korafi kike Hauwa yana da kyau don Allah ki yi amfani da shawarwarin da muke ba ki. Na gaya miki ko kin sanya ana yi miki taimako dole sai kin had'a da kissa da addu'a kuma. Sannan na fahimci matar nan ba ta da hayaniya kuma tana da kirki daidai gwargwado don girman Allah ki kwantar da hankalinki ku zauna lafiya da juna." Ta ja tsaki tana fad'in." Duk ina ko'karin yin haka Sadiya amma ba zan boye miki ba wallahi ina tsananin kishin amina. Tabbas abinda ki ka fada a kanta gaskiya ne macace mai kirki da kawaici kuma bata da mugunta ko kad'an wallahi duk lokacin da ta lura na yi fad'a da maigidan ta dinga kokari sasanta mu kenan amma duk da wannan abin da take yi ba na jin zuciyata za ta daina jin zafinta dalilin yadda maigidan ke nuna mini cewa ya fi sonta wannan zahiri ne na tabbatar da haka yana mutuwar sonta ko alwashi ya ci akan abu idan ta yi magana sai ki ga ya sassauta. Sai abu na biyu yau watana kusan hud'u da dawowa gidan nan har yanzu bai yi auratayya da ni ba. yana dai yi mini magana har na kai masa abinci ya ci amma zamu kwana d'aki daya baya kallona duk yadda na kai wajen janyo hankalinsa wallahi ba ya sauraranta Sadiya abin yana yi mini ciwo sosai na kai kaina wurinsa ya fi a kirga na yi shigar da zata sanya ya ji sha'awata amma ko gezau ba ma ya kallona balle na sanya a raina zan rinjaye shi. Abinda yake ta damuna ganin ta samu ciki ni kuma ina so na fita yawan 'ya'ya a gidan nan Wallahi....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/HmWvZBqszkCFRsRaL0UYUZ *PAID BOOK VIP 2K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA 1k VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *141* Sai na ji tana fad'in." Ai kin fita yawan 'ya'ya Hauwa maza biyu fa da mace daya mu kaddara yanzu mutuwa ta riskeshi cikin kashi uku na dukiyarsa ke ki ke da kashi biyu ita da mahaifiyarsa su d'auki kashi d'aya to menene abin damuwa nan". Ta ce." Duk da haka dai Sadiya hankalina ya'ki kwanciya wallahi tunda na ganta da ciki nake sha'awar ni ma na samu haka kawai zuciyata ta ki nutsuwa duk yadda na ke ko'karin ganin na danni zuciyata akan abinda take bijiro mini wallahi na kasa Sadiya babban kalubalan da yake damun zuciyata k'aurace mini da ya yi a shimfida ya kuma yi alkawari kan cewa ba zai sake kusantata ba balle na d'auki ciki na haihu. Kin ga kuwa idan ban tashi na nemi mafita ba ina ji ina gani nata yaran za su wuce nawa." Ta d'an yi jim kafin na ji tana fad'in." Ba zan b'oye miki ba Hauwa abokiyar zamanki ta fi ki kyawun gani tana da jiki mai kyau da diri ta ko'ina kuma mafiakasari mazan yanzu ba kasafai suke son ramammun mata ba. Ki dube ki don Allah kin yi zama 'yar fiyau ya kamata a ce kin yi ko'karin ganin kin fi haka murmurewa komad'ar jikinki ta dawo yadda zai dinga sha'awarki har ya mata da alkawarin da ya d'auka na daina kusantarki." A raunane ina jin lokacin da ta ce." Da kamar wuya Sadiya duk yadda zan zama wallahi ba ni ce a zuciyarsa ba Amina ce ya fad'i ya sake fad'i baya jin nauyi da kunyata haka yake gaya mini ya ba zan ji haushinta ba abu ne mai wahala na iya cire ganin k'yashi a kanta tunda an fifita ta a kaina ko yanzu da nake yi miki wannan maganar wallahi a buk'ace nake irin ta dabi'a amma haka zan ta dannewa wannan kaydai ya isa ya jefa rayuwata cikin garari tunda ban san yadda zan yi na kawar da buk'atar ba." Ta ce." Akwai zalinci da cutarwa amma na d'an fara zargi anya ba farra'ku aka yi muku ke da shi ba. Ina ce ai ya san zunubi ne mai girma yak d'aukarwar kansa idan yana hayyacinsa a ganina ba zai aikata hakan ba lallai akwai dalili wata kila an dasa masa kyamarki a zuciyarsa" Ta ce." Ba na tsammanin haka Sadiya ai na gaya miki hujjarsa ta k'aurace mini saboda na ajiye Sultan yana jinjiri na tafi gidanmu shine dalili wai ba zai sake kwanciya da ni ba." Ta ce." To shawara ta karshe da zan baki shine ki gayawa mahaifiyarsa domin kuwa akwai k'wara da cutarwa gaskiya idan abin ya yi yawa kina iya shiga wani yanayi wanda ba ma fatan hakan." Shiru ya biyo bayan maganar Sadiyan ban ji Hauwa ta sake wata maganar ba. A hankali jikina babu kuzari na koma d'aki na zauna tare da nazari da tunanin maganganun da na ji suna tattaunawa. A lallai ban ga lefin Hauwa ba don ta tsananta kiyayyarta a kaina dama akan ce idan ka ga gida ya gyaru daga maigida ne idan ka ga zaman lafiya ga kishiyoyi to an samu foundation daga wanda ya assasa zaman. Sau nawa ake yin irin wannan auran nasu na hadin iyaye a samu daidaito da zaman lafiya kuma a tara zuria. Na ji daga bakunan mutane da yawa cewa k'iyayyar namiji ta fi ta mace amma ban ta'ba tsammin 'kin da yake yi wa Hauwa ya kai haka ba. Babu wata mace da za ta iya jure wannan cin mutunci da zarafi ya dinga dubar tsabar idonta yana gaya mata ba na son ki ga wadda nake so. Maganar k'auracewa a shimfida shima babban jidali ne mai girma wanda waliyyai ka iya shigowa ciki. Mai yasa lokacin da ya yi mini irin haka na kasa hakuri ni ma abinda ciwo sosai kuma ta yi hakuri da shi tana kuma son zama dashi duk da a cikin maganganunta akwai wad'anda na d'ora ayar tambaya a kai amma me duk abinda yake wanzuwa a yanzu da sanya hannunsa idan Hauwa kishi da bakincin fifikon da nake samu a wajensa fiye da ita ya d'ebeta ta yi mini wata illar kamar yadda muke ji ko mu gani social media yana da kamasho tunda ya bi son rai wajen gina gidansa kuma ya take mata ha'kkinta na aure. Hauwa ko bata fad'a ba nasan ba ta sona a zuciyarta kawai tana ko'karin dannewa ne abin ya 'kara tsamari da tsanani sakamakon yadda d'aukakata ta dusashe ta ta a wajensa A tak'aice dai da yunwa ta na kwana a daran sakamakon nazari da tunanin al'amarin da suke faruwa. Da wuri na fito na samu su Baba Tabawa a kicin sun soya fanke da kunun gyad'a ya yi kyau da haske na ji dad'i kuwa muka gaisa kafin na d'ebi daidai cikina na fita. Ina karyawa suka shigo tare ita Sadiyar cikin shirin tafiya muka gaisa da sakin fuska tana fad'in tafiya za ta yi a takaice na furta." To Allah Ya kiyaye a gaishe da mutane gida. Suka fita tare Hauwa ba ta ce mini komai ba tun bayan gaisuwar da muka yi kana kallonta za ka karanci damuwa a tare da ita. A zahiri a kwai buk'atar zama a tsakaninsa da ita amma yanayin yadda take nuna mini bakin 'kyashi da kishi ya sanya na yi alkawarin cire hannuna a lamarinta. Ya kuma zame mini dole na kara yin nesa da ita dalilin gudun abinda ka iya zuwa ya dawo tunda mugun nufi ne fal a zuciyarta game da ni. Na kudi ne littafin nan kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Yammacin litinin ya dawo kamar yadda ya gaya mini da muka yi waya shekaran jiya daga d'akina ya fita ranar da zai tafi don haka ina yi masa sannu da zuwa na sau'ko k'asa. Ita kuma ta hau ba ta sauko ba sai gefin magriba shi ma ya sauko da shirin massalaci sai da ya dawo tukkuna ya zauna a falon yaran suka taru a wajensa yana ta wasa da su. Ka'ida ne idan yana falon masu aikin basa fitowa sai ya kasance ni da Hauwa ne kadai a zaune da yaran ana ta wasa da dariya. Hauwa ta ci ado da jins da 'yar k'aramar riga sai ta yafe wani bakin mayafi a kanta. Wallahi tausayi ta ba ni ainun ganin wanda ta yi wa kwalliyar ba ya yi mata irin kallon k'aunar yake yi mini. Yana dai amsa mata magana idan ta yi amma ban hangi wani shau'ki da jin dad'in kin burgeni ba abinda yake yi mata ya sanya ni jin kunya da nauyi ta tashi ta shiga d'akinta ya kai sau uku ta fito ta zauna amma ban ce ya san abinda take yi ba. Ya dube ni yana fad'in." Yarinyar nan Hajara ta sake ba ni sa'ko wajenki yana mota." Jin haka ya sanya Hauwa yin kicin-kicin da fuska domin yanayin yadda yake sako ni a maganarsa ya fara bata haushi gashi kuma ta ji an ce an bada sa'ko a kawo mini." Na furta.'' Aikuwa na gode sosai a sanya a kawo nasan abin motsa baki ne." Na fadi hakane domin ko menene a bud'e shi a gabanta kada ta zargi wani abin tunda ita dabi'arta ce." Ya d'auki wayarsa kuwa da sauri ya kira Sukairaju ya ce ya duba cikin mota zai ga wata leda mai zane-zane ya d'auko masa ita. Muna zaune kafin Sukairaju ya shigo ya miko mini wayarsa yana fad'in." Duba gidan Malam D'aha an fara aiki." Na kar'ba da sauri da fara'a ina fadin." Alhamdulillahi na fara dubawa an rushe gidan gabad'aya aiki ma ya fara nisa. Na mik'a mata wayar ina fad'in." Gidan Malam D'aha ne za a sabunta shi." Ta kar'ba da d'an murmushi irin na saman lebe tana dubawa na dube shi ina cewa." To suna ina yanzu?" Ya ce." Na sanya su a wani gidan daga zarar an kammala aikin an gyara musu ko'ina za su koma." Na ce." Na yi musu murna sosai Allah ya saka maka da alheri." Ya amsa da Amin a takaice." A maimakon ta miko mini wayar kamar yadda na bata sai ta tashi tsam! ta nufe shi da wayar a hannunta. Na bita da kallo cike da mamaki da tausayi da dariya wai ita dole sai ya ga kwalliyar k'ananun kayan da ta yi. Koda ta bashi wayar sai ta zauna a gefansa tana dan janyo hannun Sultan da yake kusa dashi a tsaye ya dafa gwiwarsa yana dabo (ta-ta-ta) Ya kuwa fad'i timm! ya tsalla kuka da kar'fi tunda daman sai da ya dafa kujera ya tashi. Aikuwa ya juya yana kallonta da harara yana ce wa." Menene haka? kina zaune can kin zo kin sanya yaro kuka yarinya ce ke?" Ba ta ce masa komai ba ta d'auki yaron domin rarrashinsa ya dinga zille-zille yana kuka shi kuma sai tsaki yake ja tabbacin haushinta yake ji dangane da kukan yaron tana jijjigashi ya'ki yin shiru sai ta dubi Khalil cikin muzanta da jin kunyar abinda yake yi mata ta ce." Kira Baba Tabawa ta zo ta d'auke shi." Ya furta" D'auke shi kai maza kai mata shi ta goya shi." Ya d'auke shi da sauri tare da nufar d'akin su Baba Tabawa da shi yana ihu shima yana son kasancewa da uban da 'yan uwansa. Sukairaju ya shigo da leda mai zane-zane a hannunsa. Mu ka gaisa cikin mutuntawa na ce." Ni za ka bawa ai." Ya miko mini ledar yana murmushi ya juya ya fita. Ko da na bud'e sai na ga dangin su goruba ne da kad'anya gauta da yalo da d'ata har da alawar madara a cikin wata farar Leda. Ina dariya na daga kaina na kalleshi tare da cewa." Yarinyar nan ta iya bada sa'ko fa." Bai ce komai ba hankalinsa na kan k'aramar wayarsa. Minal ta zo tana le'ka kanta cikin ledar "Mama menene?'' tana fad'a tana k'ara zura kanta ciki. Na ce" Zo mu je kicin a wanke kayan dadi ne." Ta kuwa biyo ni da saurinta twins suna zaune da wayarsa a hannunsa game ya kamo musu. Na cire ledar alawar madarar na jika musu gorubar domin ba za su iya cinta a bushe ba. Abu ne da ba su saba dashi ba sosai sai ya zame musu kamar nama. Yalo da d'ata da kad'anya duka na gyara musu suka kewaye ni muna ci Hauwa ta ce ba ta yi sha'awa ba wanda na tabbatar da cewa ta fadi hakane kawai saboda zuciyata tana yi mata zafi babu wata maccan da ko babu uzuri na juna biyu ta ce bata marmarin irin wad'annan kayan gonar. Ganin yadda muke ci da yaran ya ce shi ma a bashi daya. Usai ta d'auki yalo 'kato ta kai masa. Ta d'auki wani ta tafi wajan Hauwa tana mika mata. Ta kar'ba amma sai ta ajiye shi saman cinyata ta yi shiru duk ta yi sanyi abin gwanin ban haushi da tausayi domin dai Hauwa ko kana jin tausayinta idan ta kuntuka maka wani takaicin sai ka ji kamar ka rufe ta da duka saboda haushi..... Daga karshe ma sai kawai ta tashi ta shiga d'akinta ina hankalce da shi bai bita da kallo ba balle ya shiga damuwa don ta bar wajen. Ta gama kwanaki biyunta ban san wainar da suke toyawa ba. Na kar'bi girki na kasance cikin walwala da farinciki kamar yadda shima ya kasance duk wata hanyar da zata kara mini mutunci da soyayya ita nake bi a yanzu muddin bai shigo mini da son zuciya ba kalau muke zaune a yanzu kuma idan zai nemi ni sau nawa ba na nuna gajiyawata jikina ya horu kwarai da dabi'arsa sai aka yi katari da wannan cikin da nake d'auke shi ba mai k'yamatar lamarin ba ne. Na kwana biyu ban ji daga Sahura ba ina jin tun bayan wayar da muka yi take gaya mini Idiris ya buge kwado ya shiga gidanta babu yawunta sau biyu muka kara yin waya kuma idan na soko mata da maganar abinda yake faruwa a tsakaninsu ba ta saurarata fadi take yi ta daina gaya mini matsalarta tunda ni ma goyon bayansa na ke yi. Katsam yau ta kira ni tana gaya mini tana zargin fa auran da Idiris ya k'ara ya gurgud'e. Na tambayeta dalili ta ce mini kullum a gidanta yake kwana tsayin sati uku kenan kuma neman shiri yake yi da ita. Jikina ya yi sanyi sosai Idiris bai shirya ri'ke musu yarinya ba ya aura aure duka bai fi wata hud'u ba an fara cin karo da matsala. Ta ce mini ai tana zargin ma yarinyar tana da juna biyu ta ji Yayarsu wato uwar mijin Yusura tana fad'a a wata had'uwa da suka yi a gidan sunan k'aninsu amma dai ba su fito sun fad'a mata cewa sun rabu ba ta ji dai suna fad'in saura amaryar Idiris a jerin masu haihuwa domin itama ciki ne da ita.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *142* Na cika da mamaki 'kwarai da gaske da jin wannan lamari ni babban takaicina ma yadda yake ko'karin mayar musu da yarinya k'aramar bazawara tunda a yadda take ba ni labari duka bata fi shekara ashirin ba idan hakane kuwa ai da kadan ta girmi Yusura. shari'ar aure ba a yanke ta kai tsaye amma jikina yana ba ni cewa matsalar daga wajansa take wanda itama Sahura take zargin hakan domin ta ce har yanzu ya'ki yi mata bayanin komai sai kame-kame ya yi da kuma neman shiri da ita to kuwa duk yadda ya kai ga b'oyewa dole watarana kowa ya ji dalili mussaman a nasa b'angaran tunda har tana da juna biyu Allah kyauta ya kuma rufa asiri shine kawai abinda za a ce. Kwana bakwai da dawowarsa guda yake gaya mini na shirya satin da za mu shiga juma'a kenan za mu je jigawa d'aurin auran Alhaji Sulaiman mijinsu Hajiya Aziza. Idan an daura za mu kwana d'aya sai mu dawo gida. Na ce masa to shikkenan, cikin zuciyata ina ta mamaki ashe auran da na ji kwanaki yana fad'a da gaske ne. Kuma wata'kila budurwar zai aura lallai tsufa ya yi gardama an kuma shigo da son zuciya iyayen yara da su kansu masu auran yara k'ananu. To Ashe tana jika a cikin gidana ni ma. Ni dai bayan dawowarmu daga d'aurin auran Alhaji Sulaiman kamar yadda ya fad'a sai nake ganinsa wani sukuku babu irin sa'ke-sa'ken da zuciyata ba ta yi mini ba akan ganin ya canza na d'an ta'kin lokaci. Zuciyata na kawo mini ko shima ya yi sha'awar budurci ne tunda mafiakasarinsu abinda sukewa kulafuci kenan ya sanya suke ture kunya da kawaici su auro 'ya'yan cikinsu su kwanta gado daya da su. Na zura masa ido kawai yanayin yadda ya fara tafiyar da al'amuransa na rashin walwala da yin shiru da nazari ni ma sai na tsiri yin hakan muka cigaba da tafiya a haka bai gaya mini damuwarsa ba ni ma ban nemi da na ji ba. A d'ayan biyu ne ko matsalar kasuwanci ko kuma shi ma auran yake nema amma kuma yana cike da zullumi da damuwa ga yawan kallona da yake yi daga zarar mun had'a ido sai ya wayance ya tsiri yin wani abin. Yanayin da ya 'kir'kirarwa kansa bai hana shi yin mu'amula da ni a duk lokacin kwanan aurena ba. Hauwa dai har yanzu jiya iyau domin ga dukkanin alamu cutar damuwa(Depression )ddaf take da ta kamata abin gwanin ban tausayi da takaici. Ana haka Sahura ta kira ni take gaya mini Idiris suna kotu da amarya iyayanta sun buk'aci ya saketa ya ce sai an biya shi abinda ya kashe kafin auranta. Alkali da ya nemi jin dalili kaf aka gaya masa. Duk wata hidima ta gida ya gaza sai masifar kwanciya da yake yi da yarinyar mutane babu dare babu rana ga rashin k'oshi tunda ya yi na amarci ya jingine k'aramin buhun shinkafa da rabin kwalin taliya da makaroni da kwalbar manja da mangyad'a da had'in maggi. Da suka 'kare sai ya shiga auno mata wake yace ta dinga yi fate-fate yana 'kara jini tunda tana da juna biyu sai ta fi sati daya tana cin wake fate ko 'kulu da mai da yaji da safe ya sayo mata kunnu da awara. Yadda yarinyar take fad'a tana kuka sai ya shigo da leda cike da abin dadi ya zauna ya ci a gabanta ya bar ta da tsotse 'kashin da ya sale masa tsoka. Ya kuma isheta da bala'in kwanciya da daddare ga rashin abinci mai kyau. Da ta ce ta gaji da cin wake sai ya auno mata tsakin masara mai yawa da barkono da farin maggi da manja wai ta dinga yin d'anmalale. Yarinya mai garin jiki duk ta tsotse gashi baya dawowa da wuri sai sha biyu na dare wataran har da rabi tukkuna zai sanya mukkuli ya bud'eta tunda idan zai fita kulleta yake yi ta ciki yau da gobe ta'ki wasa har dai iyayenta suka gane wuya yake bata yaran shago ma suka bada shedar kulleta yake yi kuma wataran akan idonsu yake dawowa tunda suma suna kaiwa sha biyu na dare ba su tashi daga aiki ba. Sosai na tausayawa yarinyar. Ita kuma Sahura sai na lura kamar murna take yi tana fad'in hakkinta ne domin duk auran da aka gina shi akan zalinci da kwadayi k'arshensa kenan wallahi ba zata rike masa d'an ko wace shegiya ba. Na ce." Ke abinda yake damunki kenan ko Sahura an ce mijinki yana raba dare a waje shi ba wani business yake yi ba na cin kasuwar dare ba balle a ce ba ki yi tunanin wani abu ba?" Ta ce." Ba zai wuce yana yawon neman mata da d'an kudin da ya samu ba, ai ki bar d'an iskan namiji Amina kin ga ni ban ci ba haka zalika yarinyar mutane ma da ya auro bata ci ba ya tafi yana kaiwa matan banza shiyasa tunda ya yi auran nan kamar na sani ban sake ba shi kaina ba." Na ce." Lallai akwai buk'atar ki sanya ido akan Idiris Sahura kada kishi ya sanya nan gaba ki yi nadama idan ya kasance Idiris ya fad'a harkar bariki kina da kamasho tunda ke kin San wanene shi gashi kina ba ni labarin irin durzar da yake wa yarinyar mutane yanzu da babu ita ai zai sake tsunduma tunda ke kin daina ba shi kanki. Haihuwar da ta ratsa tsakaninku ta wuce komai." Ta ce." Haka kowa yake cewa Amina amma bari kiji wallahi yadda Idiris ya cire kawaici a kaina ya gwada mini rashin Imani babu wani dalili da zai sanya ni don ya shiga matsala a yanzu na damu. Na gaya miki fa yanzu ko ya sake ni ba ni da damuwa Allah ya yi mini rufin asiri ina da matsuguni da 'yan kudi a asusuna zawarci zan buga mai kasafiti Hajiya." Dariya ta kama ni na ce." Sahura ki dai yi tunani akan maganata ki yi hakuri ku samu daidaito don Allah ko saboda yaranmu babu dad'i Idiris ya lalace dole za a danganshi dake ace tsohon mijinki ne kuma uban yaranki. Ta furta." Ai ko zamu daidaita ba dai yanzu ba Amina wallahi yadda ya gumami ni ba'kinciki in sha Allahu masifar da zai tsinci kansa sai ta shige wadda ya jefa ni." Da haka muka yi sallama tunda duk ta inda na biyo sai ta doje ta nuna yanzu ba lokacin da ya dace a ce ta tausaya masa ba ne. A daran ranar da muka yi wannan tattaunwar da Sahura bayan isha'i muna falon gabad'aya masu aiki da yaran ban da Hauwa da yake girkinta ne tana ta kai wa da kawowa daga kasa zuwa sama. Na ce da Baba Tabawa ta kawo mini abinci. Towon shinkafa suka yi miyar taushe da tantakwashi. Sun jima ba su miyar taushe a gidan ba wannan dalilin ya sanya mini mugun mararin son cin towon. Ina ci muna hira da su jefi-jefi Hauwa ta sakko kai tsaye dakinta ta nufa sai ta d'an tsaya tana kallona kafin ta ce." Maigidan fa baya jin dad'i Amina." Gabana ya buga da k'arfi a take a lokacin na ji abincin ya fitar mini daga rai Allah ma dai ya sa na ci da yawa. Na daidaita yanayina sosai kafin na ce." Mai yake damunsa?" Ta d'an ta'be bakinta tana fad'in." Ciwon kai na ji yana gayawa likitansa yanzu tun rana da shi dai ya yini na yanzu ya yi tsanani ko 'daga kansa baya iya yi yana kwance." Na yi 'kasa da kaina abin har ya kai ga kwanciya irin haka wace irin matsala ce take damunsa da har zai ajiyeta a ransa ta haddasa masa ciwo. Ta shige dakinta ba ta sake yi wata magana ba. Kafin na haura saman sai da na sanyo hijabi jin cewa likitansa yana kan hanya Yana kwance shar'be a gado ya dafe kansa da hannunsa. Na zauna gefansa jiki a mace ina fad'in." Baba baka da lafiya ashe?" Ya dube ni da gefan ido ya furta." Ciwon kai ne Amina yanzu nan ya sake tsananta." Na ce." Kana jin sa ashe a hankali a hankali ba ka yi magana ba sai yanzu da ya kwantar da kai an ta'ba wasa da lafiya ashe." Ya yi shiru bai ce komai ba. Na gyad'a kaina ina fad'in." Ni ba yarinya ba ce duk yanayin da kake ciki ina hankalce ban buk'aci dole ka gaya mini sirrinka ba wata'kila baka son kowa ya sani shiyasa ka yi shiru abin yana cin ranka ya kamata a ce ka sassautawa kanka dalilin gudun faruwar mummunar abu akwai shekaran girma a tare dake kuma idan ban manta ba kana da hawan jini bai kamata a ce ka dinga ajiye wani abu a cikin ranka ba. Amma ina so na gaya maka cewa ko ka fad'a ko baka fad'a lallai kana cikin damuwa domin gabad'aya al'amuranka sun canza a tsukin lokacin nan." Ya yun'kura ya tashi zaune yana kallona da wani irin yanayi ya ce." Lallai ina cikin damuwa Amina amma ban san yadda zan yi na fitar da kaina daga cikinta ba." Na ce." Duk abinda ya yi tsanani ai maganinsa Allah kaine ka ke da hanyar fitar da kanka daga cikinta idan ka sanya hakan a ranka." Ya gyad'a kansa yana kallona amma bai ce komai ba. Jikina ya sake yin sanyi na d'an riko hannuna a hankali na ce." Idan babu takurawa ka gaya mini damuwar da take damunka ko Allah zai sanya ina da shawarar da zan baka." na kudi ne wΓ nnan littafin Yar uwa don Allah a duk inda za ki gan shi kada ki karanta sai kin biya ni hakkina. Ya furta." Malam 'Daha ne ya ba ni 'yarsa amma ban san ko wacece daga ciki ba, kin san dai gidansa cike yake da yara ko?'' Kunnena ne ya yi dumm! kamar irin kumfar sabulu ta shiga ciki na ji ya sake rintse hannuna yana fad'in." Ban zan iya bijire masa ba Amina wallahil-azim ba zan 'ki 'karbar tayinsa ba." Na zuba masa ido kawai ina kallo bakina ya yi nauyi na rasa ma abinda zan ce saboda zahiri na 'kadu da jin maganar nan gidan Malam D'aha babu wata cikakkiyar budurwa duk matasa ne kuma mafi akasari daga sassan gidan suke fitowa alamu sun nuna wasu daga ciki 'ya'yan yaransa ne irinsu malam Rabi'u. Jikokinsa kenan Hajara ita ce kadai 'yar budurwar da ta fara tasawa tunda ta fara 'kirgar dangi sun yi cibir-cibir a cikin riga ba ma su kai a sanya musu rigar mama ba. Na daure na ce." Ai duk babu wata budurwa cikakkiya a gidan Malam D'aha." Ya ce." Akwai uku da bai aurar da su ba sauran jikokinsa ne a cikin ukun ya ba ni d'aya ban santa ba ni ma." "Hajara ce abinda zuciyata take raya mini kenan. Muka yi shiru ni dashi muna duban juna Hauwa ta shigo sanye da hijabi a jikinta ta same mu a haka mun k'urawa juna ido ga hannuwanmu a ri'ke ta kasa jurewa muryarta tana rawa ta ce." Ka ce baka da lafiya maganar duniya na yi maka baka tanka mini ba kana kwance kana jina yanzu gashi kuma yanzu na shigo na gan ku ma'kale da juna wallahi Amina ku ji tsoron Allah hakkina ba zai bar ku ba ba zan ta'ba sahale muku ba a ranar lahira." Na juya da mataccen jiki ina kallonta. Wata gaud'iya da ita ana ga gabas tana ga yamma. Karamin tsaki kawai na ja ban ce komai ba na cire hannuna daga cikin nasa. Ya sake kamowa yana fad'in." Kin ce akwai shawarar da za ki ba ni ko Amina wallahi ba ni son auran da ake ko'karin ma'kala mini abinda yake zuciyata na gaya miki tunda kin matsanta ki ji kada ki d'auki maganata a matsayin dad'in baki a yanzu dai babu ajandar aure a tare budurwa ko bazawara kin san matsayin Malam D'aha a wajen mahaifina da ni kaina da irin gudumuwar da ya ba ni a rayuwa abu ne mai wahala na yi ja'in'ja akan wannan umarin nasa Amina ba ni da mafita ne dole na gaya muku halin da ake ciki daga yau zuwa ko wane lokaci za ku iya jin labarin d'aurin aurena domin gidan Malam D'aha ba'a bida'a idan an d'aura aure yarinyar zan je kawai na d'auko." Abin ya daki Hauwa k'warai da aniya ta zuba masa ido cikin k'aduwa tana fad'in." Aure da gaske za ka yi to kai yaro ne da za ka ce an ma'kala maka daman can kana so akwai wanda ya isa ya yi maka dole ne? ashe kana da lafiya ta mazantaka da kuzari irin na maza tunda har zaka iya 'karbar auran budurwa 'kan'kanuwar yarinya. Ya 'kankance ido yana fad'in." Ba ni son hauka da rashin hankali Hauwa ki kiyaye ni wallahi kada ki sake ki fusata ni." Ta ja tsaki ba ta sake cewa komai ba ta kad'a kanta ta kama hanyar fita. Ya ja tsaki tare da sake juyowa gare ni yana fad'in." Ya za mu yi ne Amina ta ina kike ganin zan warware wannan mas'alar da na shiga. Ajiyar zuciya na sauke a nutse na furta." To ai ni ban isa na hana umarinin Ubangiji ba. Na d'auka wata matsalar ce ta daban shiyasa ka ji na ce maka ka gaya mini zan baka shawara. Lamarin aure kuma ai yin Allah ne Amina bata da hurumi anan sai addu'a da fatan alheri." Ya ri'ke hannuna sosai yana fad'in. " Kin amince a yi? kina ganin babu komai idan an yi din?" Na gyara kaina gabana na dokawa na ce." Idan ma da matsala ai ban isa na sani ba tunda ni hallitar Allah ce a karan kaina ban san abinda zai same ni daga yanzu zuwa gobe ba kaga kuwa ba ni da abinda zan ce anan kamar yadda na fad'a da farko Allah Ya sanya alheri yasa abokiyar arzikinka ce. Wannan shine kawai addu'ar da zan yi." Ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta.'' Ban za ci zan samu ha'din kanki cikin d'an'kankanin lokaci ba Amina. Lallai na yi sa'ar samun mace tagari mai ko'karin ganin ta samar mini da nutsuwa cikin kowane yanayi na gode sosai Allah Ya yi miki albarka." A tak'aice na amsa da amin ina ta kallonsa ganin ya wartsake idan ma da ciwon kan to a kashi dari hamsin ya sauka sai abinda ba za a rasa ba. A haka likitansa ya zo ya dudduba shi yana fad'in jininsa ya hau kad'an shine kuma ya haddasa masa tsananin ciwon kai da jirin da yake ji ya zama dole ya daina tsanantawa kansa damuwa. Ya tashi ya fita minti talatin a tsakani ya dawo da magunguΓ±a a leda ya yi bayanin yadda ya kamata a ce an yi amfani da su daga yanzu. Ban sauka ba sai da na tabbatar da cewar ya ci abinci sosai sannan ya sha maganin a gabana tukkuna na yi masa sallama na sauka gwiwata kamar an rad'e da gora saboda mugun sanyin da jikina ya yi jin wannan batu......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *143* Ni jin wannan batu gabad'aya ya kassara mini dukkanin karsashin jikina. Na yi shiru zuciyata na harbawa tare da tariyo maganganunsa akan auran da yake yi wa lak'abi dana cushe. Ba ni fargabar ya yi aure a gidan nan saboda na riga na san matsayina a zuciyarsa idan ma yana amfani da kalaman yaudare wajen nuna mini soyayya tabbas to akwaita a zuciyarsa ko da kuwa da akwai matsugunin wata. Matsalar dai anan 'kankanuwar yarinyar da zai auro ya kawota cikinmu shine tashin hankali tun lokacin da yake gaya mini zuciyata take hasaso mini Hajara ce domin kaf yaran da suke gidan Malam D'aha itace a samansu ba su kaita girma ba ita zamu kira da budurwa amma a rashinta domin yadda take a tsamure a tsuke sai uban tsayi bana tsammanin ta fara jinin al'ada. Lallai wannan babban lamari ne da ya tunkaro mu gabad'aya domin idan har Allah Ya kaddara auran nan to sai da ya rainin yarinyar nan duk da matarsa ce ba zan yarda ya haye musu kan d'iya ta had'u da lalaruba. Malamai suna ta wa'azi kan cewa iyaye su daina irin wannan auran na cutarwa to da haka za mu kira shi ma a wannan zamanin domin dai muddin a fake da cewa sunnar manzon rahama ce yin haka to akan jefe yara cikin halin damuwa a gaba. Dalili zamanin Annabi Muhammadu S.a.w daban yake da wanda muke ciki a yanzu idan an fake da cewa za a yi koyi da shi akan abinda ya wanzar lokacin zamaninsa ana samun matsala dalili shi daban yake cikin duk wata hallita. Kai tsaye a yanzu ba zan zargi Malam D'aha da cewa shima kwad'ayin dukiya ne ya sanya shi daukar yarsa 'karama irin wannan ya bawa tsoho wanda idan da ya yi aure da wuri babu shakka ya kusa jika da ita domin dai Hajara ta wuce a ce 'yarsa idan auransa na fari ya d'ore duk da lokacin ma sai da ya zama tuzuru ya yi ya kuma fara da mace to ba ba shakka Hajara sai dai ta zo a jikanyarsa ta farko. Fisabillahi Malam D'aha bai dubawa yarinyar nan ba kuma ya tauye mata rayuwa ko da Alhaji Sulaiman ya yi aure eh tabbas budurwa ce amma wadda ta jima bata auru ba domin na ga calendar su shi da ita ta girmi Hajara sosai a k'alla ita za ta yi irin ashirin da biyar zuwa da bakwai. To idan ya zame masa dole auran budurwar sai ya nemi mai k'wari ba irin Hajara ba wadda yanzu ne take tasowa ba tasan ma menene auran ba. Na yi zaman sati daya a gidan na kuma fahimci cewa gidan na da tarbiya masu wadatar zucci da malunta ina ganin saboda kwad'ayin dukiya ba zai d'auki yarsa ya bayar ba sai don wani dalili nasa ko hango nagarta da tabbacin za a ri'ke masa 'yarsa a kula da ita. Wannan shine abinda na fi gazgatawa daga gare shi ba wai ya bashi ita ba ne domin ganin yana da kudi da rufin asiri. Kwanan tunani da zullumi na yi kan wannan lamari gabad'aya kaina ya d'aure na rasa yadda zan yi na auna mas'alar a sikeli domin hango cancanta da dacewa. Ina fitowa daga wanka kira ya shigo wayata dake ajiye a gefan gado na kΓ rasa da sauri na d'auka. Baban Saude ne gabana ya yanke ya fadi domin ban kawo komai ba sai mutuwa. Shikkenan Dada ta rasu ban je na dubata ba Allah ya raba ganawarmu. Hannuna na rawa na sanya wayar a kunnena cikin mutuwar jiki da saranda na yi sallama. Ya amsa da dakakkiyar muryarsa wadda hakan bai zame mini abin mamaki ba tunda sanin da na yi masa mutum ne tsayayye ba komai ne yake gigitashi ba ko da kuwa mutuwar ce. Murya na rawa na gaishe shi ya amsa a dakile kafin ya rufe ni da fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita. Na yi kasa'ke da waya a kunnena ina sauraransa domin dai abinda ya tsana kenan yana magana a katse shi shiyasa na bari sai da ya tsahirta tukkuna gabana na dokawa na furta." Baban Saude Hauwa sharri ta yi mini wallahi tallahi ina ko'karin ganin na kiyaye shiga hakkinta wallahi Allah d'aya kenan ban san abinda yake tsakaninta da mijinta ba. Bana ta'ba yarda ranar girkinta na 'kebe dashi na tsayin lokaci ko jiya ma ita ta gaya mini bashi da lafiya na hau domin duba shi kuma babu abinda ta same mu muna yi a zaune kawai ta same mu." Ya furta." Na dai gaya miki ki kula idan har don kina ganin kin fi ta fada a wajensa kuke had'e mata kai har ku dinga shiga hakkinta ki daina domin ba ni so a ce ranar lahira kun tsaya a gaban Ubangiji ana yi muku hisabi yadda ta kira ni tana kuka haikan shine abinda ya daga mini hankali Amina kada ki zalinci duk matan da zai kawo gidanki, ki yi iyakacin bakin kokarinki wajen ganin kin fita hakkin kowa ki kuma nuna masa kuskuran abinda yake aikatawa. Kada don kin samu dama a wajensa ki cutar da wata mu maza ba mu da tabbas watarana zai iya juyowa kan ki hakkin wad'anda ki ka zalinta ya fara bibiyarki. Ko kin ta'ba jin an ce gaskiyar mutum ta k'are. Idan kina da gaskiya da gudun hakkin wani sai ki ga kin zauna lafiya a duniya domin Allah ba ya shiri da mai zalinci.'' Ya kai k'arshen maganar da tausawa. Na ce." In sha Allahu Baban Saude zan kula na gode sosai Allah Ya kara girma." Ya amsa da "Amin Ya Allah." Muka yi sallama. Na ajiye wayar ina dubawa. Lallai Hauwa bata da mutunci yau kuma abinda ta shiryo mini kenan. Kayana kawai na zura zuciyata na tsalle na fita falon shiru ina d'an jiyo maganganun yara a d'akinsu suna shirin makaranta. Na buga kofar dakinta da d'an karfi na ji tana fadin." Wanene?" Kai tsaye na ce." Ni ce" Ta d'auki murya bata sake magana ba jim kad'an ta bude tana sanye da kayan bacci cotton riga da wando da hula. Muka had'a ido ganin yadda fuskata take a murtuke ya sanya itama ta daidaita yanayinta. Na ce." Daga yau sai yau kada jahilar k'wakwalwarki ta yi miki tunanin kiran wayar wani daga cikin alhalina ki kai masa 'karata Hauwa wai shin me na yi miki ne? Ni ce matsalarki ko mijinki Hauwa? me yasa ki ka sanyo ni a gaba ki ke haka kan ki sukuni a kaina me na tsare miki na fad'a da babban sautin da kowa zai ji na ce.'' Yau sai kin gaya mini abinda na yi miki a gidan nan Hauwa ashe rashin mutuncin na ki har ya kai ki kira Baban Saude ki juya masa magana a kaina ni na yi mini ko mijinki da za ki nemi ki hada ni da iyayena." Kada ki karanta wannan littafin ba tare da kin biya ba na kudi ne Babu damuwa a tare da ita ta furta." Abinda ki ka yi mini a bayyane yake Amina tunda kin buk'aci ki sani ai zan gaya miki ko kin zata tsoronki nake ji ne? " Ta fito falon sosai ta tsaya daf da ni ta cigaba da cewa." Na gaji da wannan kisan mummuk'en da ki ke yi mini a gidan nan, na gaji shiyasa na sanar da Baban Saude tunda na lura shi kad'ai ne yanzu zai gaya miki ki ji kuma ba mazalinci ba ne, kin had'a kai da miji kun ware ni kuna nuna mini cewa ni ba matar gida ba ce. Kin kanainaye shi da kissa kin hana shi yin mu'amula da ni, me yasa zan yi shiru a kan ki Amina ai ba ki isa ba wallahi dole ne na gayawa magabatanki." Na ce." Banza shashasha sakarai kawai to kin fad'a kin ji dad'i duk yadda ki ke ganin Baban Saude ya ba ki goyon baya ba zai ta'ba ajiye ni ya d'auke ki ba, gaud'iya kawai wadda ba ta da lissafi." Ba ta tsammaci wad'annan maganganun daga wajena ba ta tunzura ainun ta fara auno mini zagi manya-manya tana kusanto ni kamar yadda dai ta dinga yi wa Hajiya Maryam. Masu aiki kaf dinsu da yaran suka fito suka tsaya muryarta ce kawai take tashi. 'Yar iska kawai ni za ki kira jahila wanda asali da nasabata ta fi taki. Matsiyaciya na fa san tarihin rayuwar da ki ka gudanar a baya kafin ki yi tsalle ki shigo gidan nan ta karfi da ya ji kin dabaibaye mini miji ta ko'ina. Amina ba tsoronki nake ji ba fa ki ka kara zagin.......Ba ta kai ga kΓ rasa maganar ba ya d'auke fuskarta da wani lafiyayyan mari. Da yake ita kadai ce ba ta ga sakkowarsa tunda ta juya baya tana kallona tare da nuna ni da yatsa shiyasa ba ta ankara ba amma ni da masu aiki da yaran duka mun ga lokacin da ya sauko a ki'dime domin duk zurfin samansa sai da ya ji shouting dinta. Ta dafe kuncinta a gigice tana nishi ta juya suka dubi juna ita da shi yanayin fuskarsa ya canza ainun da mugun takaici da b'akinciki. Ya furta." Kin gani ko? Hauwa idan na ce miki kece matsalar gidan nan ki ji haushi yanzu tsakani da Allah menene haka wace irin sakarai ce ke mara hankali da wayo tsokane mata ido za ki yi ne ko kuwa dukanta za ki yi ba ki duba abinda take d'auke da shi a cikinta a gaban yara kina ta zaginta me ki ke so ki nuna musu?" Hawaye suka dinga karakaina a kumatunta tana fad'in." Ita ba ka ji zagin da take yi mini ba yanzu ban girmi Amina ba idan lissafi shekaru za a yi me ya sanya don ta zo a Uwargida nake mutuntata daidai gwargwado ita sheda ce har dakinta nake bin ta na gaisheta me yasa za ta kira ni da sakarai shashasha. Kuma na zauna ina kallonta da kai da ita abinda kuke yi mini Ubangiji Allah yi muku fin sa." Ya furta." Gaisuwar banza da wofi daga yau ki daina gaisheta tunda ba don Allah ki ke yi ba. Duk abinda kuke yi ina hankalce kuma nasan halin kowacce daga cikinku rashin mutunci za ki yi mini a gida abinda nake ji yana faruwa a waje shine ki ke ko'karin wanzar mini da shi a gaban yarana. Dame ki ke so su tashi ko su tasirantu, ke ba za a taba zaman lafiya dake ba ballantana na sanya a raina cewa ko bayan raina za ku had'e mini kan yarana su gaza banbance uwar da ta haife su. Wata matsalar ki ke so ki samar mini da ita a gida ta zage-zage Allah Ya jikan Maryam duka tarbiyar da ta yi musu tare da goyon bayan wad'annan bayin Allan mai inganci ce tunda nake da yaran nan ban ta'ba jin wani ya yi mini zagi a gida ba saboda baki da mutunci ki tsaya gaban uwarsu kina zaginta akan wane dalili?" Ta yi shiru tana kuka mai tsuma zuciya domin dai zahiri marin nan da ya taska mata a kumatu ya dakushe duk wani karsashi da 'kumajinta. Ya dube ni rai a b'ace yana fad'in." Wannan ya zama na farko ya kuma zama na karshe Amina ba zan d'auki wannan shashacin ba. Kada ku kuskura makamacin abinda ya sake faruwa da wannan safiya ya kara kasancewa. Duk abinda ya shiga tsakaninku a same ni a gaya mini na yi hukunci amma ban yarda da irin wannan rashin mutuncin ba a gidana a kuma gaban yara." Na daure sosai zuciya na 'yar hantsile na ce." In sha Allahu." Ya juya ya dubi yaran suna sanye da uniform sun yi tsuru-tsuru Khalil na ra'be a gefe yana kuka sauran kuma idonsu ya gwale kamar su rushe da kukan suma. Ya yi wani irin tsaki mai tsayi abinda ba da'biarsa ba ya ce da Mairo su koma ciki da yaran. Ganin ya bar wajen ya sanya ni ma da gaggawa na shige d'akina na zaune gefen gado kawai sai hawaye suka kwaranyo mini Hauwa ta zame mini annoba. Wai dama haka ake kishi shiyasa ashe ake kashe-kashen juna. Ita Hajiya Maryam na ta kishin na sabauta rayuwa ne a yi mutuwar kasko ban mora ba ke ma ba za ki mora ba. kishin ramuwar gayya da kwantar da mutun har zuwa kushewa. Lallai ne Hauwa duk ranar da ta samu dama a kaina za ta iya yi mini illah dalili na ji tsoro k'warai da gaske ganin yadda take tsalle da han'koro a kaina kamar za ta kawo mini naushi a hanci a son ranta ma kawai mu gwada 'yar kwanji tunda ta mayar da ni jaka mara lissafi da tsinkaye irinta. Har duniya ta nad'e ba na tsammanin zan yarda na had'a kwanjina dana kishiya. To wai shin me ta sani a kaina ne da take ta nanata cewa ta san irin rayuwar da na yi a baya? Me na yi mai muni wanda zai janyo mini zind'e da gori a rayuwata. Na sake goge hawayen da yake sauka a dakalin fuskata. Hauwa ba ta sona yau na sake gazgatawa asalin kishi mai muni take yi a kaina. Kuma ba kowane ya kara rura wutar tsanata a zuciyarta face shi da yake nuna mata 'kiyayya tare da kiran sunana a matsayin matar da ya ratayawa fulawar soyayya a kanta ita da take ganin ta taka tudu biyu matsayin matarsa kuma jininsa.........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700....VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *144* Ya shigo dakin yana tambayata mai ya had'a mu kai tsaye na ce." Ka je ka tambayata me ta sani a akaina kafin ka shigo ka tuhume ni. Yau ina so a yi ta 'kare a gidan nan lallai ya zama dole Hauwa ta sanar da ni da kai abinda ta ce ta sani a kaina domin yadda ta fad'i hakan to dole ne akwai abinda ta sani din a kaina wanda ta ji a duniya ko kuma a lokacin da kake neman auranta ta gaya mata wani abu kafin ka aure ni. Na ji da kunnena kana gaya mata mace mai irin jikina bata burgeka wa'ala a lokacin giyar soyayya ta sanya ka gaya sanar mata cewa Amina fasika." Subahanallahi! Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ya dinga nanata wad'annan kalmomin kafin ya zauna a kusa da ni da wani irin sanyin jiki ya riko hannuna na cire ina dubansa idona tsaye na ce." Ba zan saurareka ba a yau har sai Hauwa ta gaya maka abinda ta sani a kaina kafin 'kaddara s aure ta ratsa tsakaninmu magana ce mai harshen damo ta furta." Ya yi shiru kansa a kasa tsayin wani lokaci ya dago yana dubana lokacin zuciyata ta gama bushewa 'karyar neman fitina Hauwa take yi yanzu ne asalin rigima ta da ita zai fara. Ya furta." Ki saurare ni Amina ba ni son damuwa da tashin hankali idan kin duba halin da nake ciki na rashin wadatacciyar lafiya kada zantukan Hauwa su yi tasiri ku daga mini hankali." Na ce." Kowa cikin lalura yake ni ba ka ganin abinda ka 'kunsa mini ne, ina so ko ba na so na ha'kura ina ta ibada dashi a tare da ni. Na fi ka jinjiki a wannan ga'bar mu cire maganar ciwo ta gaskiya za mu yi wallahil-azimin idan har yau Hauwa ba ta gaya mini abinda ta sani a kaina ba sai ka sake ni." Ya zura mini idonsa ransa a b'ace ya ce." Me ya kawo maganar saki a cikin maganar da muke yi ke ba ki da hankali Amina?" "Ba mu da hankali har kai gabad'aya taron mahaukata ne a gidan. Ya furta." Zagi na za ki yi?" Na gyad'a kaina ina fad'in." Ni ka zage ni." Ya yi shiru na d'an wani lokaci kafin ya ce." Ba ki ga hukuncin da na yi mata ba kenan a kan ki ai na ji abinda take fad'a. Na ce." Wannan damuwarka ce kai da ita ni ina gaya maka cewa ka tashi ka je ka tambayeta abinda ta sani a kaina na abin kunya." Ya ce." Ba zan tashi ba tunda abinda na yi mata a kan ki bai yi miki ba ki d'auki matakin da ki ke ganin za ki d'auka ba fa tsoronki nake ji ba Amina." Na ce." Ina ruwana da abinda da ka yi mata ai ka saba zalintarta. Yau ka fara?" Shiru ya yi bai dube ni ba tashin hankali ya gama bayyana a tare da shi. Ya tashi ya fita bai sake cewa komai ba. Ban yi a kasa a gwiwa na bi shi saman sai na same shi kwance ya hard'e hannunsa a k'irji abin duniya ya ishe shi Na zauna gefansa ya kalleni na kalle shi na ce" Ka tashi mu yi magana don wallahil-azimin yau sai Hauwa ta gaya mini abinda ta sani a kaina." Bai tashi ba illa iyaka ido da ya zuba mini yana kallona. Jim kad'an ya tashi zaune idonsa har yanzu a kaina ya furta." Ni dai ban san komai a kan ki ba face alheri Amina kuma babu wani dalili da zai sanya na zauna ina 'bata ki a gaban Hauwa to na ce me kan ki wannan ba d'abia ta ba ce." Na ce." Ba zan yarda ba a wannan ga'bar domin da kunnena na ji a shekarun baya kana gaya mata kalmar kaskanci a kaina ba ka son mace mai irin suffata. Ya furta." Eh da farko ra'ayina kenan amma yanzu na canza ina so dalilin da ya sanya ma kenan ba ni yin wani doki da marmarin wannan yarinyar da aka ba ni bunkure." Na ce." Da farko kuma ka ce kaima ba kasan yarinyar ba. Anan ma ka sake tabbatar mini da cewa baka jin kunyar 'karya Ya furta." Kin d'auke ni munafiki kenan?" Na gyad'a kaina ina kallonsa ido cikin Ido. Ya ce." Na ji tashi ki je kada ranki ya 'baci.'' Na ce." A shirye nake ai ko kana tsammanin akwai wani b'acin ran da zai dame ni wanda ya danganceka." Ya yi shiru tare da komawa ya kwanta. Na cigaba da sakin maganganu masu zafi har sai da ya fusata ya sake tashi zaune jikinsa na kyarma ya nuna mini hanyar fita. Na ce." Ba zan fita ba wallahi sai ka kira Hauwa yanzu ta fad'i abinda ta sani a kaina na sharri." Ya ki'dime sosai yana d'an tari ya ce." Bala'in ki ya kashe ni Amina ko kuma kawai ki sanya fillo ki 'karasa ni ki huta wace irin masifa ce wannan." Na ce." Ba zan kashe ka ba amma ba zan yi shiru ina kallo ana yi mini abinda bai dace ba. Ya ja tsaki ya sake komawa ya kwanta na janyo kafarsa daya ya tashi zaune da azama yana kallona da mamaki abinda na yi fuskarsa gabad'aya ta canza da tsoro da fargaba dalili bai hangi nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ni ba." Ya tashi ya kama hanyar fita babu kuzari. Mintina biyar suka shigo dakin tare da ita. Har yanzu a hargitse take idonta ya yi luhu-luhu saboda tsabar kuka. Ya dube ni kafin ya ce." Gata Γ±an ki tambayeta amma ni ki daina tuhumatta akan abinda ki ke zargi." Na dube ta sosai ina fad'in." Kin ce kin san komai a kaina har irin rayuwar dana gudanar kafin na auri d'an uwanki to ina so ki gaya mini mai ki ka sani a kaina mai muni ki gaya mini kuma ki ba ni sheda da hujja a sannan ne zan saurara miki don na rantse da buwayar Ubangiji wannan lafazin naki ka iya kai mu ga hukuma domin dai ba zan yarda ki yi mini sharri ba." Ta fara kame-kame murya a dashe take cewa." Ai tsayawa yi miki bayani bata lokaci ne Amina kowa ya san abinda ki ka yi kina budurwa da kuma rayuwar zawarcin da ki ka yi a baya abinda duniya ma ta sani me yasa kike neman sheda da hujja a kaina ." Wanzar na tashi daga inda nake na nufe ta jikina har kyarma yake yi ta d'an tsorata domin ko ga yanayin yadda ta mayar mini da martani a tsorace take kuma tashin da na yi da azama na nufe ta ya bata tsoro dalili d'azu ta sha mari a kaina ta zage ni yanzu kuma ba ta san abinda zai faru ba. Na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Yana zaune yana kallonmu bai ce mana komai ba. Na ce." Ai dole sai kin gaya mini da wane namiji a kama ni a hotel ko kuma lokacin da nake sharafina a social media update dina ya fito wannan hujjar ita kadai nake so na ji daga gare ki" Ta d'an ja baya tana ta'be bakinta ta furta." Ba ta mini lokaci ki ke yi a banza ke ce ba ki sani ba amma har yanzu akwai sauran hotonanki a wayoyin wasu mazan...... Ba ta kΓ rasa na fitar da hannu na tsinka mata wani mari wanda ban san ma na iya shi ba. Ya taso da sauri ganin ta 'baci a lokacin da take han'koran rama marin da na yi mata ya shiga tsakiyarmu yana fadin." Me yasa za ki mare ta Amina zan 'bata miki rai fa." Ya rike ni da kyau na fizge na bi ta gefensa na janyo rigar jikinta botiran suka zube. Ta yi saurin dafe kirjinta. Ya juya da sauri ya tura ni na zauna d'abas a saman gado zuciyata na harbawa. Ban yi tsammanin zan iya yin cacar baki da kishiya ba sai gashi yau tsananin bacin rai da takaici na nema ya sanya ni na hada jikina da Hauwa da zumar kokawa so nake yi kawai na dake ta sosai mu fitar da raini tunda na gama gane irin sharrin da take so ta la'kaba mini. Ya rike ta da kyau ya hana ta zuwa wajen da nake zagi kuwa sai auno mini shi take tana fad'in sai ta rama marin da na yi mata wallahi." Ya furta." Yana da kyau ni ma naga hujjar nan Hauwa sai na gazgata maganarki kada ki ga na goyi da bayanta ki sanar da ni abinda ki ka sani a kanta. Ta yi shiru tana huci! wannan karon hawaye bai fita ba. Ya riko hannunta suka zauna gefan gado yana tsakiyarmu yana fad'in." Ba ki fa da gaskiya Hajiya akan wannan maganar ni ma ba zan iya barinki ba domin kina ko'karin mini 'bata mini sunan matata, lallai ya zama dole na ga sheda Amina ta ga sheda ko kuma ki bata ha'kuri a ciki biyu za ki yi daya. Idan na ga shedar abinda ki ka fada a kanta ni ma za gazgata muddin kuwa ki ka gagara kawo sheda dole ki bata ha'kuri ki kuma nemi afuwarta amma ki sani ba zan iya hana ta ta bibiyi hakkinta ba." D'akin ya d'auki shiru na wani lokaci kafin ya ce." Ya kuke so a yi muku yanzu na kwanta na fad'i na mutu shine burinku ashe da raina zan ga wannan masifar." Ta ce." Abinda ya fi haka ma za ka ga ni wallahi mutukar ba ka d'auki mataki akan dukan fuskata da ta yi ba idan ba haka ba zan d'auka da kaina duk abinda ya faru a gidan nan ka yi kuka da kan ka." Ya ce." Babu abinda zai faru sai alheri Hauwa idan kin kashe Amina ko kin yi mata wata illar sai dai na taya ki da addu'a domin kuwa da hannuna zan d'ankawa hukuma ke." Ta ja hanci ba ta ce komai ba. Na fara ko'karin tashi domin barin wajen ya rike hannuna tamau ya d'an kalle ni kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kamo hannunta yana fad'in." Ku shirya don Allah ba don ni ba kada ku yi gaba ko ku illatar da juna." Na dube shi da mamaki wai yau shine yake yi wa wani wa'azin kada ya yi gaba. Abar da ta zame masa d'abiaa. Na zame hannuna daga cikin nata tunda ya hade mana yatsu ne ya rintse da nasa gabad'aya. Ya furta." Haka zan kawo yarinyar mutane cikinku da girmanku da shekarunku kuna a matsayin iyayenta masu yi mata gyara ta same ku kuna nuna kiyayyar juna. Wani bala'in haushinsa ya kama ni. Hannuna na cire daga cikin nasu na tashi tsaye ya dago yana kallona bai ce komai ba na kama hanyar fita raina a b'ace. Ita Hauwa shirin take nema domin tunda ta ji ya riketa har yana rarrashinta ta yi lakwas kuma ko lokacin da ya had'a hannunmu waje daya ba ta yi yun'kurin cire nata ba. Ba ni tsammanin zan sake zama da Hauwa a inuwa daya idan lallai sai na cigaba da zaman aure da shi ya zama tilas ya yi abu daya daga cikin biyun nan ko na koma gidana na kano ko kuma ita ya canza mata gida......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *145* Wannan shine abinda na yankewa kaina sanadin da ya janyo mana rikici mai tsanani tsakanina da shi domin na rantse masa da Allah ba ni sake zama da Hauwa a gida d'aya kuma wannan dalilin ya sanya shi kai ni 'kara abinda zai biyo bayan haka ba zai yi mana kyau gabad'aya ba. Bai d'auki ga'barar kaini karar ba da ya yi iya yin sa domin ganin ya tankawari ni na ha'kura ya kasa sai ya kyale ni ya fara neman shiri da Hauwa duk domin na ji haushi da farko ina zaman falon ganin haka ya sanya na daina zama sai da dalili ita kuma mahaukaciyar sai ta d'auka tsoronta nake ji ina gudun ta rama marin da na yi mata. Daga lokacin da ta fahimci akwai 'yar tsama a tsakaninmu ta dage sosai wajan ganin ta kara juyar masa da tunani wanda gabad'aya rashin nutsuwa da ficewar hayyaci ya ya gigitar masa da rayuwa yana daurewa ne kawai saboda yana so ya nuna mini ba ni kad'ai ba ce matarsa a banza domin duk abinda suke yi shi da ita bai dame ni ba abinda da dai na yanke a cikin raina yana nan ban janye ba akwai wa'adin da d'iba muddin bai yanke shawara ba zan fita na bar gidan. rashin sakewa da walwala ta ya assasawa yaran da masu aikin damuwa da farko su Baba Tabawa sun d'auka ba ni da lafiya suka dinga shigowa daya bayan d'aya suna duba ni. Amma da suka fahimci akwai damuwa sai duka jikinsu ya yi sanyi mussaman da suka lura da yadda Hauwa ta saki jikinta take yin annashuwa a gidan kamar ba itace mai matsiyacin 'kuncin rai ba. Baba Tabawa tun da can ma muka dan yi maganganu na fahimta don haka ta zame kanta ta same ni a d'aki tana ce mini sai na dage da addu'a da neman tsarin jikina domin dai ta gama fahimtar Hauwa ba ta kaunata kuma idan ta samu dama za ta iya aikata komai a kaina. A tunaninta wannan k'uncin da nake ciki Hauwa ce ta yi mini asiri domin shiga tsakanina da maigidan. To ba a 'kin ta mutum na amsa mata da to kawai ina kara jaddada mata addu'a kullum a cikin yin ta nake. Ana haka Fadila ta haihu anti Yagana ta kira ni tana gaya mini ta samu 'ya mace na ce mata ina tafe. A daran ranar duk da ba girkina ba ne na hau saman da na fi sati daya rabon da k'afata ta taka shi sai dai shi ya biyo ni d'akina yawan sa'in da muke yi a tsakaninmu ya sanya ya daina shigowa domin baya jin sukari a duk lokacin da zan mayar masa da martani magana ce mai zafi wadda za ta yi masa ciwo a raina. Cikin jallabiya na same shi a can wurin da yake zama da Loptop din sa a gabansa. Ita kuma ta ci gayu da k'ananun kaya matsatsen wando iya gwiwa da wata riga mai hannun shimi breast dinta duk ya ta'be ta d'auki wata hular gashi ta sanya sai kace irin tsotstsun arnar nan. kan sa yana kasa yana ta aiki ita kuma tana motsa masa shayin da ta had'a masa. Na yi sallama cikin gaggawa ya dago kansa ya kallo bakin kofar. Ido ya zura mini yana amsa sallamar ita kuma ta sai ta had'e ranta ta yi kasa da kanta can ciki ta amsa sallamar. Gabad'aya kafatanin hankalinsa yana kaina har na zauna kujerar da take fuskantarsa a nutse amma babu walwala a fuskata na ce." Barka da dare." A tak'aice ya amsa da "Barka dai ya kike?" Ban bashi amsa ba na cigaba da cewa." Fadila ce ta haihu jiya gobe zan je maiduguri in sha Allahu.'' Kai tsaye ya ce. " To shikkenan sai a shirya tafiyar ko?" Kasa na yi da kaina ban ce komai ba mamaki dai nake yi yadda ya amince nan da nan bai yi jayayya ba can kasan zuciyata na gaya mini hanyar shiri yake nema shine dalili. Na yun'kura na tashi da niyyar fita daga d'akin ya dubi Hauwa yana fad'in." Ban ji kun gaisa ba kuma kin yi mini alkawari kan cewa za ki gyara kuskuranki haka dai ki ka gaya mini kwana biyu da suka wuce ban ga ni a aikace ba ." Na yi gaba ban tsaya jin abinda za ta ce ba. Ai wanda ya ce baya sonka da farko daga baya ko ya zo ya ce yana sonka to k'arya yake yi ya fadi hakan ne domin cimma wata manufa tasa Hauwa ba zata ta'ba k'aunata ba dalilin da ya sanya kenan nake so na nisanta kaina da ita. Idan da gaske zuciyarta babu damuwa mai zai sanya daga na shigo ta 'bata rai jikinta ya mutu saboda ganina. Na shige na yi tafiyata ina jin sa yana magana ban juyo ba. Sai da na leka d'akin yaran na same su duk sun kwanta Mairo na ta gyaran wardrobe dinsu aikin kenan ta yi tsifar kai ta wanke da yake Taburni ta iya kitson hannu itace take yi musu idan an kawo wankin kayansu ta goge ta shirya musu ta ba ni tausayi sosai ita kadai a zaune duk sun kwanta dole a rage mata wani aikin mussaman gugar kaya mai wankin idan ya wanke ya goge ta samu hutu ga tashin asuba haka suke ta fama. Na ja musu kofar na nufi nawa d'akin da sau'kin zuciya domin Ina so na d'an matsa daga wajan da nake zaune ko zuciyata za ta yi sanyi na tsani na bud'e idona na kalleshi ko na ji muryarsa saboda tsabar haushin da yake ba ni a yanzu. Har ni zai yi wa burga to Ina abin yake Hauwa dai macace amma a rashin mata domin dai da gabad'aya ta sullunce babu wata komad'a a tattare da ita idan har yana so ya tsorata ni ko kuma ya sanya mini kunci ya auro wadda ta fi ni komai shine zan daga hankali don yana soyayya da Hauwa a banza nasan duk buge ne. don Allah kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina b. Wanka na yi na sanya kayan bacci na yi kwanciyata a gado ina Kiran sunan Allah. Na ji ya turo kofar d'akin ya shigo. Na zuba masa ido har ya zo ya zauna a gefan kafafuna yana fad'in." Kin mayar da ni sakarai mara mutunci ko Amina Ina yi miki magana kin yi banza wulakancin nan ya isa haka wai me ki ka taka ne?" Shiru na yi ban tanka masa ba ya cigaba da cewa." Hauwa duk ta d'auki matakan gyara kuskuranta kamar yadda ni ma na d'auki matakin gyara akan zamantakewar da muke gudanarwa a gidan nan zan yi kokarin kwatanta adalci." Na ce." To wannan kuma damuwarka ce idan ba ka yi adalci ba duka za ka ci a lahira." Bai mayar mini da martani ba saboda ya saba jin irin wad'annan maganganun na fitowa daga bakina sai ya d'ora akan maganarsa yana cewa." A wannan lamarin da yake faruwa kece matsala domin kin d'auki wata hanya ta daban wadda na kasa gane inda ki ka dosa na gaya miki ba ni da ra'ayin raba gidana nafiso yarana su tashi tare domin su shaku." Na tashi zaune ina kallonsa na ce." To sai ka rabu da matsala mana dole ne kana da da yadda za ka yi a kaina tunda na zame muku matsala ka yakice ta ka huta, ba zan zauna da Hauwa a gida daya ba wannan shine abinda zuciyata ta yanke mini. Ya furta." Ni kuma ba zan raba gidana ba Amina ni dake shege ka fasa." Na koma na kwanta tare da cewa." Duk yadda kake jin kanka baka fi karfin hukuma ba idan ba za ka raba gida ba to sai ka ba ni da takardata." Ya furta." Wannan zoben da na sanya miki a yatsa shi yake nuna cewa ni dake mutuwa ce za ta raba auran zobe muke yi." Na ciro zoben na ajiye masa shi saman cinya ina fad'in.'' Ai ban san manufarka ba kenan ga abinka nan." Ya d'auka da mugun haushi da takaici a tare da shi ya dinga jujjuya zoben yana kallona har ya so ya d'an ba ni tausayi na d'auke kaina daga kansa. Ya ce." Na gode." Ya mayar da shi hannunsa kafin ya sake kallona a karon da bashi da adadi ya ce." Gobe ki ka ce za ki je maiduguri ko?" "Umm!" Na furta can kasan zuciyata. Ya tashi tsaye yana cewa" Sukairaju zai kai ki a mota za kuma ki ga sa'ko cikin acct d'inki sai da safe." Ya kama hanyar fita na ce." Da yara zan tafi domin ina so su ga dangina." Ya juyo da saurin gaske yana cewa." Wannan ne kuma ba ki isa ba babu inda za ki je mini da yara. Ke dai ki je Allah Ya ba da sa'a." Na tashi zaune ina cewa.'' Mai kake nufi yaran nan na ta'ba nuna maka wani iko a kansu tunda na haife su baka da hujja domin ba naka ba ne kai kadai dangina zan kai su domin kowa ya gan su." Ya ce." Ba za su je ba na fad'a ke dai tunda kin zama isashshiya ga hanya nan ki tafi, yaran ma da ba wani damuwa ki ka yi da su ba yanzu za ki ce za ki je da su wani waje su zauna a gidan ubansu kawai." Raina a b'ace na ce." Maidugurin ne wani waje kada ka manta fa asalina ne." Ya ce." Wani waje ne mana ko akwai wani nawa a garin duk danginki ne ke ce ta maiduguri 'yan biyu kuma na kano ne garin Dambatta." Ya fita da sauri tare da jan kofar da k'arfi. Bacci rabi da rabi na yi da sassafe duk na gama shirye-shiryena kaya set goma na sanya a akwati na ce Khalil ya kira mini Masa'udu ya shigo ya tsaya bakin kofa muka gaisa na ce ya d'auki akwati ya kai mota. Na koma na sanyo hijabi dina har kasa lokacin yaran sun gama shirin makaranta amma ga dukkanin alamun Khalil ya gaya musu tafiya zan yi tunda shi ya fita da akwatina. Suka fito Minal ta rushe da kukan gaske sauran sun yi cirko cirko Usai da yatsa a baki tana tsotsa na cire hannun ina fad'in ke ba za ki daina tsotsar hannu ba sai tasa kuka tabbacin a kusa take dama. Taburni da Baba Tabawa suka fito Mairo ta fito suka tsaitsaya yaran suna ta kuka har da Khalil ina kallonsa ya tsuguna bayan kujera. Na ji giwata ta yi sanyi ainun dama kamar kiris suke jira domin koda na tsiri zaman d'aki haka suke shigo mini d'aya bayan d'aya idan sun taso daga makaranta. Shi da Hauwa suka sauko yayin da nake gayawa Baba Tabawa Fadila ce ta haihu zan je ba wani abu ba ne. Hauwa fuskarta a sake ganin abinda yake faruwa ko tana zargin yaji na yi oho a gabanta dai jiya na yi masa maganar tafiya maidugurin amma ban san abinda ya assasa mata sakin fuska ba duk dambarwar da uban yake yi da Minal akan ta sake ni ta'ki sai ihu take yi Hauwan ta zo tana jan hannunta da yake yarinyar a zababbiya ce idan tana kuka sai ta gartsa mata cizo a hannu. Aikuwa ba shiri ta sake ta matsa gefe. Babu halin na ciccibeta na rarrasheta kamar lukutan baya idan tana kuka d'aukarta nake yi yanzu kuma jikina ya yi nauyi cikin da nake d'auke dashi wata shida ni kaina nauyi yake mini bana iya sunkuyon kirki. Na ja hannuna duka yaran suka biyo ni dakina. Na zaune gefan gado su uku duk sun tsaya a gabana 'yan biyu da ita Minal din ta uku Khalil ne bai biyo ni ba. Tausayinsu ne ya kama ni ta kar'fi da yaji Hassana da Husaina sun koyi ha'kuri don yadda suke shakkata ba sa shakkar ubansu wasu lukutan idan suna kiriniya da ido na yi musu gargadi suke shiga hayyacinsu shiyasa ba sa yin iya shegankatar da Minal din take yi dalilin uban yana lelenta ba kuma fin sauran ta yi a zuciyarsa ba kawai yana fad'in sunana ne da ita wai yana yi mini kara.. Kawai na ji hawaye ya silalo mini duk wannan k'aunar da shakurar da take tsakanina da yarinyar nan dole na bar wa Hauwa 'yarta domin yaran da na haifa kawai zan hada kan kayana mu tattara a waje daya bana tsammanin barinsu a gidan idan Hauwa tana ciki za mu tafi tare da yarana da mai aikina baba Tabawa kenan su Taburni da Mairo idan suna da ra'ayin cigaba da zama da Hauwa su zauna. Ya shigo dakin sai na yi gaggawar goge kumatuna. Minal na ta fad'in." Mama zan bi ki unguwa, Mama zan biki unguwa." Ya tsaya a gefe yana fad'in." In banda neman fitina Amina ai sai ki bari su tafi makaranta tukkuna ki fito ki tafi tunda kin san lallai ne za a iya samun wannan matsalar. Na yi shiru dai ban ce masa komai ba. Ya zo ya ja hannun yarinyar da ta d'ora saman cinyata Yana fad'in." Yi shiru za ku je unguwa ko?" Ta daga kanta. Ya dubi 'yan biyu da suke tsaye a kusa da ni sai ya girgiza kansa cike da jin haushi ya kamo hannayensu yana cewa." Zan kai ku da kaina ku je karatu ku dawo da daddare da kaina zan fita da ku yawo kuna so ko?" Suka daga kai babu wani karkashi a tattare da su. Jim kad'an da fitarsu ya dawo d'akin ina zaune ban motsa ba tsabar yadda jikina ya mutu. Kawai ya mayar da kofa ya rufe ya tsaya yana kallona sai da na gaji tukkuna na dube shi na dan wani lokaci. Ya yi kwafa yana cewa." Wato da tafiya za ki yi ban isa ki yi mini sallama ba ko?" Shiru na yi uffan ban ce ba. Ya cigaba da cewa.'' Yaushe za ki dawo kwana nawa ki ka yanke?" Na ce." Sati biyu." Ya girgiza kansa yana cewa." A a ban amince ba a yi sati daya dai Hajiya sati biyun da ki ka d'iba a cikinsa nake tsammanin daurin aurena da yarinyar nan Hajara." Na ce." To ni ina ruwana ni ka aurowa ita da sai lallai ina nan ko iyayenta ni suka bawa." Ya ce." Kada ki gaya mini maganar banza da wofi Amina kina d'aga mini murya fa ya ina yi miki magana cikin lumana domin mu fahimci juna kina so ki zage ni wallahil-azimin na gaji da wannan rashin mutuncin da ki ke yi mini a gidana." Can kasa na ce." Sai ka d'auki mataki ai." Ya yi shiru yana kallona nasan ya ji abinda na ce kawai ya rasa yadda zai yi da ni ne." Ya ce ki duba jiya da daddare na sa miki miliyan bakwai ki yi guziri ga 'yan'uwa na can garin naku. Biyar kuma sayi kayan kwalliya na danne kirji kamar yadda al'ada ta nuna Hauwa ma na bata." Na dubi tsabar idonsa ina fad'in." Ba ka isa ka saye ni da kudi ba wallahi bari ka ji da can ba ni kudin dannar kirjin kake yi mata biyu ka auro kafin wannan cikinsu kwabonka baka ta'ba ba ni ba don haka ban ga dalilin da zai sanya wannan karon munafurci zai sanya ka ba ni kudinka ba." Jikinsa ya yi sanyi ya furta." To shikkenan na ji zan ciko miki 10m sai ya zama sha biyar ba biya ki shikkenan ko?" Na ce." Ba ka ji mai na ce ba kenan ba ka isa ka saye ni da kudi ba wanda ka tura mini ma yanzu zan dawo maka da abinka Allah Ya rufa mini asiri." Sai ya yi shiru hankalinsa a tashe na ji yana fad'in." Allahuma ajirni fi musibati Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ya bud'e kofar d'akin ya fita cikin gaggawa. Ni ma na tashi da sauri na fito na hange shi yana hawa sama falon babu kowa na fice daga gidan. Sukairaju na tsaye jikin mota da alama fitowata yake jira tunda tun dare maigidan ya sanar masa da tafiyar ya shirya tsaf. A gurguje muka gaisa da masu hidima da gidan ya bude mini motar na shiga na zauna ina addu'a a cikin zuciyata ya shiga mazauninsa shima kafin ya kunna motar daga can maigadi na ko'karin bude gate din gidan....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *146* Gida a kawo Fadila tunda haihuwar fari ce kuma dai gidan nata ba shi da wani spece inda Allah ya ta'kaita nasa ne ba ya haya ba ce wai hausawa suna fad'in guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni. Duk da haka ya yi kokari tunda d'aki uku ne da kicin da bandaki sai dai dak'unan duka ba ma su yalwa ba ne. Haihuwa da lafiya akwai anya farinciki yarinyar tana zauna da babyna a hannu tana bashi nono na cika da mamaki kwarai da gaske wai yau Fadila ce ri'ke da jinjiri har tana shayar da shi gani ni uwarta gotai-gotai da ni ban gama haihuwa wato idan da Kamaluna ma macace haka za mu jera haihuwa da shi duk da Fadila ta girme shi sosai amma dai da mace ne a yanzu da ake yi wa yara auran wuri wata'kila da tuni na aurar ni ma Yusuran Sahura ma tana can da nata tsohon cikin haihuwa ko yau ko gobe wai a haka ma ta yi 'bari na wata hud'u. A washe da safe Sukairaju ya d'auki hanyar komawa gida bayan ya karya kummalo. Yawan shige da ficen da ake yi a gidan dangin mijin yarinyar da danginmu suna zuwa ganin jarari Hakan bai ba mu damar 'kebewa sai a daran ranar dana kwana biyu a gidan tukkuna muka zauna muna tattauna al'amura masu yawa. Nan na gaya mata irin abubuwan da suke faruwa tsakanina da Hauwa da shawarar da na yanke sannan da auran da yake shirin yi a tsukin kwanakin nan tunda ya ce satin na sama suka yanke za a daura aure. Ta dinga mamaki tana fad'a kamar ta ari ba ki wai shi bashi da bakin da ba zai ce ya yi wa yarinyar girma ba ai ana barin halas don kunya wannan babbar asara ce da jin kunya idan har ya amince aka daura masa aure da yarinyar da ko shakka ba ta yi ta ji jinkanya da shi. Abin ya dinga ba ni dariya ganin yadda ta hakikance da gaske tana ta fad'a tana cewa girmansa ya zube a idonta tunda ya shigo da son zuciya dama can yana so idan ba haka ba daidai gwargwado ya yi wa malamin alheri mutumin ya rushe masa gida ya zamanantar dashi tare da sabunta tsangayu irin na zamani aikuwa ya yi abin a yaba masa kuma idan biya zai yi akan hidimar da ya yi masa ya biya shi mai zai sanya kawai a d'auki yarinya a bashi ya kuma sanya hannu ya kar'ba har yana cewa don babu yadda zai yi ne wannan karya ce tsantsa da yaudara. Da muka wayi gari ma ta tashi da mita shiga fita dari sai ta yi maganar tana cewa kin yi daidai ya kawo yarinyar su zauna da Hauwa a gidan ke ya canza miki wani idan ma ba zai yarda ki zauna a gidanki na kano ba ai yana da iko anan abujan sai ya samar miki da wani. Irin wad'annan masifun ne ya sanya wasu mazan ko basu da wadata suke rabawa matayensu gida to balle shi da yake da suttura da wadata tunda har abinda Hauwa take yi ya'ki ya'ki cinyewa kawai ya rabawa kowa mazauni sai a samu zaman lafiya. Na ji dad'i sosai ganin yadda wannan karon anti Yagana ta goyu da bayana na saki raina sosai ina jin sasaauci Kuma ban kunna wayata ba yau kwana biyu kenan wanda nasan yana can yana ta lalubena a wayar bai samu ba. Sai da na yi wanka na karya kullumalo tukkuna na fito falon na sami yarinyar tare da kawayenta na makaranta sun zo ganin jaririya suna ta tsokanarta sai suka ba ni sha'awa muka gaisa ina yi musu dariya cikin raina ina cewa duk yadda za ta kai ga baku labarin nakuda ba za ku fahimta ba sai ta riske ku tukkuna. Anti Yagana tana ta gyara kaji a kicin nace." In ban da abinki anti Yagana ai sai ki kira ni na taimaka miki." Ta ce." Ke ma ba lafiyar ce dake ba Amina na gode Allah ni da ya hore mini lafiyar wannan hidimar ta same ni Dada ciwo ya dabaibayeta nasan da ita za ta zo ta zauna mini" Na ce." K'warai hakane shirin da na yi yanzu zan tafi can babban gidan ne na duba jikinta zan dan zaga dangi mu gaisa." Ta furta. Hakan yana da kyau." Kujera na ja na zauna na kama mata aikin Muna gyara kajin a tare na ce." Na lura yaron nan da yake auran Fadila yana da zuciya wallahi gashi nan komai ya yi na al'ada." Ta gyad'a kanta tana cewa." K'warai Kam tunda ta haihu yake hidima domin da ta fara nakudar ma bai iya kaita asibitin gwamnati ba kudi ya fitar ya kai ta wanda za a bata kulawa wallahi sai da ta haihu ya kira ya gaya mana." Na furta." Irin wad'annan matasan ya kamata ace an d'auki aure an ba su masu zuciya da dogaro da kansu da kuma ko'karin ri'ke iyali daidai gwargwado." Daya daga cikin yan matan kawayen nata ta fito tana fad'in.''Mama ana kiran ki wayar ki." Ta mika mata wayar na riga ta kar'ba domin hannunta gaja-gaja yake fa jinin kajin da take gyarawa. Ina duba fuskar wayar naga sunan Alhaji Tajuden da haka ta yi serving lambarsa Na daga tare da sanya mata a kunne ina ji yana gaisheta da mutuntawa kamar yadda ya saba itama ta amsa cikin nutsuwa har tana tambayarsa yara ya ce duka suna lafiya sannan ya yi mata barka da arziki kafin ya fara tambayarta ina nake ya yi ta kirana a waya baya samuna. Ta dube ni kafin ta ce masa gani nan a zaune. Sai na ji yana cewa da ita ta gaya mini na kunna wayata akwai muhimmiyar maganar da za mu yi. Ta ce masa to in sha Allahu suka yi sallama. Ta d'an dube ni a sanyaye tana fad'in." Na ji shi a sanyaye yana magana babu nutsuwa Amina kada dai ki ce da biyu ki ka zo nan garin kar ki ce da ni yaji ki ka yi akan wannan matsalar domin idan bacin haka ai ban ga dalilin da zai sanya ki kashe wayarki ba." Na ce." E, to ba yaji na yi ba amma dai Ina tsammanin ba ni komawa Abuja kai tsaye daga na bar nan kano zan sauka gidana na sharad'a tunda ya'ki fahimtar abinda nake nufi." Ta gyad'a kanta tana cewa." Ba ni son hakan ya haifar miki da wata matsalar Amina amma ni kaina a son raina nafiso a raba muku muhalli sai hankalina ya fi kwanciya. Na furta." Duk mai hankali da tsinkaye abinda zai duba kenan matsawar muna zaune a inuwa guda da Hauwa ba za a taba samun zaman lafiya ba Shima ba zai huta ba tunda ni dai na zame mata ciwon ido anti Yagana wallahi har mamakin yadda Hauwa take zafafawa kanta a kaina ni kuma ba ta raina kwata kwata ban kuma dauketa a matsayin kishiya da zata daga mini hankali ba. Kawai yanzu nutsuwa da kwanciyar hankali nake buk'ata shiyasa na ce ba ni buk'atar zama da ita a gida daya." Ta furta." Hakane akwai hujja mai karfi a tare dake ni ma ina bayanki amma yanzu tunda ya ce ki kunna wayarki za ku yi magana ki kunna din mu ji mai zai ce." Na ce." To shikkenan zan kuna." Sai da muka gama aikin gyara kajin tukkuna ta d'ora a wuta na wanke hannuna da omo sannan na koma d'akin na d'auki wayata na kunna minti goma sha biyar a tsakani ya kira na daga a nutse na yi sallama ya amsa na gaishe shi nan ma ya amsa babu annasuwa. Kafin ya d'ora da fad'in." Yarinyar Minal tun bayan da suka dawo daga makaranta ta samu ba kya gidan kwanta zazza'bi ya rufe ta ya hau ya sauka har takai da sai da aka yi mata karin ruwa Amina ida ta rasu wallahi ba zan yafe miki ba." Gabana na d'an fad'uwa na ce." Ban gane abinda kake nufi ba." Ya ce." Kin ji abinda na fad'a Amina ai kin san ba ki da gaskiya shiyasa ki ka kashe wayarki tsayin kwana biyu." Na ce." Mayya ce ni ma shiyasa na kama kurwar Minal na taho da ita nan maiduguri to don Allah idan ta rasu ka d'aure ni har igiya ta yi rara." Ya ce." Abinda za ki ce kenan?" Na ce." To me zan ce maka ka ce yarinya bata da lafiya saboda na taho da kurwata idan ta mutu ba za ka kyale ni ba to ka d'aure ni don Allah shine abinda za ka yi." Ya kashe wayarsa jin yadda na bud'e masa wuta idan ba rashin mutunci ba kawai ya kira ni yana ko'karin gaya mini magana ni na d'orawa yarinyar ciwo wane irin bala'i ne wannan ne." Tsabar takaici da damuwa ban iya zuwa dubiyar Dada ba a ranar saboda jikina ya riga ya gama mutuwa da rashin lafiyar yarinyar da kuma abinda ya gaya mini a kan hakan. Can wajen sha d'aya ya sake kira na na daga ban ce masa komai ba na ji yana fad'in.'" Za ku gaisa ko?'' Da yaran yake na ji muryar Usaina tana kiran Mama na ce." Naam Usai ina Hassana." Ta ce gata nan." Minal fa?" Ta ce." Ta yi bacci ta fad'a muryarta tana rawa. Na ce." Ya jikin nata." "Da sau'ki ta fad'a kamar za ta fashe da kuka. Na ce." To ba ni Hassana itama mu gaisa ko Ina Khalil?'' Ta ce." Yana 'kasa da Hassana." Na ji maganarta. "Mama ina yini." Na amsa "Lafiya lau Hassana ina dariyar da babu nisha'di na ce." Ya kuke ina Mairo." Ta ce." Tana can k'asa Minal ba ta da lafiya." Na ce." Allah Ya ba ta lafiya na kusa dawowa." Da sauri ta ce." Yaushe?" Domin na kwantar musu da hankali na ce." Gobe." Ina ji suka fara tsalle da dariya. Ya kar'bi wayar daga hannunta yana fad'in." Me yasa za ki gaya musu haka Amina kwananki nawa da tafiya." littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba A tak'aice na ce." Biyu." Ki ka ce za ki yi sati daya ko kin fasa." "Ban fasa ba." Na fad'a kai tsaye ina ji yana magana da yaran kan cewa su sauka k'asa wajan Mairo. Na daina jin motsinsu. Ya cigaba da cewa kin ga kuwa idan ba ki dawo gobe ba za su d'auke ki makaryaciya domin kuwa yaro baya mance magana kina dai jin tsalle da murnar da suke yi." "Umm! kawai na ce na yi shiru. Ya d'an yi gyaran murya kafin na ji shi yana fad'in." Yanzu kin tsane ni Amina ban yi miki komai ba wai menene lefina anan tare dake duka aka dinga wannan d'auki ba dad'in akan kwantar da ni da Maryam ta yi Malamin nan ya tsaya tsayin daka a kaina har sai da ya tabbatar da tabbatuwar lafiyata na cigaba da rayuwa da iyalina. Yanzu don Allah bai cancanci komai ba ban yi tsammanin zan samu wannan turjiyar daga wurinki ba tunda ai da farko ba haka ki ka nuna mini ba." Na ce." Har yanzu kuma ba ni da damuwa akan hakan ba. Ai kai ka ga zaka ka iya amma dai Ina gaya maka ba zan zauna a gidan da zaka haye kan k'aramar yarinya kamar Hajara ba babu ni a cikin wannan rashin sanin ciwon kai ba kuma zan kara had'a inuwa da Hauwa ba. Ka canza mini mazauni idan ya zama lallai sai ka zauna da ni." "Shikkenan za ki zauna gidanki na kano tunda hakan ki ke so amma ki sani za ki dinga d'aukar dogon lokaci kafin ki gan ni." Na ce." Babu damuwa ai." Ba tare da ya sake wata magana ba ya kashe wayarsa. Da safe da wurwuri na je na duba jikin Dada alhamdulillahi ta warware sai dai jikin girma idan abin ya motsa mata amma yini muka yi muna hira tana gaya mini abin alherin da ya yi musu a lokacin da ya zo dubata wattanin baya. Bayan sunan Fadila da kwana biyu na fara shirin tafiya tunda mun gama magana dashi kan yanke zamana a kano abinda dai ban yarda da shi ba shine barin yarana a gidansa na abuja da Hauwa dole za mu zauna akan hakan sai ya ba ni yarana wallahi ta ri'ke na ta. Ya kira ni yana gaya mini na tafi gobe domin shi ma a goben yake so ya shiga garin kanon saboda juma'ar da za ta zo za'a yi d'aurin auran a Bunkure kamar dai yadda ya gaya mini da farko. To kawai na ce masa. Ban kuma tafi a ranar da ya ce ba sai a washe garin ranar tukkuna Babansu Fadila da kansa Ya d'auke ni a mota zuwa kano. Gidan Hajja na yada zango anan shi ma ya kwana da sassafe yana karin kummalo ya d'auki hanya. Hajja ta dinga rarrashina tana tausata ban san me ya gaya mata ba amma yanayin yadda take rarrashina ya nuna mini cewa kamar ya gaya mata wata magana a kaina wadda take nuni da cewar ni ce yanzu ba ni son zaman lafiya tunda Hauwa ai ta mato a kan sonsa kuma dama kulawarsa da tarasa ne a baya ya sanya take yin hauka da tsananin kishi yanzu kam tunda tana samun abinda take so a wajensa yana juyata son ransa ba zai fad'i aibunta ba. Kuma a lokacin da ta fahimci akwai rikici a tsakaninmu ta bud'e wuta da kissa da ko'karin kafa kanta a wajensa. Ban katse ta ba na yi shiru Ina ta sauraranta tana cewa itama ta fi so na zauna anan din Hauwa da amarya kuma su yi zamansu a can abuja Sai yamma direbanta magaji ya d'auke ni a mota lokacin shi bai dawo daga bunkure ba duk da ba ranar ne daurin auran ba na lura da yadda yake ta rawar jiki da kai kawo har an yi masa invitation irin na wata da kuma na kati ya d'ora a status dinsa. A daran na kira Sahura na ce ta zo gobe da wuri dole sai ta taimaka mini mun gyara gidan. Can misalin sha daya saura na dare ya shigo gidan. Na gama shirin kwanciya ya shigo dakin ya same ni. Ya zauna gefena da alamar gajiya a tare da shi da kuma yanayi na damuwa da ta riga ta zame masa jiki yadda bai yi mini magana ba haka ni ma ban yi masa magana ba d'akin ya d'auki shiru na tsayin wani lokaci Na ji yana fad'in." Amina ya kamata mu yi gwajin nan na jini ( gyonotp) da yarinyar nan ko?" Shiru na yi ba tare da na ce masa komai ba. Ya dube ni yana fad'in." Yadda Malam D'aha ya d'aukaki wannan lamarin ba na tsammanin idan an ci karo da wata matsalar wadda ka iya rusa auran ya janye ku'dirinsa sanin halinsa na magana d'aya da kuma 'kin yarda da zamani da hasashen yahudu da nasara........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *146* Gida a kawo Fadila tunda haihuwar fari ce kuma dai gidan nata ba shi da wani spece inda Allah ya ta'kaita nasa ne ba ya haya ba ce wai hausawa suna fad'in guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni. Duk da haka ya yi kokari tunda d'aki uku ne da kicin da bandaki sai dai dak'unan duka ba ma su yalwa ba ne. Haihuwa da lafiya akwai anya farinciki yarinyar tana zauna da babyna a hannu tana bashi nono na cika da mamaki kwarai da gaske wai yau Fadila ce ri'ke da jinjiri har tana shayar da shi gani ni uwarta gotai-gotai da ni ban gama haihuwa wato idan da Kamaluna ma macace haka za mu jera haihuwa da shi duk da Fadila ta girme shi sosai amma dai da mace ne a yanzu da ake yi wa yara auran wuri wata'kila da tuni na aurar ni ma Yusuran Sahura ma tana can da nata tsohon cikin haihuwa ko yau ko gobe wai a haka ma ta yi 'bari na wata hud'u. A washe da safe Sukairaju ya d'auki hanyar komawa gida bayan ya karya kummalo. Yawan shige da ficen da ake yi a gidan dangin mijin yarinyar da danginmu suna zuwa ganin jarari Hakan bai ba mu damar 'kebewa sai a daran ranar dana kwana biyu a gidan tukkuna muka zauna muna tattauna al'amura masu yawa. Nan na gaya mata irin abubuwan da suke faruwa tsakanina da Hauwa da shawarar da na yanke sannan da auran da yake shirin yi a tsukin kwanakin nan tunda ya ce satin na sama suka yanke za a daura aure. Ta dinga mamaki tana fad'a kamar ta ari ba ki wai shi bashi da bakin da ba zai ce ya yi wa yarinyar girma ba ai ana barin halas don kunya wannan babbar asara ce da jin kunya idan har ya amince aka daura masa aure da yarinyar da ko shakka ba ta yi ta ji jinkanya da shi. Abin ya dinga ba ni dariya ganin yadda ta hakikance da gaske tana ta fad'a tana cewa girmansa ya zube a idonta tunda ya shigo da son zuciya dama can yana so idan ba haka ba daidai gwargwado ya yi wa malamin alheri mutumin ya rushe masa gida ya zamanantar dashi tare da sabunta tsangayu irin na zamani aikuwa ya yi abin a yaba masa kuma idan biya zai yi akan hidimar da ya yi masa ya biya shi mai zai sanya kawai a d'auki yarinya a bashi ya kuma sanya hannu ya kar'ba har yana cewa don babu yadda zai yi ne wannan karya ce tsantsa da yaudara. Da muka wayi gari ma ta tashi da mita shiga fita dari sai ta yi maganar tana cewa kin yi daidai ya kawo yarinyar su zauna da Hauwa a gidan ke ya canza miki wani idan ma ba zai yarda ki zauna a gidanki na kano ba ai yana da iko anan abujan sai ya samar miki da wani. Irin wad'annan masifun ne ya sanya wasu mazan ko basu da wadata suke rabawa matayensu gida to balle shi da yake da suttura da wadata tunda har abinda Hauwa take yi ya'ki ya'ki cinyewa kawai ya rabawa kowa mazauni sai a samu zaman lafiya. Na ji dad'i sosai ganin yadda wannan karon anti Yagana ta goyu da bayana na saki raina sosai ina jin sasaauci Kuma ban kunna wayata ba yau kwana biyu kenan wanda nasan yana can yana ta lalubena a wayar bai samu ba. Sai da na yi wanka na karya kullumalo tukkuna na fito falon na sami yarinyar tare da kawayenta na makaranta sun zo ganin jaririya suna ta tsokanarta sai suka ba ni sha'awa muka gaisa ina yi musu dariya cikin raina ina cewa duk yadda za ta kai ga baku labarin nakuda ba za ku fahimta ba sai ta riske ku tukkuna. Anti Yagana tana ta gyara kaji a kicin nace." In ban da abinki anti Yagana ai sai ki kira ni na taimaka miki." Ta ce." Ke ma ba lafiyar ce dake ba Amina na gode Allah ni da ya hore mini lafiyar wannan hidimar ta same ni Dada ciwo ya dabaibayeta nasan da ita za ta zo ta zauna mini" Na ce." K'warai hakane shirin da na yi yanzu zan tafi can babban gidan ne na duba jikinta zan dan zaga dangi mu gaisa." Ta furta. Hakan yana da kyau." Kujera na ja na zauna na kama mata aikin Muna gyara kajin a tare na ce." Na lura yaron nan da yake auran Fadila yana da zuciya wallahi gashi nan komai ya yi na al'ada." Ta gyad'a kanta tana cewa." K'warai Kam tunda ta haihu yake hidima domin da ta fara nakudar ma bai iya kaita asibitin gwamnati ba kudi ya fitar ya kai ta wanda za a bata kulawa wallahi sai da ta haihu ya kira ya gaya mana." Na furta." Irin wad'annan matasan ya kamata ace an d'auki aure an ba su masu zuciya da dogaro da kansu da kuma ko'karin ri'ke iyali daidai gwargwado." Daya daga cikin yan matan kawayen nata ta fito tana fad'in.''Mama ana kiran ki wayar ki." Ta mika mata wayar na riga ta kar'ba domin hannunta gaja-gaja yake fa jinin kajin da take gyarawa. Ina duba fuskar wayar naga sunan Alhaji Tajuden da haka ta yi serving lambarsa Na daga tare da sanya mata a kunne ina ji yana gaisheta da mutuntawa kamar yadda ya saba itama ta amsa cikin nutsuwa har tana tambayarsa yara ya ce duka suna lafiya sannan ya yi mata barka da arziki kafin ya fara tambayarta ina nake ya yi ta kirana a waya baya samuna. Ta dube ni kafin ta ce masa gani nan a zaune. Sai na ji yana cewa da ita ta gaya mini na kunna wayata akwai muhimmiyar maganar da za mu yi. Ta ce masa to in sha Allahu suka yi sallama. Ta d'an dube ni a sanyaye tana fad'in." Na ji shi a sanyaye yana magana babu nutsuwa Amina kada dai ki ce da biyu ki ka zo nan garin kar ki ce da ni yaji ki ka yi akan wannan matsalar domin idan bacin haka ai ban ga dalilin da zai sanya ki kashe wayarki ba." Na ce." E, to ba yaji na yi ba amma dai Ina tsammanin ba ni komawa Abuja kai tsaye daga na bar nan kano zan sauka gidana na sharad'a tunda ya'ki fahimtar abinda nake nufi." Ta gyad'a kanta tana cewa." Ba ni son hakan ya haifar miki da wata matsalar Amina amma ni kaina a son raina nafiso a raba muku muhalli sai hankalina ya fi kwanciya. Na furta." Duk mai hankali da tsinkaye abinda zai duba kenan matsawar muna zaune a inuwa guda da Hauwa ba za a taba samun zaman lafiya ba Shima ba zai huta ba tunda ni dai na zame mata ciwon ido anti Yagana wallahi har mamakin yadda Hauwa take zafafawa kanta a kaina ni kuma ba ta raina kwata kwata ban kuma dauketa a matsayin kishiya da zata daga mini hankali ba. Kawai yanzu nutsuwa da kwanciyar hankali nake buk'ata shiyasa na ce ba ni buk'atar zama da ita a gida daya." Ta furta." Hakane akwai hujja mai karfi a tare dake ni ma ina bayanki amma yanzu tunda ya ce ki kunna wayarki za ku yi magana ki kunna din mu ji mai zai ce." Na ce." To shikkenan zan kuna." Sai da muka gama aikin gyara kajin tukkuna ta d'ora a wuta na wanke hannuna da omo sannan na koma d'akin na d'auki wayata na kunna minti goma sha biyar a tsakani ya kira na daga a nutse na yi sallama ya amsa na gaishe shi nan ma ya amsa babu annasuwa. Kafin ya d'ora da fad'in." Yarinyar Minal tun bayan da suka dawo daga makaranta ta samu ba kya gidan kwanta zazza'bi ya rufe ta ya hau ya sauka har takai da sai da aka yi mata karin ruwa Amina ida ta rasu wallahi ba zan yafe miki ba." Gabana na d'an fad'uwa na ce." Ban gane abinda kake nufi ba." Ya ce." Kin ji abinda na fad'a Amina ai kin san ba ki da gaskiya shiyasa ki ka kashe wayarki tsayin kwana biyu." Na ce." Mayya ce ni ma shiyasa na kama kurwar Minal na taho da ita nan maiduguri to don Allah idan ta rasu ka d'aure ni har igiya ta yi rara." Ya ce." Abinda za ki ce kenan?" Na ce." To me zan ce maka ka ce yarinya bata da lafiya saboda na taho da kurwata idan ta mutu ba za ka kyale ni ba to ka d'aure ni don Allah shine abinda za ka yi." Ya kashe wayarsa jin yadda na bud'e masa wuta idan ba rashin mutunci ba kawai ya kira ni yana ko'karin gaya mini magana ni na d'orawa yarinyar ciwo wane irin bala'i ne wannan ne." Tsabar takaici da damuwa ban iya zuwa dubiyar Dada ba a ranar saboda jikina ya riga ya gama mutuwa da rashin lafiyar yarinyar da kuma abinda ya gaya mini a kan hakan. Can wajen sha d'aya ya sake kira na na daga ban ce masa komai ba na ji yana fad'in.'" Za ku gaisa ko?'' Da yaran yake na ji muryar Usaina tana kiran Mama na ce." Naam Usai ina Hassana." Ta ce gata nan." Minal fa?" Ta ce." Ta yi bacci ta fad'a muryarta tana rawa. Na ce." Ya jikin nata." "Da sau'ki ta fad'a kamar za ta fashe da kuka. Na ce." To ba ni Hassana itama mu gaisa ko Ina Khalil?'' Ta ce." Yana 'kasa da Hassana." Na ji maganarta. "Mama ina yini." Na amsa "Lafiya lau Hassana ina dariyar da babu nisha'di na ce." Ya kuke ina Mairo." Ta ce." Tana can k'asa Minal ba ta da lafiya." Na ce." Allah Ya ba ta lafiya na kusa dawowa." Da sauri ta ce." Yaushe?" Domin na kwantar musu da hankali na ce." Gobe." Ina ji suka fara tsalle da dariya. Ya kar'bi wayar daga hannunta yana fad'in." Me yasa za ki gaya musu haka Amina kwananki nawa da tafiya." littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba A tak'aice na ce." Biyu." Ki ka ce za ki yi sati daya ko kin fasa." "Ban fasa ba." Na fad'a kai tsaye ina ji yana magana da yaran kan cewa su sauka k'asa wajan Mairo. Na daina jin motsinsu. Ya cigaba da cewa kin ga kuwa idan ba ki dawo gobe ba za su d'auke ki makaryaciya domin kuwa yaro baya mance magana kina dai jin tsalle da murnar da suke yi." "Umm! kawai na ce na yi shiru. Ya d'an yi gyaran murya kafin na ji shi yana fad'in." Yanzu kin tsane ni Amina ban yi miki komai ba wai menene lefina anan tare dake duka aka dinga wannan d'auki ba dad'in akan kwantar da ni da Maryam ta yi Malamin nan ya tsaya tsayin daka a kaina har sai da ya tabbatar da tabbatuwar lafiyata na cigaba da rayuwa da iyalina. Yanzu don Allah bai cancanci komai ba ban yi tsammanin zan samu wannan turjiyar daga wurinki ba tunda ai da farko ba haka ki ka nuna mini ba." Na ce." Har yanzu kuma ba ni da damuwa akan hakan ba. Ai kai ka ga zaka ka iya amma dai Ina gaya maka ba zan zauna a gidan da zaka haye kan k'aramar yarinya kamar Hajara ba babu ni a cikin wannan rashin sanin ciwon kai ba kuma zan kara had'a inuwa da Hauwa ba. Ka canza mini mazauni idan ya zama lallai sai ka zauna da ni." "Shikkenan za ki zauna gidanki na kano tunda hakan ki ke so amma ki sani za ki dinga d'aukar dogon lokaci kafin ki gan ni." Na ce." Babu damuwa ai." Ba tare da ya sake wata magana ba ya kashe wayarsa. Da safe da wurwuri na je na duba jikin Dada alhamdulillahi ta warware sai dai jikin girma idan abin ya motsa mata amma yini muka yi muna hira tana gaya mini abin alherin da ya yi musu a lokacin da ya zo dubata wattanin baya. Bayan sunan Fadila da kwana biyu na fara shirin tafiya tunda mun gama magana dashi kan yanke zamana a kano abinda dai ban yarda da shi ba shine barin yarana a gidansa na abuja da Hauwa dole za mu zauna akan hakan sai ya ba ni yarana wallahi ta ri'ke na ta. Ya kira ni yana gaya mini na tafi gobe domin shi ma a goben yake so ya shiga garin kanon saboda juma'ar da za ta zo za'a yi d'aurin auran a Bunkure kamar dai yadda ya gaya mini da farko. To kawai na ce masa. Ban kuma tafi a ranar da ya ce ba sai a washe garin ranar tukkuna Babansu Fadila da kansa Ya d'auke ni a mota zuwa kano. Gidan Hajja na yada zango anan shi ma ya kwana da sassafe yana karin kummalo ya d'auki hanya. Hajja ta dinga rarrashina tana tausata ban san me ya gaya mata ba amma yanayin yadda take rarrashina ya nuna mini cewa kamar ya gaya mata wata magana a kaina wadda take nuni da cewar ni ce yanzu ba ni son zaman lafiya tunda Hauwa ai ta mato a kan sonsa kuma dama kulawarsa da tarasa ne a baya ya sanya take yin hauka da tsananin kishi yanzu kam tunda tana samun abinda take so a wajensa yana juyata son ransa ba zai fad'i aibunta ba. Kuma a lokacin da ta fahimci akwai rikici a tsakaninmu ta bud'e wuta da kissa da ko'karin kafa kanta a wajensa. Ban katse ta ba na yi shiru Ina ta sauraranta tana cewa itama ta fi so na zauna anan din Hauwa da amarya kuma su yi zamansu a can abuja Sai yamma direbanta magaji ya d'auke ni a mota lokacin shi bai dawo daga bunkure ba duk da ba ranar ne daurin auran ba na lura da yadda yake ta rawar jiki da kai kawo har an yi masa invitation irin na wata da kuma na kati ya d'ora a status dinsa. A daran na kira Sahura na ce ta zo gobe da wuri dole sai ta taimaka mini mun gyara gidan. Can misalin sha daya saura na dare ya shigo gidan. Na gama shirin kwanciya ya shigo dakin ya same ni. Ya zauna gefena da alamar gajiya a tare da shi da kuma yanayi na damuwa da ta riga ta zame masa jiki yadda bai yi mini magana ba haka ni ma ban yi masa magana ba d'akin ya d'auki shiru na tsayin wani lokaci Na ji yana fad'in." Amina ya kamata mu yi gwajin nan na jini ( gyonotp) da yarinyar nan ko?" Shiru na yi ba tare da na ce masa komai ba. Ya dube ni yana fad'in." Yadda Malam D'aha ya d'aukaki wannan lamarin ba na tsammanin idan an ci karo da wata matsalar wadda ka iya rusa auran ya janye ku'dirinsa sanin halinsa na magana d'aya da kuma 'kin yarda da zamani da hasashen yahudu da nasara........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *147* Na d'an jima ina kallonsa tare da yin nazari a kan maganarsa na kasa tantance shin shawarata yake nema ko kuma umarni. Sai kawai na yi shiru ba wai don ba ni da amsar da zan bashi ba maganar ce kawai ta sake jefa ni cikin mamaki tunda har yana maganar gwajin jini (gyonotype) ya shirya kwanciya da yarinyar duk da k'arancin shekarunta kuwa. Na yi shiru tare da juyar da kaina saboda tsabar takaici. Ya sake maimaita mini maganar . Sai na dube shi a sakarce na ce." Kai duk shige da ficen da kake yi ba ka yi gwajin jinin ba." Ya d'an b'ata ransa yana fad'in.'' Amina ba kya yi mini lafazi cikin dad'in rai ko kina magana da sa'anki ne abubuwan fa da ki ke yi sun take shari'a kuma suna yi yawa." Na d'an daidaita yanayina ina ce wa." To shikkenan na ji yanzu me kake so na ce?'' Ya sauke ajiyar zuciya tare da matso ni sosai ya kama hannuna ya rike sai kuma ya had'e yatsunmu ya matse gam. A dan tausashe ya furta." Ke ce abokiyar shawarata shiyasa da na fara wannan tunanin na tuntubeki dacewar yin gwajin jini ko ya ki ka ce." Wani abu ya sake tokare mini wuya." A tak'aice na ce." Hakan yana da kyau." Sai ya cigaba da cewa." Ba ni fatan sake auran macce wadda za mu yi ta haifar yara masu lalura Amina wannan cikin da kike d'auke shi yana raina koyaushe da tunanin abinda za ki haifa mini nake mai lafiya ne ko mara lafiya saboda wannan ciwon gaskiya ne akwai shi. Ba ni so a 'daura auran nan jinina dana yarinyar bai jitu ba ta zama k'aramar bazawara domin ba zan iya kar'bar kaddara a karo na biyu ba wannan shine." Na dai yi shiru ban ce komai ba ba wai don ba ni da abin fad'a ba. Ya sake matsowa jikina yana magana can kasa." Ya ki ke ganin ya za mu yi,?" Na dube shi babu yabo babu fallasa na ce."Fisabillahi me kake so na ce akan hakan?" "Ki ba ni shawarar yadda zan yi." Ya fad'a yana d'ora bakinsa a dokin wuyana. Na ce.''To shawarata ku je ku yi gwajin jinin ina ga kamar zai fi alheri." Na ji hucin numfashinsa yana cewa." Idan an samu matsala na yi yaya da malam 'Daha." "Sai ka yi masa cikakken bayani zai gane!" Na fad'a ina d'an janye jikina jin wani abu ya fara yi mini yawo. Ya ce." Ba zai yarda ba Amina." Na ce." To gaskiya kaima kana da lefi me yasa tun farkon fara maganar ba ku yi gwajin ba idan an tabbatar da daidaituwar jini sai a yi godiya ga Allah idan kuma jinin bai inganta daidai yadda ake so ba sai ka datse maganar da wuri ka kawo masa hujjoji da misalai." Ya furta." Ba ni da nutsuwa fa Amina tun sanda ya ba ni kyautar yarinyar na rasa sukuni gabad'aya domin ni kaina ba ni son auran irin k'ananu haka koda da k'addarar sake wani auran a tare da ni wadda ta fita shekaru zan aura amma wannan tayi yarinyata da yawa." Na ce." Hakan kuma bai hana ka nemi shawara wajan gwajin jini ba ko duk da ta yi yarinyata ai ka shirya takarta ko ba haka ba ne." Shiru ya yi bai ba ni amsa ba. Wai ni zai yi wa kalaman yaudara na janye jikina ya sake rukunkume ni yana tatta'ba wasu sassa na jikina tare da sauke ajiyar zuciya. Gabad'aya nema yake yi ya daga mini hankali a halin kuma da nake ciki ba ni buk'atarsa ko kad'an jikin dai yana so walwala da annashuwar da zata bari a tari lamarin ne babu. Babu yadda bai yi da ni ba a daran a kan dole sai ya kwanta da ni na ce a a gajiye nake ba zan iya ba. Dole ya ha'kura da asuba ya sake nemana da rarrashi da kwantar da kai ya fara ko'karin gaya mini wasu maganganu wanda suka danganci Hauwa na katse shi da sauri na nuna ba ni so ban san yaushe ya zama munafikin namiji ba ina ruwana Hauwa tana gamsar da shi bata gamsar da shi ba abinda ya dame ni ba ne. Na ci da kulafuci kamar dambun kuturu ya ma'kale ni na kasa motsi babu yadda na iya haka nan na kyaleshi ya yi abinda yake so kamar zai shid'e saboda gigita lissafinsa gabad'aya ya kwance. Da kaina na shiga kicin tunda ya sanya an kawo mini komai na bukata. Na soya doya da kwai da tea sannan na dafawa kaina indomee. Nan d'akina muka yi breakfast din babu yabo babu fallasa amma dai na kasa sakin jikina duk zantukan da yake akan auran nan da zai yi kawai ina jinsa ne da kunne dalili nema yake yi ya rainawa mutane hankali tunda yadda yake nunawa ko jininsa dana yarinyar bai daidaita ba zai iya yin jayayya da malamin ba yadda tun farko ya amince masa to abu ne mai wahala daga baya ya je ya ce masa ga matsala wadda daga baya turawa suka bijiro da ita tunda ai ko a zamanin annabawa ba a san da wani gwajin jini kafin aure ba haka kuma duka iyaye da kakanni suka ta so. Da haka dai ya yi wanka ya kintsa ya fita yana gaya mini ya yi baki daga kamaru idan ya gama dashi da wuri zanje bunkure a takaice na yi masa addu'ar dawowa lafiya Sai wajan daya da rabi Sahura ta zo lokacin ne ta taso daga aiki. Sai bayan da muka ci abinci muka yi sallah tukkuna muka fara aikin gyaran gidan wanda kusan zan iya cewa itace karfin aikin ta shasshare mini ko'ina tas aka yi mopping gidan ya dawo hayyacinsa. Sannan fa muka zauna ina zolayarta ta yi ki'ba tana ta'be baki kuma da gasken ta yi kiba wallahi alamu sun nuna bata da damuwa tana cin gashin kanta. Idan farko akwai damuwar yanzu makomar auran Idiris ta bayyana ya sanya mata nutsuwa da kwanciyar hankali domin dai alkali ya tilasta shi sakin yarinyar kamar yadda iyayenta suka buk'ata dalili shedu sun shaida babu abinci ingantacce a gidansa sannan kuma alamu na nuna cewa shi din yafi karfinta ta fannin auratayya. Ya kuma yanke masa kudin da zai dinga aikawa yarinyar na goyon ciki har sai ta haihu ta shayar masa da abinda ta haifa kafin ta yaye ya kar'bi d'ansa a bisa adalci. A wannan matsayar aka tsaya da shi. Tana gaya mini da gumu ta yi gumu ya rasa yadda zai yi ya gaya mata halin da ake ciki. Na ce." To Sahura tunda dai ya yi nadama sai ki yi hakuri don Allah kada dukan ya yi masa yawa ki kaddara cewa rabon haihuwa ne ya sanya shi rakito auran yarinyar nan." Ta ce." Ai ban hana shi kwana a gidana ba Amina kwanciya da ni ne na ce ba zai yi ba. Kuma gidan da ki ka ba ni ya balle ni kwado ya sanya matarsa sun kwashe kaya sati biyu da suka wuce na sanya a zuba mini 'yan haya a ciki. Abincin dai ina ba shi idan na yi ga waje nan ya kwanta ya tashi amma babu mu'amula ta aure. Na ce." To kin sake bashi lasisin yawon dare kenan?" Ta'be bakinta ta yi ba tace komai ba. A daidai lokacin kira ya shigo wayata ina dubawa na ga maigidan ne na ajiye ta katse ya sake kira na d'auka tare da daidaita maganata. Na ji yana fad'in." Na fasa zuwa bunkuren nan Amina gani nan dawowa gida." A tak'aice na ce." To.'' na riga shi kashe wayar na ajiye a gefana ina tsaki Ta bata rai tana fad'in." Menene haka don Allah." Na ce." Da aka yi me?" Ta gyad'a kanta tana cewa." Wallahi tallahi ki ji tsoron Allah akan mutumin nan Amina." Sosai na zuba mata Ido da mamakin maganarta haka kawai ba ta san irin zaman da nake yi dashi ba tana cewa na ji tsoron Allah akan sa. Ko da yake dama can ita 'yar dakinsa ce bata ta'ba ganin lefinsa. To mai baka kuma ya ninke munanan halaye ya bayyana kyakykyawan ya za a yi ta fahimci aibunsa tunda ba tare take rayuwa da shi ba. Ta cigaba da cewa." Menene abin tsaki don ya gaya miki cewa zai dawo gidansa ne fa." Na ce." Hajiya kamata ya yi ki tambaye ni dalilin dawowata nan ba kawai kai tsaye ki fara tuhumata ba ke matsalata dake kenan ba kya taba ganin lefinsa. A d'an sanyaye ta ce." Menene to?" Duk abinda yake faruwa na gaya mata tun daga kan matsaltsalun da yake tsakani na da Hauwa da auran da aka bashi a bunkure. Ta yi sakato da baki tana kallona gabad'aya bakinta ya mutu da kyar ta ce ni haukan da Hauwa take yi bai dame ni ba Amina sai maganar auran nan da ki ka ce zai yi ai na gane yarinyar da ki ke gaya mini ko ba itace ta kawo mini abinci a lokacin da naje ba." Na ce." E ita ce.'' Ta zura mini ido tana kallo kafin ta ce." Ai ko nono ba ta dashi wannan yarinyar ba ta isa aure ba don bata da 'barage ba na tsammanin ba ta fara jinin haila." Na ce." To ya kar'bi dai auranta sai ya cigaba da raino amma dai da kamar wuya tunda d'azu yake gaya mini wai za su yi gwajin gyonotype kin ga kuwa da sha'awar sabon waje a cikin ransa mussaman budurcin k'aramar yarinya irin wannan ba na tunanin zai zura mata tsayin wasu shekaru." Ta ce." Don Allah ki daina fad'in haka Amina kunya ma nake ji wallahi yanzu shi sai ya iya tu'bewa a gaban wannan tatsitsiyar?" Na ce." To me ye a ciki Amina wallahi ki daina mamaki da sha'anin maza abu ne mai sau'ki a wajansa." Ta yi zugum tana dubana kafin ta ce." Lallai mutumin nan ya ba ni haushi wallahi gaskiya abin bai yi mini ba ya kuma shirya cinye muku fuska yarinyar 'yar cikinku ta kalleku a banzance tunda ai duk ranar da ya kwanta da ita to gabad'aya ba ku da bambanci wallahi. Na yi shiru Ina nazarin maganarta tabbas hakane ranar da ya kwanta da Hajara to itama daga lokacin za ta ji kanta a matsayin matar gida daidai da kowa. Ba ni fargaba akan tarbiyar yarinyar amma yau da gobe idan zama ya yi zama dole wasu daga cikin d'abiunta su canza dalili itama tana ji kanta cewa matar gida ce." Sahura bakinta ya mutu duk kaud'in nan nata a kansa bakinta murus ya yi tana jin haushin haka ta yi la'asar ta yi mini sallama ta tafi. Ba ta jima da barin gidan ba ya dawo. Ya yi wanka a dakinsa na sama ya canza ya kaya na shan iska ya sauko kasan ya same ni zaune a kujera Ina kallo ya zauna kusa da ni yayin da kamshin turaransa ya game wajan gabad'aya. Na dube shi kad'an kafin na janye idona ban ce komai ba. Sai ya riko hannuna yana cewa." Ta karfi da yaji dai kin zama bebiya giwa wai me ya yi zafi ne uhum?'' Ban ce komai ba na zare hannuna. Ya kamo yatsan da ya sanya mini zoben nan ya sumbuta ya ciro shi daga yatsansa ya sake mayar mini yana fad'in." Ban yi zuciya ba amma ya kamata ki sassauta mini ki yi mini adalci akan duk abubuwan da suke faruwa ke kan ki kin san abinda ki ke yi ba daidai ba ne ko?" Na ce." Adalci wane iri kake so na yi maka na hana ka kar'bar auran da aka baka ne? A lokacin daka gaya mini addu'a na yi maka kuma dole sai ka yi hakuri a wannan lokacin tunda ni kaina ba jin dad'in jikina nake yi ba." Ya d'ora hannunsa saman cikina yana fad'in." Na sani amma me yasa ki ka cire duk wani subsidy a kaina kin daina sona ne." Ban iya kallonsa ba saboda takaici. Ya juyo da fuskata yana cewa." Zan fasa auran nan fa wallahi ba zan iya ba." Na yi shiru dai ban ce komai ba daidai lokacin ne Hauwa ta kira shi yana d'agawa ta fara kuka tana fad'in." Minal ce ta suma!" Ya ki'dime sosai hannunsa har yana karkarwa yana tambayarta ya ake ciki yanzu. Yadda take bashi amsa ya sanya na fahimci cewa k'arya take yi wallahi. Kawai dai za ta fake da ciwon yarinyar ne ta daga masa hankali. Ya kashe wayar da tsananin tashin hankali yana fad'in." Ki yi wa Allah da annabi ki tashi mu tafi yarinyar nan Minal tana sonki Amina kada hakkinta ya kama ki tunda ta dalilinki komai yana iya faruwa kada mu yi rashinta. A nutse na ce." Ka je ka kawo mini su nan gabad'aya zan ri'ke su Ina nan akan bakana ba ni sake zama da Hauwa. Idan kuma za ka canza mata gida ni ta bar mini wanda take ciki sai na koma." Ya ce." Ba ki ji an ce suma take yi ba. Na gaya miki cewa jikinta ya'ki dad'i wallahi tunda ki ka bar gidan nan." Na ce." Ni da hankalina sarai babu abinda Hauwa za ta k'irkira ya firgita ni. Minal kuwa Ina tsammanin ma uwarta ba ta kaini sonta ba." wannan littafin dai na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Ya yi shiru yana kallona na wani lokaci kafin ya haura samansa. Na dubi agogo biyar da rabi jim kad'an ya sauko cikin manyan kaya babbar riga da 'yar ciki. Cikin zuciyata na ce." Aiki ya same ka in dai Hauwa ce sharrinta yawa gare shi neman kudi ma wataran sai ka yi da gaske za ka yi." Ya tsaya gabana yana fad'in." Rarrashi da ban ha'kuri babu irin kalar da ban yi miki ba. Ba a yi maccan da zan dinga kwantar mata da kai tana gara ni kamar gare-gare ba. Ki sani Amina kina da magabata kuma hukuncin saki a hannuna yake sai na ga dama zan yi. Wallahi tallahi zan d'auki mummunan mataki akan abinda ki ke yi mini. Na ce." Sanar da magabatana halin da muke ciki shi zai kara dagula maka lamari domin wallahi ba zaka taba samun kaina ba. Shekara nawa ina ha'kuri dakai tare da bin umarinnka ina so ko ba ba na so. So kake yi na zauna da Hauwa wataran ta d'auki makami ta farauci rayuwata. Ko za ka gaya mini cewa har yanzu ba ka fahimci irin tsananin kiyayyar da take nuna mini ba. Ka kawo mini yarana na ri'ke a hannuna domin ba zan iya barin su a tare da ita ba za ta iya yi musu lahani ta kowace siga. Idan ba za ka iya rabuwa da ni ba to bar ni anan din ni wata daula ba damuna ta yi ba. Idan za ka shekara ba ka zo in da nake ba babu damuwa na sahale maka." Ya cire gilashin idonsa ya sanya hankici ya goge ya mayar dashi idon nasa. A d'an rikice ya sake cirewa ya goge kafin ya sake mayar dashi. Na d'auke kaina a raina ina fad'in zautuwa yanzu ka fara yin ta ka wani binjimo babbar riga. Gaskiya na karyawa Hauwa d'ankwali a wannan ga'bar da alama ta d'auki hanyar rama kashin da ya bata. Na yarda Minal bata da lafiya amma haka kawai zuciyata ba ta amince mini da cewa da gaske ne ta suma ba Na juya ina kallonsa a lokacin da ya kama hanyar fita kenan abujan ya nufa saboda an ce masa yarinya ta suma. Aikuwa dai ga dukkanin alamu mutumin nan so yake yi ya yi mutuwar tsaye. Kwana uku da tafiyarsa bai kira ni a waya ba ni ma ban kira shi ba ana hudun ne ya zo tare da yarinyar da akwatin kayanta. Ta ma'kalkale ni tana dariya da shafa fuskata duk garin jikin nan nata sai da ya rairaye ta yi d'an wuya. Ko da na gaishe shi sama-sama ya amsa ya bar wajen. Na ri'ke hannunta muka haura saman a tare yana wanka da ya fito ya gan ni a zaune ya sake d'aure fuska ya d'auki basiline ya zauna can nesa da ni yana shafawa a jikinsa. Yarinyar ta fara zagaye d'akin tana neman abin wasa. Ni abinda yake yi ma dariya yake ba ni abinda ba zai iya ba. Duk tsananin gabar sa ban san me ya sanya yanzu ta daina tasiri a kan kansa ba domin daga ya fara ma yake bari kwana daya biyu zuwa uku ya fara neman hanyar da za a shirya. Na ce." Ina 'yan biyu na ga Minal ita kadai ai ba haka muka yi da kai ba." Ya ce." Tunda kin haife ni Amina ai ya zame mini dole na bi umarininki kada na lalace ko?" Na danne dariyar da nake ji tana yun'kuro mini na ce." Ban haife ka ba amma abinda yake a hakkina nake tambayarka ni 'yan biyu na ce ka kawo mini." Ya furta." Wannan din da na kawo miki sai ki yi cilli da ita tunda ai ba gidan ubanta ba ne." Na ce." Mu yi magana wadda take daidai kuma ta fahimta mu kuma cire son zuciya. Ban ce ba zan ri'ke yarinyar nan ba tunda har ka kawo mini ita amma ba ni son tashin hankali daga kowane 'bangare. Idan har da sanin uwarta ka daukota ta amince da hakan babu damuwa a wajena. Amma ya zama dole a kawo mini yarana." Ya ce." Wannan ne kuma ba ki isa ba. Ba za ki dinga gindaya mini sharadai ba. Hauwa ta da ba ta yanzu ba ce domin duk yadda ki ke tunanin tana 'kin ki na tabbatar da cewa ba zata zalinci yara ba, kuma sanin da ki ka yi mata ta canza sosai ta kuma kar'bi dukkanin kuskuranta." Na ce." Babu ruwana wannan matsalarka ce kai da ita. Ni dai Hauwa ko za ta had'iyi al'kur'ani don tsoron Allah da gaskiya ba zan yarda da ita ba domin ita din mutuniyar banza ce mara tsoron Allah." Ya ce." Cin fuska ne ki dinga kiranta da irin wannan kalaman Amina kwanakin baya kin mare ta a fuska duka ta yi hakuri saboda tana jin maganata." Na ce." Me yasa baka rama mata ba a lokacin ba, ai da ka sani kawai ka d'aukar mata fansa kuma yanzu ma ai bata 'baci ba ga ni zaune kusa dakai ka rama mata kawai......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700.....0542382124. BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *148* Share ni ya yi ya tafi ya je ya d'auko rigarsa jallabiya mai yankakken hannu ya sanya a jikinsa ya fesa turare sosai sannan ya sauka kasa ya bar ni da yarinyar a d'akin. Na tashi tare da kama hannunta muka sauka baya falon k'asa da alama fita ya yi. Kai tsaye kicin na nufa na d'ora sanwar dare gefe guda kuma kasan marata na d'an yi mini ciwo kadan da cijewar kafa gobe alhamis asibiti zan yi sammakon zuwa domin duba lafiyata da abinda yake cikina a auna abinda yake cikin domin tabbatar da lafiya yake kwance. Duk inda na ajiye kafata nan yarinyar take ajiye tata tana yi mini hirar 'yan uwan nata biyu can kasan zuciyata kewarsu ta ishe ni haka kawai yanzu nake tsananin jininsu a cikin raina ba kuma na tsammanin zan iya bar wa Hauwa su wallahi sai dai duk rigimar da za mu yi muyi ta a shirye nake gabad'aya na gama dawowa daga rakiyar Hauwa. Bayan sallah Isha'i ya shigo muna d'aki ni da Minal na bata wayata tana game ya buk'aci abinci ya kama hanya ya fita da jin haushi domin ya'ki sakin fuskarsa tun da ya dawo. Na shirya masa abinda na dafa na hau saman da tire din a hannuna cikin jan kafa daya ta ri'ke mini cikin ya yi mini nauyi ainun. Na same shi yana waya na ajiye tiran kusa da shi na juya zan fita ya dakatar da ni. Na juyo ina kallonsa fuskata a had'e sai kuma ya ce" Je ki kawai." Na kada kaina ba tare da nace komai ba na sauka yarinyar tana ta game cikin nishadi cikin zuciyata na ce ikon Allah kenan ban haifi yarinyar nan ba Allah Ya jarabbeta da kaunata haka zalika ni ma ina sonta sosai domin ba ta d'auko kamanin uwarta ba fuskar ta ubanta ce garin jikin ni kuma na washeta tunda uwar da uban duka sirira ne. Ya kwana can shi kadai na kwana da Minal da safe na yi mata wanka na shirya ni ma na kintsa. Ruwan shayi kawai na iya dafawa na soya 'kawai zalla na had'a mata tea din ta karya. Ina yin nawa karin kummalon ne ya shigo ya shirya shi ma da alama fita zai yi da wuri a haka har yanzu babu nutsuwa da cikakkiyar walwala a tare dashi tana ganinsa ta fara fad'in." Baba ka ga." Tana nuna masa wayata dake ajiye game din dana kamo mata tana yi ban kashe ba. Tana ta maimaita maganar "Baba ka gani." Ya karaso ciki sosai ya kar'bi wayar yana dubawa ya d'an saki fuska yana cewa." Na gani Minal mu gaisa ko?'' Ta daga kanta sai ya mika hannu ya kamo nata yana fad'in." Haka ake cewa ina kwana." Ta sake daga kanta tana fad'in." Baba ina kwana." Ya amsa yana dariya wadda ban ga ya yi ta ba tunda ya shigo jiya. Ya d'an tsira mini ido na wani lokaci kafin ya ce." Ba za ki gaishe ni ba?" Na ajiye kofin shayin da yake hannuna na ce." Ina kwana?" Ya amsa a tak'aice tare da tankwashe kafa a gabana. Sai na yi kasa da kaina ban sake ce masa komai. Ya furta." Had'a mini tea din ma nasha. Ya janyo flat din dake gabana da soyayyan kwai fefe uku manya na d'auki kofi na tsiyaya masa ruwan shayin nasa madara kad'an da milo domin wasu lukutan ma ya fi shan tsura shima amma dai shi yana shan madarar amma kadan ba kamar Baban Saude da gabad'aya madarar ce ma ba ya sha. Yana kurbar ruwan shayin yana kallona kamar wadda ya samu tibi can na ji yana fad'in." Naga duk kin tasa kin kara girma ina fatan lafiya." Ya fad'a yana duba yatsun hannuna da suma suka d'an yi kumburi duk irin na masu ciki. Na ce." Lafiya lau in sha Allahu amma dai yanzu shirin da na yi asibiti zan je ina so su yi mini awo sannan kafata na ciwo amma dai hakan ba matsala ba ne in sha Allahu idan ciki ya yi nauyi ya shiga watanni shida zuwa bakwai akan ci karo da irin wad'annan matsaltsalun." Ya gyad'a kansa yana cigaba da yi mini kallon kurulla kafin ya ajiye kofin hannunsa ya furta." Za mu je na kai ki asibitin da kaina idan ya so zan yi magana da magaji direban Hajja idan kin kammala sai ya zo ya d'auke ki ku je da Minal ku gaisa." A tak'aice na ce to shikkenan. A mota yake gaya mini daga asibitin bunkure zai nufa domin dai gobe ne za a daura aure bayan an yi sallar Juma'a akwai zai d'auko yarinyar still su dawo asibitin a tare domin akwai likitan da ya yi magana da shi a sirrin ce zai yi mata (genotype) tunda shi dama tuntuni ya san matsayin jininsa. Na ce." Wane irin a sirrin ce sai kace munafurci me yasa baka so a san za ka yi aure ka bugo kati kana d'ora shi a status dinka menene abin boyewa. Ya furta." Ni yarinyar ce ba ni so a gani." Na ce." Kasan abin kunya ne kenan ko?" Ya yi shiru bai ce komai ba can kuma ya furta." Babu wata kunya fa akan yin koyi da annabin rahama ni dai a yadda nake garau Amina ba na shakkar zamantakewata da mu'amula ta aure da yarinya irin Hajara saboda nasan kaina zan kuma yi mata iyakacin bakin kokarina. Kawai dai har yanzu abin ne bai kwanta mini a rai ba. Maganar buga kati ai ba wani abu ba ne na bugawa bazawara ma balle budurwa." Na yi shiru ina auna maganarsa. Ni dai lokacin daurin aure na babu wani kati da ya buga tunda abin duka ya zo mana a bazata sai da aka d'aura tukkuna gidajen jaridu suka sani. Yana nufin Hajiya Maryam ne. Sai na share ban tanka masa ba duk kuwa da cewa na ji zafin maganar da yake akan yarinya ya nuna budurwa ta fi bazawara kenan ita ya kamata ace an bugawa kati. Duk tsayin rayuwar da muke yi ban ta'ba ganinsa yana tu'ka mota ba sai yau duk da yake ya ce tafiyar sirri ce har da sanya takunkumi da rufe hancinsa da bakinsa da (fecemark) Haka muka isa asibitin Malam Aminu Kano yana ta yi mini zantukan marasa dadin saurare tunda duka akan auran da zai daura gobe ne ni Ina nake da wata shawara da zan bashi a ce sai da asiki ya zo gaban goshi tukkuna zai yi gwajin jinin ya so wata matsala ta faru idan ba su samu haduwar jini ba fadi yake yi akwai matsala domin dai shi ba zai iya gayawa malam 'Daha ya fasa ba saboda wannan dalili zai bari a d'aura auran amma fa zai bar yarinyar a gidansu kafin ya yankewa kansa hukunci. Jin haka ya sanya jikina yin sanyi tabbas wannan son rai ne tsagowaronsa babu yadda za a yi na yarda ya lalatawa yarinya kuruciya wane irin wulakanci ne wannan gwara duk yadda za a yi a yau din idan results bai daidaita ba a zauna zama na mussaman da muhukunta domin su fayyacewa Malam D'aha illar hakan. Yana had'a ni da likitan da zai duba ni ya yi mini sallama a ka yi sa'a cikin asibitin in banda likitan babu wanda ya fahimci shine tunda motar da muke ciki babu tambarinsa kamar sauran motocinsa na zurga-zurga wanda suke tabbatar da zuwansa waje idan an gan su a ajiye. Scanning ya ba ni naje na yi da result ya fito ya gama dubawa ya dinga washe baki yana fad'in." Hajiya wannan albishirin ni ya kamata na yi wa Yallabai please a yi mini wannan." Na yi murmushi ina fad'in." To shikkenan duk da bai gaya mini abinda sakamako ya nuna ba a jikina na ji cewa tagwaye zan sake haifa domin yanayin wannan cikin yanayin cikinsu Hassana sai dai wannan din da d'an bambanci kad'an. Na ji yana fad'in." Yara maza ne biyu yadda sakamako ya nuna dukkaninsu cikin koshin lafiya sun kuma juya yadda ake so nan da sati hud'u sai ki sake zuwa a yi miki awo domin mu sake tabbatar da yanayin kwanciyarsu. Cikin zuciyata na kira sunan Allah tare da yin godiya a gare shi. Na ce." In sha Allahu Dr na gade sosai. Muka fito dare da Minal da takardar result din a hannuna sai sannan na sanyata a jakata can na hangi Magaji zaune a gindin wata bishiya ya taso da sauri ya karaso tare da risinawa yana gaishe ni na amsa da kulawa ya kama hannun Minal muka nufi inda ya ajiye motar a tare. Hajja ta ji dadin ganinmu su biyu kacal a falo ita da Kamalu suna hira yana 'bare ta mata lemo zaki. Ta dinga washe bakinta ganina da Minal tana cewa." Ke yaushe aka kawo ki ne k'awata." Minal ta no'ke kafad'arta ta'ki zuwa wajanta ta tsaya kusa da ni tare da dafa cinyata. Na gyara zamana a hankali cikin kulawa na gaisheta ta amsa tana ta yi mini maraba. Na dubi Kamalu lokacin da yake gaishe ni girma ya yi mini a ido kwarai ya sake yin fad'i da 'barage mazantaka dai ta bayyana tunda dama tuntuni muryarsa ta fashe an balaga ga wani gemu zororo a ha'barsa. Cikin zuciyata na ce yaron nan dai ya rantse sai ya zama d'an izala Gashi makarantar da ya yi ta almajiranci ba ni tsammanin ta 'yan alhalissuna ce. Kawai dai abinda ransa ya fi ra'ayi kenan yaro ya nutsu sosai cike da wata iriyar kammala ta mussaman zahirin kammaninsa da mahaifinsa ta fito 'baro-'baro bambamcinsu kawai shi Yaya Aminu ba shi da gemu kuma bashi da kuzarin yaron amma duk wanda ya ga Kamalu a yanzu zai tabbatar da cewa hoton ubansa ne Hajja ta fad'i take daga Ina kuke cikin wannan rana ta k'arfe d'aya Amina." Na ce." Wallahi Hajja daga asibiti nake shine na ce bari na biyo mu gaisa kawarki mata ta gaishe ki." Ta sanya dariya tana jan hannun yarinyar tana sake no'kewa a jikina. Ta ce." Ina fatan dai lafiya ko Amina sannunki da ibada Ubangiji Allah Ya raba ku lafiya." Na ce." Amin ya rabbi Hajja lafiya lau wallahi abinda sakamako ya nuna kenan. Ta dinga fad'in." Alhamdulillahi cike da godiyar da Allah da jin dadi kafin ta shiga kwalawa iyami kira mai aikinta wai ta kawo mana ruwa." Kamalu ya ce." Hajja ni me nake yi bari na kawo mata da kaina. Ya ajiye lemon zaki da yake hannunsa ya nufi kicin da sauri lokacin Hajja ta d'auki lemon da ya gama 'barewa tana mikawa yarinyar da fad'in." Zo ki kar'ba to tunda kin 'ki zuwa mu gaisa." kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Ta kuwa tafi za ta kar'bo lemon saboda rashin kunya gabad'aya muka fashe da dariya. Ta ce." Yusi ai yau tun safe ya fita kasuwa da yake ya ce bashi da karatu yau shine ya yi sammakon fita amma nan da biyar da rabi za ki gan shi ya dawo." Na ce." Ya zama sarkin kasuwa ai." Tana dariya ta ce." Haka ake son namiji ya kasance ai." Kamalu ya ajiye mini ruwa da lemo masu sanyi a gabana. Na dube shi ina fad'in." Baka da hankali wanene zai sha wannan ruwan da wannan sanyin." Yana murmushi ya ce." Mama ai na ga ana rana ne sosai ruwan sanyi zai fi kashe miki ishi." Na ce"D'auke ka kawo mini mara sanyi." Da sauri ya yi yadda na ce din ya kawo mini ya bude ya tsiyaya mini a Kofi. Na d'auka na sha na bawa Minal Tasha na ajiye kofin saman plate din da ya kawo ruwan.. Hajja ta ce me za a sanya Iyami ta dafa muku Amina ni dai ce mata na yi ta saka mini danwake." Na ce." Aikuwa a yi dani Hajja har na yi sha'awarsa. Tana dariya ta shiga k'walawa iyami kira ta fito ganina ya sanya ta risinawa tana gaishe ni na amsa mata da kulawa Hajja ta ce da ita ta kara garin danwaken ta saka shi da d'an dama. Ta amsa cike da bin umarni ta koma bakin aikinta. Kamalu ya shiga dakinsu tsayin minti goma ya fito da wasu littafai a hannunsa gabad'aya muka bi shi da ido Hajja ta ce." Makarantar za ka tafi da wuri haka?" Ya ce." E, Hajja amma kafin nan zan biya gidan Gwaggo." Ta ce." Yawwa gwara da ka tuna mini shiga kicin ka ce da iyami ta baka garin danwaken nan leda biyar sai ka tafi mata da shi." Ya ce." To shikkenan. Ta dube ni tana cewa." Abu ne na marmari duk ranar da ta yi sha'awa sai ta tsumbula. Na yi shiru ina murmushi gefe guda kuma ina kara kambaba mutunci da halin dattako irin nata ga kyauta ga kirki Hajja mutuniyar kirki ce sosai Gwaggo ta zama 'kawarta kuma aminiyarta. Na tsinkayi maganarta tana fad'in." Ai ya sanar da ku d'aurin auransa gobe ne a Bunkure ko." Na ce." Eh ya gaya mana Hajja Allah Ya sanya alheri." Ta amsa da Amin. Kamalu ya fito da ledar garin danwaken a hannunsa yana yi mana sallama tare da ce mini zai zo cikin satin nan in sha Allah. Ta dube ni cikin nutsuwa kafin ta furta." Amina Malam D'aha mutumin kirki ne kwarai da aniya kuma mutumin maigidana ne tare na san su abokai ne kuma masu rufawa juna asiri ta kowace siga. Lokacin da Tajo yake gaya mini kyautar auren 'diya da Malam 'Daha ya ba shi na yi farinciki domin sanin da na yi cewa gidan karamci ne da ilimi da addini gidan yi wa al'kur'ani hidima tabbas had'a iri da jinin Malam D'aha abin alfahari ne tare da fatan samun zuri'a nagartattu. Sai dai kuma jikina ya yi sanyi sosai lokacin da ya nuna mini hoton yarinyar na ganta 'yar karama nama sheda fuskarta tunda itace ta dinga dawainiyar kawo mana abinci a lokacin da Tajo ya kwanta ciwo a gidan. A mizani na tunanina yarinyar ba tsarar auransa ba ce domin ya yi mata nisa sosai babu hadi gabad'aya babu dacewa. Amma a mizani na shari'a hakan ba haramun ba ne domin manzon Allah s.a.w shi ma ya yi irin wannan aure ya raini Nana Aisha har ta kai munzali kafin ya fara rayuwar aure da ita. Malam D'aha Tajo ya yi niyyar bawa d'iyarsa kuma na tabbatar da cewa da zuciya daya ya kulla wannan al'amarin ba don samun abin duniya ba na sanshi sosai a can baya abin duniya bai dame shi ba mutum ne mai dattako da sanin ya kamata." Ta yi shiru tana sauke ajiyar zucciya. Ni kuwa cikin raina ina fad'in anan dai bai san ya kamata ba Hajja tunda har ya iya bawa dattijo yarinya karama irin wannan ai zamanin annabawa daban da wanda muke ciki yanzu. Ta cigaba da cewa." Na bashi goyon baya akan ya kar'bi kyautar da aka yi masa da kyakykyawar zuciya ku yi hakuri, ku kara akan wanda kuke yi in sha Allahu rabbi ba za ku samu matsala da yarinyar ba. Itama Hauwa zan kira ta a waya domin na kara tausar zuciyata dama itace fitinanniya ku yi hakuri ku kawar da kan ku na dan wani lokaci komai zai wuce." Na ce." Wallahi babu komai Hajja ai yarinyar bata da matsala zamu zauna lafiya da juna kuma na yi miki alkawari ba za a samu matsala ta wajena ba." Godiya da sanya albarka har sai da na ji nauyi da kunya na ce ta daina gode mini domin ban yi abinda ya kai ta yi mini irin wannan godiyar ba a ganina ni ce zan yi mata godiya bisa ayyukan alheran da take yi wa a alhalina. Biyar daidai na fito da niyyar tafiya har lokacin Yusi bai dawo ba fadi take yi zai ji takaici kuwa idan ya dawo ya ji labarin kin zo. Na ce." Kawai sai ya zo gida ya same ni Hajja ba zan zauna jiran dawowarsa ba zan yi abinci idan na koma." Muka yi sallama cikin girmama juna da mutuntawa Magaji direbanta ya d'auke ni a mota har gidana. Sai da na yi magriba tukkuna na shiga kicin jallop nake sha'awa ta taliya da kifi ita na yi na zuba mana ni da Minal muka ci a kwano d'aya na ajiye wa maigidan 'yar kad'an dalili nasan ko zai ci ba dayawa ba tunda ba cimarsa ba ce taliya da makaroni. Abinda ya fi so dangin towo kowane iri sakawara funkaso ko wainar masa ta bauchi Yana son faten doya ma abinci da miya bai dame shi sosai ba sai ya ce asa masa miya kad'an saman shinkafa. Yana kuma son gurasa da miya sosai. Wajan goma saura ya shigo tare da Sukairaju ashe tare suka zo garin. Ya d'an tsaya daga bakin kofa ya kar'bi wayoyinsa daga hannuna ya gaishe ni na amsa babu yabo babu fallasa ya juya da sauri ya fita shi kuma ya karaso wajan da nake zaune hannunsa ri'ke dana Minal A d'an hargitse yake gaskiya tsabar ma baya hayyacinsa gilashinsa a hannu yake abinda bai ta'ba faruwa ba duk rintsi da wahala baya cire gilashin nan na idonsa, sai sau daya lokacin da ya fad'i a garin bunkure yana dawowa hayyacinsa kuwa ya mayar da abinsa kamar wanda aka haifa tare da shi na ta'ba tambayarsa ko yana da matsalar Ido ya ce mini a a yana sanya shine domin kara karfin gani kuma dai ya zame masa jiki idan ma Babu shi a idonsa baya jin dad'i......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA,#700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *149* Na zura masa ido jikina a sanyaye ga dukkanin alamu akwai matsala. Da kyar na bud'e bakina da ya yi mini nauyi na ce masa barka da zuwa. Ya amsa yana ri'ke hannun Minal da take ta jan babbar rigar jikinsa. Da ya amsa mini bai sake cewa komai ba ya wuce. Na bi shi da kallo cikin lissafi a zuciyata shin menene ya gigita shi hakane? ko dai akwai matsala ta fannin daidaituwar jini shi da yarinyar tunda ya gaya mini zai ce ya d'aukota a yi mata genotype din tunda shi ya sanya nasa As ne kamar yadda nake As. Idan hakan shi ya hadda masa wannan gigicewar lallai ya fito da abinda yake cikin ransa wanda yake ta nuku-nuku da shi yana kuma so ya yaudare mu kan cewa baya son auranta. Alamu sun nuna lallai zuciyarsa ba ta so faruwar hakan ba. Na tashi na bi shi saman na same shi zaune gefan gado Minal na ta wasa da agogon hannunsa da ya cire ya ajiye shi kuma yana zaune ya dai cire babbar rigar ya ajiye amma har yanzu yana cikin rashin hayyaci. Motsin shigowata ya sanya shi dubana. Bai janye idonsa ba har na isa kusa da shi na zauna still idona a kansa a takaice na ce." Me yake faruwa ne?" Ya yi jim kafin dube ni da wani yanayi ya furta "Yarinyar As ce Amina. Akwai matsala tunda ni ma As ne duka d'anjuma ne da d'anjummai, gidan Malam D'aha cike yake da ba'ki na nesa dana kusa sun d'ora manya tukuwane domin abincin jama'ar d'aurin aure dalili shi mutum ne na mutane k'warai da gaske da yawa jamaarsa ta mahaifina ne cikinsu wad'anda suka rage da iyalinsu babu wanda bai san da maganar wannan auran ba. Babban abinda ya fi d'aga mini hankali anan shine yadda zan gaya masa cewa a janye d'aurin auran nan saboda wannan matsalar da bai zama lallai ya yarda da ita ba tunda ke kan ki kin sani abu ne mai wahala ya amince da koyarwar yahuduwa a matsayinsa na malamin addini kuma mutumin karkara." Na yi shiru ina kallonsa zuciya na gaya mini ba wannan dalilin kad'ai ya sanya shi gigicewa ba akwai wani dalilin dai da yake boyewa. Na ce." Yanzu wace shawara ka yanke?" Ya yi shiru kawai yana kallona sai da na sake maimaita maganata tukkuna ya furta." Ban yanke ba har yanzu Amina bana jin zan iya dakatar da Malam 'Daha dangane da abinda ya niyyata ya kuma yi gangami a kansa." Na furta." Za ka bari a d'aura auran kenan ?" Ya gyad'a kansa yana kallona." Sai na ce." To idan hakane menene abin damuwa tunda ka ji ka gani me yasa za ka daga hankalinka. Ka bar wa Allah wata'kila sai ka ga kun samar da yara masu lafiya ba irin wanda ake tsammani ba." Ya ce." Ai ba wani sonta nake ba Amina. Maccan da nake tsoron rabuwa da ita itace nake jin zan yi hakuri na zauna zaman aure da ita idan aka ci karo da wannan matsalar ga misali nan a kanki. Amma ina ji ina gani ba zan yi gangancin ba gaskiya magana kenan." Murmushin takaici na yi kafin na ce." Akwai zalinci tsantsa idan har abinda ka fada da gaske ne a cikin zuciyarka to bari na gaya maka daka kai har malamin kun zalinci yarinyar nan. Ya kamata duk wani b'oye -boye da kake yi ka fito fili ka yi wa mahukutanku bayani nufi na walliyanku wai shin kai karamin yaro ne? A tunanina saurayi dan shekara a shirin da biyar ba zai yarda a yi masa irin wannan kutsen ba ya yi shiru sai dai dama idan yana so. Idan ka bari aka daura maka aure da yarinyar nan to dama kana sonta a cikin ranka. Soyayyar da za ka nuna mata da iyayenta a yanzu ka fito musu da gaskiyar abinda yake zuciyarsa kuma ka gaya musu babban dalilin da ya sanya ka janye nasan ko wasu basu yarda ba wasu daga ciki za su yarda tunda duka yanzu kai ya waye." Cike da kosawa ya ce." Na gaya miki Amina Malam D'aha fa ba zai ta'ba amincewa da wannan batun ba. Akwai shi da hujja wadda zai fatattaki duk likitan da na kai masa domin ya fahimtar da shi. Ni dai da bakina ba zan iya furta masa cewa na janye ba saboda ga dalilina akwai hujja mai karfi a wajensa. Na ce." To shikkenan na ji idan an d'aura menene makomar yarinyar abinda nake so na ji kenan." na kudi ne don girman Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Ya daga kafadarsa yana fad'in." Wallahi ban yanke hukunci ba tukkuna amma dai ina jadadda miki ba ni yin zaman aure da ita. Na bari a d'aura auran domin kada na katse masa hanzari bayan tarin jama'ar da ya gayyato gidansa ana ta hidima. Akwai ciwo da takaici a ce an fasa abin zai yi muni da rashin dad'i." Na ce." Babban abinda zai yi masa muni shine a daura auran ka bar masa yarinya a gida a jingine wannan shine asalin cin mutunci da wulakanci don haka wallahi kada ka fara." Ya zura mini ido yana kallona kafin ya sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta furta." Ya zan yi to Amina na gaya mini dalilai na." Na ce." Gobe tunda sai an sakko daga sallar Juma'a za a daura ka buga sammako ka d'auki likitan da ya yi muku genotype din ku je dashi gaban malamin ya yi masa cikakken bayani tare da illolin ciwon da yadda yaran da aka haifa suke shan wahala iyayensu ma suke cikin wuya duk a dalilin ciwon. Ubangiji sai ya dubi zuciyarka ya sanya malamin ya fahimci abinda ake so ya gane." Ya ce." To idan an yi haka mu yi yaya da jama'ar da muka gayawa wasu daga mutanansa fa na ce miki sun zo gidansa a cike yake da jama'a." Kai tsaye na ce." An yi haka da yawa ai ba a kanku za a fara ba irin wannan idan kaddara ta gifta sai wani ya maye gurbi. Idan hakan ya kasance yadda muke so kun fahimtar da malamin ya gane sai ka yi gaggawar kira na a wayar zan nemawa wani auranta sai a daura da shi kawai." Ya yi sakato yana kallona na ce." Wannan itace hanya mafi sau'ki da za ka warware matsalarka ni ma zan baka gudumuwa daidai gwargwado amma idan har ka bari aka daura auran da wata niyya a zuciyarka ka cutar da yarinyar sosai kuma ba ka yi wa malam 'Daha adalci ba. Ya rike hannuna tamau yana sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Na gode giwa Allah Ya yi miki albarka kaina ya d'aure gabad'aya a yanzu neman mafita nake yi." Ni ma na sauke ajiyar zuciya a nutse na ce." Na kawo maka abinci ko?" Ya gyad'a kansa yana fadin." Kawo mini." Na tashi na fita. Lokacin dana dawo yana bandaki na zauna gefan gado Minal tana tsakiyar gadon nasa a zaune tana ta wasa kira ya shigo wayarsa. Minal ta d'auko wayar ta miko mini tana fad'in." Ana kiran wayar Baba, Mama ana kiran wayar Baba." Na kar'ba na duba sai na ga mamanta ce Hauwa. Na ajiye wayar har ta katse ta sake kira a daidai lokacin da ya fito da toilet din ya zo da sauri ya d'auki wayar yasa a kunne. Ya amsa gaisuwar da take yi masa. Jim kad'an ya ce." Malama na ce."A a itama Aminar za ta dawo nan cikinku in sha Allahu." Ya d'an yi shiru yana sauraranta can kuma ya ce." To shikkenan ku zo ke da yaran gabad'aya ku sauka a gidan Hajja zan yi magana da Ade ku yi duk shirin da za ku yi yau da daddare." Ya yi shiru yana sauraranta na dan wani lokaci sai ya ja tsaki ya cigaba da cewa." Wai sau nawa zan gaya miki ne gidan ba shi da spece din da za ku zauna ku biyu can gidan Hajja akwai part dina ku sauka a can hakan ya yi ko?" Ya sake yin shiru dai yana sauraranta ta jima kuwa tana yin magana kafin ya ce." To na ji za a gyara in sha Allahu, zan kira ki da safe kafin ku taho." Ya kashe wayar yana kallona kafin ya ce." Hauwa ce wai ita dole sai ta dawo kano itama yara kuma can duka suke karatu gobe Juma'a na ce su zo gabad'aya lahadi da sassafe mu koma gabad'aya har dake." Shiru na yi ban ce masa komai ba. Su zo na ji dadin hakan na kwashi yarana cikin sau'ki komawa kuma sai dai ya koma da ita da yaranta amma ni mun dawo nan gabad'aya a nema musu wata makarantar. Ganin na yi shiru ban ce masa komai ba sai hankalinsa ya sake kwanciya domin ya d'auka na yarda. Jallop din taliyar da na yi tsammanin ba zai ci da yawa ba wadda na rage masa kaf ya cinyata ya sha ruwan da lemo yana gaya mini tun tea din da muka sha tare a d'akina bai kara cin komai ba. Abinda ya faru kenan da assuba yana dawowa daga sallah ya fara kimtsawa na yi ko'karin gama abin kari da wuri domin ya karya kafin ya tafi. Gabad'aya duka a dame yake haka dai ya zauna yana karyawa yana gaya mini jikinsa gabad'aya a mace yake domin baya tsammanin Malam D'aha zai amince da duk wani bayanin da za a yi masa. Na ce." Ka yi ta addu'a Allah Ya zab'a maka abinda ya fi alhari kawai idan har ya amince na gaya maka ka sanar da ni zan nemawa wani auranta ." Ya amsa mini da to shikkenan. A gabana ya kira likitan ya yi masa bayani sosai yadda zai tsara malamin duk da aikinsa ne wayar da kan jama'a akan mas'aloli masu yawa a matsayinsa na likita amma dai ya kara tunasar dashi cewa wajan wanda za su je babban malami ne kuma mai tsauri wanda boko bata ratsa shi ba sai tsantsar tauhidi da kadaita Allah ." Ya kira Hauwa ta ce sun taso tun wajen shida yanzu kuma k'arfe shida da rabi kenan sun yi minti talatin akan hanya. Har mun yi sallama zai tafi ya dawo yana tambaya wai sai na gaya masa wanda zan nemawa auran idan dashi bai yi yuwa ba. Na ce." Me kake ci na baka na zuba, za ka san shi in sha Allah." Sai kawai ya girgiza kansa babu kuzari ya furta." Sai na dawo." Ya fice da sauri Minal tana fad'in." Baba sai ka dawo." Ya daga mata hannu ba tare da ya amsa ba ya fita.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *150* Na sake sauke ajiyar zuciyar da ba zan iya lissafa adadinta ba. Hannun yarinyar na ja muka nufi d'aki ina mamakin sha'anin Hauwa ni yanzu ma ta daina ba ni haushi da mamaki dariya take ba ni wallahi. Gefan gado na zauna kafafuna na dan rawa haka kawai nake jin faduwar gaba da fargaba akan wannan sha'aninan wani sashe na zuciyata na gaya mini bai zama lallai malamin ya yarda da duk wani nau'in bayani da za a yi masa ba akan wannan lalura. Wanda na gama fahimtar cewa abinda shima ya assasawa maigidan gigita kenan da damuwa da kuma rashin nutsuwa. A nasa tunanin idan malamin ya kafe akan ra'ayinsa sai kawai ya bari a d'aura auran wanda hakan ba ita mafita ba tunda da wani kudiri a ransa da kuma abinda ya niyyata akan yarinyar wanda yake nuna tsantsar son zuciya da rashin tausayawa kuruciya. Malam D'aha Malami ne kuma mutumin da ne kuma mutumin karkara wanda ba shi da wayewa da ilimin zamani na boko abu ne mai wahala duk bayanin da za a yi masa akan illar ciwon ya amince da cewa ba kutse aka yi wa shariar Ubangiji ba gashi dai bincike domin samun mafita ya sanya har manyan likitoci da shugabanni suka kafa dokar yin gwajin jini kafin k'ulla rayuwar auratayya ta din-din don samun sahihan yara masu wadatacciyar lafiya. Jikina a mace na dauki wayata dake saman dirowar gefan gadona babu wanda na yi wa sha'awar auran yarinyar Hajara sai Usaini. Yaro ne nutsatstse mai kuma zuciya tun yana yaro ba shi da matsala har zuwa yanzu da ya kai munzalin girma. To sai dai kuma hanzari ba gudu ba anan shine duk da bai zama dole ba wata'kila Usaini yana iya zama As tunda ni ma itace mun had'a uba uwa kowa da tasa. Na ji daga bakin mutane da dama cewa yana iya canzawa a wasu lukutan amma zuciyata ba ta gazgata hakan ba a ganina idan har sakamako na farko ya nuna matsayin jini da wahala ya sake canzawa. Can kasan zuciya na ji tana gaya mini cewa babu lallai Usaini ya kasance As don kin kasance Amina. Wannan hasashen na zuciyata ya kara sanya mini kwarin gwiwa sosai Har indai k'addara ta raba auran da za a daura shi a yau kuma za su ba mu yarinyar zan yi farinciki da hakan domin kuwa duk inda ake neman nutsuwa da tarbiya yarinyar ta kai daidai gwargwado kuma ta yi sa'a da auransa tunda shi ma bai wuce ashirin da takwas ba. Bugun farko ya daga na ji shi cikin kasuwa da hayaniya a wajen da yake. Sama-sama nake jin maganarsa na ce." Har ka fita kasuwa Usaini k'arfe nawa yanzu. Yana dariya ya furta." Takwas saura anti akwai ba'kin da muka yi daga nijar sun yi sayayya jiya mun had'a musu kayan ba su samu damar d'auka ba sai yau da sassafe suka yi mini waya yanzu na shiga kasuwar ma anti." Na ce." Allah Ya taimaka idan ka sallame su kazo gidana na sharad'a na zo garin yau kusan sati daya kenan akwai maganar da za mu tattauna." Ya furta." Ba na son rufe shago anti afuwaa zan iya jira Hamusu ya zo tunda sai tara da rabi yake zuwa kasuwar." Na ce." Babu matsala ka jira shi idan ya zo sai ka taho ina sauraranka." Sallama muka yi na kashe wayar na ajiye zuciyata na yi mini wani nazari. Kada fa Ummansu ta bijire akan wannan yun'kuri nasan ba ni da matsala da yaron haka zalika ba ni da matsala da Babanmu Ummansu Saminu itace birkitacciya dama tana jin haushi tana ganin duk sabgata idan ta tashi ba a gayyatarta gidana na abuja bata ta'ba zuwa ba Ummansu Hadiza ce ta je sau biyu ta jima tana yi wa anti Yagana wannan korafin tana gaya mata ita ba mu d'auketa a matsayin uwa ba duk hidimarmu idan ta tashi sai mu nemi Ummansu Hadiza kuma abin ba haka ba ne Ummansu Hadiza ta fita shishshigi ita kuma duk abinda zai faru sai ta ce lallai sai an gaya mata ba idan ba mu sanar da ita ba sai ta k'ullaci abin a cikin ranta. Itace damuwata kawai tunda d'anta ita take da iko da abinta idan ta ce bata yarda ba babu yadda zan yi dole na ha'kura amma zahiri na yi wa yaron sha'awar yarinyar. Na nemi lambar anti Yagana ta katse ba ta daga ba ina sake kira kuwa ta daga muka gaisa ta ce." Ya ake ciki Amina Ina fatan babu matsala rashin sukuni ya hana ni kiran ki na ji ya ake ciki." Na ce." Alhamdulillahi babu matsala ina ganin zan ci nasara akan abinda nake so in sha Allahu dama dalilin da ya sanya na kira ki wata shawara nake so mu yi shin ya ki ka ga ni?" Duka na kwashe abinda yake faruwa na gaya mata. Ta ce." To ai wannan ba matsala ba ce Amina alheri fa ki ke niyyar k'ullawa ban ga dalilin da zai sanya mahaifiyarsa ta nuna rashin amincewarta akan hakan ba ke din Yar uwasa ce kuma ba za ki had'a shi aure da yarinyar da ba ki tabbatar da tarbiyarta ba. Bayan dangantaka ta jini ke uwar dakinsa ce a karkashinki yake idan tana da kunya ai ba zata kalubance ki ba." Na ce." Hakane anti Yagana amma a cire maganar uwar d'akin nan na dai zauna a matsayina na 'yar uwarsa dalili anan shine ba ni so shi da mahaifiyarsa suga don yana karkashina zan juya masa rayuwa a yanzu ma idan ya zo zan fara tambayarsa shin yana da budurwa tsayayyiya idan ya ce bashi da ita sai na gaya masa shirina. Ina da tabbacin ba zai bijire mini ba." Ta ce." Misali na yi miki ai idan ta yi tsalle ta nuna d'anta sai a nuna mata ke kuma uwar dakinsa ce a kasuwa sanadinki har yake saya mata atama super ta daura ta yafa mayafi mai tsada ." Dariya ta kama ni ina fad'in." Anti Yagana kenan, to kin ji dama dalilin da ya sanya nace bari na gaya miki kafin na yanke hukunci Babanmu bashi da matsala hakan zai yi masa dad'i." Ta ce." Ni ma na baki goyon baya amma kafin nan ki fara tambayarsa genotype dinsa da blood group idan ya sani shikkenan idan kuma bai san matsayin jininsa ba sai ya yi maza yaje a yi masa Na ce." To shikkenan haka za a yi in sha Allahu anti Yagana a gaishe mini da masu jegon." Ta ce." Gasu nan suna bacci gabad'aya tunda aka yi wankan safe suka kwanta." Na yi dariya ina fad'in." Fadila manya a shafa mini kan Shahida." Sunan anti Yagana aka sanyawa yarinyar sai uwar tace tana so a dinga kiranta da Shahida a lokacin da ta fad'i hakan na ce wata shekarar sai ki haifo Shahid. Kunya kuwa ta kamata na ce to idan ba rashin kunya ba duk muna zaune ita zata za'bawa 'yarta suna ai ta yi kara ta bari a samu sunan da za a dinga kiran yarinyar tunda ai dole a sakaye dalilin sunan uwarta ne. Goma da sha biyu ya kira ni a waya ya shigo gate amma maigadi ya hana shi shigowa. Na sanya hijabina na fita harbar gidan suna daga can bakin gate har da Ayuba direba. Ganin fitowata ya sanya ya kafe babur dinsa Yana kallon Ayuba yake cewa." Idan shi zai ce bai gane ni ba ai kai za ka sheda fuskata ko ba kai ba ne direban da ka dinga zurga-zurgar kai su asibiti a lokacin da Babanmu ya kwana rashin lafiya." Ayuba ya dinga fad'in." Tabbas ni ne yanzu na sheda fuskarka ka yi hakuri wallahi d'ayan muka fi ganewa." Yana nufin Hamusu. Shi kuma Usaini haushi ya ji yadda suka tsayar dashi a bakin gate suna tuhumarsa domin ba mu yi kama ba ko daya gashi kuma ya ce musu shi kanina ne kuma zuwansa daya gidan shiyasa suke yi masa wanna titsiyar Hamusu suka fi shedawa." Ayuba ya biyo shi a baya yana dan bashi ha'kuri na ce ya je kawai babu komai suma suna kan aikinsu ne babu lefi don sun ga bak'uwar fuska sun nemi dalili. Da yake safiya ce ko ruwan da na ajiye masa bai sha ba muka gaisa sosai da bayan rabuwa zafin nemansa ya sanya shima ko gidana na Abuja bai taba zuwa ba kullum yana kasuwa a sanin da na yi masa tun Yana yaro manemi ne baya zama duk wasu lissafe-lissafe da za mu yi ta waya muke yin komai kamar dai yadda muke yi da Hamusu abinda ya gaya mini shima Usaini haka zai gaya mini sun yi bala'in cirar tuta a wajena dalili kuwa anan shine ni kaina sai dai na ce dukiyar itace tawa ta farko kenan da na zuba domin gudanar da kasuwancin abinda zai ru'banya daga baya kuwa duk kokarinsu ne kuma duk inda suka hango cigaba da sauri za su gaya mini a jarraba ko za a samu nasara. Shekara na yi kuwa za a yi lissafi a fitar da riba da uwar kudi a sallami kowa hakkinsa. Usaini yana tura kayanmu gari-gari ta hanyar yanar gizo an san shi sosai kamar dai yanzu da yake gaya mini ba'ki sun zo daga nijar domin sayan kaya ba ni tamtama a online suka had'u." Ya dinga jan Minal da wasa tana janyewa na rashin sabo har sai da ya samu nutsuwa tukkuna na dube shi a tsanake na ce."kasan dalilin kiran ka da na yi?" Ya girgiza kansa a hankali yana fad'in. A a anti amina Allah ya sa lafiya." Na ce." Lafiya lau kuma alheri ne." Sai ya saki fuskarsa sosai har da gyara zama yana fad'in." To Ina jinki anti ko za mu sake bude wani shagon ne?" Na ce." A a matar aure na yi maka." Saranda ya yi ya zare ido yana fad'in." Matar aure anti a ina take kuma? ban gama gini na ba dalilin da ya sanya kenan na janye idona daga kan 'yan mata domin ba ni so na fara soyayya da budurwa iyayenta su ce na fito. Ni kuma nafiso sai na kammala komai a tsanake sai na nemi mai hankali daidai da ni na aura." Murmushi na yi Ina kallonsa yana ta jero mini bayani wanda na tabbatar da cewa gaskiya ce tsantsa kuma duk maganar da ya furta tana fitowa ne da can kasan zuciyarsa. Na ce." Maganar gini mai sau'ki ne Usaini don ma dai ka d'auki irin na zamani da kyale-kyale ai da tuni ka gama ko ba shine wanda ka ta'ba turo mini ta waya ba kwanaki." Ya ce." Eh shine gidan anti amma yanzu aiki ya kara nisa." Na ce." To alhamdulillahi Usaini wata yarinya ce na yi maka sha'awarta nutsatstsiya kuma 'yar Malamai idan har Usaini ya samu nasarar mallakar yarinyar nan ina yi masa albishir da cewa ya gama dacewa da ma'aratussaliha." Ya yi murmushi yana fad'in.'' Kai anti Amina wannan yarinyar a ina take yadda na ji kina kwarzantata wallahi har kin kwadaita mini ita a cikin raina." Nasa dariya ina cewa." Ka ji d'an gari ko, sai ma ka ganta doguwa chocolate color ga ka farar fata yaranku za su zama wata kala masu kyau." Ya sunkuyar da kansa yana murmushi." Na ce." Ka amince kuma ka bar mini wuka da nama a hannuna?" Ya gyada kansa yana fad'in." Na amince anti Amina wallahi ba ni da ja kuma ba ni da haufi a kan ki na yi farinciki da wannan zabin da ki ka yi mini tun banga yarinyar nan ba har ta zauna a zuciyata. Fuskata ta kara yalwata da annashuwa na ce." Aikuwa na gode sosai na ji dadin wannan alfarma da ka yi mini amma yau din nan nake so ka sanar da Ummanku duk abinda yake faruwa kuma ina son sanin matsayin jininka." Ya ce." Zan gaya mata a yau din in sha Allah. Matsayin jinina kuwa( O) ne genotype (AA)" Wani irin sanyi ya sauka a zuciyata shikkenan an samu yadda ake buk'ata ta wannan bangaran akwai dacewa da cancanta wancan bangaran ne kuma ban san wainar da suke toya ba. Gabana ya fadi na daga kai na dubi agogo sha daya saura kuma yadda suka tsara jadawalin d'aurin auran bayan an yi sallar Juma'a ne. Na saki ajiyar zuciya ina fad'in ." Ma sha Allah ta kowane bangare an samu daidaito idan har Allah Ya kaddara wannan auran Usaini ina yi maka murna sosai domin ka yi mata." Ya ce." Na gode sosai anti Allah Ya saka da alheri ya kuma kara girma abinda ki ke yi mana na zumunci Ubangiji Allah sanya miki a mizani Allah Ya jikan iyaye da kakanni." Na dinga amsawa da Amin Amin Allah Ya taimake mu gabad'aya." Muka yi sallama kafin kafin ya tashi na gaya masa zuwa dare zan kira shi domin karin bayani. Ya kama hanya ya tafi na zauna cike da nazari da zullumi hankalina kuma yanzu ya yi can garin bunkure ko a wane hali ake yanzu bai kira ni ba nasan kuma tuntuni ya isa garin tunda babu wata nisa. Na d'auki wayata gabana na d'an fad'uwa na lalubi lambarwa wayar na shiga sai dai har ta katse bai daga ba. Na sake kira a karo na biyu nan ma bai daga ba jikina ya mutu na ajiye wayar da rashin kuzari." BUNKURE. Cike gidan yake zuri'ar Malam D'aha 'ya'ya da jikoki kadai sun isa gayya ba sai sun gayyatowa kowa ba. Amma da yake wannan sha'anin na mussaman ne a gare shi gidan cike yake da nau'in ba'ki daga gari gari nasa da na matayensa mussaman uwar bikin uwargidansa mahaifiyar amarya wato Inno. An gama towon d'aurin aure suna ta malmale shi a leda ana zuba shi a manyan kuloli gefa guda kuma kirigar tukuwanan miya ne guda biyu kan murhu suke ta cin wuta suna zab'abbaka da tashin kamshi mai shanana a saman miyar. Yaran mata surukan gidan suna can bakin turgijejiyar bishiyar darbejiya da ba a samu nasarar tun'buketa ba a lokacin da aka sabunta gidan suna ta d'aura zobo a leda suna zuba shi a wani mazubi mai girma. Kowa ka gani cike yake da annashuwa da farinciki daka kan iyayen 'ya'yansu da jikokinsu da surakansu. Zaure malamin kuwa daga can bayan gidan akwai kofar da aka yi masa ta mussaman domin ba'kinsa wanda Malam Rabi'u ya buk'aci da a yi hakan dalilin gidan akwai matansu babu cancanta maza ma bambamta na shiga gidan kai tsaye duk da sashen malamin daban yake amma dai tilas ta tsakargidan za a bi kafin a isa zauran nasa kuma wasu lukutan iyalansu na fitowa. Ta wannan kofar suka shiga zauran malamin shi da Dr Iliyas ba kowane ya san da zuwan na su ba. Malam D'aha na sanye da manya kaya babbar riga da 'yar ciki shadda mai kyau daidai gwargwado da d'inki manya cike yake da Kamala da nutsuwa amma kana duban fuskarsa za ka gane cewa lallai yana cikin farinciki dalilin wanzuwar wani lamari da wata'kila ya jima da shi a zuciyarsa. Tun bayan gaisuwar da suka yi da shi sai jikinsa ya kara mutuwa kwarai da gaske ya ji a ransa baya buk'atar wannan annashuwar da take fuskar malamin ta dusashe domin kuwa lamarin da suka zo dashi gare shi babba ne wanda zai iya rushe duk wata walwalarsa. Lallai ne akwai buk'atar zama akan wannan mas'alar mai sark'akkiya kamar yadda mai d'akinsa ta gaya masa ya makara a yanzu ba lallai ne malamin ya yarda da uzurinsa ba tunda ai ya jima da bashi yarinyar mai yasa bai kawo tasgaro ba sai yanzu da aski ya zo gaban goshi Jikinsa ya yi tubis bakinsa ya mutu d'akin ya d'auki shiru bayan gama gaishe-gaishe daga shi har Dr Iliyas din sai zare ido suke yi domin dai malamin bai fito ba sai da shirya Kuma yawanci irin wad'annan malaman masifar kwarjini ne da su da cika ido. Dr Iliyas duk 'kumaji da karsashinsa na k'wararran likita sai da jikinsa ya mace ganin yadda wanda ya gayyato shima jikinsa ya yi la'asar sai rarraba Ido yake yi yana sinne kai wannan lamari yana da wahalar fahimtarwa a wajen irin wad'annan mutanan da tauhidi ya yi wa k'awanya da kuma rashin samun ilimin boko mai zurfi ga kuma rayuwar karkara abin dai goma da ashirin.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *152* Suka juya gabad'aya suna kallonsa a lokacin da ya fara magana kamar haka. " Ya kamata a k'ara duba wannan uzurin da suka zo da shi Allah Ya gafarta Malam nasan da wahala Alhaji Tajo ya d'auki aniyyar tozartaka a irin wannan ranar da gabad'aya ta zame mana abar alfahari da farinciki mussaman da muka tabbatar da cewa wanzuwar lamarin shine abinda ka fi buk'ata a yanzu domin sake kulla zumunci mai karfi tsakaninka da abokinka Alhaji Ibrahimu Allah Ya yi masa rahama da gafara." Suka amsa da "Amin gabad'ayansu kafin ya sake nutsuwa sosai ya cigaba da cewa zahiri wannan lalura da suke magana akanta akwaita kuma har yanzu tana k'ara yaduwa a wasu wuraran da ba su d'auki abinda ya zo a zamanance da muhimmanci ba. Malam ko dai ka manta shekarun baya ashirin da biyu da suka wuce muka dinga dawaniya da mai sunan Inno har Allah Ya d'auki ranta a asibitin Murtala na cikin garin kano wanda sai a lokacin ne gabad'aya muka san ga cutar da ta zama ajalinta." ABINDA YA FARU. Shekaru ashirin da bakwai can baya Malam Nuhu ya auri matarsa ta fari Lantana wadda a yanzu ba ta raye ta rasu dalilin farfadiya tunda tana da mutanan b'oye sa'i da lokaci sukan tashi. Auran soyayya suka yi a cikin kauyen nasu kamar yadda al'ada take duk da wannan lalurar tata ta farfadiya hakan ya zauna da ita tunda yana sonta shi kansa mahaifinsa ya bashi gudumuwa kwarai wajan yi mata magani idan ciwon ya tashi. Da ta samu ciki sai wahalar da take sha ta sake ru'banya tunda kowa ya san yadda masu wannan ciwon suke shan ba'kar wahala a duk lokacin da iskar ta buge su a kan titi ne ko a kasuwa ko a gida sun dinga katantanwa kenan da jikinsu suna malkwadewa tare da taune lebensu da kumfa dafara mai hade da jini. Suka dinga bige ta a kai akai don babu wanda ya tsammaci za ta haife wannan ciki da yake jikinta lafiya saboda yadda take jigata. Cikin ikon Allah da lokacin ya zo ta haihu kalau aka samu 'ya mace wadda ta ci sunan Inno Ramatu suke kiranta da Rahma. Tun tana yarinya jinjira ta fara nuna alamun rashin lafiya ido ya jirkice daga fari zuwa yellow cikinta ya yi kurcici sai siraran kafafu da hannu. Da masifar kukan tsiya da zafin jiki domin koyaushe idan aka ta'ba jikinta radau ake jikinsa. Da yake kauyene a wancan lokacin da babu wayewa sosai kamar wadda suke ciki a yanzu sai duka daga can b'angaran iyayenta dana shi Malam Nuhu suka alak'anta lalurar da yarinyar take yi akan shafar aljanu dalili uwarta tana da su kuma sun tashi sosai a lokacin da take d'auke da cikinta a jikinta.. Suka dukufa wajen yi mata jike-jike na maganin gargajiya daga can b'angaran malamin kuwa yana yi mata rubutu da tofi ana bata tun tana jaririya ta saba da shan sassaken magani mai d'auke da ruwan rubutun da kakanta yake yi mata. Har hayaki sukeyi wa yarinyar saboda duhun kai har rukiya sai da Malam D'aha ya yi mata da abin ya ci tura duk a tunaninsu aljanu ne suke tsotse ta kuma suke hana ta bacci da daddare suke firgitata tana kwanan kuka. Duk wannan wuyar da yarinyar take ci Allah bai amshi abarsa ba sai da ta yi shekaru hud'u tukkuna cikin halin rai da rayuwa domin a duk lokacin da ciwon nata ya tashi hayaki ake yi mata aka dingi bata sassake da saiwa wadda aka dafa da jar kanwa. Wajan cirani can Katsina uban suke hira da abokinsa yana gaya masa halin da yake ciki da yarinyarsa wannan mutumin a irin bayanin da ya yi masa ya gane cewa babu maganar iska sai dai idan wata lalurar ce shine ya ba shi shawara kan cewa ya kaita asibitin cikin gari na kano general ne na kowa da kowa domin yawanci ma mutanan kauyen sun fi morarsa har ya ta'ba bashi labari shima daga nan k'atsina garinsu ya ta'ba kai mahaifiyarsa asibitin na Murtala aka dubata har ta kwanta na tsayin sati hud'u kuma ta samu kulawa kwarai ya ce masa su jarraba yin na asibiti ko za a dace. Koda ya dawo gida ya sanar da Malam D'aha da kyar ya amince da a d'auki yarinyar a tafi da ita a ganinsa abinda yake damunta bai had'a hanya da asibiti ba domin duka sun d'auka cewa lalurar uwarta ce ta shafe ta. Ba a tafi da uwar ba tunda tana halin ciwo Inno kakarta ita ta goyata suka tafi dawowar da yarinyar ba ta yi ba kenan domin kwanansu daya a asibitin ciwon ya tashi da masifar k'arfi likitoci suka dinga kai kawo a kanta inaaa babu jini ya kone ta rasu. A wannan lokacin ne likitan da yake tsaye a kan yarinyar ya zauna ya dinga yi musu bayanin musabbabin abinda ya yi ajalinta babu iska sai tsananin ciwon da Allah ne kadai yasan maganinsa. Duka ba su gazgata hakan ba a lokacin suka dawo gida da gawar yarinyar daga lokacin ne Malamin ya ce kada a sake daukar wani daga cikin zuria'arsa a kai asibiti duk cuta akwai maganinta cikin al'kur'ani mai girma. Shekara biyu bayan rasuwar yarinyar uwar ma Allah Ya d'auki rayuwarta sakamakon wata fad'uwa da ta yi iskokai da suke tare da ita suka bugeta a bakin kofar bandaki daga lokacin jikin nata ya'ki dad'i har dai rai ya yi halinsa. Wannan shine abinda ya shud'e a shakarun baya kuma a iya gwagwarmayar da yake da sauraran redio hurd'a da mutane bambamta tunda a can katsina wajan da yake gudanar da sana'arsa birni ne ba kauye ba ya tabbatar da cewa duk bayanin da ake yi akan wannan lalura gaskiya ne ya gazgata itace silar yarinyarsa ta fari Rahma wanda ada can suke d'auka shafar aljanune. Malaman D'aha ya yi shiru jikinsa ya d'an shika kadan a lokacin da yaron nasa ya tariyo masa abinda ya shud'e a cikin wasu shekaru da suka gabata. To amma shi a ganinsa wannan kadai ba zai hana k'ulla aure ba domin a zamanin baya wanene ya san da yin wani gwajin kafin a yi auran kuma cutar ba ta yawaita ba." Malam Rabi'u da jikinsa ya gama mutuwa saboda wannan lamari ya furta." Ya Malam a duba wannan lamari a kawo sasanci a cikinsa domin kada a zo a yi abu anan gaba a koka tun yanzu ya kamata a ce an magance matsalar nan domin ana yin aure ne domin samun zuri'a wadatattu kuma masu lafiya muna neman alfarma a duba a kuma yi adalci ta kowane bangare." A dan sanyaye ya furta." Rabi'u ba na 'ki ba ne zuwa yanzu ni ma jikina ya yi sanyi tunda zamani aka ce, Annabi Muhammadu S.a.w shi kansa ya yi magana akan zamani duk yadda muka kai ga ta'kawa da gudun sa'bawa Ubangiji idan abu na zamani babu yadda muka iya amma abin lura anan shine mu yi yaya da jama'ar da muka tara domin taya mu murna wannan shine abinda ya fi damuna a yanzu." Malam Nuhu ya furta." Abu ne mai sau'ki Ya Malam kana da almajira da suka 'yantu da yawa wasu sun shiga cikin gari neman arziki kamar yadda ka saba duba nagarta da cancanta a cikinsu ka bashi auran Hajara a daura da duk wanda ka zab'a mata in sha Allahu ba za a samu wata matsala ba daga kowane bangare." na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Daga can b'angaransa kuwa ya kira sunan Ubangiji babu adadi ya yi tahamidi tare da jaddada godiyarsa a gare shi ganin yadda aka samu kan malamin cikin k'ankanin lokaci ya magantu cikin kwarin gwiwa ya furta." Idan babu matsala an kuma ba ni wu'ka da nama ina nemawa wani aminttaccen yarona auran yarinyar zan kuma zame musu Uba gabad'aya." Malam Nuhu ya washe bakinsa Yana fad'in." Ka ji wani iko Allah ko Malam ina ganin duk wanda zai fito daga wajen Alhaji Tajo za a samu nagarta da sasihancin abinda ake buk'ata an samu mafita cikin sau'ki sai a juya d'aurin auran zuwa gare shi."" Malam D'aha ya dube shi cike da damuwa ya furta." Na so tabbatuwar auran nan da raina ya kwadaitu da shi Alhaji Tajuden amma ga yadda Allah Ya juya lamarin muna fatan hakan ya zama alheri da samun abinda ake buk'ata na kuma baka wu'ka da nama akan Hajara." Ya dinga godiya kuwa kamar wanda ya yi masa gagarimar kyauta Malam Nuhu fadi yake yi mu ne za mu yi godiya fa Alhaji Tajo mune muke da godiya a wurinka. Ya tashi ya fita tare da fad'in su jira shi lokacin rana ta yi sosai sha biyu da rabi ana ta haramar tafiya massalaci kai tsaye mota ya nufa Sukairaju ya hango shi ya fito da sauri ya bude masa ya shiga ya mayar da kofar ya rufe ya tsaya daga waje tare da harde hannunsa a k'irji. Ya sauke ajiyar zuciyar da ba zata lissafu ba godiyar Allah kuwa a cikinta yake yi sai dai yana d'an zullumin saurin yanke hukuncin da ya yi bai kira ta ya ji ya ake ciki ba. Shin wane yaro ne take nemawa aure a yadda yanzu malamin ya karrama shi tare da bashi amana baya tsammanin zai yarda da kowane irin za'bi. Idan wanda take nemawa auran bai yi masa ba zai aurawa Sukairaju yarinyar duk tsiya ya fi shi kuruciya kuma ya tabbatar da cewa zai rike masa ita da amana amma hanzari ba gudu ba shine menene matakin jini tunda dai shi a kan haka ya bijire yana da kyau daga kowane bangare ya samu gamsashen bayani kafin a k'ulla auran. Jikinsa ya sanyi sosai ya lalubi wayarsa dake cikin aljihu sai a lokacin ma ya lura da kiran da ta yi masa. Ina zaune jikina duk ya yi la'asar ganin d'aya saura na rana zuciyata na tabbatar mini da cewa wannan auran fa sai an daura shi da mijinki Amina tunda ki ka ga har yanzu bai kira ki ya gaya miki wata matsala ba. Dama fa yana so yaudara ce kawai yake yi miki akwai wani namijin da zai ce baya sha'awar budurci mussaman na yar k'aramar yarinyar irin wannan wadda yanzu take tashi. Na kwanta a hankali saman gado ina kallon Minal tana yi mini 'buruntu saman madubi yaran dake cikina sai wutsil-wutsil suke yi tabbacin suna buk'atar abinci ba ni kuma da niyyar shiga kicin din babu ma kuzari da karsashin da zan iya gudanar da wani abu. Na tashi da sauri jin kiran waya na d'auka da sauri shine na sanya a kunnena har muryata na rawa na amsa sallamarsa kafin na ji shi a dake yana fad'in." Wane yaro ne ki ka ce za ki nemawa auran yarinyar nan.'' Jin wannan maganar daga bakinsa na ji sanyi ya cikin zuciyata na daidaita maganata ganin yadda yake furta tasa da isa na ce." 'Kanina ne Usaini dazu na kira shi na gaya masa kuma mu yi maganar genotype domin shine akan gaba kafin komai. (AA) genotype blood group (o)" Duka na zayyano masa wannan bayanin babu hadiyar yawu. Ya furta.'' Ya kuke da shi Usainin kuma menene sana'arsa kin tabbatar dai da nagartarsa ko domin yanzu amanar yarinyar tana hannuna. Na ji maganar daidaituwar jini amma ina so kada ki rufe mini da son lallai aure ya tashi daga kaina ya koma kan waninki, ki gaya mini halinsa dalili mas'ala irin ta aure mussaman irin wannan da ta zo a jirkice ba a rufi ana fayyace gaskiya daga kowane bangare da ni da ke gabad'aya mun sheda nagarta da tarbiyar yarinyar nan shi wanda ki ke nemawa auran nata nake so na ji bayani na gaskiya a kansa kada ki rufe mini komai a kansa." Na ji kaina ya wani sara saboda tsananin mamakin maganganun da yake furta mini. Wato da irin abinda zai saka mini kenan. Kwanaki uku da suka wuce ya zama kamar wani mahaukaci saboda tarin damuwa da tashin hankali. Na shiga cikin matsalarsa na bashi shawara domin samun mafita shine yanzu zai juya maganar ta wata siga daban neman mafitata ne ya sanya na ce zan nemawa dan'uwana auranta saboda shi kada ya aureta tunda Ina kishi akan yarinyar. Wannan shine karatun kawai domin duk yadda ya yi maganar a kudindine na fahimta tunda ni ba mahaukaciya ba ce. Na daure sosai tare da danne tashin hankalin da yake yun'kuro mini na ce." Usaini kanina ne ubanmu daya ba zaka san shi ba gaskiya tunda shi namiji ne kwarai don samun kamarsa a cikin maza a yanzu dai sai an tona yaro ne mai zuciya kuma ba makwad'aici ba. Koyaushe cikin neman na kansa yake yi. Yana da shagon sayar da zannuwa a kasuwar kwari. Sannan ya tsayar da sallah ya yi karatu daidai gwargwado na addini dana boko baya sata kuma baya shaye-shaye, wannan shine abinda na sani a kansa. Amma idan kana shakku za ka iya kiran waya idan kana da ido ko wanda kake mu'amula da shi cikin unguwarmu ta kabuga ka ce a yi maka binkice akan Usaini Salisu maihula na lungun itacce sunan layinmu ya yi suna haka zalika ma gidanmu ya yi suna babu wanda bai sani ba tun daga bakin titi zuwa cikin lungun Babanmu fitacce ne." Ya yi jim daga daya bangaran ina sauraran amsarsa gabana na fad'uwa saboda tashin hankali mutumin nan mara mutunci ne tsantsa kuma mai mance alheri da ni yake magana." Na ji yana fad'in." Ni da Sukairaju na yi wa sha'awarta shima ai kin sheda nagarta da cancantarsa ko na jima dashi Amina bai ta'ba cin amanata ba." A takaice na ce." Da shi da Usainin duk daya ne ni a wajena idan ka yarda da cancantarsa a yi dashi kawai Allah Ya tabbatar da alheri." Ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in." A a ayi dai da Usanin kawai tunda yanzu shine sakamakonsa ya bayyana kuma kin tabbatar mini da cewa babu matsala na aminta a yi da shi din.'' Na ce.'' Idan an biya sadakin zan biya ka idan ka dawo a basu dubu dari biyu. Duk abinda ya kamata na al'ada wanda suke yi za mu yi musu." Ya yi shiru bai ce mini komai ba nasan haushin maganata ya ji. Na sake ce wa." Ka na jina ko idan kuma dari biyu ta yi kad'an daga dari uku zuwa abinda ya yi sama ka biya zan baka kudinka idan ka dawo." Sai ya kashe wayar bai ce komai ba. Na ja tsaki tare da ajiye tawa wayar zuciyata na tsalle tsabar takaici da b'akinciki da ya guma mini. Wai mutumin da ya rasa mafita ya gigice tare da zama sullutu shine ya yanzu saboda ya samu kansa yake ko'karin juya alheri zuwa sharri. Duk yadda nake 'kin auran a cikin raina ban ta'ba fitowa fili na nuna masa ba saboda gudun irin haka da yake ya iya sharri da lauya zance yana fad'in saboda kada ya aureta na ce ina nemawa d'an uwana auranta. K'warai wannan magana ta tsaya mini a cikin raina ko da na shiga kicin domin d'ora abinci ina tunaninta da mamakin fitowarta daga bakinsa........✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *153* Haka na kammala aikin da takaici da kuma farincikin nasarar da Usaini ya samu wajan samun damar mallakar Hajara a matsayin matarsa uwar yaransa anan gaba. Akwai daidaito ta kowane bangare a tsakaninsu babu cuta babu kuma cutarwa yadda yake a nutse haka itama yarinyar take a nutse kuma babu rawar kai da iyayi na 'yan matan yanzu matsalar kawai babu zurfin boko a tare da ita wannan kuma bai kai ace an damu dalilin rashin samuwarsa ba tunda da akwai na addinin zai kori duk wata tangard'a da za a samu a zamantakewar auran nasu wadda ba mu fatan hakan in sha Allahu rabbi. Wajan uku saura na kintsa jikina sosai kwalliya na yi irin wadda na jima ban yi irinta ba na zuba lece brown a jikina wanda ya ji stones ta ko'ina ga kyau ga kudi na yi amfani da set din gold dina da ban jima da saye ba. Tare muka ci abinci da yarinyar kamar koyaushe tana yi mini hirar 'yan uwanta da alama ta yi kewarsu nasan duk yadda aka yi sun iso yanzu suna gidan Hajja. Ina idar da sallar la'asar ya kira ni dama dakon kiran nasa nake yi domin na ji a ina a akwana. Ya ce mini an d'aura amma Malam D'aha ya ce angon ya je yana nemansa. Yadda yake magana kamar wanda aka yi wa dole ni ma na amsa da kalar sigar da yayi mini Ya nisa kafin ya sake magana." Ga ni nan a kan hanyar dawowa gida." A takaice na ce." Sai ka dawo." Na riga shi kashe wayar ban jira ya sake wata maganar ba. Kai tsaye Babanmu na kira dama da safe na sanar da shi halin da ake ciki ya ce tunda mijina ne zai kar'bi auran to a bashi dama zuwansu ba shi da amfani dalili ga yadda lamarin ya kasance amma bayan d'aurin auran za su je wajan malamin domin godiya. Na sanar da shi an daura sannan na tabbatar masa da cewa zan shigo gidan gobe domin mu tattauna da mahaifiyarsa akan yadda za a shirya hidimar biki." Ya yi ta yi mini godiya da sanya mini albarka Ina kara jin k'warin gwiwa a cikin zuciyata tare da addu'ar Allah Ya taimake ni na cigaba da tallafar 'yan uwana. Muna gama waya na kira angon na gaya masa cewa an daura ya kuma zo da daddare ina son ganinsa domin mu yi magana akan abinda ya rage na aikin gidansa da yake ginawa. Mun jima muna waya da anti Yagana tana fad'in idan mun tsayar da magana na kira ta na sanar da ita halin da ake ciki. Na sauke ajiyar zuciya tare da kashe wayar bayan mun gama da ita. Kiran sa ya sake shigowa a karo na biyu na daga amma ban ce komai ba. Na ji yana fad'in." Kashe mini waya ki ka yi saboda me?" Na yi shiru kawai sai ya cigaba da cewa." abubuwan da ki ke yi mini sun ishe ni wallahil-azimin zan d'auki mataki mai tsanani a kanki Amina." Shiru na yi ban iya ce maaa komai ba ganin yana neman fitina a irin wannan lokacin da ya kamata a ce ya kasance cikin walwala a yadda yake nuna 'kunci da damuwa a baya amma kacokan yana neman ya huce takaici a kaina shin wai ko dai yana son yarinyar nan dole ta sanya shi ha'kura saboda rashin daidaituwar jini wannan abubuwan da yake yi sun fara sanya mini zargi da shakku a kansa tunda ai zuciyarsa a kirjinsa take ba a bayyane take ba balle mu ga abinda yake 'boyewa kamar kishi yake yi. Ya karaci maganarsa ban ce komai ba haka ya ha'kura domin duk yadda ya kai ga so na gaya masa da wanda nake waya har na katse tasa ban gaya masa ba na kyale shi dai ya shigo gidan sai mu yi wacce za mu yi ai waya ta yi kad'an. Har bayan isha'i bai shigo ba na fi zargin yana gidan Hajja dalili Hauwa da yaran kuma tare za su kwana tunda nan ta zo ta same shi. Usaini ya zo kamar yadda na umarce shi yaro sai annashuwa yake yi ya nuna mini kara da hallaci kwarai ya kar'bi abinda bai ta'ba ganinsa da ido ba cikin girma da mutunci wannan dalilin ya sanya mini sake d'aukar al'amarin da muhimmanci kwarai da aniya. Ya nuna mini gidan nasa a waya ya yi nisa sosai don an yi rufi an sanya k'ofofi a wasu d'akunan da yake filin babban ne part biyu ya yi yana gaya mini d'aya bangaran zai sanya Babarsu ne idan ya gyara mata sai na ce masa mu fara gyara na amarya tukkuna duk abinda ya kamata na ado da k'awata a gida a yi lissafi da ma'aikata daga nan zuwa ranar wata juma'ar a yi kokarin kammalawa domin ba ni son yarinyar ta yi dogon zama a gidansu. Muka yanke magana a kan haka. Hamusu na kira a lokacin na ce ya had'a masa lefe akwati shida a sanya manyan kaya daga kan atamfofi zuwa leces abinda ba mu da shi a shago a sayo a had'a a kawo mini na gani. Ya ce mini za a yi kokarin hadawa kamar yadda na buk'ata. Muna tare da Minal a falo wajan tara da minti goma na dare ina dokon shigowarsa yaran sune a kan gaba kafin su shigo shi da ita. Minal ta buga tsalle a guje ta nufi bakin kofa suka rukunkume juna Hassana da Husaina suna cikin wasu 'yan kanti sabbi masu kyau sosai da wani karamin hijab a wuyansa daga inda nake zaune nake k'are musu kallo na ga sun sake yi mini tsayi ko dai don na kwana biyu ban gan su ba ne oho sun dai yi mini kyau k'warai Khalil na cikin shadda riga da wando da aiki a gaban rigar har da hula a kansa. Ita kuma tana cikin abaya baka mai jajayen dutsuna ta yafe mayafinta a wuyanta har da gilas baki a idonta da jar jaka da takalmi. Na juyar da kaina cikin nutsuwa na amsa sallamar da ta yi suka 'karaso falon ita da yaran gabad'aya shi kuma ya haura sama ba tare da ya ce komai ba. Ta zauna kan kujerar da take fuskantata fuskarta a sake kamar ba itace Hauwa mai k'uncin rai ba. Ta zare gilashin idonta tana duba na sosai ta ce."Amina ina yini mun same ku lafiya." Na amsa a tak'aice ina nazartarta. Sukairaju ya shigo ya tsaya daga bakin kofa akwati biyu ya ajiye madaidaita don basu da girma kayansu ne a ciki daga nan ya juya ya fita da sauri. Hankalina ya d'auke wajan amsa gaisuwar da yaran suke jero mini Usai ta zo ta dafa cinyata tana ta kallona sai kuma ta dora kanta a saman cinyata. Na dora hannuna a kanta ina le'ken fuskarta. Hassana cikin narai-narai da ido ta ce."Mama ki ka ce za ki dawo gobe." Ta fadi maganar muryarta tana rawa kamar za ta yi kuka lokacin na tuna da alkawarin bogi da na yi musu a lokacin ma tun ina maiduguri. Na ri'ke hannunta amma ban ce mata komai na kira Khalil da hannu Ina fad'in ."Zo mu sake gaisawa." Ya kuwa taho da sauri yana dariya yake fad'in. Mama mun yi kewarki fa sosai kullum muna labarinki shiyasa da muka zo muka ce mu dai nan a wajenki za mu kwana." Na ce." Ni ma na yi kewar yarana sosai Khalil ina su Mairo baba Tabawa da Sultan." Ya ce." Duk suna nan lafiya sun ce a gaisheku Sultan ba shi da lafiya yana zazzabin hak'ori Baba ya ce a bar shi a gida kada a zo da shi." Na gyada kaina ina dubanta lokacin da take yin magana cikin yar dariya ." Aikam yara sun yi kewarki a gida Amina shi kansa ma gidan kewarki yake yi." Murmushi na yi ina duban Minal da wayata a hannunta tana latsawa ko kusa da uwar ba ta je ba gefe guda kuma ina nazarin abinda yake so ya faru domin ga dukkanin alamu ba yaran ne kadai suka zo mini kwana ba har da ita tunda ga akwatin kayansu nan." Na danne tare da furta." Kun ci abiΓ±ci a gidan Hajja ko kuwa na kawo muku." littafin nan na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Ita ta ba ni amsa duk da ba ita na tambaya ba na ji tana cewa." A alhmdullhi ai sai da muka ci abinci muka fito mun gode sosai." Na yi shiru ban tanka mata ba ina ta sauraran labarin Mairo a bakin yaran da sa'kon gaisuwar da suka ce a gaya mini. Wajan goma daidai na tashi na hau saman domin tunda ya hau bai sauko ba ga yara suna so su kwanta. Yadda tsarin gidan yake dama can babban falo ne da dakuna manya biyu a cikinsa toilet da kicin wanda yake d'auke da store wadatattu. Saman kuwa dama can d'akuna biyu ne amma daya ne a gyare wanda yake mu'amula a cikinsa tun farkon tarewarta a gidan zaman mace daya ne babu takurawa yanzu kuma Khalil ya zama d'an saurayi ya d'an fara girma babu buk'atar a had'a shi da mata a d'aki daya tunda tun can abujan aka raba musu d'aki. Yana zaune da jallabiya a jikinsa ya yi wanka yana waya shigowata bata hana shi cigaba da wayarsa ba amma kafatanin hankalinsa yana kaina har na zauna daga dan nesa da shi waya yake yi da Alhaji Sulaiman yana yi masa bayanin yadda al'amarin ya juya har aka d'aura auran da waninsa ya yi masa fatan alheri a yayin da yake ta amsawa da Amin Amin can kuma sai ya yi shiru yana sauraransa na ji yana fad'in." Anya kuwa Alhaji ba dai yanzu ba tukkuna wad'annan ma fama nake da su amma za mu cigaba da neman zabin Allah." Daga haka suka yi sallama ya juyo yana kallona 'kuri! Na sake tamke fuskata tare da tariyo maganganun da ya gaya mini dazu amma bari mu ajiye wannan mas'alar a gefe kafin nan ina so na ji dalilin da ya sa ya kawo mini matarsa cikin gidana bayan da bakinsa na ji yana gaya mata babu waje a ina zai sauke ta. Ba ni buk'atar Hauwa gabad'aya a rayuwata bana tsammanin zan iya sake sakin jikina da ita domin bata daga cikin mutanan da Ubangiji ya ce idan sun tuba ku yafe musu Hauwa bana jin za ta yi taubatun nusu'a akan zamantakewa ta tsakani da Allah." Ya dube ni yana fad'in." Hajja ta ce ta zo cikinmu gabad'aya tunda yaran sun dage anan wajanki za su kwana can kuma ita kadai za ta kasance, amma ni ma na fi buk'atar su zauna a can gidan Hajja saboda ba ni son fitina fa na gaji idan ba so kuke na mutu ba." Na ce." Ai ita kanta Hajjan ta san gidan ya yi mana kad'an ni wallahi tallahi na gaji da wannan rashin adalci da son zuciya ba ni son had'a numfashina da matar nan domin zahirin k'iyayya ta nuna mini na bar mata can gidan na zo nan na zauna domin zuciyata ta samu nutsuwa ta sake biyo ni ko sai ta yi wa rayuwata illah tukkuna za a gane abinda nake nufi." Ya 'bata ransa ainun yana duba tsabar idona ya ce." Rashin kunyar ta tashi daga kaina Amina ta yi tsalle ta tafi kan mahaifiyata kenan ko, gidan ki ko nawa da za ki yi mini iko da abinda nake da iko da shi, ki gaya mini gidanki ne ko nawa na ce?" Ya fad'a cikin 'karaji har yana dukan hannun kujerar da yake zaune. Duk da na tsorata daga ganin yadda ya burkice na dake sosai ban sarayar da mutuncina ba na ce." Gidanka ne ai dama ban ce gidana ba ne amma dai ni ce yanzu a cikinsa kuma na ce ba ni buk'atar zama da wata a cikinsa. Idan lallai sai ka zauna dani a irin hukuncin da na yankewa kaina na rayu ni kadai da yarana a waje daya babu wata bagidajiya da za ta d'aga mini hankali ko ta nemi halakar da rayuwata. Kuma kada ka sake ka yi mini k'azafi akan maganar da na fad'a domin ni ban ga ta inda na kausasa harshe akan mahaifiyarka ba." Ya sake hasalowa yana fad'in." A ciki nake dake domin kin jima kina yi mini rashin kunya kala-kala saboda kin samu dama akaina ko kin lura ina sonki da yawa za ki samu damar taka ni yadda ranki yake so kin zo geji muddin ki ka ce za ki sanyo mahaifiyata cikin wannan rashin mutuncin naki wallahi ranki idan ya yi dubu sai ya 'baci." Na sake aro jarumuta da jajurcewa domin dai duk wannan hargitsin da yake yi bai karya mini lagona ba ko na tsorata na furta ." Kada fa ka yi mini sharri akan abinda ban yi ba babu cin mutunci balle rashin kunyar da kake magana a tsakanina da Hajja wannan alkawari ne na daukarwa kaina." Ya ce." Idan ba rashin kunya da rashin arziki ba mai yasa za ta bata da umarni ki ce ba daidai ba ne har kina fad'in ita kanta wannan ai wulakanci ne da nuna mutum bai isa ba." Na girgiza kaina cikin ko'karin nuna masa ba haka nake nufi ba na ce." Idan wannan maganar dana furta akan Hajja ta hasala maka zuciya Allah Ya baka ha'kuri amma zan fita yanzu tunda da sauran dare a gidanmu zan kwana nan gidan Hauwa ne da yaranta kamar yadda wancen ma ya zama nata. Na yun'kura na tashi a hankali yaran dake cikina suna naushin marata duk da ciwon da nake ji na yi azamar kama hanyar fita. Ya cimma ni dalili da kyar nake iya cire 'kafa. Ya tari gabana da b'acin rai a fuskarsa ya furta." Ba za ki bari mu huta ba ko Amina, ba ki duba nauyin da ki ka yi, kin ki ki bari mu fahimci juna har mu raini yaran dake cikinki kin dusashe mini farinciki da annashuwata kina nema ki dasa mini b'akinciki me na yi miki ne?" Na daga kaina na dube shi a hankali na ce." Ka bar ni na huta ni ma?" Ya yi shiru bai ce komai ba da akwai alamar sasaauci a fuskarsa. Ya rike hannuna daya na fizge tare da ratse shi zan wuce ya san janyo ni da sauri tare da sanya ni a jikinsa. Na sake cirewa rik'on karfi ya yi wa hannuna. Yana jana ina turjewa so yake mu je mu zauna a gefan gado. Na ce." Ai babu buk'atar wani zama na samun maslaha da daidaito a tsakaninmu tunda har yanzu baka fi karfin gidanka ba. Zaman sulhu da samun mafita ba za a yi shi da ni ba a yanzu zaman 'yanci zan yi da kare kaina." Ya ce." Na gaya miki tuntuni Hauwa ta gyara ta daina duk wasu abubuwa na rashin kyautawa kada ki manta da irin yadda na fifitaki a kanta na nuna miki kulawa da k'auna a kanta ki ka fitar da hannu ki ka tsinka mata mari a gabana. Na hana ta d'auka mataki ta kuma hanu. Wannan bai isheki ba Amina." Na ce." Ai baka burge ni ba daka sani ka bari ta rama marinta ko kai ka rama mata tunda ka ji mata haushi. Ka daure mata gindi tunda baka musanta abinda ta fad'a ba a kaina kawai ka mayar da abin wasa. Mataki ma ban gama d'auka a kanta ba wallahi muddin ba ta fita daga rayuwata ba." Ya rungumo kafada jikinsa yana dan rawa har yana gyara mini sar'kar wuyana ya ce." Ni ban d'auki maganganunta da muhimmanci ba saboda nasan wacece ke, nasan ta fadi haka ne domin ta 'bata miki rai da kishi irin naku na mata me yasa maganarta za ta dame ni tunda na fi kowa sanin da baiwar da Allah ya yi mini na rabauta dake giwar mata shige mu zauna mu yi magana wadda za ta kawo mana sasanci.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700...VIA 0542382124.... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *154* Ganin yana neman wuce makad'i da rawa ya sanya na tankwa'be hannunsa ya sake mayarwa tare da tarairayoni jikinsa sosai na yi 'kokari wajan 'kin barin abinda yake yi mini ya yi tasiri a tare da ni muka zauna gefan gado a tare yana ta sauke wata irin ajiyar zuciya wadda na kasa tantance ko ta mecece. Raina a b'ace na zura masa ido domin sauraran abinda zai fad'a abinda na sake kud'irewa a raina shine ko sama da 'kasa za ta had'e ba zan zauna da Hauwa ba tunda ba tare a ka hallice mu ba. A wannan karon na shirya sosai koda Hajja za ta sanya bakinta ba ni tsammanin za ta sake samun wannan alfarmar. Sai da ya daidaita kansa sosai ya furta." Za mu yi kwana biyu da Hauwa anan zuwa jibi zamu tafi tare da ita da yaran gabad'aya ba dai akan maganar raba gida kike magana." Ya fad'a yana kallona. Na gyad'a kaina ba tare da na ce komai ba. Ya sake sauke ajiyar zuciya yana ce wa." Za a yi yadda ki ke so amma ya zama dole kema ki bi umarnina tunda kin san bai zai yiwu ki zauna anan ba mu muna can kuma duk wasu d'abiu da ki ke yi a yanzu ki ajiye a gefe ba zai yuwu ki dinga juya ni ba Amina kin san dai ba ki isa ki kafa mini doka na bi ba ko?" Ta'be bakina na yi tare da juyar da kaina gefe wai ban isa na kafa doka ya bi ba. Ita din yake bi ai a yanzu na tu'ke tunda bai san alheri ba. Dole ne aka ce na zauna da wata Allah Ya gama hore masa ta ko'ina idan ya'ki raba ma mazauni bai shirya kashe rikici ba. Ya juyo da fuskata yana fad'in." Ki kalle ni mu yi magana domin fahimtar juna nake so mu yi ni dake saboda na gaji da wannan halin da ki ke yi mini ina ce akan an bani auran wannan yarinyar ne Hajara ki ka canza gabad'aya ni fa ba yaro ba ne giwa na baki shekaru sama da goma sha biyar duk yadda ki ka kai ga gogewa na fi ki kuma bai wai ina tsoronki ba ne." Na dube shi sosai ina cewa." Ni dama na ce ka ji tsorona ne? Wallahi ka ji tsoron Allah a cikin dukkanin lamarinka ka dinga gaskiya yanzu ba ka ji kunyar duban idona ka dinga fad'a mini irin haka ba me yasa ka ke da mance alheri ." Ya ce." Ni kin d'auke ni mak'aryaci kenan." Can k'asa na ce." Iyi." Ya sake sanya hannunsa ya juyo da fuskata yana ta'ba le'bena kafin ya furta." Ni ki ke yi wa Allah Ya isa Amina." Na cire hannunsa ganin kamar yana so ya shagaltar da ni, na ce." Don Allah ni ka rabu da ni babu fa wani kalami da za ka yi mini na ji dad'i tunda ka rasa Hajara sai ka nemi wata ba yanzu na ji kana waya da abokinka ba ya baka kanwar amaryarsa sai ku yi anko ina ruwana." Ya girgiza kansa yana cewa." Ko zan yi aure anan gaba sai da amincewarki ke za ki duba mini wadda ta dace." Na kalle shi a sakarce wai shi dole sai ya yaudareni da kalaman bakinsa. Na ce." Ya ake ciki ne za ka d'auki Hauwa ka mayar da ita can gidan Hajja ne domin fa hakan shine samun nutsuwarmu da ni da kai da ita gabad'aya." Ya yi d'an shiru kafin ya matso ni sosai yana fad'in." Dambatta fa aka ce Amina da tafiya sosai ki bar ta ta kwana na ce miki." Ya fad'a yana d'ora fuskarsa tsakanin wuyana. Gabad'aya ya rikice kuma na gane abinda yake so. Na cire jikina ina fad'in." Shikkenan ta kwana daya zan mata wannan alfarmar amma wallahi daga wannan kwanan ba za ta sake yi mini wani ba." Can k'asa ya ce." Na ji abinda ki ka ce." Ya sanya hannuwansa ya kewaye 'kuguna jikinsa na rawa. Tsaki na ja wanda ban san lokacin da ya fito ba. Ya dago yana kallona idonsa ya canza gabad'aya ya ce." Kin san na tsani wannan dabi'ar ko. Kin ce a bi ra'ayinki an bi me yasa kike wulakantani ne Amina." Jikina ya d'an yi sanyi jin muryarsa har tana d'an rawa bai ba ni tausayi ba ko kad'an saboda nasan akan abinda ya sanya shi rawar murya din duk yanayi ne domin ya yaudare ni ya more ni kuma Hauwa ta ci ribar abinda ta shirya domin dai ban yarda da cewa Hajja ce ta turo ta mu kwana tare ba. Na ce." Game da kudin sadakin Hajara nawa ka ba su?" Shiru ya yi mini yana girgiza kansa tabbacin ya kai 'kololuwa wajan Jin haushin tsakin da na yi masa wanda ni ma ban san lokacin da ya fita ba tsabar haushinsa da nake ji ne. Na sake maimaitawa ya ce." Ban sani ba." Na ce ." Ya asalin baka sani ba, ka fad'a don Allah a baka hak'kinka ai ba lefi ba ne." Ya ce." Ba zan fad'a ba Amina ke kina jin kin yi k'arfin da za ki nuna mini wani abu ne.'' Na ce." A a wace ni idan da irinku a wuri ban isa ba kawai dai ina so mu biya ka hakkinka ne saboda kada nan gaba a yi mini gori." Ya yi shiru bai tanka mini ba can kuma ya ce." Yanzu za ki ba ni ha'kkina ko kuwa?" Na ce." Wane hakki?" don har ga Allah ban zanci hakkin kwanciya yake nufi ba ." Ya d'ora duka hannuwansa biyu saman kirjina yana fad'in." Wannan dai mallakina ne ke kan ki ba ki da karfin ikon da nake da shi a kansa. Idan na d'ora hannu a kai ki tankwa'be kina neman rahamar Allah kuwa?" Ya fad'a yana dam'kar d'aya da k'arfi cikin mugunta gasu tubarkallq sun sake kumburi dalilin abinda nake d'auke dashi sun cika sosai. Na sake tankwa'be hannun ina fad'in." Allah Ya hallice ni da abina a jiki ka ce ka fi ni iko da shi abincin yarana ne masu zuwa." Ya kuwa gigice yana fad'in." Abincin mu dai, wallahi ba ki isa ba, abincinmu ne da ni da su." Na juya da kaina gefe ya matso ni sosai yana yi mini magana. Na girgiza kaina tare da cewa." Ba zai yiwu ba sai Hauwa ta tafi ka yi hakuri ni tunda cikin nan ma ya tsufa na daina jin wani abu Ya ce." Ni kuwa a cikinta nake koyaushe kin matse ni da yawa Amina ba kya gudun hakkina ya kama ki uhum! mu d'an yi soyayya kad'an kafin Hauwa ta shigo sai mu kwana tare kada ta ce ba a yi mata daidai ba." Na ce." To bari kawai idan ta shigo sai ku yi soyayyar gabad'aya." Ya sake rikicewa yana cewa." Ya ki ka tsara yanda zai kasance." Na rasa da wane mizani zan auna maganarsa. Ya na tsara yanda zai kasance me yake nufi. Na gane kawai a rikice yake maganarma ya fad'e ta ne cikin rashin hayyaci. Ina sane na 'kyale shi ya dinga abinda yake so ba don komai ba sai don na nuna mata cewa kowace mace da irin tata kissar. Gidana kuma ta zo sai abinda ta gani. Wajan sha biyu da wani abu muka sauko kasan ni da shi bayan ya samu gamsuwa da abinda ya buk'ata. Yaran sun yi bacci duka a saman kujera tana zaune zuru da tibi a kunne duk ta muzanta ganin sakkowarmu ta yi kasa da kanta fuskata a had'e kamar ma kuka ta yi. Na wuce d'akina ban tsaya a falon ba na ji yana cawa da ita." Tashi yaran su je su kwanta. Amina bude musu daya d'akin, shi Khalil ya zo mu kwana tare a d'akina." Dakinsu Baba Tabawa da Yusra kenan anan suke kwana na bud'e kamar yadda ya buk'ata. Ita da shi suka fara tashin yaran. Na yi shigewata d'aki a raina ina fad'in." Ki zauna da ni a gida daya ki zama 'yar aikina Hauwa, zan kuma ga abinda gobe za ta haifar ni daku ne gabad'aya. Na rufe kofa tare da cire kayan jiki na sanya na bacci na yi kwanciyata ban sake sanin wainar da suka toya ba ba. Da asuba gari ya d'an fara haske ina saman dadduma ya shigo ya jira na kammala muka shafa addu'a a tare. Na gaishe shi babu sakewa na ce." Zan je gidanmu idan an jima zan kuma tafi da yara." Ya yi d'an jim kafin ya ce." Babu damuwa amma ya za a yi da abin kari kada su tashi a bacci ko." Na ce." Za ka iya bayarwa a sayo abinda za su ci ba ni jin zan shiga kicin gaskiya wanka zan yi na shirya." Ya ce." Wace banzar magana ce wannan Amina ni zan sayi abinci bayan ina da shi a gidana, ban yi wannan lalacewar ba." A takaice na ce." To sai ka shiga kicin din ka yi da kanka kada dai ta shigar mini kicin." Ya dinga kallona cike da takaici ya ce." Jiya ba na gaya miki cewa zan raba muku gidan ba me yasa kike da neman fitina ne Amina. Ya kamata duk abinda ki ke ji a ranki ki ajiye a gefe mu fahimci juna gabad'aya mu gyara kuskuranmu Hauwa bakuwa ce anan gidan." Na ce." Bakuwarka dai ai ni ban gayyace ta ba." Ya sake had'e rai yana fad'in." Kina yin abubuwan da suke nema su wuce gona da iri fa. Ko babu Na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. dangantaka ta aure a tsakanina da yarinyar akwai dangantaka ta jini sannan uwar yarana ce kiyayyar ki a kanta ta tsananta." "Humm kawai na ce tare da tashi na bar shi zaune bandaki na shiga. Koda na fito baya d'akin na yi tsaki cikin raina na fara shirya jikina zuciyata cike da abubuwa ma su yawa. Wajan takwas na fito falon yaran sun shirya ko ita ta yi musu wanka oho suna zaune a falo gabad'aya har da Baban nasu ita tana kicin domin fitowata na ji kamshin k'wai na tashi raina ya baci sosai. amma sai na daure na cigaba da amsa gaisuwar da suke jero mini. Shi kuma ya zura mini ido da alamar na gaji da wannan abubuwan da suke faruwa. Kai tsaye kicin din na nufa na same ta tana soya dankali da k'wai ta d'ora ruwan tea yana ta k'amshi citta da kaninfari. Na cika da mamakin karfin halinta. Kai tsaye gas din na kashe ta yi sakato tana kallona. Na furta." Ba ki da hurumin yi mini yadda ki ke so a gidana Hauwa ko ni na gayyato ki ne, me ya sa za ki shigo mini kicin har ki saki jiki kina soye-soye." Ta d'an yi murmushi tana fad'in." Amina manya ai kya bari mu gaisa ko?" Na ce." Dube ni nan Hauwa ba ni buk'atar gaisuwar na ce miki tambayarki nake dalilin da ya sanya ki shigo mini kicin." Ta yi 'yar dariya cikin raini ta ce. " To Hajiya masu gida ki goya ki kai gidanku." Ta ajiye cokalin hannunta ta kama hanyar fita zalo-zalo na ce." Sakarai kawai." Ta juyo a fusace tana cewa." Amina ai ba a sakarai d'aya sai dai sakarkaru biyu." Na ce." Hakane da ke da ta Bauchi ko?" Ta zura mini ido da matsanancin mamaki tasan dai inna Uwani nake nufi Sai ta rushe da kuka mai karfi." Amina ni ke zagi, inna Uwani ce sakarai mahaifiyata." Ta fadi maganar a daidai lokacin da ya shigo kicin din ta dinga wani irin kuka hawaye na kasa tsere a kumatunta. Yana tambayarta ta yi shiru ta kasa magana ta jingina jikin wardrobe. Can ya juyo kaina ganin yadda fuskata take ya sanya shi fad'in." Me ya faru ke ba kya jin magana da rarrashi ko?" Na ce." Ni na ce Hauwa ta zo gidana?" Na katse shi ta hanyar yi masa wannan tambayar. Ya ce." Gidanki ne ko nawa?" "Gidanka ne amma kaima na fi ka iko dashi wallahi duk zan iya da ku." Ya gyad'a kansa kamar zai rushe da ihu ya ja hannunta suka fita bata sake tanka mini ba tunda ya shigo sai ta yi shiru kawai tana kuka. Wai na goya gidan na kai shi gidanmu. Magana ta gaya mini a fakaice ashe babu dadi. Ita da uwarta duka sakarkaru ne na fad'in su yi yadda za su yi da ni. Na same su gabad'aya har yaran sun tsuru-tsuru na wuce daki ban sake kallonsu ba. Muna waya da Usaini ya shigo da wani irin b'acin rai a tare da shi ya cire wayar daga kunnena ya sanya a aljihunsa. Na zuba masa ido babu fargaba domin nasan ta gaya masa na ce da mahaifiyarta sakarya. "Tunda ki ka iya zagin Inna Uwani Amina za ki iya zagin mahaifiyata yanzu kin kyauta kenan abinda ki ka yi daidai ne mace ta zo gidanki ki yi mata irin wannan cin zarafin iyaye fa aka ce miki duk iyashegen da ki ke ji da shi ina fa da yadda zan yi a kanki na kyale ki ne ganin kina da juna biyu ba ni tsoron kowa mace ni nan da ki ka gan ni sai mahaifiyata." Ya fad'i maganar kamar gaske da 'kumaji har da zare mini ido. A raina na ce a banza ai ba zaka iya fad'an ba Alhaji. Na dube shi sosai tare da fad'in." Da farko daka tambaye ni maganar abin kari ban munafurceka ba na ce a a ba zan yi ba, akwai masu yin abinci a gari ka bada kudi a sayo musu mai yasa za ka ce ta shige mini kicin ko ajiya ta yi mini ne?" Ya rasa abinda zai ce mini can kuma ya gyad'a kansa yana fad'in." Tunda kuke rashin hankalinku ban ta'ba jin lokacin da Hauwa ta zagi wani naki ba abin ya wuce kaina ya tsallaka iyaye kuma duk lalacewar inna Uwani ai idan da mutunci da sanin daraja uwace a wajenki." Na ce." Tunda haka ta gaya maka na zage ta mu tafi a haka kawai idan kalmar sakarai ce zagi to zan sake maimaitawa ai iyaye ba su fi iyaye ba." Jikinsa ya yi sanyi sosai ya juya ya fita bai sake yin wata magana ba. Na d'auki kusan minti ashirin kafin na fito cikin shiri na same su still a falon suna shan tea har da bread tare da dankalin da ta soya musu. Minal ta ta so a guje ta rike ni tunda ta ga alamar fita zan yi. Twins din suka biyota. Ba ni son d'aukar musu yarinya nawa biyu kadai zan yi gaba da su ba kuma zan dawo cikin gidan ba muddin Hauwa na cikinsa. Ya yi mana shiru bai ce komai ba. Na ce da Minal din ta je ta d'auko mini bread din da take ci. Wayo na yi mata ta kuwa juya baya da sauri nan na ri'ke hannun Usai Hassana ta biyo bayana muka fita na ja kofar da k'arfi daidai lokacin da na ji ta fasa ihu da karfin gaske. Ayuba ya fito da mota muna ko'karin shiga ya fito da yarinyar ta yi wurjajan da kuka da majina yana goge mata da tissue. Kamar kurma ya saka ta a cikin mota kusa da 'yan uwanta ya juya bai ce mini komai ba. Sai da na shiga motar tukkuna na tuna da wayata a hannunsa na ce Hassana ta je ta kar'bo mini jim kad'an sai ga ta da wayar a hannunta, ta shigo ta zauna suna cike da murna za su fita Ayuba ya ja motar muka fita daga gate din gidan. Ashiru k'aramin kaninmu yana ko'karin bud'e kwantenarsa ya tsaya yana kallon fitowarmu daga mota da yake har kofar gida Ayuba ya ajiyemu Ya taho daa sauri kuwa yana washe baki "anti Amina sannu da zuwa." Na amsa a tak'aice ina bawa Ayuba amsa yana tambayata da kamar k'arfe nawa zai dawo ya dauke ni na ce." Ya bari zan kira shi tukkuna. Muka nufi gidan tare da shi yana ri'ke da hannun Usaina yana fad'in." Anti sun girma sosai ban taba ganinsu ba sai a hoto." Na ce." Kai ma ai ka girma Ashiru ka zama saurayi ina rigimar abincin hantsi.?" Da yake yana yaro dan rigima ne idan an sha koko da safe wajan goma zai dasa rigima abinci ka'ida ne ko ba a ajiyewa kowa dumame ba shi sai an ajiye masa idan ma ba su dashi ni nake bashi ko na yi masa sabo. Idan sun dawo daga makarantar allo ba a gama na rana ba ya yi ta kuka har sai an sauke na rana sannan gidan za a samu lafiya. Ya yi ta dariya kuwa domin ko ya mance wasu abubuwan da ya dinga yi tabbas ba zai mance wasu ba. Ya bude mini kwantenar tasa cike da kayan masarufi awo ne kadai ba ya yi ina ta dubawa ina jin dadi ganin yadda yaro ya zama manemi shi bai yi fitinar su Kamalu da Saminu ba sai da kukan kuruciya. Na ce." Aikuwa ni ma zan sanya hannuna a ciki Ashiru ya kamata a ce harkar nan an fad'ad'ata." Ya dinga washe baki yana fad'in." Wallahi kuwa anti Amina Babanmu ne ya fara ba ni dubu dari da hamsin na fara a hankali a hankali Yayanmu Usaini ya sake ba ni dubu dari." Na ce." Ya yi daidai Hakan ni ma zan bada gudumuwata in sha Allahu." Muka shiga ciki shiru Ina ta sallama. Can Ummansu ta amsa ya ce." Ummansu Hadiza wata'kila bacci take yi domin kwana biyu ta yi fama da mura da zazza'bi. Ta dago labule ganina sai ta kama dariya. Na sauke ajiyar zuciya ganin yadda ta marabceta ni dama ina ta tararrabin kada ta kawo mana tangard'a a cikin lamarin nan amma yanzu yadda na hangi sukuni da annashuwa a fuskarta ya sanya na kori shakkun da nake yi. Ta fara fadin." Maraba lale Hajiya Amina sannu da zuwa ashe tare kike tafe da yaran bakid'aya yanzu nan mutumin naki ya fita kasuwa amma ya ce idan ya gama d'aure wasu kayan da zai tura Ghana zai dawo ." Na ce." Allah sarki babu damuwa dama ai zuwan na ki ne bari na shiga mu gaisa da Ummansu Hadiza na fito." Tana cike da matsanancin farinciki ta ce." To shikkenan." Na same ta a kwance a katifa shiru kamar ta rushe da ihu domin yanayin fuskata kadai ka duba za ka gane a cikin damuwa da take da b'acin rai. Ta tashi zaune tana yar dariya "Amina maraba lale marhabun ai jiya babanku yake gaya mana kina tafe maraba." Ta sake fad'in haka tana janyo hannun Usaina tana cewa." Biyu sun girma sun zama 'yan mata." Na zauna saman daddumar da ta shimfida mini ita kuma ta janyo yaran suka hau katifar da take zaune suna jereran gaisheta. Ta dubi Minal tana cewa " 'Kanwarsu ce wanann ko don na ga hangi kama." Na ce." Eh mai sunana ba Amina ce muna kiranta da Minal." Ta ce." Ma sha Allah duka gasunan sun yi wayo sosai wallahi." Na yi murmushi ina nazartata ta d'an rame gaskiya ba kamar lokacin da suka je gaisuwar Hajiya Maryam ba ramar da ta yi yanzu ta fi muni domin kallo daya na yi mata da na shigo na tabbatar da cewa." depression yana damunta.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700...0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *155* Ta ba ni tausayi sosai to ya za a yi ne shiyasa ake fad'in idan kasan farkon ka baka san karshenka ba. Kuma duk wanda ya shuka alheri shi zai gani kuma idan sharri ma ka shuka to tabbas shi za ka girba da wayo na ba zan manta da irin azabar da matar nan ta gana mini ba. Na ci wahala ainun a hannunta wankin yaranta ni ce girki da cefane shara da wanke-wanke duk ni ce ba ni da sabulun wanka a gidan balle na wanki haka za ta tura Hadiza gidan kisto da kudi a yi mata ni nawa kan ya yi sama da sati hud'u ban tsefe ba idan zan ari kibiya a wajenta na dinga ra'be-ra'be kenan har sai da Gwaggo ta fahimta. Wando pant da siket kuwa sai da ya kasance biyu gare ni duk sun yayyage haka nake sanyawa a jikina nan ma gwaggon ta ankara ta sayo mini ita da Yaya Aminu da Sahura sun taimaka mini k'warai a wancan lokacin. Na yi girki da hannuna ta zo ta raba ta cikawa yaranta kwano ni ta bar mini 'kasan tunkuya duk ranar da ta tauna tsakuwa a shinkafa kuwa ina shan zagi a gidan. Sai da Ummansu Saminu ta zo gidan na fara samun sau'ki amma zahiri Ummansu Hadiza ta wahalar da rayuwata babu abinda yake bibiyarta sai hakki. Ta dinga kuka haka kawai tana kallona na yi na yi da ita ta yi shiru ta yi mini bayanin abinda yake damunta da kyar cikin dashewar murya ta furta."Hankalina ya'ki kwanciya Amina kullum Hadiza tana raina da wannan zaman da take a wannan waje gwara su yanke mata hukuncin ta san matsayinta, ni ma hankalina zai fi kwanciya. Da yawa mutane sai su dinga fad'in na kwantar da hankalina wallahi ba zan iya ba domin ko bacci bana iya yi sai ciwon kai." Na ce." Ai ha'kuri da tawakalli ya zama dole Umma ki bar wa Allah lamarinsa domin Ubangiji yana so ya jarrabeka ka yi hakuri ki dinga yi mata addu'a idan da rabon za ta fito ta sake wata rayuwar sai ki ga dalilin wani lamari ta fito mun cigaba da rayuwa tare. Idan kin tsananta ciwo zai iya kama ki, kuma yana da kyau mu sake komawa asibiti tunda kin ce kina fama da ciwon kai." Ta gyad'a kanta tana fad'in." Shine abinda ya fi damuna yanzu." Na ce." To shikkenan in sha Allahu da kaina ma zan kai ki asibitin." Ta ce." Na gode sosai Amina." Shiru ya d'an ratsa wurin na dubi agogon da yake daure a hannuna sha daya saura na yun'kura da kyar na tashi sai a lokacin ta lura da cikin jikina ta ce." Ashe da sai dai mu ji haihuwa Amina haka ki ka yi nauyi." Yar dariya na yi kawai dama sai mai kurrula ne zai gane akwai ciki a jikina dalili duk ya bi kirjina daga 'kasa ya sake bud'e ni na yi fadi sosai sai dai yayi mini mugun nauyi a mara sosai. Ta ce."Allah Ya sauke lafiya." Na amsa da Amin a takaice. Hanyar fita na kama ina fad'in" Bari na shiga wajan Ummansu Saminu. " Ta yi shiru ba ta ce komai ba yaran suka biyo bayana na ji tana fad'in." Ba za ku zauna anan ba." Babu wanda ya waiwayeta suka biyo ni. Ummansu Saminu na zaune cikin annashuwa har da sanya sabon d'inki ta cokala d'aurin d'ankwali tana tauna cigum cike da nishadi. Mamaki ya kama ni kamar an fara hidimar bikin ita tun yau ta fara kwalliya kenan. Na zauna ina nazarinta dama d'akin gabad'aya Rumfarta makad'e da kafet mai taushi da sabbin labulaye da sabon agogon bango sakamakon na Ummansu Hadiza da ba a sabunta shi da komai ba. Wala'ala ita ta yi gyaranta ko kuma shi Usainin ya yi mata saboda taron bikin da zai gudana. Jikina ya yi sanyi sosai wato ita duniyar nan juyawa take yi amma kuma ga dukkanin alamu zaman ha'kuri Ummansu Hadiza take yi a gidan alamu sun nuna Ummansu Saminu itace mai hutawa dalilin yaranta duka maza ne kuma sun tashi suna nema ita kuma Ummansu Hadiza ga yadda rayuwa ta juya mata shiyasa ake so mutum ya shuka alheri domin ba a san inda rayuwa za ta juya ba. Ban yarda mun yi wata magana da ta shafi abinda ya kawo ni ba sai da na kira Ummansu Hadiza domin kada abin ya yi mata yawa kuma lallai idan Usaini ne ya yi wa mahaifiyarsa wannan gyaran bai had'a da Ummansu Hadiza ba to bai kyauta ba. Gabad'aya ma gidan zan sanya a yi masa fenti da sabon simitin tsakargida a canza musu kofofi da tagogi dole ne abin ya yi mata yawa ta auri zaman d'aki kunci da damuwar yadda rayuwa ta juya mata ya janyo mata ciwon kai. Ta kuwa ji dadin yadda na sanyota cikin lamarin hakan ya nuna mini cewa Ummansu Saminu iyakarta take nuna mata akan sabgar. Ban yadda na gaya musu ga yadda al'amarin ya kasance har auran ya juya kan Usaini ba bayanin da na yi Babanmu haka suma na yi musu cewa yarinyar a can k'auyensu mijina take wato bunkure kuma na je naga gidansu da mahaifinta fitaccen malamin addinin musulunci ne. Ummansu Hadiza ta saki jikinta sosai muna ta hira yayin da ita kuma Ummansu Saminu na fahimci hakan bai yi mata dadi ba sai ma ta tashi tana fad'in bari ta d'ora abinci. Ta shigo bayan fitarta da kamar minti goma tana fad'in." Hadari ne a garin nan fa wata'kila yau mu samu ruwa." Ummansu Hadiza da sauri ta ce." Allah Ya sa ai kwana biyu mun sha zafi." Ta share ta ba tace komai ba ta d'auki wani dan bokiti ta fita. Na dube ta a sanyaye sai ta ba ni tausayi kad'an wato abinda ta yi wa Mamanmu a can baya ne yanzu take ganin sakamako. Ban ji dadin irin wannan zaman da suke yi ba ai na d'auka sun girma masu yi wa wasu fad'a ne ni kaina abinda yake faruwa tsakanina da Hauwa baya yi mini dadi ko kad'an don dai babu yadda zan yi ne, amma babu abinda ya fi zaman lafiya dad'i Ubangiji Allah ka ba mu ikon zama da kowa lafiya kada mu cutar da wani domin shi sharri d'an aike ne. Hadarin ya taso sosai iska ta fara tashi garin ya turnuke farkon damuna muke ciki ga dukkanin alamu za a samu ruwan sama da wuri Yaran suna tsakargida suna wasa sun samu sake da yake tsakargidanmu akwai yalwa na ji Ummansu Saminu tana fad'in." Ina Gambon taku take ne ko dai ta fita." Ummansu Hadiza ta leka tsakargidan daidai lokacin da Usaina take k'walawa Minal kira bata gidan da gaske fita ta yi gabad'aya ba mu ankara ba, suma yaran da suke wasa tare ba su lura da lokacin da fice ba. Na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Na tashi da kiran sunan Allah gabana na fad'uwa hijab dina na zura dalili na cire shi jin abinda jikina ya kasa d'auka zafi sosai da kyaikyayin jiki ban sani ba ko dan na jima ina rayuwa cikin ac ne oho amma dai yau yini guda duk na burkice dalilin hadarin da ya had'o da kuma zafin da ake tsugawa. Muka fita tare da Ummansu Hadiza ma'kota ta dinga shishshiga ni kuma na fara duba yara da suke wasa a layin ban hangi rigar Minal ba. Kafafuna suka dinga kyarma. Ashiru ya rufe kwantena ya bazama. Kasa cire kafata na yi na koma soro na tsaya ina kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Twins kuwa da suka fahimci Minal 'bata ta yi sai kuka Hassana tana fad'in." Kuma bata da lafiya ko Usai." Ta daga kanta tare da zura yatsa a baki tana tsotsa hawaye na fita. Na sake karyewa k'warai da gaske tsautsayi ne ya sanya ni taho da yarinyar nan, na tabbatar da cewa idan ba a ganta ba daga nan zuwa dare ubanta da uwarta dole su ji a wannan ga'bar da muke ciki da ni da su na rashin samun daidaito bai zama lallai su yi mini uzuri cewa tsautsayi ne ba. Za a ce me yasa nawa yaran ban sake sun fita sun shiga lungunan da ba su sani ba sun 'bace. Ina nan tsaye cikin tararrabi kimanin minti ashirin Ummansu Hadiza ta dawo daga yawon shiga makota babu Minal babu dalilinta Muka koma cikin gidan jikina a mace k'warai da gaske Ummansu Saminu ta sauke abinci ta ce." Ya kamata ki sanar da babanta Hajiya Amina." Na zauna saman turmi a nutse ina fad'in." Bari mu jira dawowar Ashiru ba ni tsammanin yarinyar nan nisa ta yi. Ina rufe baki kuwa sai muka ji kukanta daga soro na tashi tsaye da sauri. Ashiru ya shigo da ita a hannunsa ta yi wujiga-wujiga ta ci kuka ta k'oshi har da tabon fad'uwa a goshinta da alamun jini kad'an Na kar'beta da sauri ina dudduba jikinta gabana na ta fad'uwa ta ri'ke ni tamau tana shasheka ina jin Ummansu Hadiza na tambayarsa a Ina ya same ta ya ce tsallaken titi wani mutum yana yawo da ita a hannu zai nausa da ita titin tudun yola Na zaunar da ita tare da cire mara riga jikinta da zullumi da fargaba na tube mata wando pant na duba gabanta alhamdulillahi babu wata alama. Ummansu Saminu ta juye ruwan da yake cikin fulas din shayi na surka na yi mata wanka ta zuba musu abinci suka ci cikin rashin dad'i ta b'ingire ta kama bacci. Na kasa cin komai saboda tashin hankali tabon da yake goshinta shine ya fi d'aga mini hankali kuma har yanzu zabura take yi. alamun a tsorace take har yanzu. Sai da na yi sallar la'asar tukkuna na ci abincin dafuduka ta shinkafa har da kifi da ruwan pure water. Na d'auki wayata domin kiran Ayuba ya zo ya d'auke mu na mayar musu da 'yar su. Ina laluben lambar direban shi kuma ya kira hannuna ya shiga rawa na daga ban iya cewa komai ba saboda tashin hankali sai nake ganin wata'kila labari ya riske shi abinda zuciyata take raya mini kenan duk da cewar yarinyar ba a san 'yarsa ba ce amma zuciyata ta kasa tsayuwa waje daya. "Yanzu haka Hauwa tana Dambatta na sanya an kaita Ayuba zai zo ya d'auke ku saboda ganin garin da hadari ina fatan kin kammala uzurin da ya kai ki." Na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." Na gama." Ya kashe wayar bai sake cewa komai ba. Na dubi yarinyar har yanzu bacci take yi suna kusa da ita sun kasa sakin jikinsu kamar ma sun gaji da zaman gidan suna so a tafi. Ko da na tambaye su amsar da suka ba ni kenan mu tafi. Na sauke ajiyar zuciya wadda ba zata lissafu ba. A haka na mayarwa da yarinyar kayanta dana cire mata. Ummansu Saminu ta shigo d'akin tana fad'in." Har yanzu ba ta tashi ba ko?" Kaina kawai na iya daga mata. Ta d'an dubeta cikin nazari kafin ta ce." Har yanzu a tsorace take kin ga ni duk da tana bacci jikinta rawa yake yi tana zabura wata'kila garin gudun hadari da iska ta fad'i ko wani ya gwabgeta gashi hadarin ya washe ba mu samun ruwan ba Allah sarki ai an auna arziki ma tunda ba a yi nesa da ita ba. Na lura yarinyar ta fi yan'uwanta rawar kai in ba haka duka fa suna zaune a tsakargida suna ta wasa a tare amma fitowata daga kicin na ga babu ita a wajan ta fita kuma maimakon ta tsaya a waje ta nausa. A takaice na furta." Tsautsayi dai kawai amma sam ba da ita na yi niyyar zuwa ba wallahi Babansu ya kawo mini ita cikin mota tana kuka sai ta bi ni." Ta gyad'a kanta tana cewa." Hakane abinda ya yi kiranta kenan da mutuwa ce ma haka za a shigo da gawarta." Gabana ya fadi jin abinda take fad'i itafa dama can haka take ba ta tauna magana kafin ta furta gabagadi ce. Allah Ya kiyaye. Daga yau ma ba ni ba zuwa ko'ina da yarinyar duk rigimar da za ta yi kuwa balle wani tsautsayin ya faru. Ashiru ya shigo yana gaya mini ga Ayuba can ya zo. Na ce ya d'auki yarinyar ya kaita mota. Na tashi da bismillah muka fito tare da yaran Ummansu Hadiza ta fito daga d'akinta da carbi da alama ba ta jima da idar sallah ba fad'i take yi yarinya kun zo lafiya lau za ki tafi da tabo a goshi abin nan bai yi mini dadi ba wallahi Amina Allah Ya kiyaye gaba." Na amsa da Amin Ya Allah. Akwai gyare-gyaren da nake so a yi muku a gidan amma dai zan yi waya da Babanmu tunda yau din bamu samu haduwa ba wata'kila ma gobe ko jibi a fara aikin saboda ba ni son a ja dogon lokaci cikin satin da za mu shiga nake so a kammala komai mu d'auko amarya ta tare a d'akinta. Ummansu Saminu ta dago labule da sauri ta fito tsakargidan ta tsaya ba ta ji dadin yadda na tsaya muna sake tattaunawa da Ummansu Hadiza ba. Ita kuwa sai dariya take yi tana nuna farinciki a zahiri dai ko da tana jin haushi da bakinciki ba ta fito fili ta nuna ba tana ta daurewa hakan ya kara tabbatar mini da cewa lallai ta tuba kuma duniya ta koya mata hankali sannan neman zaman lafiya da sulhu take yi a gidan. Muka shiga mota Ayuba ya ja muka d'auki hanyar gida zuciyata cike da zullumi haka zalika ma jikina cike da rashin kwari da karsashi ban iya 'karya ba kuma ba zan fara akan wannan dalilin ba domin kuwa ko da na yi domin na kare kaina watarana abinda na rufe zai iya bayyana ga yaran nan da bakinsu ba ya yin shiru ga kuma tabo na daujewa a goshin yarinyar ko shi ya isa ya nuna aya. Don haka idan ya nemi dalili zan gaya masa. Yarinya dai ban yi niyyar zuwa ko'ina da ita ba ya kawo ta cikin mota ya ajiye tsautsayi ya kira ta ba kuma a son raina ba. A gidan muka same shi shi kadai zaune a falo da waya a hannu alamu sun nuna dakon jiranmu yake yi. Ayuba ya dire yarinyar a k'asa dama shi ya daukota tunda har da muka iso bata tashi ba sai yanzu ta fara wuri-wuri na ri'ke hannunta da kyau ganinmu a gida ya sanya ta d'an nutsu ya juyo yana kallonmu. Ayuba ya juya ya fita da sauri. Kasa ce masa komai na yi na kama hanyar d'akina yaran suka nufi wajen da yake zaune babu wani kuzarin kirki a tattare da su gabad'aya.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *156* Cikin nauyin jiki na cire hijab din jikina na zauna gefan gado har yanzu zuciyata bata samu nutsuwa ba dalili nasan lallai ne akwai abinda zai biyo bayan abinda ya faru. Zamana da minti goma ya shigo shi kadai d'akin. Muka dubi juna kafin ya furta." Da gaske ne abinda yaran nan suka fad'i." Na gyad'a kaina tare da cewa." E, da gaske ne." Domin fad'in gaskiya shine abinda ya kamace ni." Ya yi shiru yana yi mini wani irin kallo na cigaba da cewa suna tare duk a wuri d'aya ta zame ta fita ba tare da kowa ya ankara ba.'' Ya tare ni da sauri ta hanyar fad'in." Ke kina ina har hakan ta faru?" Na ce." Ina d'aki a zaune tare da matan gidan su kuma suna tsakargida suna wasa." Ya ce." Babu wani abu anan face sakaci da rashin kula Amina me yasa kin san cewa ba su ta'ba zuwa waje ba ki yi nesa da su. Har sai da ta 'bace ta yi nisa tukkuna duka za ku ankara da cewa ba ta gidan saboda kun shagalta gabad'aya." Na danne haushin da ya ba ni na ce." Duk yanayin kular da zan yi a kansu idan Allah ya aiko tsautsayi babu yadda za mu yi kuma kada ka ga lefina fa yarinyar nan ban yi niyyar zuwa ko'ina da ita ba ka d'aukota ka kawo mini cikin mota. Me yasa don tsautsayi ya faru a kanta a ce ba za a yi mini uzuri ba." Ya fusata sosai yana fad'in." Ba ki yarda da cewar rashin kula ba ne kenan. Ya za a yi ki je da yara wajan da ba su saba ba ki sake su ke kina wani waje a zaune kuma ki ce a yi miki uzuri akan wane dalili ke ba za ki yi lefi a nuna miki kuskuranki ba kenan." Na ce." Ba zan fasa fad'in tsautsayi ne ba. Kuma na iya kasancewa akan kowa amma abinda nake so na gaya maka akan yarinyar cewa tana da rawar kai fiye da 'yan uwanta me ya kai ta fita ta bar su tunda tare suke duka a zaune a waje daya suna wasa. Lefin ai ba nawa ba ne gabad'aya." Ya gyada kansa yana cewa." Tunda kin ce haka wallahi babu inda za ki kara zuwa da yaran nan." Na tare shi da sauri ina fad'in." Aikuwa ba ka isa ba kaffara ta hau kan ka." Bai ce komai ba ya juya ya fita cike da b'acin rai. Na ja tsaki ni ma cikin b'acin ran na tashi domin cire kayan jikina sun yi mini nauyi yamma ta yi sosai don daf ake da kiran sallar magriba. Na sanya doguwar riga cotton mara nauyi da hula na fito falon shiru ban ji motsinsu ba na yi tunanin ko suna sama tare da shi. Kicin na shiga na dora farar taliya haka kawai nake sha'awar cin ta da manja da yaji da kifi. Na kammala na fito still ban ji wani motsi ba d'akina na shiga na yi sallah ban sake fitowa falon ba sai da na yi Isha'i na fito babu motsinsu. Kai tsaye saman na hau na bud'e d'akin nasa babu kowa shiru. A lokacin ne na gazgata abinda zuciyata take raya mini ya kwashe yaran ya yi gaba da su kenan. Ga abinci na dafa har da su. Na dibi daidai yadda cikina zai d'auka na kira Ayuba na juye musu shi da masu gadi Abincina na ci na k'oshi na samu yar nutsuwa na kira anti Yagana na gaya mata shawarwarin da na yanke ta sake bada goyon bayanta sosai amma ba lallai ne ta samu damar zuwa bikin ba tunda tana tare da maijego ba ta yi arba'in ba. Mun jima tare da Babanmu a waya muna magana har yana yi mini jajen 'batan Minal duk abinda na yanke na gaya masa ya yi ta sanya mini albarka har muryarsa tana rawa. Bana tsammanin zan kira shi domin na tambayi dalili. Mu tafi a haka kawai domin neman dalilin ma zai kara masa kwarin gwiwa ne. Hamusu na wakilita kamar yadda na gayawa Babanmu a washe garin ranar aka fara aikin gidan domin sabunta wasu abubuwan. Aikin gidan Usaini ma an cigaba da gyara bangaran amarya kamar yadda na yi masa alkawari duk dai a washe garin ranar da nake gidan namu. Da yamma sai ga Fati ta zo mini da yaranta su biyar yadda na gan su a lalace ita da yaran gabad'aya sai da tsigar jikina ta tashi Fati mai garin jiki da san girma duk ta tsiyaye yaran babu suttura ta arziki duk sun kod'e sun d'angale yaduka masu arha wanda take goyo uku da wata riga irin ta gwanjo hannun da wuyan ya yi masa yawa da wando wanda aka rage gefansa da zare da allura. Tana sauko shi daga bayanta zarni ya cika mini hanci domin dai ba ta sanya masa pampers ba ya kuma yi mata fitsari a jiki da zanin goyon gabad'aya. Na zura mata musu ido jikina a sanyaye wai shin wace irin rayuwa muke ciki ne a yanzu ki ga mace da 'yan shakaru kad'an ta tsofe ta lalace saboda rashin kula da wahalar gidan aure. Suka dinga bi daya bayan d'aya suna gaishe ni ina amsawa tausayinsu na tsirga mini wannan rayuwa Allah Ya saukaka mana ita sai na tuna lokacin da ubansu ya fito auran Fati Ummansu ta dinga murna tunda a lokacin yana tashen samun kudi sai dai babu arabi babu boko haka ta tsige mata makaranta duka ajinta biyu a sakandire ta ce karatun ai babu dole ta yi mata aure lokacin Babanmu sai yadda ta yi da shi. Tana ta washe bakinta take cewa. " Daga gidanmu nake Umma ta ce ai kin zo garin ga ma abin alherin da ya faru na ce bari na kawo miki yara ku gaisa." Cike da kulawa na ce." Kin kyauta sosai Fati na ji dad'i kuma ina fatan duka kuna lafiya ." Na tambayeta hakan kamar yadda al'ada ta gada amma a zahiri ai duk wanda zai ga Fati ya san ba ta cikin nutsuwa. Ta yi d'an murmushi tana fad'in." Lafiya lau anti Amina." Na dafa kafadarta ina cewa." Ki gaya mini idan da wata matsalar Fati ba ki jin dadin auran nan ko." Ta kuwa fashe da kuka har jikinta na rawa na rugumeta sosai a jikina idona ya ciko da ruwan hawaye yaran suka yi tsuru suna kallonmu na kyaleta ta ci kukanta ta k'oshi kafin ta dago ta goge fuskarta. Na ce." Gaya mini ko da akwai taimakon da zan iya yi miki." Ta ja hanci tana fad'in." Babansu ya karye a kasuwa tuntuni anti ga yara a tsakaninmu ba na ma tunanin rabuwa da shi tunda lokacin da yake da shi ya yi mini kuma idan na ce zan kashe auran ban san wanda zan aura anan gaba ba kuma zan yi ta tunanin yarana zuciyata ba zata nutsu ba.amma wallahi anti Amina yunwa tana damun mu ni da yara sannan sai matsalar gidan haya wani abokinsa ya bashi shawara ya sayar da gidansa suka saro kaya karshe kudi ya narke masa duka suka lalace Bai tsira da komai ba. muna gidan haya muna shan tsangwama da gori. Anti Amina ba zan rufe miki ba yunwa ta assasawa Faruku d'auke-d'auke tun bai kai shakarun haka ba ko idan ma'kota sun aike shi ya rage kud'i ya boye. Ba ki ga yaran da yake bi ba yanzu sai na kwana uku biyar har sati ban sanya shi a idona ba. Har shaye-shaye yake yi fa anti Amina." Ta rushe da kuka tana riruke hannuna. Faruku shine babban yaronta ya zama saurayi yanzu domin ya girmi ma Kamalu tunda duka sun riga ni aure da haihuwa haihuwarta bakwai da biyar ta zo mini. Na zura mata ido ina tuna abubuwan da suka shud'e a shakarun baya. Lallai Fati tana cikin jarrabawa. Ban yarda na yi magana ba sai da na daidaita kaina tukkuna na mayar da hawayen da ya ciko mini a kwarmin ido domin kara mata kwarin gwiwa na fara yi mata misali a kaina da sake jadadda mata cewa babu abinda bashi da karshe kuma dukkan tsanani yana tare da sauki. Yanzu dai babban tashin hankali matsalar yunwa domin itace musabbabin dole kuma a magance ta idan ba haka ba d'aya bayan d'aya yaran za su d'auki hanyar da yayansu ya d'auka Duk matsaltsalunta da ta gaya mini na gazgata domin ita dama halinta daban da na Hadiza sannan ba kasafai take biyewa Ummansu idan tana wani abin ba abinda dai ta dinga yi mini a lokacin kuruciya na rashin kunya wannan dama d'abia ce ta yaran da suke da uwa a gida mussaman idan an nuna musu su kad'ai ne 'ya'ya masu 'yanci ba kuma su samu tarbiya ba ko a wancan lokacin dama ni su Hassana ne da Usaina ne mutane na mun fi shiri da su haka duka muka dinga rayuwar a gidan to yanzu ga yadda rayuwa ta juyawa kowa. A dai yadda take a yanzu ko bata bud'e baki ta fad'i damuwarta ba duk mai hankali zai gane cewa tana buk'atar taimako kuma ni ta burge ni sosai da ba ta yi tunanin watsar da yaranta ba. Ta yi hankali sosai saboda idan ta fito shi kansa zawarcin wata babbar jarabawa ce sannan wanene zai kula mata da wannan yaran. Na ba su abinci suka ci suka koshi ina sake kwantar mata da hankali da bata tabbacin zan yi mata iyakacin bakin kokarina idan har ta yanke shawarar sana'ar da za ta yi zan taimaka mata da jari. Da za ta tafi na bata dubu goma sannan na sanya Ayuba ya d'auketa a mota domin ya kaita gidanta na kuma tabbatar mata cewa idan hidimar bikin nan da za mu ta kammala zan yi mata Aiken kayan abinci. Ta yi kuka kamar kamar me har sai da ta karya mini zuciya haka muka rabu da tsananin tausayin halin da take ciki a raina. Watarana sai labari in sha Allahu rabbi. Ni kadai na sake kwana a gidan hakan bai dame ni sosai ba tunda dama na saba da hakan tuntuni kafin zuwan Baba Tabawa. Mun yi waya da Hamusu yana gaya mini lefe ya hadu na ce ya kai musu can gidanmu su gani shima angon ya duba idan akwai abinda yake so ya kara a ciki to kafin ya kawo mini ni ma na gani Mintina kad'an da gama wayarmu shi kuma ya kira na d'auka cikin ko'karin daidaita muryarta. Ya amsa sallamar da na yi na ji yana fad'in." Muna Abuja gabad'aya da yaran yau Hauwa za ta tare a gidanta akwai gidana jikin massalacin da na gina wanda Kamalu ya dinga limanci shekarun baya kin gane shi ko?" A takaice na ce."A a." Ya furta." Yana cikin estate din na mu can gaba. Nan zata cigaba da zama ke kuma ki zauna a wanda muke ciki yanzu." Na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Na ce." To." Ya d'an yi shiru kafin ya ce." Idan kin kammala Uzurin bikin naki sai ki sanar da ni ko?" Na ce." Ba ni tsammanin zan dawo ko bayan bikin sai na haihu tukkuna." Ya yi shiru yana jina bai ce komai ba. Na ce." Ka ji abinda na ce ko?" Ya nisa kafin ya furta." To na ji." Ya kashe wayar bai ja maganar ba. Dariya ta su'bce mini ganin ya zama wani sukuku da shi ya daina ja'ina ni kuma na fad'i hakane kawai domin na tunzura shi tunda haihuwa da saura nan gaba kusan wata biyu kuma ba ni haihuwa a wata tara sai na goma ya shiga nasan ya amsa ne kawai ba wai don ya amince ba sai don gudun tashin hankali da alama shiri yake nema. **** To komai ya yi farko yana da k'arshe haka zalika duk abinda aka sanyawa rana sannu a hankali zai zo a yi a kammala mun yi bikin Usaini cike da annashuwa da walwala an yi komai cikin rufin asiri kuma duk abinda yake na al'ada an yi wa amarya. Gidanta na sanya a shirya mata shi sosai da kayan d'aki daidai gwargwado. 'yan uwan mamansa da Ummansu Hadiza Sahura ta jagorance su d'auko amarya domin ni ko kai kayan lefen ma ban samu sararin zuwa ba saboda hidima da gajiya sai da tare da kwana uku tukkuna na sanya Ayuba ya d'auke ni a mota ya kai ni gidan. Ta rugunme ni kuwa tsam a jikinta tana murna tana fara'a irin wadda ta saba. Ita dashi Usainin duka sun ba ni mamaki ganin yadda suke jifan junansu da kallon soyayya kamar dama can suna son juna aka yi auran. Na jima a gidan tare da su domin tun safe nake har yamma na nuna mata abubuwa da dama tare da sanya mata lambar wayata a cikin sabuwar wayar da ya sayo mata na ce duk abinda ya shige mata duhu ta kira ni ta gaya mini. Sai da na yi magriba tukkuna na kira Ayuba ya zo ya d'auke ni. Muka yi sallama da begen juna. Kwana biyu hankalina ya kwanta gajiya ta fara warwarewa Ayuba na bawa kudi ya sayo kayan abinci komai da komai na umarce shi zuwa gidan Fati kamar yadda na yi mata alkawari lokacin da ta zo mini. **** To tunda muka yi waya kwanaki biyu da tafiyarsu bai sake nema ba har aka ci biki aka cinye babu wata magana da ta ratsa tsakaninmu tun bayan wadda muka yi da a k'arshe na ce masa sai na haihu nan tukkuna zan cigaba da zaman abuja. Ban fad'a da niyyar hakan ba kawai tsokana na yi niyyar yi amma ganin ya share bai ce komai ba ni ma na sake gyara zama duk da cewar dai hankalina yana kan yarana amma nasan za su samu kulawa wurinsu Baba Tabawa tunda ya d'auke Hauwa daga gidan. Da yamma sai ga kiran Nusaiba muka gaisa sosai tana tambayata yaushe zan dawo ta zo har sau biyu sai masu aiki da yara har ta na yi mini Allah Ya sanya alheri ta ji labarin na yi biki. Ina jin dadin yadda yarinyar take girmama ni sosai na ce mata ina nan tafe a kusa in sha Allahu. Muka yi sallama cikin mutunci. Duk dai a daran ranar ina duba wayata sannu hankali na ga ya d'ora status ban ta'ba ganin ya d'ora hoton soyayya ba kai hotonsa ma ba d'orawa yake yi balle na iyalinsa ko na yara. Jefi jefi dai yakan d'ora abu nai muhimmanci walau bangaran business din shi ko kuma tunasarwa tun bayan katin d'aurin auransa da ya d'ora satikan da suka wuce kuma shima bai fi da minti ashirin ba ya goge a lokacin da yake cikin rashin nutsuwa kafin ya samu mafita sai shakarun da suka wuce lokacin auransa da Hajiya Maryam nan zan ce naga hotona barkatai a status dinsa. Sai kuma yau da ya d'ora hotona masu yawa. Na farko farko nasa ne dana Samira Yayar Hauwa matarsa ta fari tun na kuruciya lokacin da suke soyayya. Sai kuma na Hauwa da yaranmu gabad'aya na k'arshe ita dashi ne a sabon gida aka yi musu ya rungumeta ita kuma ta zagaye hannunta a k'ugunsa suna dariya gabad'aya. 'Kasan hoton ya sanya alamar heart da farkon sunansa da na ta.......Nan da nan na ji wani tashin hankali ya yi mini dirar mikiya na nemi yawu na rasa a bakina wani kishi mashahuri ya turnuko mini. Idan ma da gayya ya yi domin ya dyaga mini hankali tabbas ya samu nasara domin lokaci guda na ji tashin hankali tunanika masu yawa suka fara bijiro mini a kaina wato suna can suna cin amarci a sabon gida har da hoto gashi nan katafaran falo wanda ya ji kaya na alfarma, da bai samu nasarar yin sabon aure ba ai gashi ya tare a sabon gida da matarsa suna sha'katawa har da rungume juna da d'aukar hoto cikin nisha'di da annashuwa. Na ji tamkar an d'auki tabarya an rarrad'e mini kafafuna na ajiye wayar ko datar ma ban kashe ba na kwanta ina ko'karin sarrafa zuciyata dangane da yadda take hantsilawa tsabar kishi da tashin hankali. Da na ce sai na haihu zan dawo ashe hakan wata dama ce na bashi domin ya huta. Can kasan zuciyata na ce mini kada abinda ya yi ya dame ki Amina tunda ta wannan sigar ya b'ullo ku cigaba da tafiya haka har kin manta da halinsa kenan idan bai sake yi miki maganar ba ki yi masa shiru bari ki haihu anan lafiya cikin 'yan uwa. Abinda zuciyata take gaya mini kenan. Wani sashe kuma na'kin amincewa da hakan domin kuwa gabad'aya hankali da tunani na yana can idan har na bari muka ci gaba da tafiya a haka Hauwa za ta yi mini dariya buk'atarta ta biya. 'Ko dai ita ta d'auki wayar tasa ma ta dora hotonan domin tasan lallai zan ga ni." Zuciyata take sake gaya mini haka. Na girgiza kaina ko Hauwa ba ta d'ora hotonansu ba shi ma zai iya d'orawa domin ya jefe ni cikin damuwa, tunda duk ya bi hanyoyin da zai lallasa ni bai samu sa'a ba ya biyo ta wannan sigar. Na sake shiga Whasap din hannuna na rawa ban ma san me zan duba ba kawai sai na ga an goge hotonan ma gabad'aya babu su. Na sake shiga damuwa da nazarin hakan shine ya d'ora ko Hauwa domin ni a ka diora tunda an lura na ga ni sai aka goge wannan shine amasar, amma har yanzu tunanina ya kasa tantance mini wanda ya yi hakan a tsakaninsu. Na jima ina addu'a samun sau'kin zuciya kafin na yi shirin kwanciya na kwanta gabad'aya ba ni jin dadi jikina da zuciyata. Kiran sa ya shigo wayata da ban kai ga kashewa ba. Na ajiye ta katse ban daga ba ya sake kira ta katse. Ya kira ya fi sau biyar ban d'auka ba dana ji bacci yana shammatata ma sai na kashe wayar gabad'aya na yi addu'a cikin ikon Allah bacci ya d'auke ni......✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *157* Ko da gari ya waye ban kunna wayata ba saboda takaici zuwa yanzu na tabbatar da cewa shine ya d'ora status din saboda ya ba ni haushi kamar yadda ya yi mini a wancan karon lokacin auransa da Hajiya Maryam. Idan na ce ban ji haushi ba na yi karya abin ya ta'ba mini zuciyata sosai kuma ban sake gazgata matsanaciyar k'aunar da nake yi masa ba sai yanzu da nake ji har yanzu zuciyata ba ta daina zafi ba. Tare muka yini da Sahura muna tattauna batutuwa masu yawa har take ba ni labarin irin saranda da sadudar da Idiris ya yi abubuwa da yawa sun kamace masa kudin da ya samu sun k'are tuntuni domin gabad'aya bai san yadda za a yi ya juya su su ru'banya ba birni ya dinga yi da auran da babu ribar komai sai ta haihuwa. Na bata shawara sosai akan ta ajiye duk malamanta ta tallafe shi tunda har ya yi nadama ya kuma bata ha'kuri ai an riga an zama d'aya yaransu uku a tsakani don ma ba mai haihuwa ba ce da tuni sun fi haka. Na kuma ce mata a duk lokacin da matarsa ta haihu suka ba shi d'ansa ko y'arsa ta kar'ba ta ri'ke ta had'a da yaranta gabad'aya domin da d'a da dukiya ba a yi musu mugunta domin ba kasan wanda zaka mora ba. Wata'kila tsananin rabo ne ya sanya shi auran wanda idan ma ba a yi shi ta fannin da Allah da annabi ba za a iya samun rabon ta hanyar da Allah Ya haramta. Sosai jikinta ya yi sanyi a wannan karon ba ta yi jayayya da maganata ba kuma da alama ta d'auki shawarar da na ba ta. Sai daf da magriba muka yi sallama ta tafi. ban yi niyyar girki ba mun dai yi waya da Hamusu tun jiya da rana ya ce mini zai zo mu yi lissafi sai na ce masa ya taho mini da towo daga gidan Gwaggo shiyasa ban shiga kicin ba ko da rana ma Sahura wainar fulawa ta soya mana kayan manja da yaji muka ci cikin marmari. Sai da na yi sallar isha'i tukkuna na kunna wayata. A hankali ina duba wayar kimanin minti goma sha biyar ya kira na bari sai da ta katse ya sake kira tukkuna na daga nasa a kunnena na ji ya sauke ajiyar zuciya cikin taushin kalami ya kira sunana ." Na amsa da "Na'am." Ya furta." Kina lafiya ko ya gajiya?" Na ce." Kalau nake ina yara?'' Ya sake sauke ajiyar zuciyar da nake jin saukarta a kunnena kamar yana gabana. Ya ce." Suna lafiya Amina me yasa ki ka kashe wayarki ne?" A takaice na ce." Na huta gajiya ne shine dalili?" Ya yi shiru na dan wani lokaci kafin ya ce." To shikkenan sai da safe ko na kira ne domin na ji ya ki ke." Har zai kashe na ce." Ina son zuwa gidan Gwaggo gobe ko jibi." Ya furta." Allah Ya tsare." Na amsa da Amin jikina a d'an mace ganin duk abinda na ce zai amsa babu korafi." Ya ce." Ba dai wata matsala ko?" "Umm!" Na ce saboda na ji haushi da bai tambayeni yaushe zan koma ba. Ya sake fad'in." Sai da safe?" Na ce." Allah Ya ba mu alheri." Ya kashe wayar ni ma na kashe tawa jikina gabad'aya ya mutu da abinda ya tsiro da shi wato tunda na ce sai na haihu zan koma ya daina takura mini. Sai na ji hakan bai yi mini dadi ba. Ko da hamusu ya zo ma a daddafe mu kayi lissafin towon da ya kawo mini kad'an na ci na ajiye ragowa da safe na dumama. Na kwanta da takaicin abinda yake faruwa. haka na tashi sukuku babu kuzari. Ruwan shayi kawai na sha sai da rana ta yi tukkuna na dumama towon. Zuwan Kamalu da Yusi shi ya d'an warwarar da ni na samu walwala ganinsu cikin tsabta da nutsuwa da kamala. Na dinga godiya ga sarki Allah da ya yi mini wannan tagomashi kowa ya dogara da k'afafunsa sai a lokacin ma nasan da abinda yake faruwa shirye shirye ya gama kammala karshen watan da muke ciki na musulunci yaron zai ta fi jami'ar musulunci ta madina bisa sahalewar uban rik'on nasu shine ya yi masa jagoranci ya kuma shirya masa tafiyar. Ban nunawa yaron cewa ban sani ba muka tafi kan cewa ai na san da tafiyar na kuma yi masa addu'a kwarai da gaske da fatan alheri. Yini muka yi tare suka ce daga nan gidan Gwaggo suka nufa na ce su gaishe da ita sannan su sanar da ita ina tafe ni ma. To abinda ya dinga faruwa kenan a tsakaninmu. Zai kira ni a waya kullum mu gaisa da kulawa amma fa ba ya yi mini maganar komawa sbuja zai dai ce mini yara suna kewata amma shi ba zan tantance halin da yake ciki ba tunda yana ko'karin daurewa ya nuna mini bashi da damuwa. Ni kuma takaicin abinda yake yi ya hana ni gaya masa ga ranar da zan dawo amma zahiri hankalina gabad'aya ya koma can da tunanin kada Hauwa ta samu damar yi mini dariya ko wata kafar da mutuncina zai zube. Sati uku da bikin Usaini ya kawo mini amarya tun safe ya har yamma muna tare Hajara ta zama 'yar gari yarinya ta murmure ta kara kyau kuma ta fara koyar kwalliya irin ta 'yan birni sosai na ji dadin wannan lamari. Muna tare har dare domin cewa ya yi sai ya taso daga kasuwa tukkuna zai zo ya d'auketa su tafi da muka yi waya ya ce mini yana gidanmu amma gashinan akan hanya. muna hira a falo ni da ita maigidan ya shigo wannan karon tare da Ade suke. Haka kawai na tsinci kaina cikin faduwar gaba domin ban tsammaci zuwansa ba don bai gaya mini ba duk da da safe mun waya bai ce yana hanya ba. Daga bakin kofa Ade ya gaishe ni ya juya ya fita da saurin gaske. Ita kuwa Hajara tun kafin ya shigo cikin falon sosai ta zame daga kan kujera gwiwarta a kasa ta fara gaishe shi. Ya d'an yi jim yana kallonta kafin ya amsa ya dube ni a tsanake ya ce." Amarya ce ko?" Yadda ya fadi maganar ya tabbatar mini da cewa bai ma gama sheda ta sosai ba duk kuwa da cewa a lokacin da ake tirka-tirka auransa da ita da hotonta daya a wayarsa wanda shi ya nunawa Hajja wata'kila ya d'auketa hotone a lokacin domin ya kare mata kallo ya ga ko ta dace da abinda ake buk'ata Allah ne dai masanin dalilin hakan. Na saki fuskata sosai Ina fad'in." Itace ta zo gaisuwa da ban gajiya." Ya gyada kansa da d'an murmushi a tare da shi ya ce." Ya yi kyau, ina angon naki yake?" Ta sunkuyar da kanta kasa tana murmushi kunya take ji." Na ce." Yanzu aka yi waya da shi yana zuwa su tafi." Rufe bakina ke da wahala kuwa Usaini ya shigo. Ganinsa ya sanya ya risina yana fad'in." Barka da dare ya kuwa sanya hannu ya dago shi ganin yana ko'karin tsugunawa ya dinga mika masa hannu domin su yi musabaha yaron yana nok'ewa ya'ki kar'bar hannun cikin girmamawa sai sinne kai yake shi kuma yana yi masa dariya tare da tsokanarsa ango na amarya." Ya rike hannunsa sosai Yana fad'in." Allah Ya sanya alheri ka ji ko, ka kula na so na samu zama da kai kafin d'aurin auran Allah bai nufa ba, yanzu gashi mun had'u na yi maka murna kwarai domin ka yi dace da yarinyar arziki ka kula da amana da kuma hakkinta Ubangiji Allah Ya taya ka riko." Ya dinga amsawa da Amin ya rabbi na gode ranka ya dad'e Allah ya saka muku da alheri Ubangiji Allah Ya biya bukatu." Ya amsa da Amin Ya Allah babu buk'atar godiya Malam Usaini ai kai dan'uwana ne?" Ya fad'a tare da kallona Yana cewa." Ko ba haka ba ne?" Na gyad'a kaina jikina a d'an sanyaye na ce." Tabbas." Usaini ya dube ni yana cewa." Anti za mu tafi sai mun yi waya Allah Ya saka da alheri." Na yun'kura na tashi a hankali itama ta tashi na rika hannunta ina fad'in." Na gode da ziyara Hajara a gaida gida ki kuma kula da shawarwarin da na baki." Ta ce." In sha Allahu rabbi anti." Suka juya wajan da yake tsaye yana murmushi shima suka yi masa sallama. Ya fara laluban aljihunsa ya fito da kudi yan dubu sabbi kar da su ba su dai da yawa ba su wuce dubu ashirin ba ya mi'kawa mata yana fad'in." Ga shi a sayi jan baki da hoda." Ta'ki kar'ba da sauri ta bi bayan mijinta sai ni na kar'bi kudin na bi bayansu da sauri. Koda na dawo cikin falon baya nan ya hau saman don haka sai na bi shi a daddafe na kΓ rasa hawa na same ya cire rigar jikinsa yana zaune da singeliti da dogon wando agogon hannunsa yake ko'karin cirewa. Ya zuba mini ido har na kΓ rasa kusa da shi na zauna ya furta." Hajiya Giwa manya." 'Dan juyar da kaina na yi a gajarce na furta." Ya hanya amma ba ka gaya mini kana tafe ba." Ya ce." Hakane tafiyar ta same ni bagatatan ai kin san Alhaji sammani ko mutumin nan da ya cutar da ni shekarun baya." Na ce." Na dai ji labarinsa. Ya ce." Mahaifiyarsa ce ta rasu kin san mutanan Dambatta ne kuma tare suke da Hajja kawaye ne tun lokacin k'uruciya ni da shi kuma abokai ne na unguwa an tashi tare har dai ya zama amintaccena a wancen lokacin kafin ha'inci da son zuciya ya shiga." Na ce." Allah sarki Ubangiji Allah Ya gafarta mata." Ya amsa da "Amin a takaice. D'akin ya d'auki shiru na d'an wani lokaci kafin ya dube ni ya ce." Ya yara na ina fatan suna lafiya." Ya fad'a idonsa kan cikina. Na ce." Suna nan kalau sun ce a gaisheka." Ya saki fuska kuwa yana cewa." Ina amsawa amma ai gaisuwar iri-iri ce ko?" Na yi shiru ban ce masa komai ba illa ido dana sanya masa ganin yadda ya kara haske fatar jikinsa ta yi kar har kumari ya yi a cikin wannan satikan da ban gan shi ba idan ba gizo idona yake yi mini ba, ban hangi wata kewa da damuwa a tare da shi ba ban sani ba ko wata ga'ba ya d'auka domin daina nuna mini so da rawar jiki. Jikina duk ya yi sanyi na kasa janye idona daga kansa iina Jin wani bala'in kishi a cikin raina sabon gida sabuwar soyayya tunda nake da shi ban ta'ba zama a gefansa bai ta'ba ni ba hannuwana suna shan mutsika idan ya rike haka zalika ya dinga sumbatar wuyana kenan yana shishshige mini yanzu da muka yi kusan sati biyu bamu ga juna ba babu wani abu na kewa da marari dana hanga a tattare da shi. Ya furta." Bari watsa ruwa ki ba ni abinci ko?" A takaice na ce." Ban yi girki ba." Na yi na yi na ha'kura kada na nuna jin haushin abinda yake yi na kasa jurewa. Ya ce." Ba ki yi girki ba kamar Yaya da me ki ka ciyar da ba'kin da ki ka yi?" Na ce." Na dare ne ban yi ba dama daga gidan Gwaggo Hamusu ke kawo mini towo ba kasafai nake girkin dare ba." Ya d'an yi jim yana kallona na wani lokaci kafin ya ce." Ko ni zan yi miki girkin ne Hajiyata." "Idan za ka yi zan ci." Ya ce." Zan yi kuwa yanzu jira ni na yi wanka." Ban ce masa uffan ba ya tashi ya nufi toilet na bi shi da kallon takaici da b'acin rai. Daidai lokacin da ya fito kira ya shiga wayarsa ya zo ya zauna da babban towel a jikinsa ya d'auki wayar sai da ya kalle ni kafin ya d'aga a sake ya amsa sallama. Sai kuma ya yi shiru na wani lokaci kafin ya ce." To Allah Ya sawwa'ke ki samu bacci sosai ciwon kan zai yi sau'ki maganar masu aikin nan kuma ki ajiyeta yanzu abinda za a yi shine zan yi magana da Hajja anan Dambatta ba za a rasa wadda za ta taimaka miki ba, da safe idan Allah ya kai mu zamu tattaunar maganar sosai, ki kula da kan ki, Allah Ya sawwa'ke." na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Shiru na d'an wani lokaci yana sauraranta kafin ya sauke ajiyar zuciya ya furta ." To babu damuwa sai na dawo." Daga haka sai ya kashe wayar ya ajiye saman dirowar gefan gado... Ya sake tashi dai ya je ya d'auko basiline ya zauna da shi a hannunsa yana fad'in." Hauwa ce bata jin dadi tana mura da ciwon kai na dai fi tunanin ciki ta samu itama haka take zargi." Ya fad'i maganar yana d'an kallona. A takaice na ce." Allah Ya sawwa'ke." Ya amsa daga haka sai d'akin ya d'auki shiru Ina kallonsa ya gama shafa basiline din ya shirya cikin jallabiya mai yankakken hannu ya dube ni yana fad'in." Wane aikin zan yi miki a kicin Hajiya." Da mamaki nake kallonsa ya gyad'a kansa yana cewa." Menene a ciki manzon rahama ma ya taimakawa iyalinsa ni kuma wanene ko dakan sakwara ki ka ce na yi miki a wannan dare na shirya ke ce fa." Murmushi na yi a hankali na girgiza kaina tare da cewa." A a ka huta kawai to wai ma ka iya girkin ne?" Ya furta." K'warai kuwa mu je kicin din naki ki ga yadda ake yi wani abin ma zan koya miki wanda ba ki iya ba." Na ce." Lallai naga alama amma mu je din indomi kacal za ka dafa mini." Ya ce." Ai ni ba ni cin indomi Amina da gaske kuma yunwa nake ji na d'auka zan samu abinci." Jin ya fadi haka sai na gazgata gaskiyarsa babban abinda ya tsana zuwa gidan abinci ya jima yana fad'in tozarta kai ne ga maigidancin da yake sayan abinci a waje. Na tashi tsaye da kyar ina fad'in." To me za ka ci sai na yi maka yanzu.'' Ya riko hannuna yana cewa." A a mu je dai kicin din tare sai mu yi aikin ko?" Na gyad'a kaina ban sake cewa komai ba muka sauka kasan tare yana yi mini labarin yara da yadda suke hira kullum da masu aiki su Baba Tabawa. Na gama gane so yake yi mu yi maganar komawata can amma ya'ki yarda ya fito kai tsaye ya fad'a sai kame-kame yake yi. Muka tsaya akan dafa jallof din taliya na kunna masa gas din ya d'auki tunkuya zai tari ruwa ni kuma na d'ebo kayan miya domin marka'dawa ya ciko tukunyar taf da ruwa ya d'ora kan gas din. Ina kallonsa ya rufe da murfi yana fad'in." Sai me za a yi?" Na ce." Da wannan kurmemen ruwan za a dafa rabin taliya? Ya ce." Ya yi yawa ne?" "Sosai kuwa kuma mai ake fara soyayya tukkuna a zuba kayan miya a soya tunda za mu yi amfani da busashen kifi idan mun gyara shi mun wanke sai mu zuba mu d'an soya tare da kayan miya nan sannan mu tsayar da ruwan sanwa." Ya sauke tukunuwar tare da zubar da ruwan da ya mayar da ita kan gas din ya d'auki mai ya tsiya mai mugun yawa don wanda ya zuba zai yi gwangwani biyu ko fiye da haka." Na ce." Kenan da mai za mu tsayar da ruwan taliyar ko soyayyiya za mu yi ne Allah Ya taimake ka." Ya ce." Ana yin soyayyiya ne dama?" Ina dariya na ce." E, amma ba ita za mu yi yanzu ba kuma mangyad'ar da ka zuba ya yi yawa. Gabagad'i kuwa ya kai hannunsa zai sauke tukunyar da ta d'auki zafi man yana suyuwa. Ya cire a zabure ya matsa har sai da murfin tukunyar ya fadi kasan k'afafunsa. Ya rikice sosai yana duba yatsunsa. Dariya kamar cikina zai yi ciwo na kashe gas din na jingina jikin wardrobe Ina kallonsa ina dariya sai zare ido yake yi. Ya nuna mini yatsun yana fad'in sun toye Amina kin ga yadda suka yi jaaa ashe haka abin yake dama?" Na ce." To kai wanene ya ce ka kama tukunya haka kawai, kuma ka ce ka iya girki ashe baka iya ba." Ya ce." Idan hakane bayin Allah nan suna aiki Amina wanene yasan iya adadin yadda suka 'kone garin sauke tukunya." Na d'an 'bata rai cikin shagwaba na ce." Su kadai kenan, ni ma ai ina yi maka girki." Ya rikice kuwa ganin yanayin yadda na yi masa magana a sangarce da shagwaba ya matso ni yana cewa." Har dake mana kuna kokari gaskiya Allah Ya saka da alheri." Na amsa da Amin a takaice tare da d'an zame jikina ina cewa." To zo ka ga yadda ake yi ko don gaba. Ya kuwa taho ya tsaya a bayana yana murmushi na fara gudanar da aikin cikin nutsuwa yana yaba mini har da addu'a da tukwici sumba a wuya da kumatu a haka na yi masa jallof din taliya da dankali da kuma bushshen kifi ya ce a yi masa da manja ta yi kyau sosai tana k'amshi mai dad'i. Kusan tare muka ci amma dai shine karfin cin kuma yadda ya zage ya ci da yawa ya tabbatar mini da cewa yunwa ce mai yawa a tare da shi. Ban zaci zai iya d'auke kansa daga kaina ba a daran salin alin muka kwana bai nemi yin wata mu'amula da ni ba. Sai washe gari da rana gatse-gatse ya fara kame-kame da ya ga na'ki nuna na gane abinda yake nufi ya kamo ni wai na yi masa dabaru ta yadda zai gamsu yana tsoron ya kusance ni a haka na yi nauyi a cewarsa tausayina yake ji. Ya fad'i hakane kawai don ya kare kansa amma shi kansa ya san babu wata dubara da take kwantar masa da buk'atarsa face sai wannan abin ya faru. ban ma yi nisa wajan yin dabarun ba ya fice daga hayyacinsa maganar tausayi kuma sai ta kau ya fara ko'karin ganin ya samu hanyar zai mutunta kansa sai da na dinga ankarar da shi halin da nake ciki tukkuna a haka lamarin ya faru kamar wani sabon tuburarran mara hankali......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* *ZA MU KAMMALA A CIKIN SATIN SALLAH IN SHA ALLAHU* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *158* Haka muka kasance cikin kula da juna mussaman daga b'angaransa wata sabuwar kulawa na dinga samu a wurinsa bini bini sai ya ce tausayina yake ji amma hakan ba ya hana shi da daddare ko kuma dai duk lokacin da lambarin ya bijiro masa ya kwanta da ni, a wannan gefen sai ya manta da tausayi girki kuwa bai sake cewa zai yi ba dalili ya ji babu sugar domin yatsunsa da ya kama tukunya sai da suka ruruce suka ja ruwa. Sai dai duk lokacin da zan shiga kicin zai bi bayana ina aiki yana damuna da runguma da ta'be-ta'be lamarin nasa dai kamar na sabon ango ko kuma wanda ya koyo wani sabon darasi ai soyayya ya iya babu karya kamar sabuwar balaga ba dattijo mai yawan shekaru ba. Ranar sadakar uku ya ce na shirya mu je ya kai ni gaisuwa. Na shirya kamar yadda ya buk'ata din muka nufi dambatta a mota Ade direbansa ya ja mu. A gidan rasuwar na samu Hajja tare da jama'a tunda shi daga waje ya tsaya sai daga baya tukkuna ya shigo gidan. Hajja ta dinga nuna ni ga jama'arta wasu sun san fuskata wasu kuma ba su san ni ba dama fadi take itace uwargidan nasa ai Amina sunanta, itace wadda aka dauro auransu a saudiya. Sai na zama abin kallo na dinga jin nauyi da kunya domin na kasa tantance kallon da yawancin jama'ar wajen ke yi mini. Da la'asar muka fito daga gidan a kafa muka taka zuwa gidan Hajjan tunda babu nisa. Ta sanya Iyami mai aikinta yi mini towon shinkafa miyar zogale domin dai ko kad'an na kasa cin abincin da aka ajiye mini a gidan rasuwar dafadukan shinkafa ce amma sun yi amfani da wani irin curry ya yi rabad'au dashi 'kamshin babu dad'i. Wajan biyar iyami ta gama aiki ta kawo mini sannan Hajja ta ce ta zuba mini wani a fulas sai mu tafi dashi na huta girki. Na kuwa ji dadin hakan sosai. Sai da na yi sallar magriba tukkuna ta fito daga cikin dakinta da turaman atamfofi guda uku manya ta miko mini tana fad'in.'' Kada na manta kar'bi wannan Amina bari na nemo leda." Ya juya da sauri ta koma d'akin ta bar ni ina juya atamfofin tsala-tsala masu tsada. Ta dawo da leda viva mai zurfi tana fad'in wannan ai zata d'auke kayan ko?" Na kar'ba Ina fad'in." Eh za ta isa." Ta zauna saman kujera tana cewa." A kar'ba da hakuri ban samu zuwa biki ba amma wannan a bawa amarya Hajara idan na sanya rana Yusi zai kai ni gidan na yini in sha Allahu." Na sa dariya ina fad'in." Kai Hajja an yi abu ya wuce fa don Allah da kin bar atamfofinki ki dinka abinki." Ta girgiza kanta tana murmushi ta ce." A a dama na yi niyya Amina sai ki sanya Ayuba direbanki ya kai mata ko kuma angonta ya zo ya kar'ba a ce babu yawa kuma ina yi musu fatan alheri." Na ce." To shikkenan Hajja Allah Ya saka da alheri ya kara girma Ubangiji Allah Ya sa a fi haka, mun gode sosai." Ta amsa da kulawa tana kallona kafin ta ce." Ya gaya miki Kamalu zai tafi karatu can Madina ko?" Eh ya gaya mini." Na fadi haka duk da har yanzu bai ce mini komai ba. Sai ta gyada kanta tana cewa." Ki kara yi wa yaron nan addu'a akwai alamun haske a cikin al'amarinsa in sha Allahu za a amfana dashi." Na furta." In sha Allahu rabbi Hajja na gode Allah Ya saka da alheri." Ta yi murmushi ba ta ce komai a daidai lokacin ne kuma ya shigo yana waya ya tsaya tsakiyar falon duk muna kallonsa har sai da ya kammala tukkuna. Ya dube ta yana fad'in." Hauwa ce ta kira waya wai Sultan baya jin dad'i." Hajja ta ce." Ashsha me yake damunsa?'' Ya gyada kansa da Yar damuwa ya ce." Ciwon ciki abinda dai tace kenan ya kwana biyu bai yi bayan gida ba yana ta kuka uwar rainon nasa ce ta je tana gaya mata halin da yaron yake ciki amma ya sha magani a cewarta." Hajja ta ce." Wata'kila wani abin ya ci ya dam'ke masa ciki sai an kula da abinda za a dinga ba shi ya ci mussaman abinda ya danganci madara da fulawa." Ya furta." Sauyi ne kawai tunda yaron ya fara cin abinci bai ta'ba irin wannan ba ko ba haka ba ne?" Ya fad'a yana kallona na ce." Sosai kuwa kuma Baba Tabawa na kula kwarai da gaske da abincin da zai ci, tana kokari a kansa gaskiya. Ta ce." To shikkenan Allah Ya sawwa'ke ai tunda ya sha magani da sauki cikin zai saki zuwa dare sai ka kira waya ka tambayi jikin nasa." Ya ce." Hakan za a yi in sha Allahu, ni ma ai ina tunanin jibi zan koma." Ta gyad'a kanta tana cewa to babu lefi ai tunda an yi uku sai kowa ya koma bakin aikinsa." Ya dube ni cikin kulawa yana fad'in." Tashi mu tafi." Na tashi da bismillah tana fad'in." Sannu ai gwara ki zauna nan din Amina ki haihu ni kaina hankali zai fi kwanciya." Da sauri ya ce." Ai ba sabuwar haihuwa ba ce Hajja." Ta ce." In ji wa? au! haihuwa dama akwai sabuwa da tsohuwa ina ce idan ta yi nisa ne ma ake jin jiki, ko makaho ne ya dubi yarinyar nan ya san tana cikin ibada." Ya yi shiru bai ce komai ba amma gabad'aya jikinsa ya yi sanyi a haka muka yi sallama ta rako ni har farfajiyar gidan lokacin shi tuni ya shige mota. Ade ya bude mini kusa da shi na zauna da ledar atamfofin Hajara da madaidaicin fulas din towona. Ina zama a gefansa ya kar'bi ledar ya ajiye kasan k'afafunsa saboda kayan sun yi mini yawa a hannu Ade ya shiga mazauninsa muka d'auki hanya. Har muka isa gida bai yi magana ba. Ya rage walwala da nishadi ya yi shiru abinsa tabbacin akwai abinda yake damunsa. Na daure na fara tambayarsa ko ba ya jin dadi ne ya ce dani 'kalau yake gajiya ce kawai. Ko da na yi masa tayin towon ma kafin mu kwanta ya ce a a shayi kadai zai sha shima cikinsa ya b'aci. Na kyale shi kawai na zauna na ci towona na koshi na sauka da kayan na dawo na same shi yana waya da Hauwa jikin yaron yake tambayarta ga yanayin fuskarsa amsar da ta ba shi ba mai dadi ba ce. Raina ya ba ci sosai wai shin ya ma aka yi Hauwa ta san yaron ba shi da lafiya ne abinda ba tare suke ba, ba fa da gaske ba ne karya take yi ta mayar da shi shashasha tana daga masa hankali saboda ta gane lagonsa akan yara yake yau tace wannan gobe tace wancen kwanaki ta bugo waya tace bata da lafiya yau kuma ta kirkiri ciwo ta d'orawa yaro wane irin jahilci ne wannan. Ta gama gane damuwarsa akan yara shiyasa take amfani da wannan dama. Gashi muna cikin farinciki da soyayya da kulawa lallai sai ta rusa hakan ta kira shi ya dawo wajenta shine hankalina zai kwanta. Na bude baki ina fad'in." Idan ba ka farga da wuri ba wallahi Hauwa daf take da ta mayar da kai sakarai ko ma nace ta mayar da kai tuntuni shashasha take kallonka." Ya dube ni da b'acin rai yana cewa." Wace irin magana ce wannan Amina ana 'karyar ciwo ne?" Na ce." Tunda ba ta da hankali ita don ta yi hakan ai ba abin mamaki ba ne, watarana za ta iya kiran ka ta ce wane ya mutu tunda jahila ce." Ya yi sakato yana kallona ni ma ina kallonsa na ce." So take yi ka koma gare ta domin ku cigaba da cin amarci a sabon gida, na gaya maka Hauwa ba za ta ta'ba canzawa ba kuma ba zata zauna da ni tsakani da Allah ba sai ta yi mini bita da 'kulli a rayuwata me na tsare mata." Ya yi shiru kawai yana kallona na cigaba da cewa."Ka yarda ko kada ka yarda Hauwa 'karya take yi Sultan lafiyarsa lau." Ya ce." Na ji, ke yanzu abinda ki ka yanke a ganinki daidai ne na gaji da wannan abin da ki ke yi mini ni nake auranki ko ke ki ke aurana?" Da mamaki a tare da ni na ce." Me kuma na yi maka yanzu, gaskiya na gaya maka na ce ka farka ka kuma yi aiki da tunani akan abinda matarka take yi." Ya ce." Ni ba wannan ne damuwata ba so ki ke na kwanta ki taka ni shine karshen so da kulawa da tarairaya me zan yi miki kuma abinda ya rage kenan." Sai kawai ya kwanta ruf da ciki ya mike sosai yana fad'in." Ta shi ki hau ki bi ta kaina kawai Amina, hakan zai kara tabbatar miki da cewa kin gama da ni, sai abinda ki ka gindaya mini." Dariya ta kama ni amma na danne ban yi ba sai na kasa gane dalilin wannan rikicin da ya bijiro da shi a yanzu ban sani ba ko maganar da mahaifiyarsa ta yi a d'azu ce ta 'kara fusata shi shine ya sar'kafe maganar ya had'ota da wata a ganinsa kenan na mallake shi juya shi nake yi." Na sassauta sosai tare da cewa." Ni dai don Allah ka tashi kada ka sanya mala'iku su tsine mini me ya yi zafi zaka kwanta kace sai na taka ka." Ya ce." Kin san Allah ba zan tashi ba Amina sai kin bi ta kaina kin wuce hakan zai kara tabbatar miki da cewa kin gama da ni, haba don Allah na gaji wallahi rayuwarki kawai ki ka sani ni ko oho, ki tashi kawai ki yi yadda na umarce ki." Na yi kasa'ke ina kallonsa har yanzu yana kwance ruf da ciki. Na ce." To ai kamata ya yi ka gaya mini abinda na yi maka sai na baka ha'kuri ba wai ka kwanta ka ce na taka ba, akan wane dalili." Yana daga kwancen ya ce." Sai na gaya miki ga abinda ki ka yi ke din yarinya ce, ai duk abubuwan da ki ka jima kina aikata mini kin sani, tunda ba k'ank'anuwa ba ce." Na yi shiru kawai ina kallonsa saboda bakina ya mutu ma gabad'aya ya juyo da fuskarsa yana kallona har yanzu babu wasa a tare da shi ya ce." Ba za ki tashi ki taka ni ba." Na girgiza kaina a tsanake na ce."Babu halin hakan me yasa zan taka ka Allah kada ya nuna mini wannan rana." Na kudi ne wannan littafin kada ki karanta ba tare dΓ  kin biya ni hakkina ba. Ya gyad'a kansa tare da tashi zaune yana fitar da numfashi sama-sama ya jima a haka kafin ya tashi ya shiga bandaki na bi shi da kallo ina girgiza kaina ya fito d'aure da alwala ya hau dadduma. Haka muka kwana ko hannuna bai ri'ke ba. Da safe na gaishe ya amsa a dakile ya koma ya kwanta bacci ya yi sosai sai wajan sha biyu ya sakko kasa. Lokacin na gama had'a kayan sanyawata dana ware domin aikawa da Fati na fito da akwatin kayan domin kiran Ayuba na same shi zaune shi kad'ai ya kunna tibi abinda ba dabi'arsa ba. Ya dube ni muka kalli juna kafin ya ce." Wannan akwatin ta mecece Amina?" Na ce." Ayuba zan aika gidan 'kanwata Fati." Ya yi shiru bai ce komai ba yana kallona na ajiye akwatin na bud'e kofa na fita domin kiransa. Sai da na shigo tukkuna ya biyo bayana na ce masa ya d'auki akwatin ya kai mata sannan na ya gaya mata zan kira ta a waya zuwa dare. Bayan fitarsa na je na zauna kusa da ni bai kalle ni ba da romot a hannunsa yana duba tashar da zai k'alla. Na matsa kusa da shi a hankali na ri'ke hannunsa ya dube ni babu yabo babu fallasa ya mayar da hankalinsa kan tibin. Bakina nasa a kunnensa cikin k'aramin sauti na ce." Babyn love." Ya yi shiru bai ce komai ba. Na zura yatsa a kunnansa ina fad'in. " Ko ka zama kurma ne Allah Ya ja zamaninka my heart." Ya dube ni yana lumshe idonsa a kasalance ya ce." Menene?" Na ce." Kai ne my love dina" "Humm!" kawai ya iya cewa kafin ya janye idonsa daga kaina ya cigaba da daddana romot. Nasa hannuna a cikinsa ina fad'in." Yunwa kake ji fa, tun jiya baka ci komai ba ina sane gaskiya rayuwata tana cikin had'ari." Ya dai yi shiru bai tanka mini ba, sai ma ya fara muzurai yana d'an 'bata fuska. Na dake sosai ina fad'in." Bari na yi maka abinci ko, wane iri ka ke so na yi maka? umm ka fad'i kalar da kake so zan shirya maka yanzu." Ya yi gyaran murya bai kalle ni ba ya ce." Tafiya zan yi gobe idan Allah Ya kaimu." Na ce." Na shirya kenan mu tafi tare ko?" Ya kalle ni da sauri fuskarsa ta d'an sassauta. Sai kuma ya d'auke kansa yana cewa." Duk yadda ki ka gani Amina?" Na ce." Farincinka shine nawa Habibi za mu tafi tare in sha Allahu." Ya gyada kansa amma bai ce komai ba. Na ce." Me zan yi maka fannin abinci." Ya ce." Ki yi duk abinda ranki yake so zan ci." Na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." To shikkenan in sha Allahu." Kicin din na tashi na nufa na fara aikin cikin nutsuwa mintinta ashirin a tsakani ya biyo ni lokacin ina yanka albasa ya furta. "Kawo na taya ki ko." Kai na girgiza tare da cewa." Ka huta kawai ba ni so ka yanke hannunka ni zan yi komai na samu lada." Ya tsaya daf da ni a hankali na ji yana cewa." Wane suna ne na ji kin kira ni dashi da zu." Yafad'a yayin da ya d'ora hannunsa saman kirjina. Na d'an janye kad'an kafin na ce." Suna wane iri Allah Ya taimaki rayuwarka." Ya girgiza kansa yana cewa." Babyn love da dad'i sunan. Me yasa tuntuni ba ki kira na da shi." Na ce." Ka manta dai Ina kiran ka dashi mana a wani yanayi." Ya yi shiru yana kallona har ina jin saukar ajiyar zuciyarsa. Ya ce." Na tuna a yanayin nan da ni dake muke ganin tamkar mu kadai Allah ya hallita a duniya ko." Na gyad'a kaina ina murmushi na ce." E, amma idan kana so a cigaba da kiran ka da sunan sai a cigaba." Ya ce." A a ki cigaba da kira na dashi a yanayin nan na mussaman ni tsoho ne idan yarana suka ji ana ce mini baby dariya za su yi." Murmushi na yi ina fad'in." To haka za a yi kuwa." A haka na gama shirya abincin muna hira da kalaman soyayya. A daran Usaini ya zo ya kar'bi sa'kon matarsa na wurin Hajja. Sannan na ce masa zan je gidan Gwaggo ya ce na shirya mu je tare shima zai gaisheta. Allah sarki Gwaggo ta ji dadin ganinmu bakinta kamar gonar audiga ta samu alheri na kudi a wajensa tana ta yi masa godiya har sai da ya gaji ya hana ta ya ce don Allah ta daina yi masa godiya akan yana rik'on yaran da addini ya bashi damar zame musu uba. Koyaushe idan magana ta tashi zai ce haifarsu ne kawai bai yi ba amma tunda yana aurena ubansu ne kuma addini ya mallaka masa. *** Yadda na samu Sultan cikin walwala da wani irin kuzari da lafiya ya tabbatar da mini da cewa hasashena akan Hauwa gaskiya ne. Shi kansa uban dana d'auki yaron mussaman na kai masa shi d'akinsa ya d'aga shi sosai yana duba shi fadi yake yi ya k'ara nauyi sosai Amina kin ga dai duka sati daya rabona da shi amma ya yi mini girma a ido ashe Hauwa bata da hankali dama." Shiru kawai na yi ban ce masa komai ba zuwa yanzu ai ya kamata ace ya gane halin matarsa muguwar ma'karyaciya ce mara son zaman lafiya. Kwanana biyu da dawowa yara sun yi doki da murna haka zalika ma masu aiki aka kewaye ni ana ta farinciki na dawo na zama kamar ba'kuwa har Baban nasu ya dinga kishi yana jin haushi wai shi ba su damu da shi ba. Yadda ya hak'ikance yana fad'a abin ya yi ta ba ni da dariya. Da daddare Salim da Adam suka shigo mun jima tare da su a falo muna hira nan Salim yake gaya mini ai yana da lambar wayar Kamalu har ya kira shi ma ya taya shi murna tafiya karatun da zai yi. Ikon Allah kenan gabad'aya yaran sun samu wata iriyar nutsuwa mussaman shi Salim din da ya canza ko maganarsa ma cikin nutsuwa kuma duk wadda zai furta mai muhimmanci ce. Lallai Allah yana kishin bayinsa ya sanya musu nutsuwa da tawakalli babu uwa babu uba, haka zalika babu 'yan uwan uwa nagartattu. Dangin Babansu ne kawai masu nagarta sai Kuma uban rikonsu a yanzu wanda ya zame musu bango. A wannan ga'bar shi kansa maigidan na sara masa domin ya yi namijin kokari kwarai da gaske duk abinda uwarsu ta yi masa na illatarwa ya ture ya rungumi yaran abokinsa domin cikashe wasiyyar da ya bar masa. Hakika ya zama uban marayu ni ce sheda tunda ni ma ga nawa nan ya runguma har yana b'acin rai idan an yi masa godiya bisa abinda yake yi musu. Sati daya da dawowata komai ya daidaita a gidan mun samu nutsuwa da kwanciyar hankali tun daga kan maigayya da aiki yaran dai kaf muna tare da masu aiki muna cikin nutsuwa da walwala ba ni da damuwar komai tunda ba ni ganin gilmawarta balle ta takale ni ko ta gaya mini banzar maganarta. Ya je ya yi mata kwana biyu ya zo ya yi mini kwana biyuna haka muke yi babu canji kuma shima yana ta ko'karin ganin ya yi adalci domin dai ya nemi zaman lafiya kuma ya samu ta sashena domin ba ni da niyyar d'aga masa hankali akan komai tunda ba ni nake auranta ba abinda yake gabana a yanzu rabuwa da abinda yake cikina lafiya. Ranar wata lahadi girkinta ne tunda gari ya waye bai shigo ba. Hakan sai ya d'an dame ni tunda bai saba da yin hakan ba yana shigo mana ya jima tare da mu a yi hira haka zalika ma ranar girkina yana zuwa gidanta ya d'auki wani lokaci kafin ya shigo mana. Na fara nemansa a waya gashi dai tana shiga amma sai a katse na kira ya fi sau shida idan ta shiga sai a katse. Ga yara tun safe sun tafi tahafiz sai yamma balle na tura Khalil gidan. Bai kira waya ba kuma bai shigo ba abin dai da mamaki. Wayarsa kuma na kira ana kashe mini. Ban zarge shi kai tsaye ba sai dai zuciyata ta shiga wasi-wasi akan hakan. Gefin magriba ya kira ni na daga da sauri na ji muryarsa a dashe don da 'kyar ma yake magana yana yi tari na sar'kafe shi yake gaya mini baya jin dadin ya tashi da mura da zazza'bi har da tari. Har da ba ni ha'kuri bai shigo ba kuma bai kira ni ba." Gabad'aya jikina ya mutu na dinga yi masa sannu. Tabbas bai iya mura ba tunda ta ta'ba kama shi a gidana farko-farkon auranmu na yi jinyarsa. Na ce masa idan an jima za mu shigo tare da yaran gabad'aya mu duba ka Allah Ya sawwa'ke." Ya amsa da Amin muka yi sallama. Na zauna cikin damuwa da mamaki. Hauwa ce kenan ta dinga kashe mini waya a maimakon ta d'aga mu yi magana take ganin k'yashin yin hakan. Humm! shine yake ganin za mu zauna lafiya da ita har yanzu bai san wacece matarsa ba Gabad'aya lamarinta ni yanzu tsoro yake ba ni wallahi da jefa ni cikin fargaba. Ba ni da nufin zalintarta ko cutar da ita shiyasa ma muddin nasan ranar girkinta ne ko ya shigo wajena ba ni sakin jikina da shi balle tsautsayi ya sanya mu shiga hakkinta.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124.... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *159* Bayan isha'i na fito cikin hijabina har k'asa kai tsaye d'akinsu Baba Tabawa na nufa, ita da Taburni suna zaune cikin fahimtar juna suna hira Sultan na tsakiyarsu da abin wasansa yana ta wasa gefe guda kuma flat ne da abinci a ciki da alama nasa ne za ta bashi wasa ya d'auke masa hankali Gaisawa muka sake yi kafin na ce." Sultan za a ba ni aro za mu je gabad'aya domin duba Babansu ne ba shi da lafiya yana ta fama da mura da zazza'bi." Baba Tabawa ta ce." Subahanallahi ashe ba shi da lafiya dama?" Na ce." Yau dai ya tashi da ciwon shiyasa ai bai shigo mun gaisa ba." Taburni cikin mutuwar jiki ta furta." Tabbas kuwa, don Allah a yi masa sannu da jiki Hajiya Allah Ya sawwa'ke." Na amsa da Amin zan gaya masa in sha Allahu." Muka fito daga d'akin tare da Baba tana ri'ke da yaron tana fad'in." Hajiya Amina ko dai mu je tare ne ya yi miki nauyi ga yanayin jikin naki kema Allah dai ya budi ido lafiya." Na ce." Bari Khalil ya fito ya d'auke shi ai na ce miki tare duk za mu je da yaran." Ta ce." To hakan ya yi. Muna tsaye yaran suka fito tare da Mairo dama kafin na shiga sallah na sanar da su. Kowacce da hijabi a wuyanta. Khalil ya fito shima na ce ya d'auki yaron. Suka yi gaba gabad'aya na bi bayansu. Muna fita farfajiyar gidan masu hidima da gidan suka fara rige-rigen gaishe ni, ina ta amsawa da kulawa, tunda babu lefi tsakaninmu da su akwai mutunta juna sosai. Masa'udu da yake akwai sabo a tsakanin da yaran dalili shine yake jigalar kai su makaranta yana ta tsokanar Usaina itace mai tsotsar hannu tana hararsa tana fad'in." Na daina kai ne kake yi ai kai ka koya mini. Ta k'aramar k'ofa muka fita gabad'aya can muka hangi mota za ta shiga gidan Momi Hajiya Maryam kenan duk da ban gane wanda yake ciki ba amma ganin motar ta tsaya ya sanya ni ma na tsaya. Adam ya fito daga cikin motar ya karaso har wajan da nake tsaye yana dariya yake ce wa." Mama ina yini, ina za ku je haka da daddare, da yaran duka?" Ni ma cikin murmushi da kulawa na ce." Za mu duba babanku ne baya jin dad'i." Yanayinsa gabad'aya ya canza ya furta." Ai ba mu sani ba wallahi me yake damunsa?" Ya fad'i maganar a rikice da damuwa a fuskarsa. Cikin nutsuwa na ce." Mura ce da zazza'bi ka kwantar da hankalinka Adam ba a kwance yake ba." Ya gyad'a kansa yana fad'in." Mama mura ai ciwo ne mai tsanani tunda har Annabi Muhammadu s.a.w ya yi magana akanta bari na yi magana da anti Nabila tana cikin mota na je daukota daga airport ne sai na zo mu je tare na duba shi." Na gyad'a kaina ban ce komai ba shi kuma ya juya a gaggauce ya nufi inda motarsa take. Mamaki nake yi ashe har yanzu Nabila na gidan tare da su. Ko da yake hakan ma ya yi daidai tunda har suka aminta da zamanta wata'kila ta fi sauran 'yan uwan maman nasu gaskiya da kuma k'aunarsu tsakani da Allah duk dai ba a tona zuciyarta an gani ba A amma dai tsayin wata kusan takwas da rasuwar Maryam take zaune tare da su ban ta'ba jin wani k'orafi ba nasam idan da akwai matsala to tabbas Nusaiba za ta gaya mini." Ga mamakina sai na ga sun fito daga motar tare da ita. Duk da dare ne amma akwai haske manyan fitilu mabambamta a estate din ta hasken nake hangenta tun daga nesa a yayin da suka jero da tare da Adam din ta ci wata uwar kwalliya cikin wani lece wanda aka yi masa d'inki riga da siket matsatstsu ta k'ara ki'ba ta cika ta ko'ina d'inkin da yake jikinta ya gama bayyana hallitun jikinta tunda ba ta yi amfani da babban mayafi ba da takalmi mai tudu a kafarta wanda yake hade da wata madaidaiciyar jaka mai adon duwatsu masu kyalli. Kana dai ganinta ka ga manyan zawarawan da suka ci suka kuma tayar da kai zawarawa irin na Abuja masu kafacity amma yanayin dressing dinta ya gama bayyana cewa ba ta da mafad'i domin kuwa da da akwai shi ina ganin hakan ba zata faru ba. Irinsu na nan da yawa da suke 'batawa zawarawan da suke gefe a killace domin kare kansu. Na janye idona a daidai lokacin da suka 'karaso wajan da muke tsaye da yaran. Cikin sakin fuska da kulawa ta furta." Hajiya Amina mun yini lafiya ya yaran duka yanzu Adam ke gaya mini Yallabai babu lafiya wallahi ni ma dawowata kenan gida sati na biyu a dubai." Na ce." Lafiyarmu lau alhamdulillahi ya su Hanif wallahi kuwa amma da sauki ai ba akwance yake ba mura ce da zazza'bi ke damunsa. Da yanayi na alhini irin na al'ada ta furta." Mu je ni ma sai na duba shi, Ubangiji Allah Ya kara sau'ki." Na ce." Amin Ya Allah." Kusan tare muka jera tafiyar ni da ita. Adam ya bi yaran suka yi gaba tunda sune suka san gidan ina jinsa shima yana tsokanar Usai akan dai tsotsar hannu tana ta zum'bura ba'ki idan ya riko hannunta ta fizge ta koma gefe. Nabila sai dariya take yi tana fad'in. Usai iya rigima kenan ashe ba ta daina tsotsar hannun nan ba." Murmushi na yi wanda babu nisha'di a cikinsa na ce." Tukkuna dai zata daina idan girma ya zo da sauki ma a hakan ai ta rage. Gidan bai kai wanda nake ciki girma da tsaruwa ba. Amma dai daidai gwargwado an narka masa dukiya shima tun daga wajensa zuwa cikinsa komai na iko ne falon ya tsaru da sabbin kayan more rayuwa kamar dai yadda na gani a hoton da ya d'ora. Suna zaune shi da ita a falon tana gefansa a zaune ta yi gayu sosai cikin shadda da surfani an yi d'auri mai hawa-hawa sannan an sha yari da sarka da abin hannu. Da yake shadda ce sai ta kara mata kumburi da kwarjini ramar ta 'buya. Yana cikin jallabiya da Loptop dinsa a gabansa gefe guda kuma fulas din shayi ne a ajiye da karamin cup a kusa da shi. Muka shiga tare gabad'ayanmu. Ta yi wani bala'in shan kunu ta amsa sallamar sai kuma ta yi kasa da kanta. Shi kam rufe computer ya yi ba shiri saboda yaran gabad'aya kaf wurinsa suka nufa. "Baba sannu, Baba ina yini baba ya jikin naka?" Abinda suke ta fad'i kenan Minal har tana ta'ba wuyansa tana cewa." Zazza'bin ma ya sauka ko?" Tana kallon fuskarsa Yana dariya ya ce."DIN bai sauka ba tunda kun zo zai gudu garinsu. Hassana ta ta'ba wuyansa a karo na biyu kamar yadda Minal din ta yi ta ce." Babu zafi jikin naka Baba Allah Ya ba ka sau'ki." Ya amsa da Amin yana ri'ke hannunta, ita kuma Usaina fad'i take yi Baba maganarka wani iri kasha tomtom kaji baba!" Na ce." Wai ba za ku samu nutsuwa ba ne haka ake duba mara lafiya?" Suka nutsu tare da samun waje suka zauna. Khalil ya nufe shi da Sultan a hannunsa yana fad'in." Baba barka da dare ya jikinka?" Ya amsa yana cewa." Na ji sau'ki Babana." Ya mika hannunsa ya kar'bi Sultan da yake ta wangale masa baki yana dariya da gwalantun kiran sunansa. Khalil din ne ya fara gaisheta a hakimce ta amsa tana wani fizge kanta. Daga nan kuma yaran suka shiga gaisheta ganin yadda yayansu ya yi ta amsa tana ta'be baki. Maganar Nabila ta katse nazarin da nake na ji tana ce wa." Allah Ya taimake ka an yini." Ya dube ta babu yabo babu fallasa ya amsa da lafiya a takaice ya ce." Yau ki ka dawo ne?" Ta furta." Eh wallahi dawowata kenan Adam ya d'auko ni a airport." Ya yi shiru bai ce komai ba Adam ya shigo dama a waje muka bar shi lokacin da za mu shiga an kira shi a waya. A nutse ya kΓ rasa gabansa ya durkusa har kasa yana gaishe shi ya dafa kansa yana amsawa da kulawa ya ce." Mama na gani da yaran gabad'aya ashe ba ka ji dad'i ba Ubangiji Allah Ya kara afuwa." Ya furta." Na ji sau'ki ai tunda na sha magunguΓ±a sai dai rashin karfin jiki kuma na gode sosai Allah Ya yi muku albarka." Ya amsa da "Amin. Ita ta fara tashi tana d'an duban Hauwa ta ce." Madam ina yini ba mu gaisa ba." Shiru ta yi ba ta amsa ba. Sai ma ta d'auki wayarta tana dubawa. Adam ya dinga fad'in." Ina yini tana jinsa sarai sai daga can kuma ta amsa ba tare da ta dago kanta ba. Nabilan ta yi gaba da zummar fita kafin Adam d'in ya bi bayanta. Falon ya rage mu kad'ai Hauwa dai ko nahiyar da nake bata kalla ba balle na samu arzikin gaisuwa abin ya ba ni dariya sosai wai ita matar gida tunda ni na zo a ganinta ni zan gaisheta. A marairaice na ce." Ya jikin naka?" Ya tsira mini ido cikin wani yanayi kafin." Ya furta." Ba zan ce miki komai ba giwa, wato idan zan rasu baki damu da ni ba ko?" Ajiyar zuciya na sauke a hankali cikin 'yar shgawaba na ce." Ka duba wayarka ka ga iya adadin kiran da na yi maka gabad'aya ni da yara yini muka yi da damuwa ba ka shigo ba kuma ba ka ce za ka yi tafiya wani waje ba. Ya lalubi wayarsa yana cewa." Wajen da ba k'asa nan ake gardamar kokawa bari na duba." Ya shiga duba wayar yana fad'in." Ban ga kiran ki ba kin kare kan ki ne kawai." Ya miko mini wayar yana cewa." Duba ki ga ni." Girgiza kaina na yi a nutse na ce." A a ba sai na duba ba, amma fa babu buk'atar rantsuwa na kira ka ya kai sau bakwai da ta shiga sai a katse kiran babu matsalar network my love katse mini kiran aka dinga yi." Ya furta." Ya ban ga alama ba." Kai tsaye na ce." Wata'kila kai ne ka goge?" Ya dube ta tana zaune tana jin mu da wayarta a hannu kanzil ba ta ce ba. Ya girgiza kansa tare da ajiye wayarsa a gefansa. Shiru bai yi wata magana ba sai hayaniyar yaran Sultan tuni ya sauka daga cinyarsa ya shiga cikin 'yan uwansa. Ya dube ni muka had'a ido sai kuma ya dube ta tana zaune gim ya d'aure dai ya furta." Gaba kuke yi ne da junanku?" Kallonsa ta yi kafin ta ce.'' Ba dabi'ata ba ce amma tsakani da Allah Amina ba gidana ta zo ba, me ya sa take yi mini wani irin kallo, ni da naje gidanta haka na yi mata a gabanka fa na gaisheta ta yaya kake ganin za mu zauna lafiya da juna bayan duk abinda ta yi daidai ne a wajenka baka nuna mata kuskuranta." Ya d'aga mata hannu yana cewa." Ya isa ban ce ki gaya mini magana ba, duba da kyau akwai yara ba ni son rashin hankali." Ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba. Ya yi 'kwafa kafin ya cigaba da ce wa." Kin had'e fuskarki tamau! kina amsa gaisuwa da k'yar a matsayinki na wadda aka zo gidanki hakan shine daidai ko kina tunanin ban ga irin wulakancin da ki ka yi wa yaron nan Adamu ba." Ta dai yi shiru ba ta tanka ba. Na daure zuciyata ina fad'in." Hauwa aka ce shimfidar fuska tafi ta tabarma tunda na zauna ban ga kin yi mini duban mutunci ba to me zai sanya ni shiga sabgarki, magana akan katse mini waya kin san dai babu yaro a cikinmu ko, menene amfanin abinda ki ka yi, ko ni ina hana shi amsa wayarki ne?" Ya daga mini hannu yana fad'in." Na ce ya isa haka ko, kada wadda na sake jin ta yi magana." Ban sake cewa komai ba naja bakina na yi shiru itama ta yi shiru cikin kunyar abinda ta aikata tunda ta fahimci ni dashi duka mun gane ita ta katse mini waya.. Na yun'kura na tashi ina fad'in." Za mu tafi Baba Allah Ya kara sau'ki." Yaran suka tashi gabad'aya Khalil ya d'auki Sultan suka yi gaba k'ananun kuma suka tsaya ni har muka gama sallama da shi, na dube ta babu yabo babu fallasa na ce." Allah Ya ba mu alheri Hauwa." Ta amsa kanta a kasa domin ta kasa yarda ta dago ta kalle ni. Biyo bayanmu ya yi wai sai ya rakamu gida muka kuwa jero muna tafiya tare har bakin gate din gidana har da shi muka shiga ciki ya tsaya yana magana da masu gadi. Amma bai biyo mu ciki ba anan dai muka bar shi muka shige ciki ni da yaran gabad'aya. Washe gari kuwa gari yana yin haske na kira shi bugun farko ya daga na ji muryarsa ta fara bud'ewa ba kamar jiya ba muka gaisa yana gaya mini ya warware tarin ma da yake yi ya sassauta masa sosai. Ita ya ba ni wai mu gaisa duk a kokarinsa na ganin lallai sai mun samu daidaito ban yi jayayya ba na ce to na ji maganarta a dan sake tana fad'in." Ina kwana ya yaran?" Na amsa da lafiya lou muke suna can suna shirin makaranta." Ta furta." Allah Ya yi musu albarka." Na amsa da Amin a tak'aice." Daga haka ba ta sake cewa komai ba ta bashi wayarsa. Muka dan yi magana kad'an ya kashe tunda a ranar zai dawo gidana. **** Sati biyu da faruwar hakan. Kawai na ga kiranta na yi mamaki sosai yaushe rabon da mu yi waya ta arziki da Hauwa tun lokacin da ta ajiye Sultan ta tafi garinsu. Haka kawai sai na tsinci kaina cikin fad'uwar gaba domin kuwa zahiri zuciyata ta kasa aminta da ita tun bayan abubuwan da suka shud'e ba ni tunanin zan sake sakin jikina da ita tunda ta gama fito da aninhin abinda yake cikin ranta game da ni. Na daga cike da tarin zullumi muka gaisa ta yi shiru ba ta ce komai ba na ce." Ina fatan lafiya ko Khalil din za a turo miki ne?." Da yake wasu lukutan takan turo mai yi mata wanki da guga ya kira Khalil ban san sai dalilin da ya sanya take kiransa ba wannan tsakanin d'a da mahaifi ne shima yaron yanzu yana sakewa da ita ba kamar da ba. Ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce." Amina tun ranar da ku ka zo duba maigidan hankalina ya kasa kwanciya ganin Nabila ba ki tunanin akwai wata dangantaka ta soyayya a tsakaninsu kuwa? ko ba ki ji lokacin da yake tambayarta ta dawo ba, hakan na nufin suna da wata ala'ka tunda har yana da masaniyar shige da ficen da take yi kan harkokinta." Na yi kasa'ke da waya a kunne ina sauraranta har ta kammala maganarta. Zuciyata kwata-kwata bata ta'ba yi mini wannan tunanin ba a ganina shi kuwa me zai yi da Nabila duk nagartattun matan da suke wannan duniya. Kai gaskiya ba na tunanin zai yi soyayya da ita ko ya yi zawarcinta. Ta ce." Kin yi shiru ba ki ce komai ba, kin ga dacewar ko aure zai kara ya yi da ita. Bayan bada'kalar da ta faru da yayarta." Na furta." Ki daina wannan maganar don Allah Hauwa, ba ni tunanin haka gaskiya Nabila dai kamar yadda ya gaya mini tana zaune ne domin ta zama garkuwa ga yaran 'yar uwarta, cikinsu babu wanda ya ta'ba kawo korafi a kanta hakan ya nuna suna buk'atar zamanta a tare da su. Maganar kuma mijinki yana zawarcinta ai shi ba mahaukaci ba ne a zahiri da suffa Nabila ba macen da ta kamace shi bace balle ga abubuwan da suka faru a baya. Dole za su gaisa watarana kuma suna da lambar juna hakan kuma ba zai sanya mu ce soyayya suke yi ba." Ta ce." Jikina ne yake ba ni akwai matsala Amina wallahi ko shi baya sonta to ita tana zawarcinsa ai akace idan kaga kare yana shanshana takalmi d'auka zai yi. Sun gaji asiri fa wallahi kada ta juyar masa da tunani mu rasa gane kansa kamar yadda 'yar uwarta ta yi.'' Na ce." Ki daina tunanin haka don Allah." Abinda na iya ce mata kenan domin ni lokacin ma wani matsanancin ciwon kwankwanso ne ya ri'ke ni. Na ja kafafu na zauna gefan gado ina jin ta sama-sama a haka muka yi sallama. Tunda na ji ciwon ya tsananta sosai na tabbatar da cewa haihuwa ce. Wannan karon kuma abin ya canza mini kenan ba ni haihuwa tara sai na goma ya kama amma watannan kwanansa goma sha bakwai Allah Ya kawo mini ita. Na tashi na fito da duk abinda ya kamata mussaman kayan baby ina da su akwati guda manyan set na kayan sanyi da towels Na kira Dr Sailuba lokacin da sauran k'warina bayan ita ko shi ban gayawa ba balle masu aikin yara kuma duka suna skull minti talatin ta iso lokacin ciwon ya sake k'arfi da kayan aikinta ta taho ta gyara wajen tare da shimfid'a mini wata leda babba ta yi mini shimfid'a a kai na kwanta ta duba ni. Da saura haka na cigaba da fafatawa sai da na k'ara minti talatin da zuwanta tukkuna Allah Ya kawo ta da gaggawa babu jinkiri na farkon yana fitowa d'an uwansa ya biyo shi jim kad'an mahaifarsu ta biyo baya. Ina kiran sunan Allah itama tana yi bakinta ya k'i rufuwa. Da yake gwanace ta yi komai cikin k'warewa kowanne ta nad'e shi cikin towol fadi take kin iya haihuwa wallahi dubi yara 'kosassu na jima ban ga biyu masu wannan girman ba alhamdulillahi." Ta shiga toilet dina ta had'a mini ruwan d'umi lokacin na tashi da kaina don ba ni jin komai na canza zani na sanya audiga na kuma tafi da wata toilet din. Ina fitowa na tarar ta tattare kayan dana haihu a kai babu abinda ya 'baci a d'akin kamar ma ba a yi wata sabga ta jini ba. Na fito da kayana da kaina na sanya da kanta ta wanke yaran suna ta kusur-kusur kuka wannan idan ya dire sai wannan ya d'auka. Muka fara jin bugu muryar Baba Tabawa tana kiran sunana. Hajiya Amina. Taburni tana fad'in." Haihuwa ta yi wallahi tallahi ga kukan jariri nan. Na tashi ina murmushi a nutse na je na bud'e musu d'akin suka shigo gabad'aya su uku har da Mairo. Dr dai sai dariya take yi musu tana aikinta. Baba Tabawa fadi take yi." Ba ku kyauta mana ba amma." Gabad'aya bakinsu ya'ki rufuwa. Mairo tana dariya take ce wa." Shikkenan biyu sun samu 'yan uwa Allah mun gode maka, Ubangiji Allah Ya yara mana." Taburni ta d'an zauna gefena tana fad'in." Sannu Ubangiji Allah Ya kara lafiya Hajiya Allah Ya hore miki arziki domin wannan baiwa ce daga wurin Ubangiji Allah Ya inganta lafiya." Na amsa da Amin suma Amin." Baba Tabawa ta kwashi kayan da suka 'baci ta fita da su. Ta burni ta bi bayanta da sauri. Ita kuma Mairo muna tare tana zubar da ruwan wankan yaran tare da had'a wani a haka Dr Sailuba ta shiryasu tsaf cikin kayan sanyi kowane da towel dinsa abin dai gwanin burgewa, ni kam tunda na zauna gefan gado nake tasbihi tare da jaddada godiyata ga Allah ganin yadda ya yi mini wannan baiwa ta haihuwa lafiya ba ni jin komai a jikina ina kuma addu'a a gare shi ya sanya ko da an auna yaran a tabbatar mana da sahihancin lafiyarsu.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *160* Wannan haihuwa ta yi silar wanke zuk'atan bayin Allah da yawa. Tun daga kan masu gadin gidansa da yaransa na jiki irinsu Sukairaju da masu hidima da kai kawo na gidan muka kasance gabad'aya da su cikin murna tamkar a daran sallah. Ita dai Dr Sailuba ta samu tukwicin kujarar umara da mota. Masu aikin kuwa Baba Tabawa Mairo Taburni kowacce da alk'awarin zuwa umara ta azimi kuma tunda daf muke da shiga watan. Ya rasa inda zai sanya ransa ya ji dad'i da ya dawo ya same ni da yaran lafiya lau kuma Dr Sailuba tana gaya masa cewa ita dai a yadda take ganin yanayin kuzarin yaran bata tsammanin suna d'auke da wani ciwo mai karya garkuwar jiki mussaman irin wanda muke hasashe amma domin dai a sake tabbatar da lafiyarsu lau ya ce mata za mu je asibitinsu tare da ni dashi wajan Dr Iliyas a bincikesu sosai don mu sake samun nutsuwa da kwanciyar hankali. Sujudur Shakur ya yi a gabana ya jima kuwa goshinsa a kasa da ya d'ago sai ya kama ni ya rungume ni tsam-tsam a jikinsa yana ta furta mini kalmar godiya tare da jadadda mini so da k'aunar da bata da abin misali. Yara suka dawo daga makaranta tsalle suke yi Mama ta haihu abinda suke ta fad'i kenan sun kewayemu da Babansu. Ya ce su je su cire uniform suka 'ki lallai sai an ba su sun d'auka. Kowacce ta tan'kwashe k'afa ya dinga bin su d'aya bayan d'aya yana dora musu a cinya. Usaina sai dariya take yi tana kallonsa ta ce." Baba ka ga hancin wannan irin nawa ko? dama Mairo ta ce da ni suke kama?'' Hassana kamar wata shashasha ta ce." Ni zan dinga goya d'aya kema ki goya daya ko?" Minal ta ta'be fuska za ta yi kuka tana ce wa." Baba ni fa? ni ma ina nawa wanda zan goya." Sai kuka hawaye share-share suka shiga kasa tsare a kumatunta. Ya janyota da saurin gaske ya d'ora saman cinyarsa yana share mata hawaye. Ta rike shi tana kuka tana fad'in." Ina nawa yake Baba." Na kar'bi Usainin daga hannun Hassana na ce." Ga naki nan shine Usaini na bar miki." Ta fara ko'karin ri'ke shi nasa mata a jikinta ya tare da hannunsa. Ta saki dariya tana ta'ba kumatunsa ya d'an bud'e ido d'aya sai kuma ya rufe tasa dariya tana cewa." Baba ka ga ya bud'e idonsa nan d'insa ya yi ja ko ciwo ya ji." Ta nuna kumatunsa da wani tabo a wurin wanda ya yi jaa sosai ya bambamta da fatarsa. Da wannan alamar Allah Ya bambamta mana su Amma kamanninsu daya shi Usainin ne mai wannan tabon. Ya ce." Ba ciwo ya ji ba haka Allah ya yi masa baiwa." Ta ce." Mama kin bar mini shi ko?" Na d'aga kaina. Yarinyar bakinta ya'ki rufuwa tasa yatsanta a cikin hannunsa ya kuwa d'amke ta dinga k'yalkyala dariya tana duban 'yan uwan "kin gani ko ya rike ni, Usaina kin ga ya rike mini hannu." Su dai dariya kawai suke yi mata. Khalil ya shigo bakinsa har kunne da yake sun riga shi dawowa shi yana cikin yaran da za su yi saukar al'kur'ani sun bambamta musu lokacin tashi mahukunta makarantar. A nutse na ce." Shigo sosai mana." Ya shigo yana ta washe baki ya ce." Masa'udu ne ya gaya mini Mama ta haihu kuma guda biyu Irina." Uban ya kama yi masa dariya. Ya matsa kusa da shi yana ta duba fuskar yaran ya kar'bi na hannun Usaina yana cewa." Wannan shine a babban mama." Na ce." Shine na hannun Minal kuma Usaini." Abinda ya yi gabad'aya sai da ya ba mu mamaki har uban ya rungume shi a kirjinsa ya rintse idonsa kimanin minti biyu ya bud'e cike da kwalla ya dinga fad'in." Allah Ya raya ku, Allah Ya sa mu yi zumunci domin Allah mu so junanmu domin Allah, Ubangiji Allah Ya yi wa Babanmu tsayin rai." Na yi saurin sunkuyar da kaina kasa jin k'walla ta cika mini ido. Yaron nan yana da kaifin basira da tunani. Yasan shekarun girma sun cimma Babansu gasu k'ananu shine yake wannan addu'ar yana so su girma tare dashi Shi kansa jikinsa sai da ya mutu. Amma da yake namiji ne bai nuna rauninsa ba yaron ma yana addu'a amsa masa yake yi. Sai da ya gama tukkuna ya ce." Za mu je umara bayan mun yi bikin suna ni da kai ko Babana." Ya gyad'a kansa cikin dauriya da ko'karin hana 'kwallar idonsa zuba." Ya furta." Akwai wurin da zan nuna maka jikin d'akin Allah sai ka tsaya sosai ka roke Allah Ubangiji Ya raya ni cikinku na ga girmanku ko?" Shiru ya yi bai ce komai ba 'kwallar dai da yake ko'karin hana ta zuba ita ta fara d'igowa saman towel din jaririn da yake hannunsa. Ya ce." Menene haka kuma Baban masu gida, a gaban 'kananka za su yi maka dariya." Ya d'an share hawayen ya fakaice ya dube ni yana cewa." Mama." Na amsa Ina kallonsa da wani irin yanayi gabad'aya duk ya dakusar mana da walwalarmu." Ya cigaba da cewa." Mama ta ji kin haihu ko na je na gaya mata?" Na ce." A a bata ji ba dama jira nake ku dawo daga makaranta." Ya tashi tsaye da yaron a hannunsa Usaina na mik'a hannu ya bata ya k'i ya mi'ko mini uana fad'in." Zan je yanzu na gaya mata." Na kar'be shi a hankali na ce." To hakan ya yi." Fita ya yi daga d'akin da d'an sauri. Muka dubi juna ni da shi bai ce komai ba haka zalika ni ma haka. Na dube su a nutse na ce. "Ku je ku cire kayan makaranta a yi alwalar magriba sannan a samu nutsuwa a ci abinci." Suka tashi a tare har ita Minal din da take saman cinyarsa ya kar'bi yaron dama kusan rabi a hannunsa yake ta dira kasa tana kallona ." Mama za ki goya mini shi idan an jima ko?" Na gyad'a kaina alamar E ta juya da niyyar fita tana d'an tsalle. Shiru na wani lokaci kafin na ji sautin numfashinsa." Ko yanzu Ubangiji Allah Ya d'auki raina Amina kin gama biyana hakika alherin da yake tattare da tarayyata dake ba zan k'idaya shi babu abu mafi girma da arziki face wannan. Allah Ya saka da alheri, ba zan boye miki ba na jima ban tsinci kaina cikin yanayi na farinciki kamar wannan rana ba. Sai dai jikina ya yi sanyi ainun da lamarin yaron nan Khalil ko lokacina ya kusa ne zan tafi na bar ku." Hararsa na yi ina fad'in." Kai ma abinda za ka yi kenan wace irin magana ce wannan don Allah." Ya dubi fuskar yaron da yake hannunsa a tsanake ya ce." Sai dai shekarun girma suka cimmani Ubangiji Allah Ya azurta ni da 'yan baiwa gasu nan kin san dai ba zan maimaita shekarun da na yi a baya ba ko Annabi Muhammadu s a w ya ce sittuna au saba'una. Yanzu hamsin da takwas nake." Shiru na yi ban ce masa komai saboda takaici mutuwa dole ce amma a ganina bai kamata a kawota a yanzu da muke cikin annashuwa ba. Wannan littafin na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Wayarsa aka kira ya canza harshe larabci yake yi sosai. Na tsinci wasu daga cikin abinda yake fad'a wasu kuma ban fahimta ba yana dai ta fad'in sunan Sukairaju a maganarsa ya gama ya dube ni yana fadin." Ba'ki na yi daga madina akan wani lamari ina barar addu'a." Na ce." A cikinta nake kullum Allah Ya yi riko da hannayenka, ni ma na gode sosai Allah Ya saka da alheri." Ya tsare ni da ido yana fad'in." Me na yi na godiya Amina?" A takaice na ce." Abubuwa da yawa. " Ya yi shiru bai ce komai yana dai ta kallona ina kici-kicin gyara rigata ya taimaka mini Hasan din ne yake mamulan baki da neman abinci ya d'ora mini shi saman cinyata na tallafe shi sosai nasa masa nonon a baki. Ya kuwa kama yana sha yaran yanzu duka da wayonsu ake haifarsu amma dai duk da haka na d'an taimaka masa wajan ganin ya rike a bakinsa. Ya ce." Idan Allah Ya kaimu za mu je asibiti tare kamar yadda na fadi da farko domin a duba mini su." Na ce." Allah Ya kaimu." Ya duba agogon dake d'aure a hannunsa magriba ta yi ya shiga toilet dina ya dauro alwala ya fita zuwa massalaci. Duka su biyun na shayar. Baba Tabawa ta shigo tana fad'in.'' ko akwai abinda nake buk'ata wanda zan ci. Na ce ta dama mini kunun gyada kawai na fara dumama cikina an jima idan na yanke shawara akan abinda zan ci zan gaya mata. Ta dubi yaran suna kwance a gado bacci suke yi ta furta." Ko za a goya su ne Hajiya?" Na yi dariya tare da fad'in." Sultan din fa?" Itama tana dariya ta ce." Ai ya girma shi ya zama saurayi." Na ce." Mu bari zuwa gobe tukkuna Babansu zai dawo." Ta gyadq kai tare da juyawa da sauri ta fita. Cikin kwanaki biyu da haihuwa dangina da nasa babu wanda bai ji ba. A kuma yau da suke da kwanaki uku a duniya Hajja da yayarsa Hajiya Saratu suka sauka a garin da abin arzikinsu akwati biyu cike da kayan yara kowanne da tasa Anti Yagana kuma ta ce mini itama dai tana tafe da muka yi waya da ita. Baban Saude kuwa kwana d'aya da haihuwar ya zo bakinsa kamar zai yage ganina kalau yaran ma haka domin ni da shi baban nasu mun sake samun nutsuwa da kwanciyar hankali a lokacin da aka tabbatar mana da ingancin lafiyarsu sai farinkinmu ya sake hauhawa. Kwana ya yi da safe bayan ya karya kummalo ya yi mana sallama ya wuce wajan sana'arsa har yana yi mini alkawarin zuwan iyalinsa tunda mun ce da taron suna ko dai ba su zo gabad'aya ba Anti Saude da Mamansu za su zo idan mun tsayar da ranar da za mu yi bikin sunan ya ce na gaya masa. Na yi ta murna kuwa ina yi masa godiya kafin ya tafi. Shud'ewar wannan kwanakin babu Hauwa babu dalilinta. Khalil ya gaya mata ranar dana haihu haka zalika ma mijinta ya gaya mata da bakinsa ya gaya mini ta sani. A yadda na fahimta yana tunanin ta zo tunda ba yini yake yi a gida ba tunda ya yi ba'kin nan bai zauna ba sai da daddare yake shigowa kuma kwana daya da haihuwar ta kar'bi girki. Yau da su Hajja su ka zo ya dawo gidana. Zuwa yanzu ni ma na fito falo cikinsu amma ta ko'ina jikina a rufe yake kafafuna ma koyaushe suna cikin safa. Tunda na haihu Allah ya hore mini lafiya ba ni jin ciwon irin na gigita bayan haihuwa kuma babu abinda ba na gudanarwa na abinda ya shafe ni. Wannan kad'ai ya isa na godewa Ubangiji. Rashin zuwan Hauwa ya ta'ba mini rai ainun na kuma yi mamaki ba kad'an ba. Masu aiki na hidima da yara ta kowace siga kowa k'auna da kulawa yake nuna mini me zan ce da Ubangiji. Salim baya garin yana Legos amma Nusaiba zuwanta biyu Adam ma tunda na haihu yake shigowa haka zalika ma Nabila ta shigo mini kwana daya da haihuwa ta yi mini barka sosai ta fita... Kwanansu Hajja biyu ranar biyar kenan suka fahimci akwai matsala daga bangaran Hauwa dalili da ni da maigidan da masu yi masa hidima daga waje har zuwa cikin gidan kowa cikin annashuwa yake yi. Hakan ya ta'ba ran Hajja sosai ina d'aki ta same ni, ganin yanayinta ya sanya na nutsu ta zauna a gefena tana duba fuskar Usaini ta ce." Wannan tabon kamar sake rinuwa yake yi a fuskarsa Amina." Na ce." Ni ma na lura da hakan, amma dai Dr Iliyas ya ce babu matsala in sha Allahu." Ta sauke ajiyar zuciya a hankali kafin ta dube ni ta ce.'' Menene a tsakaninku da Hauwa, Amina kada ki b'oye mini komai wannan lamarin naku ya fara damuna ya kamata a ce kun girma tunda duka babu yaro a cikinku." A hankali na furta." Babu komai sai alheri Hajja ranar da zan haihu ma mun yi wa da ita a sanina dai babu wata hatsaniya da ta ratsa tsakaninmu." Ta yi shiru na d'an wani lokaci kafin ta ce." Ki gaya mini gaskiya ta shigo gidan nan tunda ki ka haihu?" Na girgiza kaina ina fad'in." Ba ta shigo ba." Ta furta." Ki ce kuma babu komai Amina haihuwa irin wannan akwai dai wani abu da kuke b'oye mini?' Na ce." Hajja babu komai wallahi ni dai a nawa b'angaran ban san nata b'angaran ba." Ta ce." Ke ai na yarda dake Amina kuma na gazgataki domin da da akwai matsala za ki gaya mini, Hauwa ba ta jin maganar kowa, ta raina ni ta raina uwarta kuma ba ta jin shawara." Na yi shiru ban ce komai ba. Ta girgiza kanta da damuwa a tare da ita ta tashi ta fita. Sai ta d'an ba ni tausayi domin na gane duk fafutukar da take yi akan gidan d'anta ya gyaru da kamar wuya wai gurguwa da auran nesa Hauwa ta bari hassada ta yi mata illah a rayuwarta. Da daddare muka yi waya da anti Yagana cewa suna tafe ita da Ya Falmata ta dawo sati biyu da suka wuce. Na yi musu addu'ar isowa lafiya. A daran dai da ya dawo wajan goma da wani abin ban jima da yin sallama da su Hajja ba na shiga d'aki domin gasa jikina na kwanta na fito daga toilet na same shi rungume da Hassan yana kafadarsa ya tashi daga bacci yaran suna da tsotso mussaman da daddare Usainin na goye a bayan Taburni yana bacci. Na sanya kayan bacci a gurguje na kar'be shi domin kuka yake yi sosai na zauna nasa masa nono ya kama. D'akin ya d'auki shiru na wani lokacin kafin ya ce." Gobe ba'kin nan da na yi za su tafi amma jin labarin k'aruwar dana samu suka ce za su zo yi miki barka wasu labarawan Madina ne sharifai ne jinin Annabi Muhammadu S.a.w suka ce wai na tambaye ki za ki ba su yaran?" Na dube shi cikin rashin gane inda maganarsa ta dosa na basu yara kamar Yaya?" Ya gyad'a kansa yana fad'in." Sun ji irin jikokin Annabi Muhammadu S.a.W ki ke haifa kin san akwai su da kara da karamci da tsantsar ha'din kai sun ta ya ni murna sosai da abin alheri suka ce a baki." Dariya na yi na ce." Aikuwa na gode sosai amma dai su yi hakuri ba zan ba su ba." Yana dariyar shima ya furta." Kai tsaye abinda na gaya musu kenan, sun ce wai ke y'ar baiwa ce ta mussaman kina haihuwar yara masu daraja da albarka." Murmushi kawai na yi Ya nisa kafin ya cigaba da cewa akwai kud'i da na bawa Nabila za ta had'o musu kaya akwati hud'u Hasan biyu Usaini biyu idan kin duba abinda bai yi ba ko ake buk'ata sai ki yi magana ko?" Na dube shi sosai ina fadin." Akan me za ka bata kudi kace ta had'o mini kaya, me yasa ba ka yi shawara da ni ba ko ni ban san abinda ya dace da su ba?" Ya ce." Hajiya sassauta mana ita ta nema ba ni naga dacewar bata kudi ta sayowa yarana kaya ba business d'in ta ne da take yi kenan da aje waje a sayo sai a saya a wajenta ko?'' Shiru na yi ban ce komai ba. Ba zan yarda da wannan shishshigi ba duk abinda yake tsakaninsu ba ni buk'atar ji, jiki magayi ne duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwan kan doka. Ba ha'ka mai ya kawo rami, idan ta yi wari sai mu ji ai! Ya cigaba da cewa." 'Kiyasin kud'in nan da mutanan nan suka ba ki a matsayin alheri na haihuwar yaran nan sun haura miliyan saba'in. Ni kuma na ba ki tukwucin 'karamin kamfanina na soap (sarrafa sabulun wanka) wanda yake mariri." Da wani irin mamaki na dago ina kallonsa miliyan saba'in! Ya gyad'a kansa yana fad'in." Kad'an kenan daga irin alherinsu ba wani abu ba ne, kin cancanci fiye da haka Allah Ya yi miki albarka." Na ce." Me yasa za ka ba ni kamfani guda?'' Kai tsaye ya furta." Saboda ina shirye-shiryen bud'e wani zuwan da suka yi kenan!'' Na girgiza kaina a hankali na ce." A a ba zan kar'ba ba gaskiya ka haihu fa, nan gaba da ni da kai ba mu san iya adadin yaran da za ka sake haifa ba duk neman da za ka yi a yanzu saboda su za ka yi don haka ka bar shi na gode sosai da kulawa da addu'a abinda ka yi wa yarana wad'anda ba kai ka haife su ba wallahi ya ishe ni." Ya furta." Wanne yara ne ban haifa?'' Ya tsira mini ido da jin haushin maganata. Na cire idona daga cikin nasa a hankali na kwantar da yaron ina fad'in." Ni dai ba ni neman fitina don Allah idan alheri ka yi niyyar yi mini ka yi daidai gwargwado wannan ya yi yawa.'' Ya ce." Abinda na yi niyyar bayarwa kenan Amina." Na yi shiru ban ce komai ba amma zuciyata cike take da mamaki bayan zunzurutun kudi har miliyan saba'in da kamfani guda abin kamar ya yi yawa fa. Koda su anti Yagana suka zo na gaya musu Ya Falmata ta dinga fad'in bake ki ka ro'ka ba baki ya yi akan me za ki ce masa ba kya so. Kowace haihuwa da alherinta tunda har ya iya mallaka miki kamfani to dukiyarsa takai ta kawo wata'kila shima bai san adadinta ba, idan kin lura bayarwa yake yi tana sake ru'banya. Allah Ya kawo wasu abokan nasa su sake baki arzikinki ya ninka na da mu abinda muke so kenan. Ita dai anti Yagana shiru ta yi da alama yadda abin ya girgiza ni haka ya girgizata. Ta kasa cewa komai sai kallo. Zuwansu anti Yagana ya 'karawa gidan walwala domin dama can akwai jituwa tsakanin Hajja da ita gefe guda kuma ga Ya Falmata sarkin barkwanci da bada dariya ta zauna tana ta ba su labarin matan da suke zaman shahada a makka da yadda suke shan tiriri da wahala guje-guje itama abinda ya koro ta kenan. A daran ranar duka muna falon an gama cin abinci sai ga Hauwa ta yi sallama ta shigo Khalil na biye da ita a baya.......✍️ *GARKUWAR BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *161* Ni tausayi ma ta ba ni ganin gabad'ayanta kamar a ki'dime take da wannan yanayin na rashin gaskiya da kame-kame duk a k'okarinta na kare a kanta suka gaisa da Hajja tana ta nanata musu cewa ba ta da lafiya a kwance take har yanzu jikinta babu dadi har da 'yar 'kwallarta wai an gaya mata kwanansu biyu da zuwa amma ba su je gidanta ba. Hajja dai shiru ta yi mata kawai ta zuba mata ido Hajiya Saratu ce ta tanka mata itama ba wata magana mai tsayi da muhimmaci ba. Yadda dai ta girba 'karya tare da d'orawa kanta ciwo duk mai hankali yasan da cewa k'arya ce tsagwaronta babu wani mashahurin ciwo a tattare da ita balle ya hana ta zuwa duba jininin d'an uwanta. Ko ba ta zo domin ni ba tunda kishiyarta ce ta zo domin mijinta kuma d'an uwanta balle ma ni ban ga abinda na yi mata mai muni ba da zata sanyawa ranta k'iyayyata mai zafi. Haka kowa ya bi ta da abinda take fad'i ana ta yi mata sannu da jiki tana rantsewa da Allah wai bata da lafiya itama. Ni kuwa na tabbatar da cewa k'arya take yi tunda halinta ne d'orawa kai ciwo haka take yi ko kunya ba ta ji. Da haka muka gaisa da ita suka gaisa da su anti Yagana babu wanda ya nuna mata wani abu a fuska Ya Falmata ma sai tsokanarta take wai ko itama ta ci wake ne. Ganin haka ya sanya ta saki jikinta saboda yadda aka goya mata baya cewar bata da lafiya har su Hajjan gabad'aya. Khalil ya dinga jin dadi yaron ya d'auki yaran d'aya bayan d'aya ya kai mata tana duba su tana dariya wadda nasan ba ta jin dadi ba ce fadi take kamarsu daya da Babansu yadda ake ta fad'a haka take cewa har tana kallona mun fi ki karfin jini Amina. Ban iya ce mata komai ba sai kallo kawai domin koyaushe sabon darasi nake d'auka daga gareta. Ana haka maigidan ya sakko ya kuwa ji dad'i ganinmu tare da ita gabad'aya ana wasa da dariya shima ya zauna duk da akwai rashin sakewa tsakaninsa da su anti Yagana mussaman Ya Falmata kunyarta yake ji tunda yasan 'kanwar Mamana ce, bai dai za'ke sosai ba ana hira da shi jefi-jefi hankalinsa ma yafi karkarata kan yaransa da zamansa a wajan ya sanya suka kewayeshi. Ita kuwa Ya Falmata bata suruktaka da shi ta cigaba da sakin bakinta daidai misali a yi dariya idan ta kama a kuma jajanta a cikin abinda aka tattauna. Tare suka tafi tunda dama kwanaki d'aya kenan da kar'barta girki gobe ne zai dawo gidana ya kwana. Washe gari da wuri yarinyar nan Lad'ifa ta zo ta zauna zaman yi mana 'kunshi ta fara yi mini jaa kimanin awa biyu aka cire ta zana mini fulawa ba'ki a kafafu da hannu. Ya Falmatace za ta yi mini kitso idan sun cire lallan da aka yi musu domin ita da anti Yagana sun ce suma ba za a bar su a baya ba. Wajan biyar na yamma sai ga tawagar gidanmu Gwaggo ce kawai babu domin bata jin dadin shine dalilin da ya sanya ba ta samu zuwa ba tabbas da nasan tare za su taho da su Hajja. Mamaki ya kama ni sosai mota suka biyo ta haya hakan kuwa bai yi mini dadi ba tunda da sun kira ni sun gaya mini nasan idan na gaya masa zai iya sanya direba ma daga can ya d'aukosu duk yawansa. Sahura da Yusura da yaronta da ba su jima da yin arba'in ba. Ummansu Hadiza da Ummansu Saminu Fati da Hassana da Usainar gidanmu sai matar Hamusu itama amma ba ta zo da yaran ba suna can wurin Gwaggo Yusi shine jagora. Da kuma Ummatu babarsu Sunusi uwargidan Baba Sule kuma k'anwar Ummansu Hadiza ce ubansu d'aya. Sai Fiddausi yarinyar da ta zauna a hannuna lokacin bud'e gidana na kuntau ita da Yusura a lokacin da na ta fi umara ta farko kaddarar aure ta ratsa tsakani muka rabu ta koma gidansu. Duk ga su yau dalili ya kawo mini su. Ita kuma amarya Hajara matar Usaini ana can babu lafiya yadda Fati take gaya mini suna zargin ciki ne da ita ciwo take yi sosai har da su k'arin ruwa. Ikon Allah kenan Wannan zugar da suka yi ta tabbatar mini da cewa dama sun shirya sun kuma tsara yadda tafiya za ta kasance amma rashin gaya mini shine abinda ya b'ata mini rai. Sashenmu na ba'ki dake gidan na sanya aka gyara musu 'yan gidanmu kenan suka yada zango a can su Baba Tabawa na ta hidima da abinda za su ci. Sahura da Yusura kuma muna tare da su. Ita kadai ce na san da zuwanta a yau din saboda kayana da za ta kawo mini tunda mun yi waya da Hamusu ya ce mini ya kai mata tun kwana biyu da suka wuce amma shima bai gaya mini matarsa na tafe ba. Sun yi mini bazata kuma na ji dad'i masu k'orafin ba su ta'ba zuwa ba dalili ya kawo su. Amma har yanzu ni dashi ba mu tsayar da ranar walimar ba. Kwana shida da haihuwa a yau din kenan gobe yara za su sake amsa sunansu amma ba ni tsammanin a ranar za mu yi taron walima kamar yadda ya saba duk haihuwar da za a yi masa alamu sun nuna akwai shirye shiryen da yake yi. A daran da ya shigo na bi shi saman duk da ba girkina ba ne na Hauwa ne amma wasu lukutan yakan shigo ya yi sabgoginsa kafin ya fita kamar yadda idan ya je can yake yi, kuma ban ta'ba kalubantarsa ba ganin yadda shima yake takatsantsan da gujewa abinda zai kawo masa rikici yana wanka na zauna ya fito da ya gan ni a zaune sai ya d'auke kansa ya tafi ya tsaya gaban mudubi kad'an ya shafa basiline a jikinsa ya fesa turare ya sanya kayan shan iska fuskarsa ta nuna mini akwai abinda yake ji wa haushi. Gaishe shi na yi ya amsa tare da zama gefena na d'an tsura masa ido ina kallonsa shima yana kallona kafin na ji ya furta." Zan ga ranar da zan yi miki abu ki yaba mini Amina har yanzu ban iya ba a wurinki na gode k'warai kin kyauta." Na ce." Wani abu ne ya faru kuma?" Da wani irin yanayi ya ce." Saboda na baki wani abu da bai kai ya kawo ba shine ki ke bin 'yan uwanki kina gaya musu menene abin magana akan abinda na yi anan a gaya mini hujjar da ta rahamta mini yin kyauta da abinda nake so da dukiyata. Ke na ce na bawa wannan wuri ba 'ya'yan da muka haifa tare ba. Ko na ta'ba yi miki wata babbar kyauta duk tsayin zamana dake bayan wannan?" A d'an sanyaye na ce." Wa na gayawa ka ba ni kyauta?" Don har ga Allah ban yi tunanin su anti Yagana za su yi masa wata magana ba tunda ni su kadai na gayawa Babanmu bai sani ba haka zalika ban sanar da Baban Saude ba. Ya gyad'a kansa yana fad'in." D'azu da safe kafin na fita 'yar uwarki ta same ni a haraba tana yi mini wasu maganganu shin me kuka d'auke ni ne? jahili wanda ba shi da ilimin addini ko me? kyauta ke na bawa ba yara ba. Ko kuwa idan na yi Hauwa ko a ahalinta alheri sai kowa ya sani. Za ku nuna mini yadda zan yi da abina ne Amina. Duk abinda nake yi ina sane babu wani yaro da zan haifa walau ke ki ka haifa ko ba ke ki ka haifa ba na fifita shi akan d'an uwansa. Ko an ce dole idan na kwanta dake a daren girkinki itama sai na kwanta da ita. An tilasta mini cewa idan na yi jima'i da Hauwa yau gobe sai na yi da Amina?." Shiru kawai na yi ina kallonsa da mamaki. Lallai anti Yagana ashe shiyasa ta yi shiru bata tanka mana ba ashe da akwai abinda ta kud'irta a ranta yadda dai ransa ya 'baci hakan ya tabbatar mini da cewa ta fad'i maganar da ta tunzura shi kamar yadda yake nanata cewa dukiyarsa ce kuma duk abinda yake yi yana sane shi ba jahili ba ne. Ya cigaba da cewa." Babu d'ayanku da nake da ta'kidin takewa ha'kki ko na fifita yaranta duka ni na haifa kuma babu wanda bana so a cikinsu ina kuma addu'a Allah kada ya kama ni da hak'kinku, hakan kuma baya na nufin na sarayar da iko da mutuncinta ba duk wadda ta yi mini ba daidai ba a cikinku zan yi mata hukunci daidai gwargwadon abinda ta aikata mini. Idan har ba ki son abinda na baki shikkenan kada ki kuskura ki kara wata magana da wani zai tsaya gabana ya kalubalence ni. Na duba dacewa da cancanta a kanki ne Mutum nawa ne suke 'kasan ki? kuma mutum nawa suke ci da sha a karkashinki? mutum nawa ki ka tallafa suka tashi? ko kuma kin d'auka haka nake zaune dake kara zube ba ni bin abubuwan da ki ke gudanarwa arziki na Allah ne amma menene makomar yaranki da koyaushe ki ke nanata mini cewa ba ni ne ubansu ba. Idan yau na fa'di na mutu a shari'a ba su da gadona. Idan na d'auki abu na baki sai ya zama lefi da tiri-tiri da magana kamfanin majizai na baki ne Amina?" Na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Har yanzu bakina a mace yake na kasa cewa komai saboda mutuwar jiki da mamaki duk yadda yake ganin k'ima da mutuncin anti Yagana yau ta kai shi bango tunda gashi yana ba ni sa'ko zuwa wajenta. Na rasa abin cewa kawai sai na yi shiru da bakina domin ba ni so kuma lamarin ya girmama shi da ita anti Yaganar babu wanda zan za'ba tana da hujja shima yana da tasa hujjar kamfani kuma muddin ana so na kar'ba akashe shi ya daina aiki koma gabad'aya a sayar mini da shi a bani kudin na had'a da wanda suke hannuna alherin da abokansa suka yi mini na nemi plaza cikin kasuwa na saya ko Kuma na sanya k'wararru su gina mini na sake fad'ada harkokina wannan shine magana. Adamu ne ya kira shi a waya ina ji suka gama magana yana gaya masa gasu nan shi da Yusi za su kawo sa'ko in ji anti Nabila ita ba ta kira shi ba saboda tasan yana gida sai ta sanya yaran. ya ajiye wayarsa to a nan ne na magantu cikin had'e rai na ce." Ka ajiye wannan kaya domin kuwa yarana ba za su sanyasu ba Allah shine d'aya ko kuma kawai ku yi tanadi kai da ita idan kun yi aure kun haihu shikkenan kun huta. Ko sun kawo kayan nan a banza, idan lallai sai Nabila ce za ta sayowa yaran nan kayan sanyawa a bar shi kawai zan saya musu a matsayina na uwarsu." Bai juyo ya dube ni ba ya ce." To shikkenan ai tunda kin ce haka ta riga ta sayo sai a ce mata me? ki a ajiye kada Allah Ya sa ki yi musu amfani da shi din." Na ce." Ba kuwa zan yi ba, ai ga shawara nan na baka za su yi maka amfani idan kun haihu." Ya dube ni yana fad'in." Kina da hankali kuwa Giwa da wa zan haihu?" Na tare shi da sauri ina ce wa." Da ita mana ko ka d'auka shashashai ne mu, ka ji kunya wallahi." Ya 'bata ransa yana fad'in." Yanzu ke tsakani da Allah ba ki ji kunyar yi mini wannan maganar ba, duk kalolin matan da suke duniyar nan Amina na rasa wadda zan aura sai wannan matar me zan yi da ita?" Na ce" Me yasa zan ji kunya tunda kai ba ka ji ba. Haba Malam babu wata magana da za ka fad'i wallahi tallahi na yarda da kai, ina ruwanka da ita da business dinta ka sayi kaya a wajanta saboda kana tausayata mata ko akwai shagunan sayar da kayan baby's cikin garin nan da yawa me yasa ba za ka je da kan ka ka sayo ba, ka bi dare da rana ka samar da cikinsu sayo musu kayan da za su sanya ne zai gagareka." Ya girgiza kansa yana ce wa." Ba zan shiga shago sayan kaya ba. Ni ma wanda nake sanyawa telana ne yake kawo mini su a dinke ya san irin yaduka da shaddodin da na fi so ko tafiya na yi kin ta'ba ganin na sayo muku abu, idan kina ganin za ki iya zuwa ki sayo musu abar maganar don Allah don Annabi zan baki kudi wannan din kuma sai a ajiye idan Allah Ya sanya na samu wasu biyun daga wajan Hauwa shikkenan na huta. Ta'be baki na yi tare da d'auke kaina ban ce komai ba. D'akin ya d'auki shiru na wani lokaci kafin na ji maganarsa yana fad'in." Kafin na shigo na ga alamar muna da ba'ki tun daga haraba hakene?" " 'Yan gidanmu ne!" Na fad'a a takaice. Ya saki fuska yana fad'in." Sun zo taya mu murna kenan, na ji dad'i sosai kuma idan na ci abinci zan sakko 'kasa mu gaisa sai a yi musu magana." "To." Kawai na ce na tashi tsaye. Ya rike hannuna na koma na zauna kusa da shi. B'akin lallen da ya zanu a saman fatar hannayena ya shiga dubawa. Ya bud'e tafikan hannayen yana kallo yatsun ya yi marron sosai zanan fulawar ya fito. Ya dinga sauke ajiyar zuciya yana fad'in." Ya yi kyau sosai mu ga na 'kafafun." Gim na yi kawai ta yaya zan iya nuna masa k'afafuna na cikin safa. Ya sunkuya kuwa ya cire safar yana ta dubawa na zubawa 'keyarsa ido takaici da haushinsa ya ishe ni. Maganar Nabila idan har ta yi nisa akwai wani gagarimin lamari da zai faru tunda shi bashi da tunanin yin nesa da mu'amula mai tsayi da ita bayan gaisuwa. Ai tsakanin mace da namiji idan sha'kuwa da tausayi suka shigo ciki akwai alamun kauna. Ya nuna son cigabanta da tausaya mata tunda idan an yi magana sai ya ce business d'inta ne a saya a wurinta kada a je waje a saya. Ya d'ago da wani irin yanayi na yi saurin d'auke kaina ya tsira mini ido har yanzu hannunasa yana cikin nawa ya ce." Za ki ba ni abinci ko na tafi na kwanta a haka?" Na furta." Duk yadda ka ga ni, amma ai ba ni ce mai baka abincin ba." Ya ce." Kwana biyu itama tana ta ciwo kullum a kwance take ciki ne da ita ba kuma sosai take sarrafuwa ba ke kuma kin ga kina da masu aiki." Na katse shi da gaggawa ina fad'in.'' Na hana ka d'aukar mata aiki ne? tana da lafiya bata da lafiya ba abinda ya shafe ni ba ne. Cikin dai masu aikin gidan nan Wallahi babu wadda za a d'auka.'' Ya ce." Ba a ce dama za a d'auki ko daya ba, za a kawo mata nata masu aiki itama." Na d'auke kaina ban ce komai ba. Ya ce." A kawo mini abincin dai ko ba shi da yawa kada abin ya yi mini yawa kuma." Na tashi kawai na tsinci hannunsa saman tudun mazaunaina. Na juyo da sauri ina kallonsa. Ya cire hannun shima yana kallona. Wato da bai samu sararin d'ora hannunsa a kirjina ba kamar yadda ya saba sai Allah Ya bashi sa'a ya d'ora a na baya. Ya furta." Menene fuskata za ki buge na tare." Na janye idona daga kansa kawai na wuce cike da mamaki wai tambayata yake yi menene saboda na kalleshi wato shi bai d'auki abinda ya yi a matsayin wani abu ba." Ina saukowa na tarar da ita ta zo ana ta hira da ita. Usaini ma yana hannunta. Hasan din na goye bayan Taburni yana bacci. Ta miko mini shi tana fad'in." Tun d'azu yake neman nono." Ban ce komai ba na kar'be shi na zauna gefan Hajja wadda suka ta hirar duniya da Ya Falmata tana ta basu labarin rikici da masifar tashin hankalin da aka shiga a maiduguri lokacin farkon boko haram. Khalil na sanya ya d'auko mini wayata a d'aki na kira Fati na ce su zo gabad'aya za su gaisa da maigidan. Ta ce mini abinci suke ci da sun kammala za su zo.....✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *162* Ganinta a zaune ya sanya na share kawai ban kai masa abincin ba idan ya koma gidanta sai ta bashi abinda taci su kwanta duk rashin moruwarta da yake fad'i ai ba zata kwana da yunwa ba. Na ji tana magana da Hajja kan zuwa inna Uwani gobe wai sun yi waya Hajjan ta bata amsa da cewar itama ta sanar da ita. Ya sauko cikin mutunci da kulawa ya zauna a falon bayan shigowarsu Fati gabad'aya ya gaisa da su har yana jan su Hassanar gidanmu da tsokana haka dai suka dinga sinne kai irin na rashin sabo yadda ya zauna ya kula su shine abinda ya d'an sassauta mini zuciyata domin kuwa ko babu komai bai 'kyamace su ba ya nuna suma cikakkun mutane ne masu kima da karamci zuwansu ya sanya shi farinciki har yana mik'a godiyarsa wannan yana daya daga cikin kyawawan halayensa karrama mutum duk rauni da rashinsa baya ta'ba nunawa na 'kasa da shi cewa shi ba komai ba ne, fuskarsa a sake zai mu'amulanci mutanan da ya tabbatar da cewa ya fi suttura da rufin asiri. Mun d'an jima tare da shi a falon da su ma gabad'aya kafin ya yi wa Hajja sallama ya fita. Jim kad'an itama ta tashi ta bi bayansa bayan ta yi mana sallama kamar dai gaske ta saki jikinta tana walwala tamkar babu komai a zuciyata Hauwa kenan . Yusi kuwa kam ganina da shi biyu tunda suka zo yana can tare da Adamu sai da gari ya waye tukkuna suka shigo su biyu da akwatina hud'u jiyan ba su samu damar kawo kayan ba. Muna d'aki gabad'aya anti Yagana Ya Falmata da Sahura. Yusra tana bacci saman kujera bata tashi ba. Na bi su da ido har suka gama shigo da akwatinan kayan suka ajiyesu a gefe ban ce komai ba. Muka gaisa da su suka zauna cikin nishadi da jin dad'in had'uwa da juna wannan so da k'aunar da suke yi wa junansu har mamaki yake ba ni. Hassan na hannun Adam Usaini shi kuma yana hannun Yusi na ji shi Adam din yana fad'in." Mama Baba ne ya ce mu kawo miki kayan nan akwai wasu kayan ma da za mu d'auko da yamma anti Nabila ta ba ni lambar wayar direban idan suka iso zai kira ni." A takaice na ce." To shikkenan." Ya mi'kawa anti Yagana yaron da yake hannunsa ya riga Yusi fita shi yana zaune kamar akwai magana a bakinsa na dube shi ina fad'in." Kai ma ka zama munafiki ko?" Ya dube ni da sauri yana fad'in." Munafiki Mama?" Na gyad'a kaina ban ce komai saboda takaici to bayan wad'annan kayan akwai wasu kenan. Ya Falmata ta b'ata rai tana fad'in." Menene abin munafurci Amina." Na ce." Haushi yake ba ni wallahi idan yana yin wani abin Ya Falmata yaron nan baya goya mini baya ya manta da ni ma gabad'aya." Ta kama dariya tana fad'in." To yanzu me ya faru da kike barar goyan baya daga gare shi a da can fa shine shalele ko don yanzu kin samu wasu shine za ki cillar dashi." Na ce." Shi ya fara cillar da ni ai Ya Falmata." Murmushi ya yi kawai bai ce komai ba ya mika mata yaron yana fadin." Bari na je na same shi Mama zan dawo sai mu yi magana ko idan na yi lefi a yi hakuri.'' Hararsa na yi yasa dariya da sauri ya fice. Sahura ta fito daga toilet wanka ta yi ta ta zauna tana shafa mai. Na dube ta a hankali wata irin ki'ba ta yi zamanta a gefena da d'aurin kirji na sake gazgatawa na ce." Wai ke maganin ki'ba ki ka sha ne?" Anti Yagana ta ce." Kin riga ni magana Amina na ce ko idona ne yake yi mini gizo ne." Dariya kawai take yi tana fad'in." Kwanciyar hankali ne kawai. Ya Falmata na fad'in idan haihuwa ma ta tsaya ana samun canji irin haka." D'akin ya d'auki shiru na wani lokacin na dubi anti Yagana ina fad'in." Wai ya kuka yi da maigidan nan ne?" Ta yi shiru tana d'an kallona kafin ta ce." Na same shi ne domin na yi masa godiya bisa abinda ya yi miki na alheri da farko na yi tunanin ke kad'ai ya ware ya bawa tare da yaran nan sai daga baya kuma da yayi mini bayani na gane dalilinsa wallahi abin ne ya ba ni tsoro Amina shiyasa na gaza ha'kuri na ce bari na yi magana akai saboda ina jin tsoron k'aramar magana ta zama babba a zo ana ta maganganu marasa kyau a kan ki." Ya Falmata ta b'ata rai tana fad'in." Akan wane dalili za ki tare shi da wannan maganar Yagana kin yi kuskure anan gaskiya tunda ta zo ta gaya mana na ce ta kar'ba tunda ba ita ta ro'ka ba shi ya bata. Amina mahad'in arzikinsa ce don ya dauki 'karamin kamfani ya bata bai nakasa kansa ba kuma yana da ninikin abinda ya bata din amma shine ki ka zame jiki ki ka tare shi ba ki ji nauyi ba don Allah Yagana." Ta gyad'a kanta tana ce wa." Ni fa ba da wani abin na yi masa magana ba Ya Falmata kin san irin haka yana haddasa rigima tsakanin iyali ki ga gida ya rikice ana ta fad'a kuma da yawa wasu mazan sune suke asassawa wajan fifita wani bangare. kuma ba ita kad'ai ce matarsa ba Hauwa yar uwarsa ce kuma matarsa itama tana da yara tana kuma da hakki." Ta ce." Lokacin da zai yi mata kyauta kin sani ne Yagana? ke dai ba yar uwarki ki ka sani ba me yasa ba za ki goya mata baya ba bisa abin alherin da ta samu kin ga kenan anan gaba zaki sanya masa shakku idan ya yi niyyar yi mata wani alherin." Ta yi shiru bata ce komai ba. Na gane dalilinta na magana kuma tana da hujja amma yanzu tunda ya fito ya fad'i da bakinsa ni ya bawa ba yara ba shikkenan. Na ce." Ya ji haushi har yana ta fad'a wai babu wanda zai nuna masa yadda zai yi da abinsa. Ya gaya mini dalilai masu muhimmancin da ya sanya shi ba ni kyautar wannan kamfani. Na kar'ba kuma na gode amma abinda na yanke shine ya sanya mini shi a kasuwa a kar'bi kudin domin idan har zai cigaba da aiki da sunana akwai matsala babba a tashe shi daga aiki idan ya so na nemi plaza na saya na fad'ad'a harkokina na kuma sanya haya a wasu wuraran." Ya Falmata da annashuwa ta furta." Wannan tunanin naki ya yi Amina. Ya kike gani Yagana hakan ya yi ko?" Ta furta." Ya yi sosai Ubangiji Allah Ya dafa miki amma ta wace sigar za ki tunkare shi har ki gaya masa ya sa a kasuwa ya baki kudin." Na furta." Ni ma ban san ta sigar da zan gaya masa ba wallahi tunda yanzu fad'a yake ta yi kan cewa ba ya yi mini gwaninta duk abinda ya yi mini na alheri sai na gwasile na ce ga yadda nake so." Sahura da ta gama sanya kayanta kuma tunda muka fara maganar ba ta ce komai ba sai yanzu ta furta." Sister na taya ki murna sosai Ubangiji Allah Ya yi ri'ko da hannunki lallai kin cancanta da fiye da abinda ya fi haka ma, an yi gwagwarmaya kuma an tari kalubale mabambamta amma ni a shawarce ki bari a kwana biyu lokacin da kuke dad'i da shi sai ki gaya masa tunaninki idan kin ci sa'a zai amince tunda gaskiya yana da sau'kin kai a wasu lukutan." Anti Yagana ta ce." Ni ma tunanin da na yi kenan ki bari a kwana biyu kun samu nutsuwa dake da shi cikin lumana sai ki gaya masa abinda ki ke so." Na sauke ajiyar zuciya a hankali na furta.''In sha Allah." Yusura ta tashi daga bacci ta shiga toilet ta fito na ce ta janyo mana akwatinan kayan nan. Ta d'auko su d'aya bayan d'aya aka bud'e kaya ne masu kyau da kud'i kuma ta duba quality sosai babu wani k'aramin abu a ciki ko na son zuciya ban san dai iya adadin kud'in da ya bata ba amma ta yi kokari kuma sun yi kyau kayan kwarai Muka gani gabad'aya Ya Falmata 'yar gayu mai son abu mai kyau sai yabawa take yi da kayan. Muka gama gani yarinyar ta mayar da su inda suke. Gaza ha'kuri na yi na sauke ajiyar zuciya ina duban anti Yagana na ce." Nabila ce fa ta had'o kayan nan." Ta yi kasa'ke da alama ba ta gane Nabilar da nake magana akai ba Sahura ta yi caraf tana ce wa." Nabila wadda na sani 'kanwar Hajiya Maryam mai rasuwa." Na gyad'a kaina ina kallonta. Anti Yagana da sauri ta ce." Kamar Yaya dama ba shine ya sayowa yaran ba?" Na ce." Kudi ya bata ta sayo musu anti Yagana mu zube lamarin nan a fefe mu kuma aunashi da ma'auni na hankali da adalci shin me kuka fahimta don Allah?" Ya Falmata ta yi shiru domin bata san bada'kalar da ta faru ba fadi take yi aikuwa kaya dai sun yi kyau Amina ina ganin ko ke ce abinda za ki sayo kenan domin dai babu abinda babu kuma kowacece wannan ba ta yi cuta da almundahana ba Anti Yagana ta ce." Ba ki gane ba ne, ita wadda ya bawa kudin kayan k'anwar wannan matar tasa ce fa Maryam da ta rasu mahaifiyar yaron nan Adamu da suka kawo kayan tare da Yusi." Na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Ta d'an yi shiru na wani lokaci sai ta ce." Ba ta da aure ne?'' Ta gyad'a kanta tana fad'in." Bazawara ce tana zaune gidan yayarta tana business da kuma kula da yaran. Shi babban ma Salim baya gari ita kuma Nusaiba tun iyayansu na raye suka yi mata aure sai shi wannan karamin Adamu." Na ce." Yana ta jaddada mini cewa business d'in da take yi kenan kuma da a sayi kaya a waje gwara a saya a wurinta. Ke anti Yagana kin san wuya da masifar da muka shiga dalilin Maryam ko, me kike tunanin zai faru yanzu tunda shi ba shi da tunani bai gane cewa sonsa take yi ba." Ta dinga girgiza kanta tana fad'in." Lallai mutumin nan to ina ruwansa da ita idan ba yana so ya d'auka ba shi yanzu don girman Allah sai ya yi zawarcinta duk matan da suke duniya." Ya Falmata ta yi shiru fuskarta ta canza da wani yanayi ta ce." Wata'kila wannan kyautar da ya yi miki yana so ne ya kashe miki baki kin ga ai idan ya yun'kuro domin auranta baki da bakin magana to mutumin da aka bawa kamfani na miliyoyin kud'i. Ai ya jefi tsuntsu da dutse biyu ne. Zuru na yi ina kallonta Ya Falmata macace mai tsinkaye sosai ni ban ma ta'ba yin wannan tunanin ba, amma har yanzu zuciyata bata gama aminta da cewa zai iya yin zawarcin Nabila ba idan an yi duba da irin muguwar wahalar da muka ci domin dai ba shi kad'ai ya shiga tasku ba har da mu gabad'aya Allah ne ya sa da kwanansa a gaba. Anti Yagana ta ce." Hakan za ta iya kasancewa ya yi da wannan niyyar ne, amma abin ya ba ni mamaki wallahi, wai me yasa wasu mazan ba su da tunani ne?" Sahura ta furta." Sai ki tsananta da addu'a Amina ni kaina wallahi na tsorata wad'annan mutanan sai kace mayu ita ta yi ta gama ita kuma wannan zata kutso kanta ba wani abu ta hange ba sai dukiya ce sun zama annoba wallahi. Anti Yagana ta dubi Ya Falmata da mataccen jiki ta shiga bata labarin irin abubuwan da suka faru baya kafin rasuwar Hajiya Maryam din. Ta dube ni tana fad'in." Ki ajiye kayan kada ki yi wa yaranki amfani da su. Ya bada wasu kudin kafin mu tafi mu sayo musu sannan ko ya ba ki takardun kamfanin nan kada ki kar'ba har sai ya gaya miki abinda yake tsakaninsa da ita irin wannan fa sai dai ki ji an d'aura tunda haka ya yi lokacin auran 'yar uwarta." Shiru kawai na yi ban iya cewa komai ba. muka yini muna tattauna lamarin shima tun jiya da daddare da ya fita bai sake shigowa ba. Sai bayan la'asar duk muna falo yaran suka sake shigowa a karo na biyu wannan karon har da Masa'udu kowanne kafad'arsa sa'be da dilar atamfa suka jibge dila biyar a gefe sai wasu manyan kwalaye hud'u da suka shigo da shi suka tattara kayan waje daya. Suka fita jim kad'an Hauwa da inna Uwani har da yaran gabad'aya suka shigo a gidanta suka yini, alamu sun nuna itama Inna Uwanin bata jima da sauka ba kuma kai tsaye gidan yarta ta sauka. Hakan kuwa ya bawa Hajja haushi domin a takaice ta amsa gaisuwarta yayin da ita kuma take ta washe baki da Hasan a hannunta tana yi mini sannu da barka da arziki ina amsawa tare da kallonsu daga ita har Hauwan nema suke yi su mayar da mutane shashasai Jim kan da zamansu shima ya shigo ganinsa sanye da kayan shan iska irin wanda ya saba sanyawa idan yana gida ya tabbatar mini da cewa bai fita ba gabad'aya amma bai shigo ba sai yanzu. Ya zauna a ka shiga gaisawa nan na ji yana gayawa Hajja bacci ya yi tun safe shiyasa bai shigo da wuri ba. Ya Falmata ta fara tashi ta shiga d'akina. Da kamar minti goma anti Yagana ta bi bayanta Sahura da Yusura dama suna ciki ba su fito ba. Sauran kuwa suna can sashen ba'ki tun safe da muka gaisa na ce su koma can su yi zamansu sai sun fi sakewa. Ni ma ban yi dogon zama ba na tashi na bar musu yaran gabad'aya. Ina daf da shiga d'akina mai sunan Mamana ta fito Hajiya Saratu kenan da yake d'akin Hauwa na da suka sauka ita da Hajja tunda asali d'akin da suke yada zango idan sun zo Khalil ne a ciki yanzu ta tsaya cikin raha tana fad'in." Uwargida kuma uwar biyu sau biyu." Dariya na yi na ce." Hajajju kenan ina yini." Ta amsa da kulawa tana fad'in." Na ce bari na fito nasan yanzu Falmata tana nan ta fara bada labari." Ina dariya na furta." Yanzu kuwa ta shiga d'aki yau tun safe bata jin dadin jikinta zazza'bi ne amma ta sha magani da sauki." Na fad'i mata hakane kawai domin ban san abinda zan ce mata ba bayan haka dalili tunda suka zo ake yin wannan zaman a yi hira a yi wasa da dariya amma tunda na gaya musu abinda yake faruwa jikinsu ya yi sanyi mussaman ita din. Kishi ne da su haka Mamanmu take da wannan kishin da rashin son kishiya yanzu nan duk sai su damu. Gashi dai ba ita za a yi wa ba jin labarin wahalar dana sha a baya ya sanyayyar mata da jiki gabad'aya ma kyautar da take ta murna an yi mini ta daina burgeta don tunaninta yana gaya mata danne mini kirji zai yi kawai sai dai mu ji d'aurin aure. Na shiga d'akin na samesu suna sake tattaunar maganar Ya Falmata duk ta yi wani kicin-kicin da rai na ji tana fad'in zaman ya isheta yau kwana bakwai tunda yara sun amsa sunansu su yi shirin tafiya kawai. Na zauna gefanta ina fad'in." Wane irin tafiya kuma Ya Falmata ku bari a kΓ rasa shagalin sunan mana. Tsaki ta ja kafin ta ce." Mijinki haushi yake ba ni Amina wallahi sam shekarunsa ba su amfanar da shi komai ba gabad'aya ba shi da tunani da hangen nesa." Dariya ce ta kama ni ganin yadda ta hak'ikance tana ta fad'a. Na shiga wanka na fito na shirya jikina sosai d'aya daga cikin sabbin d'inkunan da na yi wanda Sahura ta zo mini da su. Still dai maganar suke yi anti Yagana tana fad'in." Wata'kila ma ita ya bawa kudin raggon suna tunda yau da ake da kwana bakwai a al'ada ya kamata a ce an yankawa yara rago duk da ba a ce dole yin hakan farilla ba ne. Waya ta yi kara tana can saman dirowa kusa da Sahura ita ta miko mini don yadda ake ta caccakar ubangidan nata bata iya sanya baki ba yanayinta dai da yar damuwa itama abin ya bata haushi da mamaki. Na d'aga wayar cikin nutsuwa ya kira yi sunana na amsa ya ce." Ki zo ki same ni mu yi magana ina sama." Na ce." To shikkenan." Ya kashe waya ni ma na kashe tawa. Suna falon Hajja Inna Uwani da Hauwa da kuma mai sunan Mamana suna ta hira Hajja yanzu ta sake da 'yar uwarta. Sannu na yi musu na d'an tsaya muna magana da ita akan farin kwalli wai ta sanya Magaji ya nemo a can kano din ya kawo had'e da garafuni na ce to shikkenan an gode. Ina kallon Hauwa tana d'an satar kallona domin ni kaina nasan na yi kyau sosai atamfa ce a jikina amma duk jikinta aiki ne da uban stones ko ta ina dinkin buba ne ya zauna a jikina yadda ake so. Na haye saman zuciyata sam babu dadi ina kallon tarin kayan da su Adam suka jibge wajan 'kafar benan zan dai ji dalili. A zaune na same shi yana waya aikin kenan na zauna har ya gama ya juyo tana kallona tare da kiran sunana. Na sake amsawa ni ma idonsa a kaina. Ya cigaba da cewa." Ki yi hakuri yau tun safe ban shigo ba kin san Allah bacci ne ya shammace ni mai nauyi na ce da Hauwa ta tashe ni kafin azuhur wai ta manta sai uku da wani abu na tashi sallah sai a lokacin na yi." Na yi shiru ban ce komai. Ya ce." Na so yau a yi wa yaran nan yanka hakan bai yiwu ba amma gobe idan Allah ya kaimu za a yi da wuri akwai shanu biyu wannan na jama'ar da suke kewaye damu ne ku d'iba Hajja ma ku bata nata ku bawa Hauwa da duk wanda yake da hakki. Ragona hud'u ne wannan naki sai kin ga dama za ki ba ni." Ya fad'a yana kallona na daure zuciyata na ce." To an gode Allah Ya saka da alheri da budi." Ya ce.'' Ni ne da godiya ranar juma'a mai zuwa kuma za mu yi walima kamar dai yadda na saba abokaina da Malamai za su halarta in sha Allahu rabbi za a yi adduoi kamar yadda annabin rahama ya koyar da mu. Ubangiji Allah Ya raya mana zuria." Na sake amsawa da Amin Ya Allah. Ya yi shiru na d'an wani lokaci kafin ya cigaba da cewa." Duk abinda za a buk'ata fannin ci da sha za a yi order babu buk'atar a wahalar da wani sai dai akwai turaman atamfofi da Nabila ta yi mini tallansu gasunan na saya miki ki rabawa jama'arki." Na sake godiya a ta'kaice kafin na ce.'' To abinda yake cikin kwalayen fa." Ya d'an yi shiru kafin ya furta.'' Zannuwa kawai na saya a wurinta amma bari mu gani." Ya fara neman lambarta tunda wayarsa dama tana hannunsa bugu d'aya ta shiga ta d'aga na ji suna gaisawa ya ce." Bayan zannuwan da na saya menene ki ka aiko yara da shi a akwali?" Shiru ya yi yana sauraranta da yake can k'asa take magana ban ji komai ba. Sai da suka yi sallama tukkuna ya dube ni yana fad'in." Kin ji gudumuwa ta yi mana wai abin rabo ne duk wanda a ka bawa zani sai a sa masa cikin jaka mun gode ko?" Na ce." Ka gode dai ai kai ta yi wa ba Amina ba. Ya yi shiru yana kallona na cigaba da cewa." Ka ce da ni soyayya kuke yi ba wai ka zaunar da ni kana kwantar mini da kai ba. Soyayya kuke yi a fakaice ka yi mata alheri ta yi maka zaka maye gurbin Maryam da ita ko ba haka ba ne." Ya gyad'a kansa yana cewa.'' Sai ta iya kasancewa hakan ne amma ana ta 'bangaran fa wata'kila sona take yi." "Kai kuma da ka gane hakan sai ka cigaba da biye mata tunda kana hangen jin dadi da nagarta a tattare da ita ko?" Ya yi banza da ni kawai ya mike 'kafarsa ya kwanta tare da lumshe idonsa. Na ce." Wallahi tallahi wannan abin ya ba ni mamaki da tsoro yanzu kai ba ka jin wani iri a jikinka. Ya bude ido yana dubana kafin ya furta." Ba ni jin komai, kuma ba zan yi rigima dake ba a cikin mutane Nabila dai idan za ta sare kanta ta ba ni shi saboda so wallahi ba zan aureta ba. Idan kun ce tana sona ba zance a a ba, amma ni fa ba ni sonta ba kuma ni da niyyar auranta. Wannan maganar idan ba ku daina yi mini ita ba daga ke har ita Hauwa wallahi sai ranku ya 'baci tunda babu wadda ta haife ni a cikinku ina dalili ne za ku dame ni da wata Nabila." Na ce." Kai zaka daina idan har kana so a daina yi maka maganarta cikinmu babu yaro k'arami da za ka yi wa wasa da hankali." Ya furta." Zan daina amma ba zan wula'kantata kamar yadda kuke so ba wallahi, idan zan nemi aure a cikinku akwai wadda ta isa na yi wasa da hankalita, abinda Allah da Annabinsa suka halasta mini me yasa zan ji tsoron wata hallita wadda take da rauni kuma take a k'arkashin ikona........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK.* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *163* Share shi na yi ban 'kara tanka masa ba ba kuma don ba ni da abinda zan ce ba. Na tashi na sauka k'asa jikina babu wani karsashi ya rantse da Allah ya kara rantsuwa ba zai iya auranta ba to yaudararta zai yi kenan tunda shi ma zuwa yanzu ya gane sonsa take yi muddin bai fito fili ya nuna mata baya ra'ayinta ba za ta cigaba da bibiyarsa da zaman saurare daga gare shi tunda yana sayan kayanta yana kuma bata kudi yawanci mu mata wayayene shi yanzu ga abinda yake cikin zuciyarsa a game da ita duk da ba wai ya bankad'a mini zuciyar tasa ya yi na gani ba amma dai akwai k'amshin gaskiya a maganarsa don da ya na sonta da niyyar aure ba zai yi rantsuwa da Ubangiji ba tunda ya san girmansa. Shirunsa da yanayin yadda yake mu'amulantarta shine abinda zai k'ara mata kwarin gwiwa ta ji a ranta kamar buk'atarta za ta biya domin samun nasarar mallakarsa duk abinda take yi a kansa da wanda ya dangance shi sone ba wani abu ba. Bandir din atamfofin irin mai sha biyu ce bandir shida kuma mabambamta ba duka iri daya ba ne, sun yi kyau sosai duka cotton irin 'yan dubu goma nan ne da ake ya yi idan za a yi ankon biki. Duk abinda ya kamata da a yi na al'ada da fita hakki su anti Yagana sun yi hatta da atamfofin sai da suka d'ibarwa Hajja nata duk da ba ta yi wata gayya ba amma ai tana da jama'a a can garin Dambatta idan ta koma gida sai ta raba. Nama kuwa da aka soya zallar tsoka da yawa suka zuba mata cikin fanteka tace ya yi yawa Hajiya Saratu ma kad'an ta d'iba yayin da inna Uwani ta yi kamar ta dora hannu aka ta dinga rusa ihu ganin yadda Hajja ta ce da masu aikin su kwashe nama ta d'ibi daidai gwargwado. Hauwa d'anye ta kar'ba ba ta bari an soya ba ita kuma Inna Uwani koda anti Yagana ta nuna mini wanda ta zuba mata na ce ya yi kad'an ta 'kara ashe duk da haka ba a yi mata gwaninta ba ta ji haushi sosai saboda Hajja bata kar'bi naman da yawa ba ta bawa masu aiki. Su kansu su anti Yagana sun samu soyayyan nama sosai fatar shanun na sanya aka gyara musu (Ganda) da kawunan suka d'iba Sahura ma ta d'ibi daidai gwargwado sannan sauran na sanya baba Tabawa zubawa a buhu biyu yan gidanmu Ummansu Hadiza gabad'ayansu dai da suka zo tare na ce idan sun je sai su yi rabon a tsanake a tamfofi kuwa kowacce sai da ta tsira da turmi shida duka cikin kowane bandir sai da kowa ya samu har da ragowar wasu. A ranar da muka yi walima k'warai na samu alherai masu yawan gaske daga wurin manyan mutane daga cikin abokanansa da suka samu. Kud'i kaman sai godiya yara sun samu kaya masu yawa. Babu shakka kowace haihuwa da goshinta don haka ni dai ba ni da bakin magana sai dai godiya ga Allah. Washe gari masu aiki na ta hidimar gyara gidan ciki da wajensa. Su anti Yagana na ta had'a kaya don 'yan gidanmu ma su Ummansu Hadiza da sassafe suka d'auki hanya bisa bin umarnin Babanmu ya ce su taho lallai shi kuma maigidan ya yi musu shirin tafiya cikin mutunci da rufin asiri don da ya ji a motar haya suka zo ya yi fad'a sosai har yana cewa lefina ne nasan za su zo mai yasa ban gaya masa ba tun daga can ya sanya a kawo su ya fi nutsuwa. Sahura na ta gyara mini wardrobe ita kuma Yusra na shiryawa yaran kayansu. Hauwa ta aiko Khalil wai na bata atamfa turmi bakwai jin haka Ya Falmata ta fara fad'in ba a d'ibar mata ba dama." Sahura ta ce." Ni na d'ibar mata turmi shida cikin kowane bandir na d'auki daya." Ta ce." To kuma wace atamfa za a bata." Anti Yagana ta ce." Tunda da akwai a bata mana wata'kila wani zata bawa." Yaron ya ce." E, na ji suna magana da inna Uwani za ta tafi da su can bauchi ta yi rabo." Ya Falmata ta dube ni tana ta'be baki ban ce komai ba na ce da Yusura ta d'ebo abinda suka rage saura turmi sha uku gabad'aya na ce a cire bakwai din da suka buk'ata a bashi ya kai mata. Bayan fitarsa Ya Falmata ta kwashe ragowar kaf katon kwalin da suka shirya kayansu a ciki ta watsa atamfofin tana fad'in." Ke ma kina dangi idan mun je gida za a ba su ke da haihuwa wata da iko da kayanki idan haihuwar biyu banza ne ta yi zuciya ta yi." Sahura ta dinga dariya tana fad'in." Wallahi baiwar Allah nan Hajja tana burgeni suruka ce tagari babu ruwanta da sa ido akan duk abinda yake faruwa ki ga dai uban naman da a ka bata ta dibi kad'an ta bayar da shi. Hauwa da mamanta sai ka ce mayu ita tsabar rashin yarda ma d'anye ta sanya a ka kai mata gida kamar ita ta haihu." Anti Yagana ta ce." Abu dai ya wuce alhamdulillahi an tashi lafiya wata matsala dai ba ta faru ba ni na gaji ma da zaman nan wallahi Ya Falmata tunda mun had'a kaya an jima muna yin wanka mu kama hanya." Na ce." Sai dai gobe tunda ya fita kuma har yanzu bai shigo ba ai ba za ku tafi ba tare da kun yi masa sallama ba." Ta ce." Bashi muke bin sa da sai mun jira ya dawo Amina." Na ce." Duk da haka dai anti Yagana a bari ya dawo din ya fi mutunci." Ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba. Itama Ya Falmata din ba ta tanka ba maganar dai da take ta jaddada mini shine kada na yarda ya auri Nabila domin babu haske a cikin al'amarin. Yadda ta zafafa sosai abin har mamaki yake ba ni, kishi take taya ni sosai Hauwa ma don dai tana ciki ne muna tare da yaranta babu yadda za a yi da ita. Ba su tafin ba kuwa sai da gari ya waye tara na safe sun fito lokacin Masa'udu ya kwashe kayansu tsaf ya kai mota su Hajja na d'aki ba su fito ba muka shiga tare muka same su ashe inna Uwani a gidan ta kwana duka muka gaisa cikin mutunci da raha. Ya Falmata tana fad'in." Bako zai yi halinsa Hajja mun yi shirin tafiya, mun gode sosai Allah Ya kara girma yara kuma Allah Ya raya su." Ta dinga amsa da "Amin mune da godiya Allah Ya saka da alheri." Tare da ni su gabad'aya muka yi musu rakiya bakin mota suka shiga Ya Falmata da anti Yagana ita Sahura sai gobe yadda muka yi da ita za su tafi. **** To sati uku da haihuwa gidan na mu ya daidaita kamar ba a yi wata dabdala ba kowa ya watse an bar ni da yara da masu aiki kamar yadda muke a da. Hassan da Usaini basa zuwa hannuna sai idan yunwa ta kawo su suna can wurin Baba Tabawa da taburni da daddare ne kawai nake kwana tare da su, shima maigidan muddin ranar girkina ne sai dai ya sakko kasa ya same ni a d'akina. A tsukin suka tafi saudiya umara shi da Khalil kamar yadda ya fadi ranar dana haihu. Sati biyu suka dawo a cikin satin kuma ya sabunta mini komai na gidan tun daga kasa har zuwa sama komai sabo da sabbin kayan kicin abin dai kamar wata sabuwar amarya. Hatta da kayan da yara suke sanyawa sai da aka fitar da su aka yi musu sabbi Taburni da Mairo sune masu iyali a kauye Kuma sune masu wahala da yarab na ce su kwashe suka kuwa cika manyan bacco suka ajiye da jiran lokacin ziyara tunda sun ce sai sallah za su ganin gida yanzu muna daf da shiga wataran Ramadan kuma a watan dai za su tafi umara in sha Allahu rabbi. Tun bayan watsewar kowa Hauwa ma ta d'auke kafarta tun ma dai washe garin ranar da muka yi walima ba ta sake shigowa ba, hakan bai wani dame ni ba dalili nasan dama abin ba d'orarre ba ne. Na ma yi mamaki sosai da ta iya jurewa a yadda na santa da tayar da fitina har aka gama wannan kacaniyar ba ta ce ga abinda aka yi mata ba. Shi kuma daga nasa bangaran babu yabo babu fallasa ya ce muna damunsa da maganar Nabila zai fita daga harkar kowacce domin da akwai abubuwan da suke gabansa ba mu isa mu raba masa hankali ba. Da gasken ne sabgogi sun yi masa yawa domin tunda suka dawo daga umara shi da Khalil bai fiye zama a gida ba. Ya je Kano kusan sau uku a kasa da sati hud'u. Ba ma shi da lokaci sosai idan ya dawo da daddare ya ci abinci ya dinga lissafi kenan yaran ba kasafai yake zama da su sosai ba, na yi wankan tsarki tuntuni amma bai lura ba saboda abubuwan da suka sha kansa a tunaninsa har yanzu ina cikin jinin 'biki bai ta'ba nema na ba sai dai 'yan ta'be-ta'be kafin a kwanta. Order na yi daga kano wurin GARKUWAR MATA 08089965176 package irin na masu jego na ce ta had'a mini na aminta kuma na gazgata sahihancin maganinta shiyasa ba ni shakka da shakku a ko'ina zan yi mata TALLAH da k'umaji da karsashi. Ta kuwa yi mini delivery har garin Abuja na sanya Masa'udu ya je ya kar'bo komai cikin girma da arziki nannad'e da salatif. Na durfafi gyara jikina domin bahaushe ya ce wai idan kana da kyau ka kara da wanka. Yau da yake girkina ne baya gari ya tafi kano Amma ya ce lallai a gida zai kwana. Na yi tatul ta ko'ina kuma buk'ata na ke ji. Sosai yau kwana hamsin da shida da haihuwa na dawo Amina sosai Ado da kwalliya na yi mai kayatarwa don an sake yi mini wani sabon lallen ma baya wanda aka yi mini na bikin suna ba. Sai yanzu na sake gazgata alfanun raba gida hankalina a kwance yake sosai a yanzu Hauwa na can gidanta ni ma ina nawa duk ta ta zame mini jiki amma wallahi watarana har mancewa nake yi da ita mussaman yanzu da muka sake yaiwata a gidan ko ta ina babu kad'aici akwai kuma fahimta mai kyau da masu aikina muna girmama juna Na kudi ne littafin nan kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. mutuntawa tabbas da maza da yawa za su gane jin dadin da kwanciyar hankalin da yake tattare da rabawa iyali mazauni da dayawa ba a sa samu rikici da rabuwar kai ba. Khalil ne yakan d'an je gidan jefi-jefi wataran kuma idan babu makaranta ya ja 'yan uwan su je su d'an zauna mata babu kuma wata matsala da ta ta'ba faruwa dalilin zuwansu nasu domin yadda na fahimta so take itama ta ja su a jiki ta samu irin soyayyar da suke mini har sultan yanzu ya daina tsoronta da shi suke zuwa idan za su tafi hakan yana yi mini dadi sosai yaro ne Khalil amma mara mantuwa shiyasa ake cewa idan za ka yi sharri ko wani abu na rashin kyautawa kada ka yi a gaban yaro dalili baya mance abu. Yanzu da ya fara girma ya gane cewa mamansa itace matsalar gidansu gashi a aikace cikin hikima yana ta ko'karin ganin ta gyara ta dawo mutuniyar kirki tunda ba zai mance abubuwan da suka dinga faruwa ba. A bakin yaran nake jin Ladidi suna yawan kiran sunanta sai da na tambayi yaron wacece ita yake gaya mini mai aiki ce da ta zo daga bauchi sunanta Ladidi take wasa da su tare da yi musu tatsuniya ashe kenan an kawo mata mai aiki wata'kila ma ta jima domin lokacin da ta jibgi danyen naman nan na yi ta mamakin yadda za ta yi dashi Ashe tana da mai yi mata hidima ko tare suka zo da inna Uwani Allah ne ya sani. Sai dare ya dawo bayan ya yi wanka ya ci abinci ya bukaci ganin yara har saman suka same shi ya kuwa kasance da su na tsayin mintina talatin ana ta gaisuwa masu hawa jikinsa na yi masu tsokanarsa na yi Usaina ce me jan gemunsa tana fad'in ya yi fari furfurar ce bata iya fadi ba har tana nuna masa sabon kitson hannu da Taburni ta yi musu tana cewa." Ka ga nawa ba'ki naka kuwa fari baba ka goge ya dawo irin nawa." Tana ta jan gemun yana dariya kallonsu kawai nake yi har suka gama ya ce su sauka k'asa zai huta da suka fita d'akin ya rage mu biyu ya ce." Na ga lokacin da zan huta Amina, wallahi jikina ciwo yake mini ga shekaru ga wahalhalun rayuwa." A takaice na ce." Sai sai shekarun amma kai yanzu har wata wahala kake Sha?" Ya d'an harareni yana fad'in." A a ba na sha a kwance nake samun kudin tunda mafia nake yi." Dariya maganarsa ta ba ni na yi a takaice ban ce komai ba sai kallonsa da nake yi masa Ya yi kwafa yana cewa." Yarinyar nan Nabila nema take yi ta matsanta mini fa wai zuwa ta yi can wajan Hajiya Ayya mahaifiyar Alhaji Ahmadu akan na aureta." Ban ce komai ba sai Ido mu je dai zuwa. Jin ban yi magana ba ya sanya ya ja goron numfashi kafin ya furta." Ni yanzu karfina duk ya 'kare kun karar mini da shi bana ji jin zan iya ajiye mata uku a yanzu kuma kowacce tana jira na kwanta da ita ni na fara gajiya wallahi." Duk yadda na kai ga dannewa sai dariya ta subce mini na ce." Haba kaine fa na ji kana fad'in babu abinda ya fi wannan sabga dadi a duniya kuma sai kace ka gaji." Ya furta." Da gaske na gaji Amina duk da sunna ce mai kyau ai duk fafutukar da na dinga yi a baya wallahi ina son haihuwa ne, Ubangiji Allah Ya ba ni sai godiya yanzu ma ban ce ba ni so ba ina neman kari ina nufin abinda aka yi a baya yanzu ba za a yi ba." Na girgiza kaina ina kallonsa kafin na ce." To sai ka ce mata me?" "Na ce sai na yi shawara tukkuna." Na yi 'kasa da kaina ban sake cewa masa komai ba saboda takaici wace shawara kuma ya fito fili ya gaya musu gaskiya daga ita Nabilan har wadda ta yi kamun k'afa da ita tunda babu buk'atar aurenta a ransa babu amfanin yi mata yawo da hankali. A daran dai wani lamari ne ya kasance a tsakani na dashi mai armashi da wahalar mantawa. Soyayya bata tsufa muddin za mu had'u muka zama tamkar sabbin ma'aurata ah to me za a fasa tunda da rai da lafiyar da kuma sauran kuruciyar shima duk fadi yake yi ai yana shiga hannu ya fara makyarkyata tamkar wani d'an magyaru! GARKUWAR MATA ta gama gigita lissafin attajiri sai ya dawo ustaz a daran yabo da kalaman soyayya a cikin harshen labarci ya dinga zuba a yayin da jikinsa yake tsananin neman abinda duniyar ta ginu a kai. Allah Ya sa mu dace Amin. *** Kwana biyu haka muka dinga gwangwajewa Muna shan soyayya a kuma wannan lokacin ne dana samu dama na gaya masa bukatata kan kyautar da ya yi mini da farko ya ce a a bai ba ni don na sayar ba yanzu haka ana ko'karin sabunta takardun wajan da sunana don haka babu niyyar sayar da shi a tsarinsa. Na yi ta ko'karin ganin na ganar da shi nufina ya ki ya ce idan ba ni so kawai na gaya masa ba zai yi mini kyauta ba kuma na canza masa tsari ba ana cigaba da gudanar da abinda ake yi a kamfanin duk abinda ya kama na shiga da fita mallakina ne. Ganin bai amince ba sai na kyale shi. Da yaje ya yi kwana biyu a gidan Hauwa ya dawo na ce masa ina so ya ba ni rancen kudi tunda dama wanda na samu na wurin larabawan nan suna hannunsa bai sa mini cikin acct dina ba. Babu wata fargaba ya tambaye ni abinda zan yi da kudi kuma nawa nake buk'ata. Na ce miliyan hamsin. Ya jima yana kallona kafin ya furta." Me za ki yi da su?" Da mamaki sosai a tare da shi ya yi mini tambayar." Na ce." Kasuwancina zan kawo nan garin zan kama shaguna cikin wuse market na zuba kaya tunda yanzu raba 'kafa ake yi." Ya ce." Yaushe za ki biya ni?" Na ce." Mu yi a rubuce shekara uku ko hud'u, in sha Allahu rabbi zan biya ka kudinka." Ya gyad'a kansa yana kallona kafin ya furta." Ki ce kawai na baki kudi Hajiya kai tsaye amma ai kin san babu rance a tsakaninmu ko?" Na gyad'a kaina ina fad'in." Da akwai mana idan da yarda da amana ko kana ganin ba zan iya biyanka ba?" Girgiza kansa ya yi kafin ya ce." Za ki iya tunda me nema ce ke amma ki bari zan yi shawara akan hakan. Zan kuma sanya miki kudinki da suke hannuna." Na 'bata rai tare da cewa." Tunda sai ka yi shawara za ka ba ni me yasa ba za ka amince da shawarata ta farko ba abin nan ni ka ce ka bawa to me yasa ba za ka bari na yi iko da shi ba ashe kyautar ba har zuciyarka ka yi mini ba tunda ka hana ni na yi iko da shi." Ya furta.'' Ai ni ban baki don ki sayar ba, kin ga kuwa babu wani dalili da zai sanya ki ce mini na ba ki umarnin sayarwa, amma dai yanzu tunda na ji hanzarinki ki bari na yi tunani tukkun ko an gaya mini haka ake tafiya kai tsaye komai yana buk'atar nazari da tunani." Shiru na yi ban sake yi masa wata magana ba, muka cigaba da tafiya a haka shima bai sake tashin maganar ba ya kuma sanya mini kudina da suke hannunsa kamar yadda ya fad'a. Ranar wata lahadi da sassafe na hau saman na same shi da yake a d'akina nake kwana wataran ya biyo ni mu kwana tare ranar da yake da ayyuka kuma ko ya biyo ni yana fita idan muka kammala uzurinmu. Na same shi suna bidiyo call da Kamalu shigowata d'akin na ji yana fad'in." To ga tanan ma ta shigo Amina zo ga Ustaz sunan da yake kiransa da shi kenan tun lokacin da ya dawo daga makarantar horon da muka kai shi ni da Hamusu. Na zauna cike da wani irin farinciki. Tunda ya tafi ba mu gaisa ba kusan wata uku da wani abu bana jin ma sun yi magana da Hajja don da sun yi din za ta gaya mini......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *164* Mama ya kuke ina fatan duk kuna nan lafiya."Na kasa 'boye murnar ganinsa cikin suttura da nutsuwa tare da wata iriyar kamala ta mussaman na amsa idona a kansa. Lallai Ubangiji shine isashshe idan har mumini ya yarda da kaddara da jarabta ya kuma kar'bi abinda Allah ya wanzar a rayuwarsa tabbas hakuri da tawakallin da ya yi zai haifar masa da wani irin farinciki da murmushi na mussaman daga wajan Ubangiji. Yana zaune yana kallonmu shima fuskarsa a sake da alama ya ji dadin ganin yanayinmu ni da yaron ya dinga murmushi bai dai tofa ma komai ba a cikin maganar da muke yi har muka kammala ya juyo kansa suka yi magana kad'an kafin mu yi sallama gabad'aya ya kashe wayar yana kallona har yanzu da murmushin a fuskarsa idonsa a kaina ya furta." Na jima ban gan ki cikin nishadi irin wannan ba Giwa, ke ko kunya ba ki ji irin ta iyaye da yaransu na fari." Ni ma da murmushi a fuskarta nake kallonsa haka kawai sai na ji wani bala'in sonsa ya kara ninkuwa a cikin raina. Tabbas da sanya hannunsa da kuma kokarinsa tare da tasirin addu'ar da muke yi Kamalu ya kai matakin da yake a yanzu. Na hangi abubuwa da yawa a tattare da yaron kuma ni ma na yarda bayan wahala sai dad'i kamar yadda da yawa mutane ke fad'in akwai haske cikin lamarinsa ina ji a jikina yaron zai zama abin alfahari gare mu bakid'aya.. Na ce." To ai ni ba mutuniyar da ba ce, addu'a kawai fa na yi masa akwai abinda na yi na rashin kunya bayan wannan?'' Ya girgiza kansa yana kallona bai ce komai. Na kama hannuwansa a hankali na sanya idona a cikin nasa na ce." Ba ni da wata kalma da zan yi amfani da ita wajan nuna godiyata a wurinka. Ka cancanci duk wani abu a wajena na gode Allah Ya saka da alheri yadda ka tsaya mini akan yaran nan ka ke yi musu wahala da jiki da dukiyarka Ubangiji Allah saka da alheri. Yaranka Allah Ya kula da su." Ya matse hannuna dake cikin nasa a nutse ya ce." Babu buk'atar godiya a tsakanina dake Amina ni ma ai kin yi mini alheri, kin cancanta kuma abinda ki ka haifa da wani namijin na sha gaya miki ki sa a ranki kamar da ni ki ka haifa, ni ne ubansu har yanzu kuma abinda nake ban yi domin a yi mini godiya ba ina neman aljannata ne." Na ji idona ya ciko da ruwan hawaye kuma duk yadda na kai ga ganin na hana su zuba sai da suka kwaranyo ina so na yi magana na kasa kawai sai na fashe da kuka. Ya kuwa ki'dime jikinsa har yana rawa ya d'an rungume ni a jikinsa yana fad'in." Menene kuma abin kuka abinda zai b'ata mini rai kenan me aka yi da za ki yi kuka Amina?" Na kasa cewa komai saboda maganar ma da yake yi ta sake raunatar mini da zuciya na dinga yi cikin k'aramin sauti ya matse ni tsam a jikinsa yana dago fuskata tafin hannunsa yasa ya dinga goge mini fuska. Na daure da yar rawar murya na ce." Na dai gode kuma ba zan fasa godiya ba Allah Ya saka da alheri." Ya yi shiru bai ce komai ba sai shafa fatar hannuna yake yi ya kama hannun ya sumbuta a tsanake ya furta." Godiya za ki yi ga Allah ki kuma ajiye a ranki cewa yaranki ba za su yi maraici ba muddin ina raye. *** To wannan ya wuce da sati uku muna zaune kalau zuwa yanzu hankalina ya d'an fara kwanciya dangane da lamarinsa da Nabila domin kuwa bayan rantsuwar da ya yi mini tun farko kan cewa ba zai aureta ba ya sake yin wata tare da jaddada mini cewa ko da Allah ya sake k'addara masa aure to ba ya tunanin zai auri mace kamar Nabila saboda a cewarsa ya hangi tarin matsaltsalu mabambamta daga wajenta. Ranar dana kar'bi girki ya shigo da yamma anan gidana ya yi wanka ya shirya ya ce mini akwai ba'kin da ya yi yanzu zai fita zuwa guesthouse din shi.. Yana tsaka da kimtsa jikinsa Hajja ta kira ya daga suka gaisa da yake handsfree ne duk Ina ji tana tambayarmu da yara ya ce mata kowa lafiya sai na ji tana fad'in. "Ashe neman aure ka ke yi ban sani ba?" Ya kuwa diririce ya juyo ya dube ni da sauri dalili yana da tabbacin na ji abinda ta ce tunda murya ya bud'e.. Ya nemi gefan gado ya zauna da wayar a kunnansa yana sauraranta ni ma duk Ina jin abinda take gaya masa wato Hajiya Ayya ta je har gida ta same ta maganar Nabila domin a yadda ta yi mata bayani ma tana gaya mata sun daidaita junansu amma shi ya ce mata ta d'an saurare shi sai bayan sallah sai a d'aura auran tunda daf muke da mu shiga wataran azimi. Ya cika da mamaki ainun gabad'aya yanayinsa ya canza da b'acin rai ya shiga rantse mata da Allah kan cewa bai san da maganar ba Nabila dai tana sonsa tuntuni ya gane amma bai yi mata alkawarin aure ba, duk abinda ta je ta gayawa Hajiya Ayya karya take yi. Hajja ta ce." To ni dai abinda ta zo ta gaya mini kenan sai nace ban sani ba don baka gaya mini ba amma zan tambayaka na ji shin da gaske ne?" Ya girgiza kansa kamar yana gabanta ya ce." Karya take yi wallahi ban ce zan aurta ba." Ta ce." Ba ka ce zaka aureta ba amma ka san tana sonka tunda gashi ka fadi da bakinka me yasa ka biye mata har aka yi magana da kai kace za ka yi shawara idan da ni za ka yi shawara to babu yawuna ga mata nan da yawa a gari idan lallai auran zaka 'kara ba zan hana ka ba, domin na fahimci tunda aka samu akasin auranka da yarinyar nan Hajara ka ke ta kame-kame babu yawuna wajan auran Nabila kanwar Maryam domin idan ka manta ni uwarka ban manta ba. Abinda ya faru a baya ba ni fatan ya sake faruwa ba. Idan za ka yi aure ka duba nagarta da cancanta kada kyale-kyale ya rudeka ka jefa rayuwarka a masifa ka jefa jama'ar da suke kewaye da kai. Tunda zuciyar taku a haka ta ginu kuma kana ji kana da kudi za ka iya to sai ka zo nan d'ambatta a duba maka wadda ta dace wadda kuma zata zauna lafiya da iyalinka." Ya furta.'' Babu ma buk'atar karin aure a yanzu Hajja, kuma in sha Allah yadda ki ka ce hakan za a yi dama ba ni da ra'ayin auranta a cikin raina." Ta ce." Abinda na gayawa Hajiya Ayya kenan zan tambayeka na ji ta bakinka wata'kila duk bada'kalar da ta faru ba ta da labari shiyasa har ta iya zuwa ta same ni domin na hada jini da dangantaka da zuriar Maryam Allah Ya yi mini tsari da su." Haka suka yi sallama ta yi masa tas! Ya kashe wayar yana kallona a hargitse ya ce." Wato duk kara da kawaicin da nake yi wa yarinyar nan ba ta duba ba take bin iyayena har tana fad'in mun tsayar da magana bayan sallah d'aurin aure ni mahaukaci ne Amina?" Na d'aga kaina alam e amma ban ce komai. Ya nuna kirjinsa da yatsa yana fad'in." Mahaukaci ne ni ko?" Shiru ban ce masa komai ba dai ya d'auki wayarsa da sauri yana fad'in." Kin ga ni da idonki na goge lambar wayarta tunda bata da hankali ni me zan ci da yar banza." Bai goge ba ya sake kallona yana cewa." Kafin na goge yana da kyau na yi mata gargadi ba ni son sakarci da shirme?" Na ce."Tambayata kake yi?" Ta gyad'a kansa na furta." Lokacin da ku ka yi serving lambar juna ai baka nemi shawarata ba. Me zan ce maka yanzu duk abinda za ka gaya mata domin ta kiyayeka ka sani ba sai ka nemi shawarar wani ba. Ya ja tsaki yana fad'in." Dogon rubutun ne ba ni so ai kar'bi ki shiga Whasap din ta ki rubuta mata cewa ba na sonta babu kuma maganar aure a tsakaninmu ta nemi miji daidai da ita ta aura. Na sanya hannu na kar'bi wayar kamar zan bi umarinsa. Whasap number dinta na shiga ya yi serving da sunanta Nabila. Nan na dinga cin karo da stickas na soyayya da gaisuwar Juma'a iri iri tare da wasu irin wasik'u da kalaman soyayya masu motsa sha'awa irin dai yadda matan bariki ke janye hankalin mazan mutane. Gasu nan birjik kuma idan ta turo yana bud'ewa ya gani amma bai mayar mata da martani ba. Maganarsu da ta d'an yi tsayi akan tallan kayanta da ta yi masa shine ya kula ta har ya yi mata rubutu a takaice ya ce da ita yana so zai saya. Kunya da takaice suka hana ni cewa komai na yi kasa da kaina tsabar b'akinciki wasu matan dai rako wasu suka yi duniya. Babban abin b'akinciki da takaici shine ka turawa mutum sako ka tabbatar ya gani kuma yana hawa online bai baka amsa ba gobe ma ka sake tura masa saboda rashin zuciya messages kuma irin na soyayya da nuna kulawa har da fatan alheri amma mutum ya share abin da ciwo sosai amma ita kamar kidahuma mara sanin ciwon kai ko wannan ma kora da hali ne an nuna ba a yin ki a fakaice amma kin nace su kansu wasikun da suke d'auke da zantukan soyayya masu tattare da batsa babban dalili ne da zai sanya ya k'yamaci auranta bayan wad'ancan dalilah masu girma. Duk wayewarsa a gida yake yi a d'aki kuma tare da iyalinsa akwai gogewa a wannan fannin kam yanzu ya yi mata wannan wulakancin tana sake ma'kale masa sautari maza sun fi naci da bibikon macan da take wahalar da su wadda take nuna musu so da k'auna kuma sai su d'auketa sakarai su yi ta wasa da hankalina kamar dai yadda yake yi mata a yanzu ta kasa ganewa. Na dube shi ina fad'in." Ashe ga dalilin da ya sanya ka kasa fitowa ka gaya mata gaskiyar abinda yake zuciyarka. Tana yi maka irin wannan zantukan na rashin mutunci ai ka ga duk ranar da ka fito fili ka gaya mata ba ni da ra'ayin auranki za ta daina turo maka kai kuma ba ka so ta daina kana so ta turo ka karanta domin ta motsa maka sha'awa ko? Ba ka ji kunya ba don girman Allah. Wataran fa sai dai ka ga ta d'auki hoton wani sashi na jikinta ta turo maka tunda baka tsawatar mata ba ka yi shiru hakan ya nuna mata cewa ta cigaba kana so tunda yar iska ce ita wallahi tallahi ka yi bala'in bani mamaki." Ya yi shiru jikinsa a mace ya kar'bi wayar yana dubawa messages din da ta tutturo. Ya jima yana karantawa daya bayan d'aya kafin ya dube ni yana fad'in." Bai zama lallai ki yarda da abinda zan fadi ba. Amma ki sani cewa ban ta'ba tsayuwa na duba messenges dinta ba balle na fahimci abinda yake a rubuce. Wannan stickers din kuma idan kin lura wasu sun bud'e da kansu wasu kuma ba su bude ba, ba ni da lokacin wannan sakarcin nata kuma ban san da cewa bata da hankali ba sai yanzu." Na jima ina kallonsa da ko'karin gazgata maganarsa za ta iya kasancewa gaskiya ne abinda yake fad'i tunda wasu sticks din ni na bud'e su da hannuna Rubutu da karantawa abu ne da dama can yake bashi wahala k'aramar magana idan zai yi ya fi gane ya kira waya zaman sa ma a online babban jidali ne domin da ya hau baya mini goma cikakku yake sauka sai wata goben Kuma idan kuma ka gan shi a online tabbas akwai muhimmin abu. Na ce." Ka dai ji tsoron Allah wallahi tallahi kuma ka suturta furfurarka ka haihu mata gasunan a gabanka duk abinda za ka yi ka tuna Allah Ya na ji yana kuma yana kallonka sannan kaima kana da zuria. Ya yi bala'in shan kunu! yana fad'in." Me ki ke nufi ne Amina duk bayanin da na yi miki ba ki aminta ba, har yanzu kin kasa fahimtar abinda zan yi da wanda ba zan yi ba, bayan rantsuwa da Allah da na yi hakan bai yi miki ba kina ganin akwai abinda na boye wanda nake aikatawa, idan har na fahimci maganarki anan kina so ki ce mini ina neman matan banza a waje?" Na ce." Ni ban fad'i hak..... Ya katse ni ta hanyar buga gefan katifa da hannunsa na kalle shi cikin kad'uwa da mamaki yanayinsa gabad'aya ya canza. " Ya furta." Ba ki fad'a ba na yi miki k'arya kenan kuma za ki k'aryata kan ki ne, gashi kina misali akan yarana idan na 'bata na wasu ni ma za a 'bata nawa. Duk tsayin shekarun da na yi a can baya ban yi aure ba kuma ban yi zina ba sai yanzu da girmana da kuma shekaruna. Kin jima kina kausasa mini kalamai irin yadda ranki ya so, ba ki da mutunci wasu lukutan ba ki daraja ni, kuma ba kya kar'bar kuskure da ajizancina. Idan ina neman mata tsayin zamana dake duk takatsantsan dina watarana za ki gane hakan me yasa ba ki da kirki ne Amina." Cikin tashin hankali nake kallonsa ganin yadda gabad'aya ya rikice har zufa yake yi kamar ba wanka ya yi yanzu ba fitowarsa ya kashe Ac din dake d'akin. A rikici da b'acin rai ya nuna ni da yatsa yana cigaba da cewa. " Idan har zan nemi matan banza bari na gaya miki yadda nake fitacce masu aji da tsabta zan nema irina ba irinsu wannan matar ba da kuka matsanta mini a kanta ba, ina so ki kara sani ni mutum ne mai kishi idan ba dole ba da kuma 'kaddara ba ba ni so na yi tarraya da abu wani ma ya zo ya yi, ban ta'ba sha'awar wannan harkar ba duk tarin ni'imar da Ubangiji ya yi mini, abinda kuma ki ke fata ya kasance kan abinda muka haifa ba zai faru ba tunda ban yi ba Allah ba zai jarrabe ni ba." Daga haka ya tashi tare da d'aukar hularsa ya sanya ya nufi ma'adanarsa da yake ajiye gilasansa ya zari daya ya sanya ya kwashi wayoyinsa ya kama hanyar fita babu annuri a fuskarsa. Shiru na yi bayan fitarsa na gaza tab'uka komai saboda mamaki yadda ya burkice. Can k'asan zuciyata na ce mini tabarmar kunya ce fa yake nad'eta da hauka domin ya k'waci kansa duk hargagin banza ne. Na yi shiru sosai ina sake nazarin maganganun da ya furta. Tabbas kamar yadda ya fad'i mutum ne mai tsananin kishi. Tun bayan haduwarmu ta farko a ofis dinsa da ya zo mini da maganar banza bisa wata hujja tasa to tun daga lokacin ban sake ganin wani abu na sakarci da b'acin suna daga wajensa ba. Yana da ibada daidai gwargwado sadaka kyauta ciyarwa kulawa da marayu wasa da dariya da iya mu'amula. Da'biarsa mummunan da na sani gaba da k'ullaci kuma cikin ikon Allah da zama ya yi zama a tsakaninmu ya rage. Ban ta'ba cin karo da wasu alamu da za su nuna shi din manemin mata ba ne gaskiya idan na ce na gani na yi masa sharri tunda a yanayin yadda yake mu'amulantarta a shimfida ma wannan ya isa sheda da tabbatar mini da cewa bashi da lokacin bibiyar wasu matan a waje. A yanzu dai idan na fahimci abinda ya hasala shi bai wuce don na ce ya ji tsoron Allah ba saboda shima ya haifa wannan maganar itace ta tunzura masa zuciya har ya fita da b'acin rai! Mai tsanani hakan na tabbatar mini da cewa ya ji ciwon maganar sosai kuma abinda duk ya fad'a gaskiya ne yau kan an kira ni da mara mutunci mara kirki dole na bada ha'kuri Allah Ya sawwa'ke.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *165* Ban yi zaton fushin zai tsananta da yawa haka ba. Tunda a daran ranar da lamarin ya faru na bashi ha'kuri tare da nuna masa na yi kuskure sai ya dinga ciccijewa haka muka kwana bai ce mini komai ba da gari ya waye na gaishe shi ya amsa da k'yar. Still da ya fita ya dawo da yamma nan ma na sake bashi ha'kurin bai huce ba. Abinci ya'ki ci na dare da jiyan da yau a gidan Hauwa yake zuwa ya ci. Ganin kamar kwantar da kan da nake yi ina bashi ha'kuri yana Kara masa kuzari da karsashin yi mini wulakanci sai kawai na 'kyale shi Hauwa ta kar'bi girki ya je ya yi kwanaki biyu ya dawo mini babu fuska har yanzu zai amshi gaisuwata amma akan dole ko na hau saman na same shi sai ya tsiri aiki a loptop ko ya kira yara su yi wasa. Abin ya fara ba ni dariya da mamaki. Na yarda na yi kuskure kuma ban kyauta ba na nemi afuwa sai a yafe mini ai a cigaba da cud'a rayuwar amma sai ya samu hanyar hura hanci da d'aga kai ganin ina binsa da kwantar da kaina dama dabi'arsa ce haka idan ana ba shi ha'kuri sai ya kara hawa ba zai sauko ba. Gaisuwar ma sai na daina na zura masa ido ko ni nake da girki ba ni hawa saman abinci kuma tunda ya daina ci na daina kai masa. Muka cigaba da tafiya haka tsayin sati biyu babu wani sukuni a tattare da shi domin alamu sun nuna ya fara gajiya yana ta kame-kame. Da daddare na yi shirin kwanciya tsaf ina zaune Ina bawa Hasan nono shi bai yi baccin ba tukkuna ya turo kofar d'akin ya shigo cikin jallabiya k'amshin turaransa ya mamaye d'akin gabad'aya ya had'u da wanda na yi amfani da shi. Na d'aga kaina na kalle shi muka had'a ido sai na yi 'kasa da kaina dama ni ban zafafa ba ai ya nemi wuri ya zauna a gefena babu yabo babu fallasa na sake kallonsa muka had'a ido a hankali na ce." Sannu." Bai amsa ba ya d'ora hannunsa saman goshin yaron yana fad'in." Minal ta ce mini ba shi da lafiya?" Na ce." Lafiyarsu lau fa ta ji yana dan tari d'azu shine take tambayata wai bashi da lafiya na ce mata kalau yake." Ya kar'be shi daga hannuna yana fad'in." Tari ba ciwo ba ne Amina." A takaice na ce." Ciwo ne amma ba irin wanda nake tunani ba. Nono yake sha sai ya d'an 'kware shine bashi da lafiya in ji ta." Ya d'an yi shiru na wani lokaci kafin ya furta." Jiya Hauwa a asibiti ta kwana bata da lafiya!" Na dube shi da sauri " Bata da lafiya?" Ya gyad'a kansa ya ce." Ciwon ciki ta yi sosai daga karshe dai cikin nata ne ya fice! amma alhamdulillahi ta samu sau'ki tana gida." A d'an sanyaye na ce." Ban sani ba wallahi, kai za ka gaya mini kuma kana jin haushina." Ya ce." Gashi yanzu na gaya miki ai." "Allah Ya bata lafiya." Na fad'a cikin jin wani yanayi ta ba ni tausayi wallahi domin ta kallafawa ranta cikin Allah bai yi zai zo duniya ba. Shiru na tsayin lokaci kafin ya kwantar da yaron kusa da d'an uwansa. Ya gyara kwanciya a gadon. Na dube shi yana lumshe idonsa yau anan za a kwana kenan. Bai ji ma da kwanciya ba ni ma na kwanta a gefensa tunda dama na yi shirin kwanciyar. Ya bude idonsa yana kallona ni ma shi din nake kallo wai akace labarin zuciya a tambayi fuska duk kame-kamen da yake yi na gane. Ya d'an janyo ni kusa da shi can k'asa na ji maganarsa yana fad'in.'' Kin yi mini abubuwa da yawa na kyautatawa da kuma alheri ba kuma zan mance ba." Ya nisa kafin ya cigaba da cewa." Wad'annan maganganun da ki ka yi a kaina sun yi mini zafi k'warai da gaske ina so wannan ya zama na farko ya kuma zama na k'arshe kada ki kara dangantani da haramci da abinda Allah ya la'anta. Ki san irin maganar da za ki dinga gaya mini wadda ta dace da wadda ke kanki kin san kuskurene. Ba ni da nufin auran Nabila a cikin raina na fad'a muku maganar ba d'aya ba sau biyu ba wallahi ba ta ta'ba ba ni sha'awa ba balle har na yi tunanin yin zina da ita ba zan boye miki ba har yanzu idan na kalleki na tuna abinda ki ka jingina mini raina yana b'aci wallahi." A hankali na ce." In sha Allahu, Allah Ya ba ka ha'kuri." Ya sauke ajiyar zuciya tare da d'an matse ni a jikinsa shikkenan daga lokacin kuma sai komai ya sauya.. Wai aka ce fad'an masoya hutu ne. Da gari ya waye duk da bai sake yi mini maganar Hauwa ba amma ni da ita na kwana a raina domin yadda ya ke fadi ta sha wahala sosai kafin ma cikin ya fita tunda har sai da aka kwanta a asibiti kwana da yini. Sai da yamma na shirya lokacin yara duk suna makaranta muka tafi da Mairo saboda yaran ita goya Hasan na ri'ke Usaini a kafadata. Mai aikinta Ladidi tana ta goge -goge ita kadai a falon muka gaisa ta ce mana tana ciki a akwance na ce ta shiga ta gaya mata. Minti uku ta fito tana sanar da mu cewa gata nan. Ta nufi kicin da sauri. Mun kai kusan minti goma sha biyar a zaune kafin ta fito daga cikin bedroom dinta ta d'ashe sosai kamar wata mara jini duk sanda take da ciki haka take irin wannan mugun hasken fau! yanzu abin ya hadu da d'aita domin da alamu cikin nan a k'alla zai yi wata hudu zuwa biyar ta sanya rai. Ta ba ni tausayi sosai ta zauna kamar mara laka a jiki babu kuzari da karsashin tana fad'in." Ashe kune in banda shiririta irin na Ladidi ai da sai ta gaya mini cewa ke ce." Na ce." Ba sai ta san ni ba Hauwa." Ta d'an yi murmushi kafin ta ce." E hakane bata ta'ba ganinki ba sai dai labarinki wurin yara." Na gyad'a kaina ina sake nazarinta a nutse na ce. Ya jikin Ubangiji Allah Ya baki lafiya Allah ya mayar da abinda aka rasa." Ta amsa da "Amin suma Amin na gode sosai." Mairo ta gaisheta da jiki ta amsa tana kallon Hasan dake goye a bayanta sai kuma ta dube ni tana yar dariya ta ce." Sun k'ara wayo sosai yaran nan Amina." Na ce." Sosai ni ma na ga girmansu wata uku muke yanzu." Ta ce." Hakane kam." Ta yi shiru tana lumshe Idonta na ce." Za mu tafi Hauwa Allah Ya kara afuwa." Ta bude idonta tana kallona a daidai lokacin dana tashi tsaye ta ce." Na gode sosai." Muka kama hanyar fita ni da Mairo. Na ji tausayinta gaskiya abin babu dadi. Da ya dawo ya ji labarin na shiga dubata ya yi murna sosai yana fad'in da haka kuke yi tun farko ai da na ji dad'i Amina." Kwana biyu ba sai jikin nata ya kara rikicwa ba ranar girkina ne da daddare wajan sha biyu da wani abu lokacin muna shirin kwanciya ta kira waya cikin mayuwacin hali ciwon kai matsananci jini kuma ya tsinke mata. Tare da ni da shi muka nufi gidan a ki'dime lokacin ma ta fice daga hayyacinta mai'aikinta na ta ihu jini ya bata jikinta da bedsheet din da take kwance a kai. Muka gigice ni da shi domin dai kamar babu rai a jikinta. Jikina na tairairayota ina kiran sunanta ko'ina a sake. Ya fita da sauri yana kiran waya. Kuka na fara yi ganin yadda take wata irin jijjiga ina kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! taune lebanta take yi hakan ya tabbatar mini da cewa jijjiga take yi domin duk rik'on da muka yi mata ni da Ladidi sai da ta fi karfinmu. Ya shigo da kansa ya ciccibeta tunda dama ba wani nauyi ne da ita ba. Na ce ya bari tukkuna a kintsa mata jiki domin a 'bace take da kaina na gyara mara jikinta cikin wannan yanayin ya fita da ita rai a hannun Allah muka bi bayansa Sukairaju ya kunna mota. Ya ce da mai'akin ta koma gidan tare muka tafi asibiti a daran emagency da yake sananne ne a take manyan likitoci suka rufu a kanta. Muka kwana a zaune da jiran saurare sai gefin asubahi tukkuna wani likita ya fito ya ba mu tabbacin cewa sun shawo kan matsalar da ikon Allah yanzu haka har an daura mata jini jini tana da buk'atarsa. A lokacin ne hankalinmu ya kwanta ya ce Sukairaju ya mayar da ni gida saboda yara ni ma hankalina yana kansu amma duk da haka sai nake ganin kamar ina matsawa za a ce mini babu ita. Babu wanda na gayawa halin da ake ciki har yaran gabad'aya. Sai Baba Tabawa itace ta sani tunda a hannunta na bar su hassan. Har yaran suka tafi skull ba ni da kuzari na kira shi ya fi sau biyar a safiyar yana gaya mini ta ji sau'ki bacci ma take yi shima gashinan zai dawo domin ya yi wanka. Da 'kyar na iya yin karin kummalo na zauna a d'akina sukuku don yaran ma dana lura za su dame ni da koke-koke na ce da Mairo ta zo ta d'auke su. Na zauna ina ta tunanin rayuwa yadda Allah ya jirkitar da hallitar Hauwa jiya kadai shine abinda ya tsaya mini a raina. Muna ta hauka rai da rayuwa da jin dad'i duka ba a hannunmu yake ba. Hawaye suka ziraro mini kaina ya d'auki caji da tunani da zullumi tare da nadama da addu'ar kada Allah Ya d'auki rayuwarta a yanzu ina so mu yi nisan kwana tare mu raini yaranmu. Wajan tara da arba'in ya shigo. Ganinsa cikin nutsuwa ya sanya ni sauke ajiyar zuciya ba mu yi wata magana cikakkiya ba har sai da ya yi wanka da breakfast tukkuna na fara tambayarsa jikin nata ya ce.''Ta ji sau'ki alhamdulillahi jininta ya hau sosai sanadin damuwar da ta tsanantawa kanta ba ta bacci ga ciwon kai mai tsanani abinda ya fita Allah ya yi ba rayayye ba ne na gaya mata tun ranar da lamarin ya faru tana ta kuka da tsananta damuwa idan da rabo ai za a samu wani." Na ce." Sosai kuwa in sha Allahu za a samu damuwar ai bata da amfani tunda itace ta haddasa mata shiga wannan yanayin. Ya ce." Abinda nake so ta gane kenan, za mu cigaba da ro'kon Allah Ya kawo mana masu albarka." Na ce." In sha Allahu rabbi." A takaice dai sai da ta yi kwana bakwai a kwance a asibiti tukkuna ta warware sosai kullum sai na je na dubata ban taba d'auke rana d'aya ba. Inna Uwani ta zo kwana biyu da suka wuce babu yabo babu fallasa tsakanina da ita Muna gaisawa sai dai babu wani sakin jiki da juna. Yara ma sun je sun dubata sau d'aya masu aikina ma haka. ranar da suka bata sallama da wuri na je ban kuma jima ba na dawo gida. Sai dai ganinsa tsaye a bakin gate din gidan Hajiya Maryam shi da wasu 'kwarori guda biyu da jami'an tsaro abin ya ba ni mamaki da d'an tsaro duk da yana da masu tsaro a kewaye da shi da gidajensa amma ganin shi da wad'annan da kuma 'kwarorin sai abin ya ba ni tsoro yanayin da suke ciki ya nuna kamar akwai matsala. Na hangi fitowar Nusaiba da Adam daga cikin gidan fuskokinsu dai babu nisha'di. Sukairaju ya shige da motar ciki bayan an bud'e gate din hankalina ya kasa kwanciya ko da na shiga ciki gidan kai tsaye d'akina na zarce ban bari sun san na dawo ba. Allah dai yasa lafiya. Na kudi ne don Allah kada ki karanta ba tare da kin biyani hakkina ba Minti goma sha biyar a tsakani ya shigo ya biyo ni har cikin d'akina yana ta fad'a. Ashe wad'an-nan k'warorin abokanan business din Nabila ne mazauna jahar lafia sun kashe wani d'an uwansu suka gudu ita kuma tsautsayi da azal ya sanya da suka kira ta a waya suka ce sun shigo Abuja za su zo su yi magana akan wata harka ta alheri ta gayyace su zuwa gida a jiya da daddare a yadda take fad'a cewa ba ta ta'ba tunanin za su kwana ba balle har ta ba su mafaka domin da suka gama tattaunawa ta yi ta yi da su su tafi suka 'ki suka wayi gari a zaune. A jiyan da daddare akwai wanda jama'an tsoro suka sanya domin yi musu bincike da yake Ubangiji Allah baya bacci kuma cikin gaggawa yake tona asirin hakkin rai mutumin ya gaya musu ga inda mutanan suka fake nan. Abinda ya tsananta domin har itama Nabilan na cikin tasku saboda bincike dole ya bi ta kanta tunda sun ce har da ita da kuma sanya hannunta alhalin k'arya suke yi. Tana cikin gidan taki fitowa sai da ta ji duka tukkuna yanzu sun tasa keyarsu gabad'aya can garin nasarawa lafi'a. Allah Ya tsare mana imaninmu. Da ya gama gaya mini ya shige toilet domin yin wanka ya barni da tu'ajibi da mamaki wai 'ya mace ta'ki kama kanta saboda masifar son abin duniya. Ba a hana mace yin kasuwanci ba amma a yi mai tsafta da aji da kuma ilimi. Gashi dai sun dilmiyata cikin case dinsu bayan su kansu sun san bata da hannu a ciki. Wannan shine abinda ya yi rayuwar Hadiza illa kenan. Ya fito daga toilet din yana cigaba da fad'a tare da jaddada mini cewa ba zai ta'ba sanya hannunsa a cas din ba tunda ba shi ya aiketa ba hanya yake nema dama tunda rayuwar da ta d'aukarwar kanta kenan shikkenan babu ruwansa abinda dama ya sanya shi barin ta a gidan a zaune saboda yaran sun buk'aci hakan ne shikkenan gida za a rufe idan Salim ya tashi aure yana da ra'ayin gyara wani bangare daga ciki sai ya zauna da iyalinsa tunda sun ce ba sa so a sayar kuma ba sa so zuba y'an haya. Adamu zai ba shi za'bi zaman kano gidan Hajiya Ayya wurin kakarsa ko kuma zama anan wurinmu duk wanda ya zab'a daidai ne. Ko da ya tambaye shi kuwa yaro ya ce kano gidan Hajiya Ayya ko gidan Hajja. Ya ce gidan Hajja ya fad'i hakane saboda Yusi ya ce zai yi waya da kakar tasu domin sanar mata da halin da ake ciki. Lamarin nan na jima yana ba ni mamaki da tsoro duniya ta lalace yanzu mutum akan abinsa dukiyarsa sai a halaka shi tunda bincike ya tabbatar da cewa akan kudinsa ne suka kashe shi gashi dai tare suke su uku kuma kowa ya sansu a tare amma an wayi gari sun kashe shi. Abin tausayi da jimantawa ita Nabilan da Allah ne kadai zai fitar da ita. Shiyasa ko abota za ka yi kasan da irin wad'anda za ka yi. Saurin yarda da sakin jiki ga mutumin da baka sani ba sai ya janyowa rayuwarka barazana. Allah ya k'ubtar da ita tunda babu gata ta ko'ina ba uwa babu uba, yan kudin nata da take nema ba su isa su fitar da ita daga wannan masifa ba ga yaranta biyu duk maza sun zama yan samari wata'kila ganin sakarcin da take yi ne ya sanya ubansu kar'be su suna can jos din tunda a can ne ta yi auran kafin ta fito. Yau kwanaki biyar kenan da fitowar Hauwa daga asibiti Hajja ta zo dubata a gidana ta sauka sai da ci abinci tukkuna ta huta sannan muka nufi gidan tare tunda ni ma tun bayan an sallamota daga asibitin ban sake duba ta ba.Kafin mu isa gidan Hajja na jaddada mini jikin Gwaggo babu dad'i kwanakin nan itama tana fama domin ta kwanta a asibiti na kwana uku kafin a sallamota ban ji dad'i ba kuwa ba a gaya mini ba Hamusu bai sanar da ni ba haka zalika ma Yusi. Raina ya baci sosai amma ban nuna mata ba tunda babu halin kalubalantarta. Duk da saura kwanaki mu shiga ramadan hakan ba zai hana ni shirin zuwa dubata ba jikinta ba ta d'an jima a tsaitsaye tana ciwo ashe har da kwanciya a asibiti gashi masu aiki na shirin tafiya umara kamar yadda maigidan ya yi musu alkawari a farkon farkon watan azimi.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *166* Sosai na yi dana sanin bin Hajja zuwa gidan Hauwa da ina da masaniyar abin da zai faru. Wannan shine dalilin da ya sa da yawa wasu daga cikin mutane ba su son yin auran zumunci a tsakanin yaransu koda kuwa akwai soyayya mai karfi a tsakanin yaran akan samu suka da kalubale daga wurin dangi kowa na fad'in albarkacin bakinsa akan zumuntar da za a had'a ta aure wadda ake da burin ta d'ore ta ginu ta kuma kara karfin zumunci tare da albarkar haihuwar yara. Mafiakasari shi auran zumuncin bai fiye yin armashi ba wani tun daga farkon k'ulla shi ake fara cin karo da rigingimu mabambamta wanda ka iya janyo rabuwar kai da tashin hankali tare da zama a teburin sulhu idan ma ba akai zuciya nesa ba har hukuma kan iya shiga domin kawo sasasanci dalili daga kowane bangare yana ganin ba a yi masa daidai ba. Wannan tashin hankalin ya sanya da yawa iyaye suka gwammace su aurawa na waje yaransu domin samun nutsuwa da kwanciyar hankali duk da cewa rikicin aure da matsaltsalunsa abu ne da ya zama ruwan dare ko da babu dangantaka a tsakani a duniya a ka hadu har aka kulla auratayya matsala na faruwa iri-iri tunda dama kafatanin auran ha'kuri ne jin dad'insa kad'an ne. Amma dai da sauki akan ace abu biyu ne suka hadu waje daya dangantaka ta jini zumunta mai karfi kuma da dangantaka ta aure sai abin ya zama wani iri iyaye su shiga idan an kai magaryar tu'kewa lamarin ya yi tsamari a tsakanin jini d'aya a samu rabuwar kai da zargin juna daga kowane b'angare duk domin kiwatar kai bisa zargin zalintar juna. Abinda ya faru kenan da shigarmu gidan Hauwa ni Hajja gaisuwa kawai ta ratsa a tsakani Inna Uwani ta dinga kuka tamkar wadda ta yi rashin jinji nan abu tana fad'in idan abin nan bai zai yiwu ba a rabu tunda akwai maslaha a sha'anin aure Ubangiji da ya umarci a yi shi ya hallata rabuwa (saki) domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali tana kuka tuk'uru tare da jadadda Hajja Hauwa ce kadai ta rage mata a duniya a yanzu tana ji tana gani kuwa ba za ta bari ta yi asararta ba saboda bak'incin da kishiya take gumamata miji ma ya guma mata nasa. Hajja dai shiru kawai ta yi jikinta a mace tana kallonta ita na kuka Hauwan ma na kuka irin mai ciwon nan.. ganin haka ya sanya na yun'kura na tashi jikina a sab'ule gwiwata duk ta sage saboda ganin wannan lamari bai yi mini dadi ko kad'an ba amma Allah ne shahidi idan har ina cutar Hauwa a zamantakewa to ina ro'kon Allah Ya saka mata. Na ji maganarta tana fad'in." Dole ki tafi ki tafi Amina ke ma kin san abubuwan da kuke yi wa yarinyar nan ba ku kyautawa idan har tana da hakki a kan ki da shi mijin naku ta bar ku da Allah." Tana kuka ita Hauwan ta ce." Ban ce miki Amina ta yi mini wani abu ba inna, ni kawai na gaji da zama da mutumin da bai san raunina ba bai kuma yarda ya haihu da ni ba sannan bai san ya rarrasheni ya tausaya mini idan ina cikin b'akinciki ba. Wallahi da gaske nake Hajja na gaji yara Allah Ya raya su tunda dama ai ba hannuna suke ba." Hajja ta dube ni a sanyaye ta ce." Zauna yadda muka zo tare haka za mu tafi tare ai ke ma ba bare ba ce." Na koma na zauna din Kamar yadda ta umarta. Ta dube yar uwarta cikin nutsuwa ta furta." Tunda kun yanke shawara kan cewa rabuwar kuke buk'ata abu ne mai sau'ki ai Uwani dalili ni kaina lamarin nan ya ishe ni wallahi ba zan tantance wanene mai gaskiya ba a tsakaninsu Tajo ne ko ita Hauwa. Amina kuwa ku daina sanyata a ciki babu abinda ya shafeta ban fad'i haka don ina goyon bayanta ba. Ita da Hauwa duk daya suke bambanci kawai ita tana bin umarnina tana kuma yi mini biyayya bisa duk abinda na umarceta tana son abinda nake so wata'kila ba ku san da cewa asalin auranta da mijinta umarni ne daga gare ni ba gani daya rana d'aya da ni da ita mun roki Allah kuma ya amsa mana bata san ni ba, na nemi alfarma ta yi mini a lokacin da mata da yawa suka guji auransa saboda ceton ransu ita tace ta ji ta gani duk da tana da labarin abinda ya faru da shi a baya. Wannan shine abinda ya dasa mini kaunarta cikin zuciyata kuma ban fifita ta a kan ki ba Hauwa na dai gaya miki bambancinku amma tunda kun yanke shawara a tsakaninku zan same shi domin gaya masa uzurinku sannan kuma ina so nasan abinda yake yi miki na take hakki ai dole ne shima a nuna masa kuskuransa tunda ni uwarsa ce kuma har yanzu yaro ne a wurina dole ya bi abinda nake so." Littafin nan na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba Cikin jan hancin da kame-kame ta fara magana." Abubuwan da yake mini ba za su lissafu ba Hajja dole a cikin aure nasan ana cin karo da matsaltsalu da yawa kuma dole a yi hakuri, amma ni tunda na faru a tare dashi ban ji dad'i irin yadda nake so ba duk wanda ya ba'kunce mu yasan zaman ha'kuri nake yi ya gaya mini ya kuma nuna a zahiri zama yake yi dani saboda yaran da muka haifa da kuma zumuci, duk haihuwar data ratsa tsakaninmu tsananin rabo ne yakan jima bai kwanta da ni a shimfida daya ba, ni zan ta bin sa domin neman hakkina wallahi bai ta'ba yi don dad'in ransa ba. Ya karkata b'angare d'aya ya fifitata fiye da ni ya k'aunaci yaranta Y yana biya mata dukkanin buk'atunta Hajja ya zan yi da rayuwata na samu ciki ya zube ya nuna bai damu ba alhalin da kyar na same shi tunda ba kwanciya muke a gado daya ba ya cigaba da abinda yake gabansa ba shi da damuwa tunda ya nuna ga da wadda ya fi buk'atar haihuwa da ita." Ta ja hanci hawaye na silalowa a saman kuncinta ta cigaba da cewa." Ni na gaya muku ba ta yi mini komai lefi nasa ne tunda ya kasa daidaita tsakani na da ita ya fifitata ni kuma yana nuna mini kamar akan dole yake zaune da ni." Hajja ta tsira mata ido kawai tana kallonta. Ni kuwa na shiga nazarin maganganunta. Abinda ya kara tashin hankalinta zubewar cikinta tunda kowa ya san yadda ta jarbatu da haihuwa idan har gaskiya ne abinda ta fad'i a kansa to bai kyauta ba wata'kila ita tana d'aya daga cikin jerin mata masu buk'ata shi kuma ba a jarrabe shi da ita ba. Ga ciki ta samu tana murna tunda ta fad'i dama ba ta so na fita yawan yara a gidan to sai kuma ya zube shi mai cikin bai nuna damuwarsa ba, ga ni kuma ina haihuwar bibbiyu shine babban tashin hankalinta abubuwa da yawa suka taru a zuciyarta." Na ji Hajja tana fad'in. " Haihuwa ta Allah ce Hauwa itama Amina bibbiyun da take haifa ba ita ta bawa kanta ba rabo ne, kuma akwai gadonta a jininta. Amma kuma idan har da gaske ne abinda ki ka fada lallai akwai buk'atar zama a tsakani domin ai ke ba baiwa ba ce mutum ce me zai sanya shi ya dinga take hakkinki a shimfida wannan cutarwa ne ki yi hakuri ki barwa Allah ikonsa kin ji ko, wad'annan da ki ka haifa uku ki yi ta yi musu addu'a Allah Ya raya miki su sai ki ga sun tara miki garke guda. Wani ma yana can Allah bai ta'ba bashi haihuwar ba kuma haka zai koma ga mahallicinsa. Lallai zan yi masa magana idan har ba zai gyara ba to sai ya baki takarda ba dalili ba ne wannan Allah cewa ya yi idan har ba za a yi adalci a tsakanin mata biyu uku hud'u ba to kada a yi domin gujewa sa'bawa Ubangiji." Inna Uwani ta goge fuskarta tana fad'in.'' Ni kaina abin nan ya ishe ni wallahi na gaji da bata ha'kuri da danneta akan ta zauna. Yanzu ga shi ta hadu da hawan jini saboda tarin damuwa." Hajja ta ce.'' Uwani na ce miki abin zai zo da sauki ai, shi wanda yake da alhakin sakin a yau zan zauna da shi domin mu samu matsaya kada wannan ya dame ki." Ta yi sakato da baki tana karyar da kai gwanin ban tausayi. Ta yun'kura ta tashi a hankali tana gyara yafan mayafinta ta dube ni tana fad'in." Tashi mu tafi." Na tashi da sauri domin dama kamar akan 'kaya nake a zaune a wurin. Ta dubi inna Uwani tana Fadin." Idan an yi Isha'i sai ki shigo domin jin ina aka kwana." Da sauri ta ce." To shikkenan." Ta sake duban Hauwa a karon da ba zai lissafu ba ta ce." Ke Kuma ki kara hakuri kin san dai illar yawan tunani da damuwa ko tunda ga abinda ya haifar miki don haka ki cire duk wani zullumi da tunani da ba'kin kishi a ranki Hakan shi zai sanya ki samu zaman lafiya." Daga haka sai ta kama hanyar fita na bi bayanta cikin rashin karsashi. Muka isa gidana babu wanda ya yi magana. ban ta'ba ganin tsananin bacin rai a fuskarta ba sai yau damuwa gabad'aya duk ta dabaibayeta ga tarin shekaru don ma da kula sosai amma matsalar nan kadai ka iya tayar mata da ciwonta. Na rasa da wane kalami zan rarrasheta domin kwantar mata da hankali saboda gabad'aya yanayinta ya canza da bakincikin abinda ya faru. Na gyara mata fillo a masaukinta ta kwanta tare da mike kafarta na fita daga d'akin cikin mutuwar jiki da tunanin mugun kishin Hauwa a kaina shi zai halaka mata rayuwa kamar yadda hajjan ta fad'a domin kuwa duk mai hankali yasan tsananin kishi ne yake damunta da ganin k'yashi. Ban san yadda ta kaya a tsakaninsu ba domin tunda na shiga d'akina ban fito falo ba ya dai kira ni a waya da ya dawo to nasan dole za su zauna zaman tattaunawa yara ma sai Mairo ce ta kawo mini su tunda wurin baba Tabawa na bar su. Sai can wajan goma da arba'in na dare ya kira ni a waya lokacin nasan sun tashi. Na leka domin dubata tana saman dadduma a zaune da cazbaha a hannunta ganin haka ya sanya na ja mata kofar kai tsaye saman nasa na nufa zuciyata na dokawa haka kawai rashin hakurinsu na nema ya d'agawa tsohuwa hankali. Ya fito daga wanka yana sanya kaya a jikinsa kafin na zauna ya ce na kawo masa abinci ban ce komai ba na sake sauka kasan da zummar bin umarinsa. Abinci ya ci ya koshi sosai ina kallonsa babu wata damuwa mai gigitarwa a tattare da shi ya kammala ya goge bakinsa da tissue ya ja gefe na sauka da tiran abincin kasa na dawo na same shi jingine jikin gado yana duba wayarsa. Zamana bai sanya ya dube ni ba. Abin nema yake yi ya shafe ni kenan tunda magana ma ta gagare shi. Ban nemi lallai sai na ji halin da ake ciki ba tunda bai shafe ni ba idan shi ya gaya mini zan saurare shi ba ni da wata shawara da zan ba shi akai duk abinda ya yanke a tsakaninsu daidai ne. Na daure zuciyata na kalle shi a nutse na ce." Ina tsammani tare za mu tafi da Hajja zuwa Kano Gwaggo fa jikinta babu dad'i tun lokacin haihuwar yaran nan take ta fama wallahi ya kamata na je dubata." Ya yi shiru bai ce komai ba. Sai da na sake maimaita maganar tukkuna ya dube ni yana fadin." Don Allah kada ki k'ara mini wani b'acin ran Amina a bar ni cikin wanda nake a yanzu." Na ce." A a ban gane kada na bata maka rai ba, zuwa duba jikin Gwaggo shine abin b'acin rai kuma?" Ya shiru bai tanka mini ba." Na ce." Ka dai duba don Allah babu rashin dacewa fa kuma ciwo ake dubawa." Ya ce." To zan duba idan zai yiwu ." Na ji wani takaici ya yun'kuro mini amma sai na danne na yi masa uzuri saboda yanayin da yake ciki na damuwa. Haka muka wayi gari zuciyoyi babu dad'i da safe kafin na sauka kasa ta kira shi a waya aikuwa ya fashe tunda dama ya kumbura sumtum! jira yake yi a zungure shi ita in banda abinta tasan abinda ta yi kuma ai sai ta ja gefe ta yi zaman saurare. Fadi yake yi "Ban yi niyyar sakinki ba Hauwa ku kaini 'kara kotu mara mutunci masu mance alheri. Ni za ki yi wa wannan iskancin duk abinda nake yi miki ba ki ga ni ba sai kin had'a ni da uwata tuntuni na gaya muku ba ni son abinda zai d'agawa mahaifiyata hankali da girmana ku dinga yi mini terere babu wadda za ta rufa mini asiri ba ni da sirri a gidana. Kin cire kunya kin gaya mata karya da gaskiya ba ni baki hakkinki ni za ki yi wa sharri Hauwa wato duk ko'karin da nake yi miki ba ki gani ko? Ga ni ki ke yi yawan kwanciyar aure shi yake kawo haihuwa kina ganin daga 'bangarena ne haihuwar biyu da Amina take yi ba baiwa ba ce da rabo daga wurin Allah. Shikkenan kin buk'aci rabuwa ni kuma ba zan yi rabuwar a lokacin da kuka buk'ata ba. Na ji cikin rawar murya tana fad'in." Ni wallahi ban ce mu rabu ba, cewa na yi ka gyara kuskuranka ni ma na gyara kuskurena mu zauna lafiya ai kowa ya sani ka fi buk'atar haihuwa da Amina kuma soyayyar da kake yi wa yaranta ya fi wanda kake yi mini da abinda na haifa." Na cika da mamaki kwarai jin yadda take fad'in ita ba tace su rabu ba kenan k'aryata Hajja za ta yi bayan su suka fad'i haka. Ya ce." Kina nufin Hajja ta fad'i hakan ne kawai domin ta ji dadin bakinta kenan, so ki ke na lalace a gadonki na dingi jima'i dake saboda ki tara yara kin d'auka sakarai ne ni da ban san abinda nake yi ba, ko kin yi zaton ban fahimci gasar haihuwa ki ke yi da Amina ba. Duk abubuwan da kuke gudanarwa a gidan nan daga ke har ita ina sane kuma ina bibiya shiru kawai nake yi muku. Ba zan sake ki ba, kuma ba zan sake yin cikin da za ki haihun ba sai mu ga yadda za ki yi." Ya kashe wayarsa yana huci! Na dinga kallonsa gabana na fad'uwa. Oh! ikon Allah wata ta kunno bala'i yana nema ya shafe ni Ubangiji Allah Ya sawwa'ke musu wannan masifa. Na tashi na sauka bai ce mini komai ba ni ma ban yi masa sallama ba. Bayan kwana biyu da kansa ya ce na shirya da safe sai mu tafi tare gabad'ayanmu zuwa kanon shima zai duba jikin Gwaggon. Na yi godiya a takaice babu wani sakin fuska domin haushinsa nake ji ganin yadda yake nema ya jingina ni a jikin badakalarsu. Tare muka nufi kano a washe gari wanda ya yi daidai da saura kwana biyu a d'auki azimi a ranar da daddare ni da shi muka je har gida duba Gwaggo da sauki za a ce amma dai da kyar ta gane ni. Hamusu kuwa ya sha fad'a a wajensa ganin haka ya sanya ban yi masa nawa fad'an ba tunda an had'a gabad'aya an yi masa menene amfanin abinda ya yi wai kada a d'orawa mutane nauyi wannan maganar ta yi bala'in bata mini rai. Da sassafe a ka d'auketa a kai kaita asibitin Malam tunda dama tana file Dr Iliyas da abokanan aikinsa suka shiga bata taimakon gaggawa. Kwana daya ya yi ya juya ya ce yana da uzuri amma da shara'din na biyo bayansa da kwana biyu na ce masa to kawai ba ni kuma tsammanin bin sa sai na yi sati gidan Hajja na zauna bangaranmu na gidan. Ban zo da mai aiki ko daya ba tunda tafiyarsu a cikin satin nan ne azimi da kwana uku ko hudu yaran kuma sun dan yi wayo ni da iyami mai aikin Hajja muke kula da su. Da daddare ma da zan sake zuwa duba jikin Gwaggon a gida na bar su wajanta Magaji ya d'auke ni a mota zuwa asibitin Malam din. Wani ikon Allah wai ana tunanin samun sau'ki da rangwami a wajan da aka kaita domin kula da lafiyarta sai abin ya kara rikicewa jikin ya'ki dad'i yadda ake buk'ata Gwaggo ta kai ta kawo sai da aka sanya mata abin numfashi a hanci saboda bata iya yi da kanta. Kuka na dinga yi a fakaice saboda tashin hankalin ganin yanayinta wani siririn hawaye na zuba ta gefan idanunta tana daga kwance a gado(tun muna yara Iya kakarmu ta wajan Uba da zata rasu ta dinga yin wannan hawayen na gefan ido aka ce mana wai na sallama da duniya ne) Gwaggo na mike a gado ana ta cuku-cuku a kanta duka rai ake yi wa wannan fafutukar amma zahiri ciwo ya ci karfinta sosai Gwaggo lokaci take jira domin tun ganin da na yi mata a gida na sare. Babu wani kuzari muka fito daga d'akin ni da Hamusu ba mu jima muna magana ba muka yi sallama saboda dare ya yi na shiga mota Magaji ya ja muka fita daga asibitin. Bacci mai cike da mafarkai marasa kyau na yi da asuba na tashi jiki a mace Ina zaune saman dadduma Yusi ya shigo da tsananin tashin hankali. Ganinsa a hargitse sai gabana ya fadi ya furta. Mama Allah Ya yi wa Gwaggo rasuwa. Baba Hamusu ne ya kira ni a waya yana gaya mini wai yana ta kiran wayarki a kashe d'azu da asuba ta rasu.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *167* Mutuwa dai itace karshe mai yanke nisha'di da walwala mai jefa zuk'ata cikin firgici a lokacin da aka yi tabbas mutane na shiga cikin hankalinsu tare da tuna yaushe tasu zata riske su kuma a wace rana ne. Mutuwa ko ta kafiri ce takan sanya tsoro da nadamar duniya to balle mutuwar mumunai daga cikin salihan bayin Allah. Ha'kika mu da muke ahalinta mun yi rashi kuma mun koka 'kwarai da gaske bisa rashin ta da muka yi amma wani abin mamaki da ikon Allah yadda ma'kota ke kuka wiwi har da yara k'ananu bisa rashinta shine abinda yake bawa kowa mamaki. Lallai Gwaggo tana d'aya daga cikin wad'anda Ubangiji Allah Ya fadi cewa tundaga mutuwarsu ake gane cewa 'yan aljanna ne. Sosai ta samu jama'a kwarai da gaske haka zalika duk wanda zai zauna ya tashi sai ya fadi alherin da ta yi masa da jikinta ko kuma da aljihunta. Gwaggo ta samu sheda daga wurin ma'kotanta da sauran abokanan arziki duk tsayin zamanta a garin kano a kuma cikin unguwar da take aure babu abokin fad'anta tsakaninta da kowa lafiya ta rabu. Gari yana yin haske kad'an muka tafi ni da Hajja da Yusi lokacin tuni an kawo gawar daga asibiti ma'kota mata sun cika gidanta mazansu a waje da sauran danginsu abbansu Yusi tunda dama ba wani yawa ne da su ba layin cike yake da jama'a yara da manya cikin alhini da tashin hankali. Sai yamma tukkuna mutanan maiduguri suka iso cikinsu har da Dada kakarmu na dinga mamakin ko'karinta tunda itama bata da wani 'koshin lafiya. Ta ci kuka kuwa sosai tana fad'in ta so ta zo ta samu gawar aminiyarta ta yi mata addu'a. Anti Yagana Ya Falmata da kuma iyalin baban Saude dana Babanmu Babagana mahaifinsu babandi tare muka yini da su da magriba Hajja ta ce na kira mata Magaji suka yi waya ta ce ya d'auko babbar motar da za ta d'auke mu gabad'aya mu tafi can gidan nata mu kwana gabad'aya har da su tunda gidan Gwaggo bashi da girman da zai d'auke mu duka. Haka kuwa aka yi bayan isha'i magaji ya zo a lokacin ne muka yi sallama da Ummansu Hadiza da Fati suka tafi tunda suma tare duk muka yini Babanmu kuwa da shi aka yi jana'izar Gwaggo shine akan gaba. Ita kuma Ummansu Saminu tana kwance bata jin dadi dalilin da ya hana ta zuwa kenan. Shi ma Usaini ya yi wa Hamusu kara sosai domin yinin ranar rufe shago aka yi duk suka zauna wajan kar'bar gaisuwa har ya kawo matarsa Hajara muka yini tare da su gabad'aya tana ta fama da d'an cikinta da ya huda zani ya fito kurcici sosai na ji dad'i bisa wannan karar da suka yi mana. Hajja ta sanya aka gyara musu d'aki a cikin falonta tunda da akwai dakuna hud'u duk kuma a shirye suke gyaran da Iyami ta yi kad'an ne tace su shiga su huta kafin a kawo abinci. Muna tare da su gabad'aya don sai a lokacin ma iyalin baban Saude ke yi mini barka tunda ba su samu ikon zuwa taron sunan da muka yi ba kamar yadda ya yi mini alkawari saboda rasuwar mahaifin Mamansu Abahuraira amaryarsa kenan. Na ce da su babu damuwa komai nufin Allah ne. Sun yi godiya sosai wai ba su zo ba amma sakon turaman atamfofi ya iske su har gida. Ranar Kamalu muka yi bidiyo call da Kamalu ya yi wa kowa ta'aziyya tare da jajantawa cikin alhini to ya za a yi abinda kowa yake fad'i kenan lokacinta ne ya cika amma abin farincikin rahamar Allah da ake yi mata zato. Ban yi tunanin zuwansa a ranar ba tunda duka bai fi kwanaki uku da komawarsa ba Allah sarki sai gashi wajejan k'arfe goma sha biyu na dare har da mintina akai ya shigo gidan Hajja wata'kila tafiyar mota ce kuma bai fito da wuri ba. Ya d'an ba ni tausayi ganin yadda rayuwarsa take gudana a tafe daga nan sai can babu wani hutu idan har an kwanta to dare shima a cikinsa sai an yi wata ibadar ta jijjiga jiki. Lokacin da ya samu kwanciya da wadataccen hutu na dole da rashin sukuni shine lokacin da Hajiya Maryam ta shimfid'ar dashi shine ya yi kwanciya mai kamar mutuwa hutun dole ba don dad'i ba. Muka kwana tare da shi a b'angaransa na gidan inda na sauka da zuwana. Sosai ya yi mini ta'aziya ya jajanta rasuwarsa ya kuma bayyana alherinta tare da jadadda mini ri'ke amanar da ta bashi kafin rasuwarta. Da gari ya waye ya riga mu yin gaba domin ko cikin gidan bai shiga ba wurin su Hajja basu san ya zo ba. Ya ce duk idan sun had'u gidan rasuwar sai su gaisa. Haka kuwa aka yi a can gabad'aya suka gaisa da su Dada ya zauna cikin jama'a ana ta kar'bar gaisuwa da shi Babanmu a gefensa da Baba Sule sai Idiris dana hange shi a gefe a zauna kusa da Baba Sule duka muka gaisa kafin mu shiga ciki nan ma ma'kotanta suna ta hidima da wasu daga cikin danginta da suka sauka jiya da daddare. Ranar sadakar uku daga gidan Hajja aka yi abin sadaka abinci mai kyau ciki har da wainar shinkafa fanke da wainar gero da sauransu haka Magaji ya d'auki kololin abincin ya tafi ya kai gidan da sassafe. Kafin ya dawo ya dauke mu gabad'aya zuwa gidan. A ranar ne Sahura da Yusura suka zo mini gaisuwa da yamma kuma sai ga anti Maimuna uwargidan Alhaji Muntari tare da Salima babbar yarinyarsu goye da d'anta a baya. Na ji dadin ganinsu kuwa abubuwa da yawa suka hana ni neman inda suke a duk lokacin da na zo garin amma ina samun labarin Turmuzi a wurin Hamusu tunda ragamar kula da shi tana hannunsa har yanzu shine ma yake zuwa duba shi makaranta kamar dai yadda ya dinga d'awainiya da Kamalu. Muka gaisa sosai cikin karamci da kulawa ta ce mini itama labarin rasuwar ta ji ta ce bari su zo tun kafin a watse tasan ina nan ban tafi ba sai su yi mini gaisuwa. Na dinga godiya kuwa ina tambayarta yara ta ce mini duk suna nan lafiya lau. salimat ta kwanto mini yaronta daga bayanta tana sinne kai Sahura na tsokanarta to abin ai ba wahala tunda dama 'kawar Yusura ce kusan sa'annin juna ne itama gata nan da d'anta daga zarar an yi auran ne sai haihuwa yanzu shiyasa wasu samarin a cikin irin abinda suke saye na angwanci suke hadawa da pampas da set din kayan sanyi domin jiran ko ta kwana. Anti maimuna ta ce mini tana nan tana sana'arta sai abinda ma ya yi gaba domin har ta kama shago gaba da su kad'an ana sauke mata motar itace da buhuhunan gawayi tana gaya mini ita Jamila tana can harkar film take yi. Kuma sau biyu ta zo ta duba yaranta tun bayan rasuwar Babansu ta tayar da masifa a sayar da gidan a bata gadon yaranta sai da aka yi mata rubdugu jama'ar unguwa suka yi mata tara-tara kamar za su daketa sannan ta kama borin kunya yaran unguwar marasa kunya masu jini a jikina suka ce duk ranar da ta sake shigowa unguwar sai sun zane mata jiki. To tun daga lokacin ne bata sake zuwa ba wai da har ta yi barazanar shigar da kara kotu tana fad'in ba ta yarda da wajan da aka kai mata yaro ba sannan ba a nemi shawararta ba. Kuma shiru har yanzu dai ba a sake jin doriyarta ba sai dai suna ganin seriars film dinta mai suna *Gidan kashe ah* tana fitowa a magajiyar karuwai wai acan garin lakwaja ake shirya film din gidan karuwai. Abin ya dinga ba ni mamaki da al'ajabi Jamila mai take nema a duniyar nan ita a maimakon ta zauna ta yi hakuri ta kula da yaranta marayu kamar yadda 'yar uwarta ta yi sai take ganin kamar cutar da kai da kuruciya ne gwara ta fita yawon bariki domin dai a matsayinta na ya mace mai sauran kuruciya bai kamata ta wulakanta rayuwarta irin haka ba. Salima ta d'auko wayarta daga cikin jaka ta lalobo film din tana nuna mini. Na kar'bi wayar ina dubawa Sahura na leko kanta muka cika da mamaki tana tsakiyar karuwai da sigari a hannunta suna buga karta ana shewa da tafi kuma wai film ne. Na yi sauri na mik'awa yarinyar wayarta ina kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Lallai idan ka ga wannan tambad'ewar akwai hakki ko kuma baki na iyaye. Ai akwai y'an film 'din masu nutsuwa da suka mayar da harkar sana'a kuma ta yi musu riga da zani wasu har da mahalli da jari amma ita hanyar da ta d'auka ba za ta yi mata kyau ba domin su kansu masu d'aukar film din suna duba dacewa akan abinda za su d'ora mutum akai wata'kila shiga da mu'amularta ya nuna musu ga abinda tafi k'warewa a kai Ubangiji Allah Ya tsarkake mana zukatanmu. kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Washe garin ranar da Gwaggo ta yi uku a gidanta na gaskiya muka tashi da azimin farilla na Ramadan. Kowane bawa ya samu nutsuwa da kuma kad'aita kansa ga mahallici domin samu rabauta da dacewa. Ranar sadakar bakwai addu'a kawai aka yi mata ba a zauna ba tunda dama azimi ake yi Yallabai din yana nan bai tafi ba tukkuna shi da mahaifiyarsa suna ta fitar da abinci buhu buhu da abin masarufi domin sadaka da aka sha ruwa aka fita da d'anye hadiya ga marigiyar kamar yadda na ji Hajjan tana fad'in. goma ga azimi suna ta wannan aikin harabar gidan Hajja cika take yi da mutane har da mata abin dai gwanin ban tausayi daga waje ma jama'a ne cike buhun shinkafa ce da kudi dubu goma ga mai rabo ban san iya adadin mota nawa ya sauke ba bayarwa ake yi jama'a na k'aruwa har sai da azimi ya raba tukkuna abin ya yi sau'ki. Lokacin kwanan su baba Tabawa tara da a kasa mai tsarki tunda hud'u ga azimi suka tafi a yadda yake gaya mini yaran suna can gidan Hauwa duk da har yanzu jikinta bai dawo daidai ba akwai mai aikinta Ladidi da kuma Inna Uwani ba ta tafi ba wai sai bayan sallah. A lokacin ne na ji hankalina ya yi gidan gabad'aya saboda ban yarda da zaman yarana a gidan Hauwa ba. Na fara yi masa maganar tafiya ya ce sai ashirin ga wata yana lissafin zakka ne sai ya kammala. Babanmu ya kira ni a waya yana ta godiya wai an kai musu abinci har buhu biyar da taliya da sukari har da gero shi da Baba Sule na ce babu komai sadaka ce anan yake yi mini albishir din fitowar Hadiza kwana biyu da suka wuce gwamnati ta yi yasa da sasaauci a gidan gyaran halin da take zaune duba da watan da muke ciki an duba iya adadin shekaru da zamanta a gidan Allah Ya taimakata ta shiga cikin wad'anda suka fito ba tare da tsananta bincike akan lefin da ta aikata ba. Magana ce ta gwamnati bisa sahalewar gomna duk abinda aka ce hukuma a gidan duniya ai k'arshen magana kenan sai dai idan an je can lahira anan Ubangiji zai fitar da sakamako. Yana gaya mini tana nan koyaushe cikin sallar dare da ro'kon Allah gafara kuma duk ta tsangwami kanta bata fitowa ta yi walwala da jama'a. Tausayinta ya kama ni sosai na ce ya gaya mata zan kira ta a wayar Ummansu mu yi magana idan na yanke shawara dama dole hakan ta kasance fita ma gagararta za ta yi tunda kowa ya san abinda ta aikata jama'a za su yi ta kallonta wasu ma har su jefe ta ko kuma a farauci rayuwarta kamar yadda suka farauci ta wani ita da abokiyartata Hajiya Alili da har yanzu ba san a ina ta boye ba. Da yamma ranar Hajiya Saratu ta zo domin yi mini ta'aziyya ba ta samu zuwa ba a lokacin rasuwar sakamakon ciwon kafafun da ta d'an yi a cikin kwanakin. To da daddare kafin mu kwanta nake gaya masa halin da ake ciki tare da yi masa godiyar bisa alherin da ya yi. Bai yi jayayya ba ya amince mini akan abinda nake so yana fad'in Hadiza 'yar uwata ce kuma gida dai sunan nasa ne amma ni nake rayuwa a ciki da yarana tunda har na aminta da zama tare da ita shima yana yi mata murna samun ku'buta tare da addu'ar Allah Ya tsare gaba. Ban samu yin waya da ita ba sai da gari ya waye tukkuna na gaya mata hukuncin dana yanke ta dinga kuka tana yi mini godiya tare da jaddada mini a shirye take domin na ce zan turo Magaji ya zo ya d'auketa mu zauna tare a gidan Hajjan kafin lokacin da za mu tafi can abujan. Ummansu ta yi kuka kamar me a waya tana yi mini godiya ina fad'in hannu baya rub'ewa a yanke a yar Hadiza har yanzu tamu ce kuma 'kaddara tana kan kowa farincikin ayadda ta tuba take kuma neman afuwar Ubangiji lallai shi din mai gafara ne da jin kai. Kuma hakika fitowarta da wani lamari da yake kwance wanda mu ba mu san shi ba, da ya so da tun farkon lamarin ya kar'bi rayuwata don haka ni ma daga nawa b'angaran wannan kad'ai zan yi mata domin ta samu sassaucin zuciya killaceta a waje daya da ababen more rayuwa da kula domin ta dawo nutsuwa da hayaccinta. Shi kansa Babanmu rasa abinda zai ce ya yi domin da da farko ya nuna rashin yardarsa yana fad'in Hadiza ta yi girman da za a ce ta je ta zauna mini a gida ita ba yarinya k'arama ba. Akwai wani abokinsa matarsa da ta rasu ya buk'aci auranta yaransa tara marayu a yanzu auran shine rufin asirinta. Na ji gabad'aya lamarin bai kwanta mini a rai ba abokin Babanmu ai da shakarunsa kuma ko auran za ta yi a yanzu akwai buk'atar zuciyarta ta nutsu kada don an ganta cikin ibtila'in rayuwa a yi kokarin k'Γ rasa kassara mata rayuwa saboda bata da jayayya tunda mafaka take nema kai tsaye zata amince ko da ranta baya so. Da yake ni ce na zo da maganar kuma nake buk'ata sai ya ha'kura ya amince mini. Anti Yagana ma ba ta yi jayayya ba ta nuna goyon bayanta dangane da hakan tana fad'in idan ta huta hankalinta ya dawo jikinta shekara daya zuwa biyu sai ta dawo gida ko kuma ta yi aure. Akan haka muka tsaya kuma a ranar da yamma Magaji ya je ya d'aukota duk abinda ya faru ga rayuwarta na labartawa Hajja har da kuka tana fad'in sannu baiwar Allah kin ga jarabawa Allah Ya yafe miki mu kuma mugun ji da gani Ubangiji Allah Ya kare mu. Hadiza tun a gidan Hajja ta fara yin dawainiya da su Hasan sai ta kar'be ni tunda da tare muke yi da iyami Hajja na dan yin abinda za ta iya amma zuwanta sai ta kar'be ni a duk sanda zan daga ido na kalleta sai k'walla ta cika mini ido. Mace 'yar garu da ta samu gatan uwa a lokacin da take sharafi da jiki mai kyau ta koma haka Hadiza ko da can ba ni da abinda zan nuna mata tunda ta yi tashen 'yan matanci kuma bata ta'ba yin saurayi talaka ba masu arziki ne daidai gwargwado ne suke zuwa neman auranta. Fara ce tas haka suke dukansu tunda Ummansu ma fara ce ta fi ni haske tana da kirji sosai a wancan lokacin ni kuma baya na fita da tsayuwar hallita mai kyau dalili ni jikina ta ko'ina dumur yake koda na yi haife-haife nan babu inda ya saki ya ragaje alhamdulillahi. Ita kuma irin jikin Ummansu ne da ita a sake amma akwai kirji cikakke a lokacin budurci ba yanzu da suka risina ba saboda wahala da shekaru tunda kwanaki biyar kacal ta ba ni ba wani nisa a tsakaninmu amma wallahi ta fi ni tsufa hakan yana da ala'ka da wahala da rashin samun hutu zullumi fargaba da rashin 'koshi. Alhamdulillahi ni kam kullum cikin hutu nake da kuma cima mai kyau tunda tsakani da Allah idan ba a zaman makokin nan na Gwaggo ba sai na ce na fi shekara tara rabona da shan ruwan pure water sai da mugun dalili ko maiduguri na je gidan anti Yagana ruwan gora Babansu Fadila yake sayo mini har na gama zaman da zan yi a gida. Rabon zakkar da ya fitar ta zagaye dangina kaf daga can maiduguri Baban Saude ne wakili nan kuma Sunusi ne wakilinsa babban yaron baba Sule duk wanda sako ya same shi sai ya kira ni a waya ya yi godiya domin babu hanyar da za su same shi su yi masa godiya Y 'yan biyun gidanmu da su fari ana gobe za mu tafi suka zo muka yini tare muka sha ruwa cikin sakewa a bangaran da nake har ya shigo ya same mu muna raha abin mamaki sai ya zauna a cikinmu kunya kuwa duk ta kama su mussaman Hadiza da ta kasa daga kanta ta kalleshi dalilin abubuwan da ta yi a can baya ta dinga kar'be masa kudi tana shirya k'arya. Ya dinga jan ta da magana duk domin ta sake amma ina ta kasa kanta a kasa har ya tashi ba ta dago ba. Sahura ba ta samu zuwa mun yi sallama ba sai dai ta kira ni a waya ta yi mini godiya sosai domin itama ta kar'bi zakka da kayan abinci rigijib a wajan aikinsu Komai nasa cikin tsari da lissafi duk yadda ya yi mini haka ya yi a b'angaran Hauwa domin da kunnena na ji Hajja na waya da Inna Uwani kan kayan abincin da aka fitar musu da zakkarsu ta ce abincin dai a sa direba ya kai mata can bauchi kudin kuma bayan sallah za ta kar'ba sai a lokacin ne ma Hajjan ta san da cewar har yanzu tana abujan ba ta koma gida ba. Ranar da azimi ya yi ashirin muka tafi bayan mun yi sallama da Hajja Yusi ya na gaya mini cikin sallah zai zo ya yi mana kwana biyu cikin 'yan uwansa na ce to Allah Ya kawo shi lafiya.........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *168* Abinda ya so ya d'an ba ni mamaki bai wuce ganin ya tafi gidanta ya kwana ba. To matarsa ce har yanzu tunda bai saketa ba a tunanina ni zaman da nake yi ba su samu matsaya ba har yanzu a cikin rikicin suke tunda bai ta'ba nuna mini cewar sun daidaita ba a lokacin dana tambaye shi ina yara bayan tafiyar masu aiki umara a takaice ya ce mini suna gidanta. Ni da Hadiza muka kwana a gidan da safe muka tashi da aikin gyare-gyare zuciyata ta'ki tsayuwa waje daya sai tunanin yadda aka yi suka iya shawo kansa cikin k'an'kani lokaci duk da fusatar da ya yi akan lamarin to ko shine manufar rashin tafiyar inna Uwani a lokacin da ya koma bayan mun zo duba Gwaggo nake tunanin suka daidaita tsakaninsu amma abin ya ba ni mamaki sosai. Na yi kokarin dannewa saboda samun kwanciyar hankali da nutsuwa zuciyata tana gaya mini gwara duk rintsi su shirya domin ko da ya yi musu abinda suke so zai iya auro wata tunda ya riga ya saba zama da mata biyu. Amma yanayin yadda suka dinga jujjuya maganar ne ita da uwarta ke ba ni mugun mamaki tabbas Inna Uwani tsufa ya yi gardama kuma an yi fad'uwar ba'kar tasa. Bai shigo ba sai wajan d'aya da wani Abu yanayin shigar da ya shigo mini da ita ya tabbatar mini da cewa daga massalaci ya fito. Babu wani abu dana nuna masa a fuska ya zauna a falo cikinmu ni da Hadiza har k'asa ta durkusa ta gaishe shi Hadiza wani irin ladabi ta koyo a gidan gyaran halin da ta zauna Ya amsa kuwa cikin kulawa ta tashi tsaye da Usaini a hannunta za ta nufi bedroom dina Hasan ya sanya kuka yana mika mata hannu wai sai ta d'auke shi. Kwanaki shida kacal a tare damu yaran sun yi sabo da ita. Uban ya kar'be shi daga hannuna yana fad'in." In ban da rigima da wane hannun za ta d'aukeka ka ci girma mana." Ya dinga tsala ihu yana zillo tare da mika mata hannu shi kuma Usaini na kwance a kirjinta ya yi luf. Na kar'be shi daga hannunsa abin mamaki ya'ki yarda wai lallai sai ta d'auke shi, kishi dai irin nasu. Haka duka ta ciccibe su a 'kui'binta ta rirrikesu da hannunta ta nufi bedroom dina tana dariya yaron ya yi shiru ya daina kuka da zanbarwa. Ya dube ni a nutse yana fad'in." Tausayi take ba ni sosai 'yar uwar nan taki Giwa." A takaice na ce." Mun gode sosai Allah Ya kara rufin asiri?" Ya zuba mini ido babu halin ri'ke hannu ko runguma saboda muna cikin ibada tunda ma Gwaggo ta rasu muka fara azimi ba mu yi wata kwanciyar kirki ba saboda abubuwa da ya wasa da suka sha kansa. Ya sauke ajiyar zuciya ba tare da ya janye idonsa daga kaina ba ya ce." Zan tura miki kudi kamar yadda muka saba kowace shekara domin ki sayi abinda ki ke buk'ata na sallah. Yara Hauwa ta saya musu wurin k'awarta suna wurinta ta ce a gaya miki idan an jima suna shigowa yi miki gaisuwa. " Na ce." Ban gane hausar ba?" "Ina nufin kayan sallar yara takalma da riguna na kanti an saya akwai saura wurin telansu zai kawo cikin satin nan inshallah." Na d'an yi jim ina nazarin maganarsa a wannan karon kenan ita ta kar'bi kudin ta saya musu kayan wajan k'awarta sanin da na yi duk salla marigayiyace Maryam ke yi musu wannan hidimar amma dai har yanzu telansu da yake yi musu d'inki yana nan shi yake yi musu ko bayan rasuwar wadda ta d'auke shi aikin ya cigaba domin ni ma wasu lukutan yakan yi mini d'inkin amma ba sosai ba watannin baya ne da ya ce a fitar da kayansu gabad'aya ya sanya a aka kawo musu sabbin 'yankati to me hana wannan karon ma bai sanya an kawo musu ba. A tak'aice na ce." To shikkenan." Ya dube ni yana fad'in.'' Ko hakan bai yi miki ba ne?" Na ce." Ko bai yi mini ba ai dole na ha'kura tunda zaman lafiya nake so ko, amma ai da can ba ita take saya musu ba." Ya gyad'a kansa yana fad'in." To yanzu don ta nuna ra'ayinta ai ba lefi bane ki duba kayan sosai idan ba su yi ba sai a canza musu ku dai zauna lafiya da juna, ita mun samu daidaito da ita kuma mun yi alkawari a zaman da muka yi domin har sai da kawunta ya zo mun zauna da ita Inna Uwanin ta yi alkawari kan cewa za ta gyara tare da ko'karin kawo zaman lafiya a junanku.'' Shiru na yi ban iya ce masa komai ba saboda mamaki. Ya tashi ya hau sama ban bi shi ba na yi zamana ina nazarin yadda abubuwa suke canzawaa daga wannan sai wannan zuciyata tana gaya mini kudi ta kar'ba masu kauri a hannunsa domin ta 'karu tunda dama neman hanyar da za ta dinga samun kudi take yi. Ita kuwa wadda ta rasu tana yi ne da dukiyarta bata neman kwabonsa ita nata salon kenan tunda tana da arziki. Ita kuwa Hauwa na tabbatar da cewa ta yi hakane domin 'karuwarta. Da yamma muna kicin tare da Hadiza muna shirin abu bude ba'ki suka shigo.. Na bar ta a kicin din goye da Hassan ya yi bacci na fito falon na same su a zaune Inna Uwani ta d'auki Usaini yana saman cinyarta da abin wasansa a hannu. Na d'an saki fuskata ina yi musu barka da zuwa na zauna kujerar dake kallonsu yaran gabad'ayansu suka shigo Khalil twins da Minal wurina suka rugo a guje k'ananun shi kuma Khalil din yana ta dariya kafin ya d'an risina yana fad'in." Mama ina yini?" Na amsa da kulawa ni ma ina dariya na ce." Kai ya na ga duk ka yi zuru-zuru azimin nan fa bai wajaba a kan ka ba." Ya sa dariya yana fad'in." Ko bai wajaba a kaina ba ba zan asha ko daya ba Mama. Minal tana ta'ba mini cinyata ta ce." Mama ni kin ga haka na yi." Ta had'a yatsunta biyar ta d'ora d'aya a kai." Na bude baki cikin mamaki ina fad'in." Da gaske." Karaf Usai ta buge hannun tana cewa." Ma'karyaciya ko daya ba ta yi ba wallahi." Cikin wasa ta yi maganar don har tana dariya ma. Abinka da yarinta ita kuma Minal din sai ta fashe da kuka tunda dama dangwalolo ce. Nan da nan Hauwa ta 'bata fuskarta na ji lokacin da ta ja tsaki mai tsayi. Ina Uwani na fad'in." Ke kam Usaina kin fiye saurin hannu wallahi menene abin duka Kuma?" Khalil da sauri ya ce." Ba dukanta ta yi ba fa Inna." Hauwa ta harareshi tana fad'in." Ba mu da ido ko kaine kake da Ido don ubanka zaman da suka yi a can ma kenan ba dukanta take yi ba." Ya yi shiru yana yin fuskarsa ya canza. Na ce." Ai saurin hannu gare ta na gaya mata kuma 'kanwarta ce." A d'an sanyaye ta ce." Ban doke ki ba ko Minal?" Sai ta d'aga kanta. Tsakanin yara ba a shiga Usai din ta sanya hannu tana goge mata fuska. Daga haka na ce." Ku je dakinku ku zauna kafin mu gama gaisawa.. Suka kama hannunta suka bar wajan. Cikin kulawa na fara gaishe da Inna Uwani itama ta amsa a d'an sake ta yi mini ta'aziyya tare da jajanta mini rashin da aka yi. Haka itama Hauwan mun gaisa babu yabo babu fallasa ta yi mini gaisuwa kafin ta dubi Khalil tana d'an harararsa ta furta." Ba ni ledar kayan nan?" Na dube shi da sauri wata babbar leda ce da ya shigo da ita sai ya ajiyeta gefan kujera. Ya d'auka ya mika mata ta kar'ba kafin ta kalle ni tana fad'in." Babansu ne ya bada kudi aka saya musu 'yan kanti wurin Sadiya wannan shekaran ta kawo kaya sosai ai baki mance ta ba ko?" Na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biyani hakkina ba Na gyada kaina a nutse ina fad'in." Ban mance ta ba." Sai ta mi'ko mini tana ce wa." Na ga sun yi kyau sosai set takwas ne kowanesu hud'u." Na kar'ba na ajiye a gefena ina fad'in." To madallah." Suka amsa tare kafin ta cigaba da cewa." Takalma ne kawai babu sizi d'insu a wurinta shine ban ce ta aiko ba amma gabad'aya yaran an saya musu da mayafai sauran suna wurin telansu yadda ya ce cikin satin nan zai kawo." Na ce." To shikkenan wannan na Hasan da Usaini ne kenan?" Ta gyad'a kanta na ce." Ina na su Hassana?" Sai ta d'an diririce kafin ta ce." Yana can gida zan aiko miki da su gobe ko kuma an jima da daddare. Shiru na yi ban ce komai ba. Hadiza ta fito daga kicin da yaron a bayanta cike da walwala a fuskarta ta zauna suna gaisawa. Inna Uwani ta yi caraf ta ce." Wannan kamar 'yar uwar nan taki ko?" Na ce." E, itace Hadiza ba?" Sai ta ri'ke bakinta tana fad'in." Itace ta lalace haka sai ka ce wadda take d'auke da siga ko kanjamau!" Maganar ta dake ni sosai cikin fad'uwar gaba na kalleta bakina sai ya yi nauyi na kasa ce mata komai. Hadiza cikin gaggawa ta tashi ta bar wajan domin itama da alama maganar da Inna Uwanin ta yi akanta ba ta yi mata dad'i ba. K'asa na yi da kaina zuciyata na hantsilewa akwai dalilan da suka sanya nake d'agawa matar nan 'kafa ba wai don tana uwar kishiyata ba ina kallonta kamar Hajja tunda ciki daya suke amma an kusa kaiwa matakin da zan fara mayar mata da raddi a duk lokacin da ta yi mini wani rashin hankalin. Ya sauko ya same mu a zaune a falon ya zauna gefana yana kallon Inna Uwani da ta k'irkiri yi wa Usaini wasa har da yi masa rawa tana dariya shima yaron yana yi. Hakan kuwa ya yi masa dad'i sosai aka ce wai mai d'a wawa sai ya shiga washe bakinsa tana fadin." Yara duk sun yi wayo kamar ba biyu ba sun yi kyau uwarsu na da kafar nono mai kyau." Ya ce." Haka aka yi goyon 'yan uwansu ma." Ta miko mini yaron tana fad'in." Ai ban mance ba. Ubangiji Allah Ya raya mana su domin su zama cikon addinin musulunci duniya kuma ta amfana da su." Ya dinga amsawa da Amin ya rabbi Inna Uwani Ina godiya sosai." Suka tashi tafiya bakina ya mutu kwarai dangane da salon da suka shigo da shi. Da k'yar na ce su gaida gida ya tashi ya bi bayansu kafadarsa sa'be da yaron. Ina nan zaune ya dawo ya zauna cikin walwala a ganinsa mun fahimci juna tunda gashi har ya sakko ya gan mu kuma yaronsa na hannu Inna Uwani tana yi masa wasa wannan ne dalilin da ya assasa masa annasuwa da farinciki bai san da cewa wani sabon salo ba ne. Na zazzage kayan yaran ina dubawa. Eh rigunan manya ne kuma sun yi kyau sosai zan iya kar'ba na yi musu amfani da shi tunda an riga an saya na su Hassana ne ban ga ni ba. Na juya ina tambayarsa "Ta kawo mini kayan su Hassan ban ga na su Hassana ba?" Ya dube ni da kulawa yana fad'in." A a ba ta had'o da su ba ne?" Na ce." Eh" Sai ya dan yi jim kafin ya nutsu yana kallona ya furta." Ki bar mata su su yi sallah a hannunta idan hutun makaranta ya 'kare sai su dawo gabad'aya jiya ta fara gaya mini cewa tana son yaran su yi mata hutu.'' Girgiza kaina na yi tare da cewa." A a, yaranta dai ka kai mata su amma nawa yaran su dawo gidansu ba ni son abinda zai daga mini hankali a yanzu dai cikin ibada muke abinda ba zai yiwu ba ne.'' Ya d'an 'bata rai yana fad'in." Ke dai duk ta inda aka biyo miki ba a yi miki gwaninta Amina menene lefin nan da can kuma duk gidana ne akwai buk'atar a ko'ina yarana su sake su kuma yi sabo, ki yi hakuri ki bar mata su hutu kawai ta buk'aci da su yi a hannunta sai su dawo, ki duba kawaicin da ta yi miki a kan nata yaran mana." Na sake girgiza kaina a karo na biyu na furta." Na gaya maka fa ba zai yiwu ba ai ni ban buk'aci zaman yaranta ala dole a tare da ni ba. Kai ka kawo mini su kuma ba zan hana su zama ba tunda gidan ubansu ne. Maslaha anan shine ka kwashi yaranta a kai mata tunda zahiri ana shiga hakkinta alamu sun nuna kad'aici ya isheta hayaniyar yara take buk'ata. Kowa ya rike nasa shine zance na gaskiya." "Kamar yadda na isa na bata umarni ta bi ke ma haka za ki bi. Na gama yanke magana yara za su yi hutu gidan Hauwa idan sun 'kare su dawo ku cigaba da zama gabad'aya tuntuni yaranta dake suka saba kuma suna kaunarki babu wani dalili da zai sanya ni raba su dake saboda suna sonki itama ta yarda da hakan." Yana gama fad'in haka ya d'ora mini yaron saman cinyata ya kama hanyar samansa yana magana." Idan Hakan bai yi miki ba ni ma sai ki raba ni biyu ki d'auki b'angaran da kike so a jikina sai ki bata rabin tunda duk a kaina kuke wannan 'kiyayyar junan idan na mutu kowa zai huta ai." Na dinga kallonsa har sai da ya gama hawa steps na daina hangensa na dawo da kallona kan yaron da yake ta zura hannunsa cikin rigata nono yake nema. Babu kuwa halin ba shi domin tunda suka fara wayo nake had'a musu kamu irin wanda Sultan ya sha yana kan matakinsu balle yanzu da ake yin azimi ba ni yarda su tsotse ni da tsotsan jaraba. Bai sauko ba sai daf da za a sha ruwa mun gama aiki Hadiza na gyara kicin din muka dinga jin kuka a falon na fito da saurin gaske. wanda ya yi daidai da saukowarsa Minal ke kuka tare da Sultan Hauwa ta turo mai aikinta Ladidi wai su tafi tare. Sauran sun yi cirko-cirko. Kuka fa sosai Minal ta ri'ke hannunsa tana fad'in." Baba ba kaine ka ce mu zauna a can ba sai Mama ta dawo, to ina za mu je ai nan ne gidanmu Ladidi za ta d'auke mu." Sultan da tafiyarsa ta yi k'wari sosai ya taho da d'an gudu ya rige gefan rigar uban yana kuka ya sunkuya ya d'auke shi yana kallon Khalil ya ce." Je ka dauro alwala lokacin sallah ya yi." Yaron ya juya da sauri ya bar wajan. Sai ya dubi Ladidin yana fad'in." Je ki abin ki idan an jima zan shigo da yaran." Ta risina da sauri kafin ta juya ta kama hanyar fita. Khalil ya fito da alwala sai ya dire Sultan din a kasa ya ce." Ri'ke hannunsa muje massalacin tare." Ya yi gaba da sauri su kuma suka bi bayansa.. Na dube su Usaina ta ri'ke hannun Minal din tana zaune dirshen 'kasan ties amma kukan ya tsagaita. Na ce." Ya isa haka ta shi kuje ku yi alwala a yi sallah sai a ci abinci ko?' Ta daga mini kai tana sakin ajiyar zuciya ta tashi 'yan uwan suka tasa 'keyarta zuwa dakinsu. Daga ni har ita Hadizan cikin damuwa muke amma ni na yi kokarin ganin na kawar da tawa damuwar domin samar mata da kwanciyar hankali. Ba wani abu ba ne yake nukurkusarta face maganganun da Inna Uwani ta gaya mata d'azu. Bud'e baki ma da 'kyar ta iya saboda damuwa. Babu komai ai rayuwace duk wanda ya yi wa kaddarar wani dariya watarana Ubangiji shima zai jarrabe shi da abinda zai zama abin nuni da zind'e a idanun jama'a. A fakaice na d'an dinga jan hankalinta da wayo da rarrashi ta ci abinci tana ta nuku-nuku da hawayen dake ma'kale a kwarmin idonta. Tunda yau ma din a gidanta zai kwana ban tsammaci sake dawowarsa ba mussaman tunda ga irin rabuwar da muka yi wajan goma da ashirin muna falo muna kallo gabad'aya har da yaran ba su kwanta ba. Ya shigo ri'ke da hannun Sultan yana ta sauke ajiyar zuciya yaro idonsa ya yi jawur da kumburi almar ya ci kuka ya k'oshi. Khalil dake biye a bayansu Fadi." Yake yi ga ta can Usai din je ka." Ya kuwa tafi wajenta da sauri yana sauke numfashi. Na dubi Khalil din ina fad'in." Me ya same shi?" 'yar dariya ya yi kafin ya ce." Wai ba zai kwana a can ba shine yake ta ihu yana kiran Usaina." Abin ya ba ni dariya da tausayi. Na d'an janyo hannunsa ya taso ya tsaya kusa da ni tare da dora hannunsa saman cinyata na ce." Anan kai ma zaka kwana ko Sultan?" Ya d'aga kansa. Na furta." Ashe kwanciyar dole kuke yi a can din ko Khalil?'' Shiru ya yi bai ce komai ba sai ma ya yi k'asa da kansa. Hadiza ta mike tana fad'in." Bari a gyara musu shimfid'a." Ta nufi d'akin nasu da sauri. Na ce su tashi su bita su canza kaya sannan duk su yi alwala kafin su kwanta. Duk abinda ake yi yana tsaye yana kallonmu bakinsa ya mutu da alama ya rasa abinda zai ce. Bayan shigowarsu na dubi Khalil Ina fad'in" D'auko Usaini ka biyo ni dashi d'aki." Dama Hasan yana ri'ke a hannuna na tashi da shi a kafa'data kai tsaye bedroom dina na nufa ba tare da na sake kallon wajan da yake tsaye ba, a haka yara za su yi hutu a wajanta na kwanaki suna yi kamar za su mutu saboda kuka ashe da babu kowa a gidan ha'kuri kawai suka yi suka zauna tunda yanzu na dawo kuma sun nuna mata basu san wata ba bayan ni. Da nata da nawan gabad'aya don ni sai nake ganin twins ma sai su zauna a hannunta ba tare da koke-koke ba nata ba su zauna ba Minal dai da Sultan sun tsaneta wallahi abin har mamaki yake ba ni. Ita Minal yadda take bala'in sona shine abinda yake sanya mini sanyin jiki shi kansa Uban na lura da yadda jikinsa ya mutu abin ya fi karfinsa Hauwa ta haifar mini yara Allah mai iko......✍️ *GARKUWAR MATA* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *169* To ban san abinda ya kasance a tsakaninsu ba washe gari dai da misalin sha d'aya da wani abun Ladidi mai aikinta ta kawo musu kayansu kaf na can wanda suka yi amfani da shi bayan tafiyata kano da kayan sallar tasu da suke a hannunta pants takalmansu da kayan kitso abin wuya da hannu kowanne da na shi da alama duk ta had'a ta yi order din wurin Sadiyar gabad'aya girkina ne a ranar bai shigo ba sai bayan magriba tukkuna ya buk'aci abin bud'e baki na hada masa babu wata sakewa don sai nake ganin kamar akwai abinda ya boye mini. Kunun tsamiya muka yi da k'osai yadda ya kusa shanye dogon jug hakan ya tabbatar mini da cewa kunun ya yi masa dad'i k'osan ma ya ci fiye da biyar saboda sakin manya muka yi. Ya sha zo'bon dana had'a daidai gwargwado ya kammala yana godiya ga Allah kafin ya dawo da hankalinsa gare ni Na yi shiru ina sauraransa." Akan maganar da muka yi dake kwanakin baya kin ce kina buk'atar a musanya miki wannan kamfanin ko?" Na gyad'a kaina a nutse na furta." E, idan zai yiwu ba wai na raina kyautar ba ne kawai dai na fi gane business din da nake yi ina ganin idan na sake samun wani reshen anan za a samu alheri." Ya ce." Shine dalilin da ya sanya ai na sake tambayarki tuntuni nake ta shawara a kan hakan kyautar za ta koma kan Hauwa tunda ni ba ni so a tashi kamfanin ko babu komai kadara ce mai girma da ta kafu tunda a 'kalla da kafa kamfanin zuwa yanzu ya haura shekara goma sha shida duk yanzu muna kan aikin fad'ad'a waninsa ammana akwai buk'atar shi d'in a cigaba da aiki da shi. Na mallakawa Hauwa shi ke kuma akwai tallan wasu tsoffin shaguna da aka yi mini cikin kasuwar wuse din idan mun kammala da masu shi zan sanya ma'aikata su rushe tare da sabunta shi zuwa plaza din kamar yadda ki ka buk'ata a k'alla dai za a iya samun shaguna sha biyu 'kasa shida sama shida a hankali idan Ubangiji Allah Ya sanyawa abin albarka sai ki yi wadda ta fi wannan din ko?'' Na ce." Hakane na gode sosai Allah Ya saka da alhari ya kara arziki ya kuma jikan iyaye." Ya dinga amsa cike da jin dadi yana jifana da wani irin kallo wanda na gama fahimtar ko na menene. A daran kam na kar'be shi sosai kuma na yi kokarin ganin na yi masa bajinta wajan ganin na bashi farinciki yanayin yadda na tallafe shi ya k'ara dilmayar dashi cikin yanayi na shau'ki da sambatu irin wanda ba a tonawa wannan lamarin ai ba zai fasu ba idan da rai da lafiya a jikin gangar jiki. Kwanaki biyu bayan wannan su Baba Tabawa suka dawo murna a wurin yara ba a cewa komai tsalle mussaman Sultan ya rirriketa tana dariya itama ta rungumeshi bakinta kamar gonar audiga gabad'aya sun canza da wata iriyar nutsuwa alamu ibadar da suka gudanar ta samu karb'uwa a wurin Ubangiji domin fes suka dawo da wani annuri na mussaman a tattare da su. Dawowarsu ta sake bud'e wani sabon babi na farinciki a gidan ya kasance koyaushe cikin wasa da dariya da juna mussaman da bikin sallar ya gabato Mairo ta tsefewa yara kitso an wanke tas Taburni itace makitsiya Lad'ifa mai lalle saura kwana uku sallah ta zo ta yini tana yi wa yara washe gari ta dawo ta yi mini tare da Hadiza aikuwa tasha kudi wurin maigidan mussaman da ya ga na yaran ja da ba'ki ya fito sosai ya dinga duba kafafun nasu yana murmushi ta had'a kayanta ta tafi cike da farinciki dubu dari biyu kudin lalle kawai duk da Hajiya Maryam ta saba yi mata kyauta amma wannan ta yi mata bazata domin duk zuwan da take yi mini lallen ni nake sallamarta yau sai ga shi rabonta a ya rantse, ta samu kudi da turaruka da sabulai na hada mata da gyale mai kyau. A daran mai dinkinsu ya aiko da shi kowanne k'alla gudu leces biyu a tamfa daya sai shadda daya wadda ta ci uban aiki abin mamaki har da na masu aiki set biyu Hadiza kuma aka yi mata uku manyan atamfofi. Sai na 'kara mata da lece daga cikin kayana dake d'inke wanda ban sanya ba. Takalmi na bata set biyu masu tsayin dunduniya duk sabbi da abin wuya da hannu. gaskiya babu lefi ya yi kara ya kuma nuna halin dattako domin duk wanda yake karkashina yana sane da shi yana kuma ko'karin fitar da hakki ban ta'ba tunanin zai yi wa Hadiza d'inkin sallah ba duba da ganin yadda abubuwa suka yi masa yawa ashe yana sane da ita a gidan ya kuma fitar mata da hakkinta. Wannan shine abinda ya gudana bayan ramadan mun yi bikin sallah cike da annashuwa da farinciki tun daga kan masu aikin gidan maza dake waje da na cikin gidan su Baba Tabawa kowa ya kasance cikin nishadi da jin dad'i. Washe garin sallah yaran gabad'ayansu gidan Nusaiba suka yini bisa jagoranci Adam sai magriba suka dawo ta had'o su da snacks da yawa da kud'i Babansu ya dinga fad'a wai me yasa za ku kar'bo mata kudi ina lefin hidimar da ta yi musu. Na ce sallah ce ai don ta ba su kudi ba lefi ba ne. Sun je gidan Hauwa amma ba wasu wani jima ba suka dawo itama ta had'o su da tarin chocolates masu yawa har da sa'kon gaisuwa zuwa gare ni. Cikin raina na ce tunda kin fara dafe wasu kadarori ai fitina ta kusa zama tarihi kyautar kamfanin da ya yi mata ya taka muhimmiyar rawa wurin dakushe mata damuwa tun bayan abinda ya faru ba ta sake fito da wani salon ba ga yaranta har yanzu suna hannuna. Salim ya zo hutun sallah tunda yana can legos yana aiki a sabon kamfanin da suka bud'e shi ya dinga fita da yaran wuraran wassani ashe lokacin da Mamansu na raye haka yake yin jigila da su duk shekara ya ce ma saboda su ya dawo domin yin bikin sallah. Sati daya ga sallah Inna Uwani ta shigo har gida wai sallama ta zo yi mini zata tafi. Na bata turaman atamfofi uku da kudi dubu ashirin na ce ta kara guziri. Babu jin kunya ta dinga yi mini godiya daga lokacin na sake tabbatar da cewa muguwar kwad'ayayyice mai son abinda duniya Allah ne ka'dai yasan abinda Hauwa ta had'a mata domin tafiya dashi wanda kuma nake da tabbacin cewa shi kansa maigidan ya yi mata sallama mai kyau Allah Ya kyauta ya rufa asiri yanzu zamani ya lalace tundaga lokacin dana ganta a shekarun baya tana yi masa yarfen magani a kafar bane na tabbatar da cewa bata da hali kuma bata tsoron Allah kuma za ta iya aikata komai a kan biyan buk'atarsu tunda ai ba zata za'be shi ba ta ajiye 'yarta ba duk wannan jidali da koke-koken da take yi akan abin duniya ne tana taya 'yarta kishi tana kuma yi wa 'yar uwarta ciki daya zagon 'kasa a yanzu idan ya fadi ya mutu Na kudi ne littafin kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. damuwarta kad'an ce tunda ba ita ta haife shi ba mahaifiyarsa da yaransa sune suka yi rashi. Bala'in damuwar da suka shiga a lokacin da cikin nan ya zube ba zai misaltu ba domin an same shi ne da k'yar ni ma na gazgata maganarta bai fiye kwanciyar aure da ita ba domin da yana yi da ita ka'in da na'in zan samu sasaauci ta wannan fanni amma Allah ne da kullum duk ranar girkina sai ya neme ni idan har ba mu yi sunna ba to akwai dalili mai karfi wanda ya assasa rashin faruwar hakan koyaushe cikin doki da sambatuna yake ya sha fad'in shi kullum tamkar sabuwar budurwa nake a wurinsa abin ya yi ta ba ni mamaki haihuwa biyar ciki har da biyu sau biyu tun ina d'aukar maganarsa da dad'i ne na shau'ki har na gazgata domin da dukkanin gaskiyarsa yake fad'in hakan. To wannan shine dalilin da ya sanya su shiga tashin hankali a lokacin da cikin ya lalace har suna neman rabuwa saboda ganin kada a yi biyu babu yanzu kuwa na tabbatar da cewa ko da bata samu kula ta fannin auratayya daga wajansa ba to za ta cigaba da hakuri tunda ta fara samun abinda take buk'ata. Hadiza wata uku a gidana ta murmure haskenta ya dawo ta yi ki'ba jikinta ya fara cikewa domin dawowar masu aikin gidan na hana ta yin wata wahala mai yawa sai dai duk da haka takan yi mini d'awainiya da yaran amma ba sosai take shiga kicin ba. Hakan ya yi mini dadi sosai domin ta fara sakewa na saya mata sabuwar waya domin ta kara d'eba mata kewa da mantar da ita irin wahalar da tasha a baya wajan zamanta a gidan kurkuku idan tana ba ni labari irin wahalar da ake sha ni kuka ita kuka daga karshe ma na ce ta daina gaya mini domin yadda ta ba ni labarin wani ma'aikaci da ya dinga farautarta a lokacin da bai samu hadin kanta ba kullum sai ya sanyatawa kwashe busashen kashin band'akunan gidan da hannu kuma ba zai bata sabulu ta wanke hannunta ba haka idan an kawo musu abinci za ta ci bayan ta wanke da ruwa kacal tana gaya mini hannunta har sai da ya kame da d'oyin kashi. A d'akinsu kuwa mutum biyar sai da suka mutu saboda wahala tasha kwana da gawa a d'aki daya. Tun daga lokacin na ce ba ni son labarin saboda shiga tashin hankali nake yi na ce ta dage da addu'a tare da neman afuwar Ubangiji tsautsayi da mugun ji da gani asara tare da danasani Ubangiji Allah Ya kare mu. Ranar wata lahadi ya kasance girkina ne maigidan bai tashi a bacci da wuri ba sai bayan sha biyu na rana yana tashi kuwa ya ce mini towo zan yi masa kuma da hannuna miyar zogale. Aka duba kicin kaf babu zogale dole sai an shiga kasuwa Masa'udu ya je gida ganin iyalinsa tun sallah bai dawo ba shi kad'ai ne ya yi wannan nisan zaman domin ko su Taburni da Mairo satinsu hud'u suka dawo bakin aiki bayan sun je sun gaisa da iyalinsu tare da yi musu alheri daga cikin alherin wanda yake ri'ke da su. Mairo da Hadiza sune suka shirya shiga kasuwa sayo zogale dalili Taburni da Baba Tabawa na aikin abincin rana. Suka shirya suka tafi Sukairaju ya kai su na hada musu da sautin tsamiya domin ya dingi shan kunun tsamiya ko bayan wucewar Ramadan sai ya ce a dama masa kuma ba dare ba rana duk lokacin da buk'atar son shan kunun ya bijiro masa wadda muke da ita tana daf da k'arewa da zo'bo tunda ana yi masa baya shan lemo mai gas. Ba su yi awa d'aya ba kuwa suka dawo da komai da komai har da daddawa duk da ban buk'ace ta ba dalili ina da ita da yawa kuma mai mugun kyau wadda Hajja ta sanya aka yi mini ita mussaman lokacin haihuwar su Hassan da Magaji ya zo ya kawo mini kwalli da garafuni ya had'o mini da ita manya mai dadi a miya. Na ce ita din ma da suka sayo ba za ta'ki ba za ta yi amfani. Tsaf na shirya masa towon shinkafa da miyar zogalen kamar yadda ya buk'ata na yi amfani da zallar tsoka na k'aramar dabba wurin had'a miyar da ta ji gyad'a da manja ta yi kyau sosai tana ta tashin k'amshi. Cikin santi ya ci towon nan wurin malmala biyu kad'an ne bai cinye ba ina ta yi masa dariya ganin yadda yake sud'e hannu ina fad'in idan baka koshi ba sai a sa wani bai ce mini komai ba ya sud'e yatsun hannunsa tas ya shiga toilet domin yin burush Bayan kwana biyu ya je gidan Hauwa ya yi kwanakinsa ya dawo yake gaya mini wata magana. Jikina ya yi sanyi sosai na zuba masa ido a hankali na ce." Hadiza fa ka ce, bai duba shekarunta ba kwanaki biyar kawai ta ba ni shekara arba'in da biyar muke ni da ita ba budurwa ba ce.'' A nutse ya furta." Akwai haramci ne cikin abinda Annabi Muhammadu S.a.w ya yi. Kada ki yi mana sa'bo hajiya shima Sukairajun ai ba saurayi ba ne ya ta'ba aure." Na zuba masa ido sosai da mamakin jin maganarsa. Ya gyad'a kansa yana fad'in." Ya ta'ba aure shekarun baya a can mahaifarsa mutumin Zamfara ne kin ta'ba neman labarinsa a wajena?" Na girgiza kaina a hankali ina cigaba da kallonsa sai ya cigaba da ce wa.'' Ya zo nan kano cirani muka hadu da shi a titin Yahya gusau watarana tun kafin na yi shura a duniya yana sayar da fetur da kanikanci ya gyara mini mota a lokacin da lalace daga lokacin ya zama wanda nake bawa gyaran mota a duk lokacin da ta samu matsala muka yi sabo sosai har dai ya zama direbana kafin Ade da D'ahuru Sukairaju yaro ne mai Amana da nutsuwa da kuma girmama mutane ya gaya mini ya yi aure amma matar ta rasu wurin Haihuwa sasha zuwa garinsu wurin mahaifiyarsa kafin ta rasu. A duk lokacin da ki ka gan ni tare da Ade to Sukairaju ya je ganin gida tunda duk 'yan uwansa suna can garin. Kuma ba na tsammanin Hadiza za ta girma shi sai dai su yi daidai a shekaru to menene aibu shine ya gaya mini da zata amince sai ya aureta shi yana sonta duk da na gaya masa abubuwan da suka faru a baya ya amince da hakan, don haka ina nema masa auranta a wajenki tunda kece uwar dakinta idan kin ce a yi za a yi." Na yi kasa'ke ina kallonsa kafin na ce." Allah sarki wallahi ni kam ba ni da jayayya ko na kawo tasgaro muddin Hadiza ta amince zan fi son haka tunda har ka yabi kyawawan halayensa kuma ni ma na sheda hakan idan tana sonsa sai mu sha biki." Ya yi dariya yana kallona kafin ya ce." To ta wace hanyar ki ke ganin za a sanar da ita halin da ake ciki, kin ga ni yayata ce da kunya na tunkareta ko." Na d'an harare shi ina fad'in." Yayarka fa ka ce." Ya gyad'a kansa yana fad'in." K'warai kuwa ko da yini guda ta girme ki ai sunanta Yaya Hadiza a wajena." Na yi kasa da kaina ina murmushi na ce." Shikkenan to ni zan gaya mata in sha Allahu rabbi za ta amince." Ya furta." Da na fi kowa farinciki kuwa, ni kuma na yi alkawari zan yi iyakacin bakin kokarina.'" Na gyada kaina ina fad'in." Ubangiji Allah Ya tabbatar da alheri." Ya kama hannuna yana cewa." Amin Ya Allah." Ai a daran na same ta da maganar ta dinga dibi-dibi da 'kyar ta bud'e baki jikinta a mace babu wani karsashi da sukuni a tattare da ita ta kalle ni sai na hangi k'walla mai yawa cikin kwarmin idonta ta ce............. In sha Allahu da ni daku mu sanya rai saura 8 chapter littafin nan ya kammala Allah Ya taimake ni ya kuma yi riko da hannuna dan isar Annabi. Ina miko godiya kwarai da fatan kowa ya sha ruwa lafiya. Ubangiji Allah Ya kar'bi ibadarmu ya 'yantar damu.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124... BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *170* Shiru na yi ina sauraranta a yayin da take gaya mini abinda yake damunta har tana zubar da hawaye na damuwa da kunci tare kuma da fargaba. Jikina ya yi sanyi sosai domin dai na riga na gama fahimtar manufarta ba wai auran ne abin gudu a wajenta ba abinda zai haifar bayan yin sa shine take ji wa tsoro da zullumi. To ai babu wata cuta da Ubangiji bai yi maganinta ba duk da infection wani irin ciwo ne da yake saurin dakusar da mu'amula da auratayyar da aka gina cikin tsananin so da sha'kuwa. Bayan rashin ha'kuri daga b'angaran ma'aurata abu na biyu da yake saurin kassara aure da lalatashi shine infection mussaman idan an yi katari da cewa macace taje da shi ta shafawa namiji abin sai ya yi muni da tsanani aure ya gurgu'de ba tare da yaje ko'ina ba. Hadiza na ga wautarta kwarai domin yanzu a k'alla da fitowarta daga gidan gyaran hali za a samu wata hudu to tun a lokacin ya kamata a ce ta sanar mini da abinda yake damunta domin neman magani ka'in da na'in. Zubar ruwa da kumburin gaba abu ne mai tsanani watarana zata iya wayar gari da susa tunda shi infection din idan ba a yi sauri an tare shi ba girmama yake yi har wasu su d'auka ta dalilin da rashin kula. Dama tun zuwanmu daki daban na ware mata a falon nan take kwana hakan ya sake yi mini amfani kywarai domin kuwa ina ganin da an yi had'akar toilet to wani zai iya d'auka wannan lamarin ba abin yin shiru ba ne kenan da wannan mas'alar ba ta zo ba haka za ta cigaba da zama da ciwo yana cin ta har sai ya zama babba irin wanda ake gudu. Tabbas babu maganar aure a wannan yanayin da ake ciki tukkuna sai an magance matsalar idan ya so ko ma menene sai ya biyo baya babu amfanin gaggawa cikin kowane lamari kuma aure ba abin wasa ba ne idan har an yi shi to kowace mace tana bukatar zama a dakinta rayuwa ta din-din din ai abinda ya fi infection ma za a iya d'auko shi a wannan gida domin da ta biyewa mazan dake bibiyarta wata'kila da da cutar 'kanjamau za ta dawo tunda yanzu maza da yawa sun lalace da neman matan banza ba wai ma'aikatan gidan ba manyan mutane ma da suke yawo cikin manyan riguna da motoci na alfarma tare da wata suttura ta Allah amma sai ka same su a hotels tare da karuwai suna amfani da su kuma suna da iyali a gida har da yaransu. Haka dai na kwana cikin tunani da nazari da safe ashe yana hankalce da ni yana ta shirin fita ya ce na fito masa da takalminsa sahu ciki dake ma'ajiyarsa na fito masa da shi din kamar yadda ya buk'ata ya fesa turare ko'ina na jikinsa ya zo ya zauna gefena a nutse ya fara sanyawa k'afafunsa safa sai da ya kammala tukkuna ya dube ni amma bai ce komai ya gyara zaman gilas dinsa ya furta." Akwai abinda yake damunki Giwa ashe mun kai matsayin da yanzu za ki dinga yi mini b'oye -b'oye, an yi wani abu ne a gidan?" Na kalleshi cikin kame-kame na furta." Wallahi akan maganar Hadiza ne ba wai boye maka nake yi ba abin ne dai yake buk'atar nutsuwa kafin wanzuwarsa." Ya nutsu sosai yana kallona." To ai babu dole Amina shi aure na mutum biyu ne don Allah idan ba ta so kada ki tursasatata ai ba yarinya ba ce ita tana da damar zabin namijin da ya yi daidai da rayuwarta shi da ya nemi auran nata zan gaya masa ya nemi wata." Na gyad'a kaina a hankali na ce." Tana sonsa kuma tana son yin auran yadda ta nuna mini to amma kamar yadda ka ce babu munafurci a sha'ani irin wannan itama abinda ta duba kenan ta gaya mini tana da matsala tun fitowarta daga wancan gidan take ta fama da matsanancin infection." Jim ya yi yana kallona kafin ya furta." Hakan ba zai hana a aureta ba tunda muna da asibitai da masu maganin gargajiya kowace cuta tana da maganinta don haka ku je asibiti tare ko kuma ku yi waya da Dr Sailuba duk abinda yake damunta a sanar da ita ni kuma na d'auki nauyi jinyyar in sha Allahu." Na ce." Mun gode sosai Allah Ya saka da alheri, amma za mu fara yin na hausa ina da mai maganin Islamic masu kyau da inganci mafiakasari ina ji ana fad'in na Hausa ya fi kassara shi ya lalata tasirinsa har abada in sha Allahu za a yi dace Ina ganin idan har ta yi amfani da maganinta to duk wani nau'in sanyi za ta yi fitsarinsa." Ya gyad'a kansa yana fad'in." To hakan ya yi ki yi magana da ita din a jarraba Allah Ya sa a dace Amin." Na ce." In sha Allahu zan yi magana da ita. Ya mike yana duba agogonsa cikin zolaya ya furta." Ni ma a samo mini maganin karfi idan da akwai a Islamic din kwana biyu ba ki gan ni ba kuzari ba." Ban san lokacin da na wurga masa harara ba, ya fashe da dariya yana fad'in.''Menene to Giwa idan na ce ki nemo mini maganin karfi waye ya fi amfana." Na tashi ina d'an yin tsaki 'kasa-kasa saboda takaici na ma rasa abinda zan ce masa. Ya riko ni sosai a jikinsa yana yi mini magana a kunne. Da sauri na dube shi, wai maganar wata haihuwar yake yi mini yana son mai sunan Hajja Halimatussadiya. A ganina idan na sake haihuwa da wannan shekarun kamar zan zama abin kallo yara na yi kai ma kana yi Kamalu da Yusi sun zama zagada zagadan samari. Ya rike hannuna sosai muka kama hanyar fita daga d'akin yana cigaba da yi mini maganar samun ciki. Wai ana samun mace mai sunan Hajja shikkenan Allah Ya sallame shi. Shiru kawai na yi ban iya ce masa komai ba saboda gudun kada na fad'i abinda zuciyata take gaya mini ya zama lefi tunda shi tsakaninsa da Allah da kuma iya gaskiyarsa yake maganar Allah dai ya kyauta Sai da na samu nutsuwa tukkuna da yamma na kira anti Yagana a waya muka gaisa sosai tare da tambayar bayan rabuwa ta ce mini Fadila nan tana ta shirye shiryen zuwa domin yi mini kwana biyu na ce ina sauraranta. Daga nan na shiga gaya mata halin da ake ciki da farko ta dinga murna har tana kwarzanta d'abiu da kyawawan halin Sukairaju tunda ya zauna a gidanta shekarun baya da na je bikin babandi garin a lokacin da ya had'a ni da shi domin ya zame masa security lokacin da yake kan sharafin kishinsa. Fadi take yi lallai Hadiza ta yi miji kwarai da gaske abin godiya ga Allah ne. Ban katse ta ba sai da na bari ta gama murna da adduarta tukkuna na gaya mata matsalar da take damun Hadizan. Jikinta ya yi sanyi sosai cikin kasala da sanyin murya ta furta." Har kin sanya jikina ya mutu Amina wannan matsalar ai babba ce kuma ba zai yiwu a rufe ta ba akan son ranmu amma tasan bata da lafiya mai yasa tun farkon dawowarta ba ta yi magana ba wannan ai rashin hankali ne, domin da ta yi magana tun farko da tuni yanzu an ci karfin magani. Na ce." Ni ma abinda na ce kenan wallahi anti Yagana Hadiza fa sai da na yi da gaske sosai amma duk ta susuce wallahi idan tana yin wasu abubuwan sai ki dauka ta samu matsalar kwakwalwa." Ta ce." Dole hakan na iya faruwa domin can inda ta zauna din wani darasi ta koyo mai zaman kansa gida ne da idan Allah ya sa mutum ya shiga a sa'a yake fitowa da raunin zuciya da jin tsoro tare da nadama. Idan kuma mutum bai shiga a sa'a ba sai ki ga ya fito da bushewar zuciya tare da koyo wasu dabi'un marasa kyau wanda suka fi na da muni! Mu dai godiyar da za mu yi wa Allah yadda ta fito da kyawawan halaye." Na ce." Hakane yanzu dai mun yi magana da maigidan ya ce a nema mata magani ko na asibiti ko na hausa zai saya." Ta ce." Ubangiji Allah Ya saka masa da alheri ki yi masa godiya sosai mun gode Allah Ya jikan mahaifa." Na ce." In sha Allahu zan sanar masa bayan kwanaki biyu duk yadda ake ciki zan sanar dake in Allah Ya yarda." Muna yin sallama na kira GARKUWAR MATA. ita ce mai maganin da na tabbatar da inganci da sahihancinsa duk eanda ya san ni da ita ya san ni domin kuwa tunda na fara amfani da magunguΓ±anta ban kuma marmarin amfani da wani wanda ba na ta ba. 08089965176 Duk halin da Hadiza take ciki na gaya mata a take a lokacin ta ce sanyi ne amma bai riga ya girmama ba kuma idan har an dage da magani za ta rabu dashi. Na ce ta had'a mini mai kyau ta aiko mini dashi har da set din kayan mata irin wanda nake saye. Ta ba ni tabbacin za ta sanya a mota da sassafe. Muka yi sallama cikin amince sannan na duba details dinta na tura mata kudi har da karin dubu goma akai ta kira ni tana yi mini godiya taga dubu goma ita kuma me nake buk'ata na ce ta sayawa yara sweet domin yadda nake jin dad'in magunguΓ±anta sai nake ganin babu abinda zan bata wanda zan biyata. To wata'kila shi ma da abin ya yini duk da ba girkina ba ne da daddare da ya shigo yi mini sallama sai da ya sake tuntubata ya muka yi da mai magani har yana gaya mini anti Yagana ta kira shi a waya tana yi masa godiya. Na ce eh na gaya mata halin da ake ciki ne, mai magani kuma mun gama magana da ita ya ce nawa ne kudin. Shiru na yi ban iya bashi amsa ba sai nake ganin da kunya ace na bari ya biya tunda ina da halin biya shima ya san haka yau da asibiti ne babu yadda zan yi tunda likitocin da suke duba mu shi yake sallamarsu. Ya dinga tambayata na share shi har abin ya bashi haushi ya shiga fad'a na ce." Kudin fa ba su da yawa ka bar shi na biya gobe za ta aiko da shi." "Tunda dai na ce a gaya mini ai sai a gaya mini komai k'ankatarsu ai ni na yi niyya ko ke ki ka sanya ni ne da zan ta yi miki magana kina ji ki yi banza da ni." Na ce." Allah Ya ba ka ha'kuri dubu hamsin ne." Ya gyad'a kansa ba tare da ya sake cewa komai ba ya d'auki wayarsa ya kunna sai kuma ya sake dubana cikin had'e gira ya ce." Na 'karfin mazan fa? tunda duk inda aka samu maganin sanyi ko na basir ba za a rasa na maza dana mata ba." Na ce." Yanzu fisabillahi sai na ce mata mijina yana son maganin karfin maza ai sai ta raina ni wane irin kallo kake so ta yi maka ko a jikin jarida da kafafan sadarwa idan ta ga hotonka za ta tuna ashe lusari ne na taba saya maka maganin k'arfin maza a wurinta ba zan iya ba." Ya dinga dariya yana kallona kafin ya tsagaita still idonsa na tsaye a kaina ya ce." To menene abinda ba ni kad'ai ba ne muna nan da yawa a gari fa, gwara ni ma akan wasu." "Ni dai mijina gwarzo ne tunda har ya iya bada biyu sau biyu a jera aikuwa ba shi buk'atar wani maganin mazantaka gaskiya ba ka yi wannan lalacewar ba tukkuna ai baka wani tsufa ba." Ya lumshe idonsa ya bud'e tare da k'ankance su a hankali ya ce.'' Ba ki ji an ce idan da kyau a kara da wanka ba Giwa, ai ba ni nake bada bibbiyu ba Allah ne da damar a hannuna take da tuni na sallami Hauwa itama na bata nata biyun ko na huta da mita." Ta'be bakina na yi ban ce komai ba domin ba ni so idan muna magana yana yi mini maganarta tunda yanzu sun samu daidaito a tsakaninsu shikkenan kowa ya yi zamansa amma bai fahimci hakan ba sau tari idan muna magana sai ya kira sunanta a ciki. Ganin yadda na kawar da kaina da kallonsa ya sanya shi sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce." Kin sanya mini wani shauki da buk'atar kasancewa dake a wannan dare. Kin yaba ni kin kuma nuna bajintata har kina tabbatar da gwarzontakata na tabbatar da cewa har cikin ranki haka maganar take da gaske da za ki ba ni dama a wannan dare da na sake nuna miki jarumtata na kuma roki Allah bisa k'wanjin da zan zage domin raya sunnarsa ya azurta ni da mai sunan mahaifiyata." na kudi ne littafin kada ki karanta ba tare da kin biyani hakkina ba A sanyaye na dube shi. da gaske fa yake shi so yake yi na sake haihuwa kuma ciki yake jajibo mini yara ko shekara d'aya ba su cika ba. Yanzu kuma na yi wata magana cibi ya zama k'ari sannan da yake wannan maganar yau da ba girkina ba ne ta hanyar satar kwana za a samu cikin mai sunan mahaifiyar tasa kenan. Ya ri'ko hannuwana yana dora bakinsa a wuyana yayin da hucin numfashinsa ke sauka a hankali. Tsigar jikina ta shiga tashi na d'an janye daga jikinsa ya kara riko ni a d'an rikice yana bin jikina yana sansanawa kamar muzurun da ya samu nama bayan ya d'auki shekaru bai yi arangama da shi ba. Na sake janyewa a karo na biyu ina fad'in." Ya kamata ka tafi wata'kila a can idan rabon ya rantse sai ka ga an samu abinda ake muradi tunda ai ka ga ba zai yiwu ba a cikin hakkin wata ka dinga ikirarin samun mai sunan Hajja idan fa muna neman albarka da kwanciyar hankali. Ya sake riko ni yana fad'in." Hakan ba haramun ba ne Amina, ki dan ba ni dama mana a cikin wani yanayi nake kwarai da gaske duk da kin nuna ba ki son maganar Hauwa ya kamata ki lura da yanayina ba ni da wata nutsuwa a ranakun girkinta ina kwanciya da ita ne domin hakkinta amma abinda ba ki sani ba shine ba ni gamsuwa irin yadda nake buk'ata. kuma ban fad'i maki haka don na tozartata ba ke ma kada ki yi mata kallon wadda ta gaza a wurin miji Amina ba ni tunanin ko budurwa na kawo ta wadatu da baiwa tare da tarin ni'imar da Allah ya yi miki kin fita daban a cikin mata koyaushe ina alfahari da wannan kyauta da Ubangiji ya yi mini." Jikina ya mutu sosai to ko dai ya yi ne domin ya ja hankalina tabbas ya samu nasara domin kuwa jikina lakwas ya yi kwakwalwata na tariyo mini zafafan kalaman da ya furzar da su a yau a kaina duk da shi din namiji ne mara k'waron baki ko a shimfid'a ne idan yana nisha'dantuwa ya kan rasa inda zai tsoma rayuwarsa kalaman soyayya da yabawa ina shansu masu tafe da sheshaka da kuma gurnani mai tafe da d'igar hawaye. Na kan ajiye wannan akan shau'ki tunda ni ma ina yi a wasu lukutan ni da shi din sakarkaru muke zama amma na yau sun sagar mini da gwiwa jikina ya mutu murus ya samu damar tatta'ba ni son ransa amma ban bari lamarin ya wanzu ba domin sai zuciyata take gaya mini idan har kun yi sunna Amina Allah Ya bada rabo to zai iya jarrabarku ta wata sigar domin hakki kuka take babu ruwanki da abinda yake faruwa a tsakaninsu idan yana gamsuwa da ita ba matsalarki ba ce haka zalika ma idan baya gamsuwa da ita. Na k'wace da k'yar sai kace wasu k'ananun yara ni da shi yana kamo ni ina dojewa na samu na sauka 'kasa cike da mutuwar jiki da tunanin wannan lamari. Washe gari da safe kalau ya shigo kamar wani abu bai faru ba a tsakaninmu na dinga tunanin yanayin da na bar shi a jiya amma kuma a wartseke ya shigo babu kasala ko k'ankancewar ido gashi kuma da bakinsa ya furta baya gamsuwa irin yadda yake so da Hauwa hakan ya nuna maleji yake yi. Bai yarda ya amsa gaisuwata a falon k'asa ba sai ya haye sama Hakan ya nuna mini yana buk'atar na bayansa. Ban kawo cewa ga dalili ba ko bayan da na bi bayan nasa gaisawa kawai muka yi ya ce ga abinda ya shigo dashi tunda Allah Ya sa gari ya waye to ya dawo hannuna Wallahi ni abin ma dariya ya ba ni na zauna ina ta yi ina kallonsa a yadda tun farko muke ai bai dawo hannun nawa ba tukkuna sai da yamma dare ya shiga sai ya shigo na bashi baccin dare daga nan kuma komai ya faru. Yanzu saboda da rigima ya dage yana fad'in kwana biyunta sun k'are har dariyar da nake yi ta bashi haushi ya fara fad'a yana cewa na mayar da shi wawa kenan yana magana akan hakkinsa ina yi masa dariya saboda rashin tausayi. Ni dai sauka k'asa kawai na yi na kyale shi. Amma daga zarar abin ya fado mini zan yi murmushi ikon Allah. Baccin dole ya yi daya saura na rana na sake haurawa saman saboda lokacin sallah ya yi na same shi ya tashi daga baccin yana ko'karin sauka daga bed din ko kallona bai yi ba ya tashi ya nufi toilet.. Aikuwa dai a daran na gayawa 'yan garin mu abinda duk fitinarsa baya wuce yi sau biyu yau kam uku ya yi yana ta ko'karin yin na hud'u na rasa inda zan tsumbula rayuwata domin kuwa da gayya yake yi yana fad'in tunda ke uwar mata ce bai kamata a ji tausayinki ba. Na galabaita sosai na dinga gwada 'karfina domin na zame amma ina duk ya taushe mini jiki ko'ina na jikinsa 'kwarin gaske k'yam-k'yam! Ya sossoke ni da k'ashin hannu da gwiwarsa. Da gari ya waye na dinga galla masa harara yana ta murmushi na ce." Ba maganin k'arfin maza ne ya dace da kai ba zumar ki'ba zan saya maka ka yi zuciya don girman Allah ka yi ki'ba kai ko irin tumbin nan na masu kudi ma baka da shi Allah Ya saka mini." Duk ciccijewar da yake yi sai da ya fashe da dariya ya kishingida lafiyar lau ya ce." Ai na gaya miki irin wannan hawan zan dinga yi miki abinda ba yarinya ba ce ke, giwa wai har kece me yi mini dariya saboda kin raina ni, namiji nake har yanzu." Na girgiza kaina ban ce komai ba na kama hanya na fita daga d'akin yanzu lamarinsa ya daina ba ni mamaki tunda kullum sabon darasi nake d'auka a wajensa.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *171* To 'kasa da kwanaki goma Hauwa ta fara amfani da maganin infection din Islamic din GARKUWAR MATA kyakykyawan result ya fito domin da bakinta take gaya mini wurin da ya kumbura ya sa'be sannan ruwan da yake fita yana b'ata mata pant da karni karni da wari shi ma ya daina zuba tana dariya sosai take jaddada mini cewa a matsanancin buk'ace take tun lokacin da ta fara amfani da maganin take matse-matsen cinya sha'awar da ta mance ya ake jin ta shekara da shekaru to yanzu itace take bijiro mata. Lamarin ya ba ni dariya sosai da mamaki lallai na yarda da maganar GARKUWAR MATA da tun farkon had'uwarmu take gaya mini cewa babu buk'atar rantsuwa akan duk abinda take sayarwa ni zahiri ce kwarai da gaske gashi yanzu na sake gazgatawa maganin ne ya wanko mata duk dattin mara har ta fara jin sha'awar d'a namiji tunda gashi da bakinta tana fad'in cewa ta mance ma yadda ake jin feeling din sai yanzu da tasirin maganin ya tasirantu a gangan jikinta. Aikuwa sai ta zama abar tsokanata bini bini da abin ya fado mini sai nasa dariya ina kallonta har dai ta tsargu ta fara kame-kame tana sake jadadda mini da gaske take yi kuma ba ta fad'i domin na yi mata dariya ba tsabar farinciki ne ya sanya ta kasa rufe bakinta. Ni kuwa na ce ai dariya kam yanzu na fara tunda har lafiya ta samu to auren zai tabbata da izinin Allah. Ban sanar da maigidan ba sai da ta gama shan maganin na tsayin sati uku tukkuna lokacin ta kara kasantuwa cikin jazaba irin ta buk'atar ruhi da gangar jiki kuma ba ta jin kunyar gaya mini yanayin da take ciki ba. Ranar da girki ya dawo hannuna bayan mun nutsu ni da shi na gaya masa halin da ake ciki. Ya yi murna sosai yana fad'in abu na gaba a tsakaninsu zuwa yin gwaje-gwaje kamar yadda zamani ya zo da shi domin samun nutsuwa da kwanciyar hankali. Ni ma hankalina zai fi nutsuwa da yin hakan daga kowane bangare a samu daidaito. Alhamdulillahi kowane irin tes an yi kuma sakamako mai kyau ya fito na genotype ya yi mini dadi sosai Hauwa AS Sukairaju A-A Bangaran blood group ma komai ya daidaita yadda ake so. Tsakanin shi da ita sai na rasa wanene ya fi farinciki kasancewar yanzu na taka tudu biyu sai girman da yake ba ni ya kara tsananta duk da maigidan ya gaya masa yayata ce amma risina mini yake yi kuma ba shi yarda mu had'a ido. Ni dai da muka dawo daga asibitin a mota na bar su shi da ita suna zantawa. Ina shiga ciki na riski Hauwa tare da Mairo a falo suna hira yaran dama sun tafi skull tun safe. Na zauna kan kujera cikin hijabi don ban iya cire shi ba ganinta a falon a zaune sai nake tambayar zuciyata dalilin zuwanta. Muka gaisa sosai da sakakkiyar fuska abin har ya so ya ba ni mamaki amma dai na share ban nuna mata na ji dadin zuwanta ba haka zalika kuma ban nuna mata na ji haushin ganinta ba ta ce mini sallama ta shigo ta yi mini farkon wataran maulid wanda saura kwanaki uku kacal mu shiga za ta tafi umara kasa mai tsarki. Na taya murna sosai da fatan alheri mu kad'an ta'ba hirar yara kad'an kafin ta tashi da zumar tafiya ni ma na mi'ke har bakin kofa na taka mata ta fita tukkuna na dawo falon na ce da Mairo ta shiga kicin ta cewa Baba Tabawa su dafa zogalen nan da Masa'udu ya kawo mana tsaraba daga garinsu domin kafin maigidan ya fita ya ce a yi masa kwadonsa idan ya dawo da yamma zai ci. Ta tashi da azama kuwa ta nufi kicin goye da Hassan a bayanta. Usaini kuma ina da tabbacin yana bayan Taburni tunda kusan tare suke rainon su biyu wasu lukutan Hadiza da Baba Tabawa na sanya musu hannu. Hadiza ta shigo cikin annashuwa sai na fashe da dariya ina kallonta cikin zolaya na ce." Masoya masu kafasiti Hadiza na fahimci Sukairaju ya saye zuciyarki kina sonsa ba." Ta zauna tana kallona da murmushinta har yanzu ta ce." Sosai kam, kin san lokacin kuruciya sakarci muka dinga yi na zo na za'bi mugun mutumin nan Alhaji Halilu Umma da Baba Sule suka rud'e saboda watsi da kudin da yake mini, lokacin wallahi ban san menene so ba Amina ni ma kudi da jin dad'in kawai nake hange ashe mugu ne azzalimi na ci wahala a hannunsa ba kad'an ba." Na gyada kaina a tsanake na ce." Kaddara ce ai Allah ya zano shi a matsayin mijin da za ki aura amma shawara anan shine kada ki yarda ki nuna masa tsananin son da kike yi masa maza suna da wani abu a duk lokacin da suka gane mace na mutuwar sonsu to sukan kwatanta rashin adalci a kanta. Amma ba duka ne suke da wannan halin ba. Ban ce kada ki nuna masa k'auna ba amma daidai misali." Ya gyad'a kanta a hankali tana fad'in." In sha Allahu zan lura amma fa ni kaina yanzu ne nake jin ina soyayya Amina." Na yi shiru ban ce komai ba sai ta cigaba da cewa yanzu muka gaisa da Hauwa a farfajiya ta tare ni da fara'a sosai abin har ya ba ni mamaki." Na ce." Ta sauko ai tana neman shiri ta zo yi mini sallama ne wai za ta tafi umara cikin satin nan." Ta ce." Allah Ya kar'bi ibada ya sa ta je lafiya ta kuma dawo lafiya." Na amsa da Amin ta d'an yi jim kafin ta cigaba da cewa." Wai tambayata take yi yaushe zan je gidanta mu gaisa sai na ce mata zan zo in sha Allahu. Shine ta wuce tana cewa wai tana saurarena kafin ta tafi umara." Na ce." Wata gaisuwar kuma za ku yi bayan wadda kuka yi a yau Hadiza?" Ta ta'be bakinta tana fad'in." To ni ma haka na gani sabon salon makirci ne ai babu inda zan je kuma ni ban yarda da wannan faram-faram din na ta ba, hausawa suka ce ruwan da ya dake ka shine ruwa. Ban ce komai sai murmushi na saman lebe Hauwa kenan neman mutane take yi yanzu ga shi kuma ba ta iya mu'amula ba. Nusaiba ta sha gaya mini wai tana kiranta a waya ita har tana mamakin a ina ta samun lambarta yarinyar da ta yi wa zagin tsamar nama da cin zarafi shine yanzu take janta a jiki saboda tana kishin yadda yaran ke dabdala a gidana domin ko zuwan Salim hutu nan wurina yake d'aukar abinci kamar yadda d'an uwansa ke zuwa ya d'auki na rana da daddare Adam kwana ne kawai ba ma yi a tare a gidan. A can gidansu yake kwana tun bayan abinda ya faru da Nabila to yanzu kuma sun juya Legos din shi da Salim din domin cigaba da gudanar da abinda zai kawo musu cigaba a rayuwarsu. Lamarin yana yi mata zafi ba tun yau ba na lura da cewa ta tsani duk wanda zai ra'be ni shima sai ta dasa masa k'iyayya. To yanzu kuma taga hakan bai yi ba ta fito da wani salon. Lambar waya ai ba za ta yi mata wahala ba ko a wurin mijinta za ta iya samu. Kafin ya shigo gidan ya kira ni a waya yana fad'in zogalan nan da Masa'udu ya kawo dama buhu guda ne d'anye sai uwar doya da albasa ya ce a dibarwa Hauwa na ce to ina mamaki shin shine ya gaya mata ko kuwa a takaice dai na ce." Zogalan kad'ai ka gaya mata an kawo ko da sauran abubuwan?'' Na ji shi yana fad'in.'" Shi tace tana buk'ata idan ma aka ajiye shi zai bushe ko ya lalace ku d'ibar mata tunda tace tana buk'ata." Na ce." Ba wani lalacewa da zai yi ai kana son miyar zogale sai mu busar da shi." Ya ce." A d'ibar mata dai na ce." Sai na tare shi da sauri ina fad'in." Ai shine na ce iya zogalan kawai ka gaya mata an kawo ko da sauran tsarabar." Ya ce." A a ni ban gaya mata ba Giwa mun yi waya ne yanzu take gaya mini ta shigo yi miki sallama bayan ta fita suka gaisa da Masa'udu tasan ya yi tafiya zuwa garinsu shine ya gaya mata abinda ya kawo muku." Na ce." To tunda hakkinta za ta fitar mata ai kamata ya yi ta buk'aci sauran kuma saboda neman magana ni me yasa ba zata gaya mini ba." Cikin k'osawa ya furta." Ba ni son 'karamar magana ta zama babba Amina kwana biyu abubuwa sun yi sanyi dalili na fahimci kowacce a tsakaninku kada ki girmama lamarin don ta sanar da ni ba wani abu ba ne, ni kuma ai gashi na gaya miki." Na ce." Munafurci ne kawai idan da yarda babu wani nufi a zuciyarta ai ni ya kamata ta gayawa tana buk'ata tunda tana da lambar wayata." Ya datse kiran ba tare da ya ba ni amsa ba. Kicin din na shiga na ce su raba tsarabar nan kashi biyu daidai a bawa Hauwa. Hadiza dake gyara alayyahu ta ce." A a ai nan kuke da yawa Amina na yi zaman gidan iyali na gani kin san dai Alhaji Halilu matansa biyu ni ce ta uku ko, to duk abinda ya kawo nawa ne kad'an tunda ba ni da yara. Me zai sanya za a yi haka kuma?" Ina dariya na ce." To Masa'udu garin kaud'insa ya gaya mata ya kawo tsarabar zogale da albasa tare da doya shine tana zuwa gida ta kira maigidan wai tana son zogale. Taburni ta ce ." Ban da abin Hajiya Hauwa ai ke da ita duk daya ne sai ta gaya miki tana buk'ata ta shigo ta dibi yadda ranta yake so." Murmushi kawai na yi ban sake tankawa ba Ina jin su suna ta magana. Hadiza na fad'in." Idan an raba an bata biyu ba a yi miki adalci ba." Anan ne na ce to wannan tsaraba dai ta Masa'udu na neman ta janyo cecekuce ayi dai yadda na ce din idan ma kyautar da su za ta yi shikkenan a bata zogale ne dama yake yi mana wahala don ta doya da albasa wannan ai ba matsalarmu ba ce ko ku raba daidai a had'a mata cikin buhu sai ta aiko ta d'auka." Na juya na fita daga kicin ina jin maganganunsa akan lamarin. Yana kuwa shigowa da abinda ya fara kenan na ce an raba kashi biyu ta aiko ta d'auka ko kai ka d'auka ka kai mata. Yadda na fadi maganar a harzuke shine abinda ya sanya shi tsirawa fuskata ido yadda ya nuna kamar abin ba na tashin hankali ba ne gashi ina ko'karin girmama shi. Ni abinda ya ba ni haushi yadda ta kasa tambayata sai shi zata tambayata tunda ai Masa'udu direbansa kuma shi ya kawo kayan babu buk'atar ta tambayeni wanda yake zaune dominsa shi za ta tambayata ni ban isa ba. Yanayin yadda ya damu da lallai sai an bata tamkar wadda ta bawa umarni. Haka dai ya dinga kaucewa neman fitinata domin so na yi ya tanka na fad'i abinda yake raina sai ya'ki biye mini ya kira ta a gabana yana fad'in ta turo Ladidi ko yaron dake bawa shokokin gidanta ruwa ya d'aukar mata. Ya kashe wayarsa. Ya dinga jana da hira a lokacin da nake zaune a gefansa yana aiki a computer na ki biye masa ni ma. Sai ya ja bakinsa ya yi shiru tsayin minti ashirin da biyar ya gama abinda zai yi ya rufe Loptop din Yana kallona ya ce." In banda dole sai an janyo mini tsiya a gidana ya za a yi rigima akan zogale Amina wai don Allah menene yake damunku ne?" Na dube shi ina fad'in." Halin tsiya ai yana wajanta Allah Ya yi maka mai kyau duniya da lahira ni ai ban ce komai ba, ka ce a dibar mata zogale an yi yadda ka ce din to kuma sai ya zama lefi." Ya gyad'a kansa still idonsa a tsaye a kaina ya furta." Shine na ce ai kuna nema ku ba ni kunya saboda rashin tsinkaye da tunani ita tana can tana surutai na banza bisa wani zargin da bashi da toshe ke kuma gaki ba ki da fahimta wato cewar da na yi a dibar mata zogalen da Masa'udu ya kawo sai ya zama a lefi a wurinki Amina har ki dinga ko'karin zagi na." Da sauri na ce." Yaushe na zage ka don Allah?" Ya nuna kirjinsa da yatsa yana fad'in." Kin san dai ba zan yi miki k'arya ba ko, ai ni ba kurma ba ne na ji lokacin." Kasa'ke kawai na yi ina kallonsa da mamakin yaushe ya koyi 'karya mai lasisi irin haka. Nasan dai gwani ne shi wurin juya magana idan yana so ya kare kansa ko ya kashe wata rigima yanzu nan zai sar'kafe ya cukurkud'a magana ya kuma dage shine da gaskiya yanzu ma abinda ya shirya yi kenan uana so ya d'aure ni da jijiyar jikina ban zage shi ba amma gashi yana fad'in na zage shi ai ba mahaukaciya ba ce ni. Ya cigaba da sakin maganganu." Duka kun raina ni wallahi saboda na yi sanyi ina bin kan kowacce da abinda take so babu wadda nake tsoro na yi miki ta bafulatani aradu na d'aga 'kafa ne kawai don ganin yarana suna girma nan da shekaru takwas twins dina sun zama cikakkun 'yan mata 'yan 16years lokacin ko ina raye ko ba na raye Allah ne ka'dai masani." Ya sassauta maganar cikin alhini tare da 'kura mini ido. "Hum kawai na ce kafin ajiyar zuciya ta biyo baya na furta." Allah Ya kyauta dai Ina ganin dai ko tsufa muka yi gaskiya da wahala matarka ta canza domin ko kai kasan yadda nake hakuri bisa dabi'unta yanzu don girman Allah menene don ta kira ni ta ce tana son zogale kai ba ka yi tunanin cewa akwai wani abu a zuciyarta ba har yanzu." Ya gyad'a kansa yana fad'in." Yadda ba zata canza ba haka zalika kema ba za ki janza ba giwa. Na san halin kowacce a cikinku. tunda Ubangiji na ya jarrabeni daku a matsayin abokanan rayuwa dole na yi hakuri mussaman kuma da kuke ha'kuri da ni." "To yanzu dai idan na fahimta ka goyu da bayan abinda ta yi kenan tunda na ga kamar kana kare ta." "Ban goyu da bayanta ba Amina na nuna mata cewa tana da ikon shiga kicin dinki ko kuma ta tambayeki ba ni son kumbiya-kumbiya fa wasu lukutan daga cikin dabi'unki na burge ni domin ba ki da rufi kuma ba ki da munafurci na gane shine dalilin da ya sanya idan an yi miki hakan yake yi miki zafi." Na janye idona daga kansa ba tare da na ce komai ba. Ya saki ajiyar zuciya yana fad'in." Kafin na shigo Sukairaju ya yi mini bayani har results din duka ya nuna mini. Na yi murna na kuma yi addu'a kwarai abinda za a yi yanzu da kaina zan tashi zuwa Kano wajan Baba domin nemo auran hakan ya yi ko?" Na d'an saki fuskata ganin yadda ya karrama ubana har yana kiransa da Baba na ce hakan ya yi sosai Allah Ya tabbatar da alheri." Ya amsa da Amin yana fad'in." Idan kuna da idon sanin can garin nasu Sukairaju hakkinku ne domin fad'ad'a bincike a kansa da zuriarsu domin sake gazgata abinda muke hasashe da wanda na sani a kansa." "Gaskiya ba mu da kowa a garin wallahi, amma komai na Allah ne kuma tunda ka ba da tabbacin akansa da zuriarsu ai ba sai an sake wani binciken ba alheri dai muke ta addu'a akan Allah Ya wanzar musu damu gabad'aya.'' Ya ce." To hakan ya yi in sha Allahu rabbi cikin satin nan zan shirya zuwa Kano kuma babu buk'atar d'aukar dogon lokaci tunda dukkaninsu babu yaro a ciki." *** To idan Ubangiji na ikonsa babu wani mahaluki da duk iko da shahararsa a duniya da ya isa ya dakatar buwayar Allah domin kuwa rahamominsa suna da yawa. Ni dai ban taba tunanin wai akwai dangantaka ta aure tsakanin Hadiza da Sukairaju ba sai yanzu da Allah ya bankad'a abinda yake rubuce a kudirarsa. Kamar yadda nake wannan tunani da mamakin itama nasan haka take cikin wannan tunanin na kasantuwar auransu da Ubangiji Allah yake shirin tabbatarwa. Bayan zuwansa wajan Babanmu an samu nutsuwa sosai da fahimtar juna tare da amincewa daga kowane bangare domin kuwa ba su riga ma sun tsayar da maganar d'aurin auran ba sai da kawunan Sukairajun suka zo su biyu daga Zamfara aka yi zaman dasu tare da bada sheda da tabbacin cewa sun kar'ba bisa amana. A take a lokacin ya biya sadakin Hadiza bisa jagorancin kar'bar auran da ya biyo ta hannunsa. Hadiza ta yi goshi dubu dari biyar sadaki suka tsayar da ranar d'aurin aure ranar takutaha ranar da aka haifi manzon Allah s.a.w domin samun falala da dacewa. A ranan da daddare Ummansu ta kira ni a waya godiya kamar za ta yi kuka har sai da na ji wani iri a raina na dinga tausarta domin dai kukan da ta dinga dannewa sai da ta yi shi a cikin waya da kyar muka to sallama. Na kira anti Yagana a gaban Hadizan na sanar mata da yadda aka yi itama murna kamar ta zuba ruwa a k'asa tasha. Hadiza na gefe sai murmushi take yi domin tunda na gaya mata mun yi waya da maigidan ga yadda ake ciki ta rasa yadda za ta yi da ranta saboda farinciki. Kwanansa hud'u a kano ya dawo da daddare tare suka je da angon dama. Na tarbe shi sosai tare da yi masa bangajiya da godiya a daran kuwa ya samu tar'ba mai kyau mai tafe da sabon salo wanda bai san shi ba. Muka shirya tafiya kano kafin zuwan ranar ni da ita da yaran duka tunda an yi musu hutun boko da islamiyya mun shirya walima domin nuna farincikinmu ga Allah anti Yagana ma tana can tana shiri domin ta ce kaf yaranta da su zata zo. Saura kwana biyu mu tafi Hamusu ya kira ni yana gaya mini Sukairaju ya sanya shi had'a lefe akwati shida tambayata yake yi aure zai yi?" Hadizan tana zaune a gefena a lokacin da muke yin wayar na gaya masa aure zai yi kuma Hadizar gidanmu ya kuwa shiga farinciki sosai yana ta fad'in ta samu lefe domin milayan shida ya tura ya ce a had'a lefe na kece raini kuma a shagonmu." Lamarin ya yi mini dadi sosai na juya ina kallonta tana murmushi bayan mun yi sallama da shi na dube ta kafin ma na yi magana ta furta." Kudin ya ce zai ba ni sai kawai na ce ya yi magana da Hamusu ya kuma tura masa shi zai had'a komai." Da murmushi a tare da ni na furta." Na taya ki murna Hadizan gidanmu ta yi goshi kin zama bazawara mai kafasiti yanzu abinda ya rage muna dira kano a yi gyaran jiki sannan na kai ki gidan GARKUWAR MATA ta had'a mini ke da kyau! Ta kuwa fashe da dariya sai ka ce wata shashasha. Na shiga taya ta sai muka zama kamar sakarkaru rayuwa kenan bayan wucewar kalubale mabambamta da 'kin jinin juna tare da 'kyama ashe akwai ranar da Hadiza za ta k'aunaci cigabana duk son kud'inta sai ta ce a a gwara a yi sayayya a wurina saboda na cigaba. Lallai bahaushe ya yi gaskiya da yake fadin ranar naka sai naka.............✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *172* Duk abinda ya kamaci Hadiza na gyaran jiki ni na d'auki nauyi don har tana cewa za ta gayawa angon ya bata kudin gyaran jikin na ce a a kada lalacewar ta yi yawa yadda ya fitar da kudi masu kauri domin yi mata lefe irin na budurwa mai jini a jika bai kamata a ce ya bada wasu kudin ba. Sosai na yaba masa dangane da abinda ya yi mata duk a kokarinsa na ganin ya dakusar mata da damuwa kuma da alama yadda Allah Ya jarrabeta da sonsa haka shima yake k'aunarta domin matar so ai ake yi wannan hidimar a matsayin dai Sukairaju tsayayyan namiji mai suffa da mazantaka ina da tabbacin ba zai rasa 'yan mata da suke kawo masa caffa ba. Amma shi so babu ruwansa Hadiza ya hango cikin dubbanin 'yan mata da zawarawan da suke a wannan duniya. Anti Yagana ta riga mu zuwa domin da muka isa kanon a gidana na sharad'a muka sauka sannan gari yana wayewa muka yi gidan GARKUWAR MATA yini muka yi a tare da ita ta sabunta ni ta kuma sabunta Hadiza da ciccibi tare da dahuwar 'yan shilla aure biyu da duk wani abinda ya kamata. Kuma Koda muka gama da ita gidana muka sake komawa sai da gari ya waye bayan mun kintsa muka nufi can gidan na mu gabad'aya ni da ita da Baba Tabawa domin tare muka zo da ita saboda yaran Mairo da Taburni suna gida Abuja muka bar su. Gidan an yi masa sabon fenti ciki da waje har da ties a tsakargidan da d'akunansu wannan aikin Usaini ne ya gyara gidan sosai bayan wanda na yi musu ya yi musu sabbin d'inkuna Babanmu tsaf da shi cikin manyan kaya ya sake murmurewa. Sosai hankalina ya kwanta ganin yadda aka samu daidaito tsakanin matan gidan duka sun daina abinda suke yi Ummansu Saminu ta fito ana ta hidima da ita yayin da 'yan uwan Ummansu Hadiza suka cika gidan zuwa na ya sake bud'e babin gaisuwa har da rige-rige a tsakaninsu lamarin nan dai ya tabbata da ake cewa kudi suna sayan girma kuma suna kankaro mutunci. Ma'kotan gidanmu da ada suke yin surutu a kaina a duk lokacin da Ummansu Hadiza ta yi musu gulmata sai na zama abar fadanci da gurfana tamkar wata basarakiya. Ranar da aka d'aura auran da daddare ya kira ni yana gaya mini bai tafi ba sai gobe don haka Ayuba zai zo ya d'auke ni da yaran mu kwana can gidana na sharad'a. Na ce masa ya bari gari ya waye domin duk mun gaji har yaran su Hassan ma sun yi bacci tun d'azu. Ya ce a a mu Ayuba zai zo. Haka na kintsa ina gayawa anti Yagana yadda muka yi da shi ta ce mu tafi din kawai tunda hakan ya bukata. Wajan tara da arba'in Ayuba ya zo ya kwashe mu a mota amma banda amaryar tukkuna dole za ta yi sallama sosai da mahaifiyarta. Kwanciyar aure zai yi da ni a daran ashe shine dalilin da ya matsanta lallai sai mun dawo dalili matar da yake d'an ragewa da ita tana can saudia basu dawo ba shi ya gaya mini tare ya biya musu da mahaifiyarta da kuma Kawunta da ya zo ya yi musu sulhu wattanin baya. Daga lokacin na gane dalilin da ya sanya ta sassauto har take taka kyasa da k'arfi ganin ta fara samun kansa kyautar umara ya yi wa iyayenta biyu wannan kuma shine karo na biyu tsakaninta da Inna Uwanin a shekarun baya tun kafin ya kai k'arfin haka ya ba su kujerar ita da Hajja da Samira duk su hudun suka je lokacin suna soyayya kafin auransu. Ya yi yadda yake so ban hana shi ba dalili nasan ya jure tunda kusan kwanaki biyar kenan rabon da mu had'u da safe yake gaya mini gidan da ya mallakawa Sukairaju amma ba a cikin estate din da muke ba ya d'an yi gaba da mu. Ya nuna mini shi a waya maidaidaci ne plate wanda aka yi wa ginin zamani daidai gwargwado kuma ya ja kudi sabo ne kuma na yi masa murna sosai ya kuma tabbatar mini da cewa a shirye gidan yake shiga kawai za su yi. Yini guda muka yi da shi a d'aki yana ta maimaita abu daya don a k'alla sai da ya neme ni sau uku bayan wayewar gari da safe bayan mun karya da azuhur ya yi sallah sai kuma da yamma wanda shi ya yi bala'in gabalabaitar da ni na yi kwance a gado ina nishi wai lallai sai an samu ciki bayan shi kansa ya san yawan yin wannan abu ba shine yake bada ciki ba. K'addara ma a samu d'in amma ai ba mu da hurumin nunawa Allah abinda muke so idonsa gabad'aya ya rufe har na rasa inda tunaninsa yake har da cewa yana ganin a shekarar nan zai mutu shiyasa ya damu da ganin na sake haihuwa. Baba Tabawa ita ta dinga hidima da yaran gabad'aya domin ban sauko ba sai bayan biyar da rabi a gajiya tubis ga gajiyar bikin Hadiza ga wadda ya tara mini Ta yi abinci tsaf ta gama shirya ko'ina da yaran gabad'aya suna zaune a falo suna kallon cartoon Hasan na wasa a kusa da ita shi kuma Usaini na dafa kujera yana mi'kewa tsaye Sultan na ri'ke hannunsa. Na zauna cikinsu zamana kuwa ke da wuya suka rufe ni kowa da abinda yake fad'i mussaman Minal duk ta kanainaye ni ta ko'ina. Yana dawowa daga sallar magriba yake gaya mini rasuwar Malam D'aha a lokacin ne Malam Rabi'u abokinsa ya kira shi a waya ya sanar da shi amai da gudawa ya yi kwana daya don asibitin zana ya rasu. Na kadu sosai da rasuwar malamin jikina ya mutu na zauna ina Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un babu babu shakka maza sun tafi Allah Ya kar'bi ayyukan alherin da aka yi dominsa. Da sassafe mu ka dauki hanya ni da shi domin samun ta'aziyya a daran dama na kira Usaini na ce cikin hikima ya san yadda zai sanar da Hajara domin kuwa tsohon ciki ne da ita haihuwa ko yau ko gobe ya tabbatar mini da cewa da wuri za su tafi shi da ita inshallah. Aikuwa a can muka same su gidan Malam ya kacame unguwar ma gabad'aya motocin manyan mutane ta ko'ina da yake karkara ce akwai filaye sosai da aka samu damar ajiye motacin. Hajja ma can muka same ta lokacin an gama shirya gawar za a fito da ita domin a sallace ta. Sai bayan da aka d'auke shi zuwa gidan sa na gaskiya tukkuna na samu sararin bin dakunan matan gidan ina yi musu gaisuwa da yaransa mata aurarru Hajara na cikinsu sun yi kuka har sun gaji na yi musu gaisuwa sosai kafin na koma na zauna wurin da Hajja take a killace muka sake gaisuwa tare da yi wa juna ta'aziyya. Wajan biyu na rana Babanmu anti Yagana Hadiza da su Fati da Ummansu Saminu suka zo Ummansu Hadiza kawai a ka bari a gidan Saminu da Ashiru duka tare suke Hajara da kanta ta dinga bi da su d'akuna suna yin ta'aziyya sannan mazan suka fita waje su kuma su anti Yagana muka zauna a tare a wuri d'aya. Hajja can muka barta da za mu tafi ta ce ba zata iya wannan kai kawon ba sai anyi addu'ar uku tukkuna. Amma ni da shi haka muka dinga wannan kai kawon muje mu dawo har sai da aka yi addu'ar uku tukkuna. Ranar sadakar bakwai kuma shi kadai ya tafi bai ce na shirya ba sai ya dawo tukkuna yake gaya mini tare suka je da Hajja. Kwanaki goma da rasuwar Malam D'aha muka shirya komawa abuja lokacin Hauwa ta kwana kusan shida da dawowa kira shi a waya babu adadi ya kuma gaya mata babban rashin da aka yi ba wai jin dad'i ne ya zaunar da shi ba don a ganinta tunda muna tare wata'kila ni na hana shi dawowa bayan kwanakin da ta yi a saudia ya kamata a ce ya yi d'okinta. Ranar da muka koma kuwa a gidanta ya kwana domin hura masa wuta ta yi babu kintsi ya tafi ba cikin dad'in rai ba. Hadiza a can muka bar ta. Sai bayan sati daya tukkuna angon ya je ya daukota kai tsaye kuma gidanta ta sauka sai da ta kwana biyu da tarewa tukkuna na je na ga gidan alhamdulillahi Hadiza ta 'yantu ta yi gida gayun nan da ake ta nema yanzu ya samu an ci ado da kwalliya irin na amare abin dai gwanin burgewa da sha'awa nan take gaya mini Ummansu ta ce bayan ta dan yi wattani sai su shirya zuwa ganin d'aki dangin babamu da danginta na ce hakan ya yi Allah Ya sanya alheri. Kwanaki talatin da uku da rasuwar Malam D'aha Hajara ta haihu mace tun daga haihuwar aka ce mini an yi mini takwara dole haka na shirya tafiya da gudumawar kayan baby kwanaki uku kacal na yi a daddafe domin da 'kyar ma ya bari na dawo gida tunda ba taron suna aka yi ba saboda rasuwar mahaifinta. Amma alhamdulillahi ta haihu lafiya lau ita da baby suna cikin koshin lafiya yarinya kamar Usaini ya yi kaki ya tofa saboda tsananin kammani. Na kudi ne littafin kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. **** Bayan wata hud'u zaman namu ni da Hauwa yana ta tafiya a waskace babu tsari sai dai zangon 'kasa da kuma bita da 'kulli tunda nake kafata bata ta'ba taka gidan Nusaiba ba wallahi don wasu lukutan har kunyarta nake ji yarinyar har ta gaji da tambayata yaushe zan zo nakan ce mata ina tafe in sha Allahu amma Hauwa ta riga ni saboda gulma tana cin ko'kon ranta kawai yarinyar ta kira ni a waya tana gaya mini wai Hauwa ta je mata ta yini har ta kai mata mayafai biyu da hijabai irin wanda ta zo da su daga makka har tana gaya mata cewa Hadiza ba tsaran auran Sukairaju ba ce dalili karuwa ce kuma 'yar kungiyar shan jini an cutar da shi kuma ta girme shi nesa ba kusa ba wataran za a wayi gari babu shi ta nemi wani sassa na jikinsa domin alamu sun nuna zaman da ta yi gidan gyaran hali bai koya mata darasi ba don haka dole za ta matsantawa maigidan ya dawo mata da yaranta saboda tana jin tsoro kada a wayi gari babu daya daga ciki mun had'a baki mun bawa dodon tsafi tunda ni kishiyartace kuma ba ni k'aunarta zan iya yin komai domin ganin bayanta da yaranta saboda ni da 'ya'yana mu gaje dukiya. Wallahi bakina mutuwa ya yi na rasa abinda zan cewa yarinyar kaina ya yi bala'in d'aurewa wata'kila fahimtar hakan ta yi daga wajena yasa ta shiga ba ni ha'kuri tana fad'in ba ta san hankalina zai tashi ba kuma ta yi rantsuwa da Allah ba ta ta'ba gazgata maganarta ba domin ni din ma na fiye mata ita sau dubu. Har muka yi sallama ban iya ce mata komai ba saboda mamaki lallai wannan al'amari ya daga mini hankalina ba kad'an ba. Duk wasu kaidi da sharri Hauwa ta yi mini na jure saboda dalilai masu yawan gaske amma ina ganin wannan kam ba zan iya ha'kura ba dalilin da ya sanya kenan yana shigowa ban ma bari ya huta ba saboda da abin na yini shima ganina a hargitse cikin rashin nutsuwa ya shiga hankalinsa na shiga gaya masa abinda kunne na ya ji wanda nake da tabbacin cewa yarinyar nan Nusaiba ba za ta yi mini karya ba. Ya shiga mamaki kwarai shima jikinsa ya yi sanyi mussaman yadda ya ga hankalina ya tashi ina kuma sake jaddada masa cewa shari'a ce zata raba tsakanina da ita idan kuma bai yadda da hakan ba ya zama dole ya za'bi zama da ni ko'ita domin ba za a cigaba da tafiya a haka da ni ba ya zame mini dole na nemi mafita. Kwanan rarrashi ya yi duk da girkinta ne sai ya kashe wayarsa ma gabad'aya domin kada ta kira shi ya rufe dakin da key ya boye shi saboda kada na fita rarrashina ya dinga yi sosai lamarin na sa'barsa shi kansa yanzu yadda yake nunawa lamarin Hauwa ya kai shi ma'kura akwai dalilan da ya sanya yake daga mata kafa wanda ni ma su nake duba mussaman yaranta Khalil dai biyayyar da yake yi mini kwatankwancinta ba ta samu ba ga Minal da take jarabar kulafucina uwa uba kuma ina duba Hajja domin duk lalacewarta tata ce idan na yi tutsu abubuwa da yawa marasa dad'i za su faru wanda za su sanya kunci da zubar hawaye a idanuwan yaran. Wallahi kwana cur ba mu rintsa ba har sai da ya karya mini lagona da rarrashi da kalamai tare kuma da al'kawaruruka da tabbaci akan idan ta sake aikata abu makamamcin wannan da kansa zai d'auki mataki. Sai da ya yi mata ya ji na sati d'aya bai je gidanta ba ta kuwa zama kamar mahaukaciya ta zo gidana ya fi sau hud'u ba ni ma sanin zuwanta sai dai idan na fito daga d'aki yara ko masu aiki su ce mini ta zo. Shi kuma ba ta ma riskarsa domin yakan fita da wuri kuma baya dawowa sai dare. A ranar da ya cika sati guda ya koma gidan wanda na tabbatar da cewa wannan ba shine iyakacin horon ba akwai wasu mabambamta yadda ya yi wannan fushin kuma sai ta gayawa aya za'kinta. Hakan da ya yi sai ya kara sassauta mini rai amma dai duk haka cikin k'unci da takaicin abin nake don sai da na sanya aka yi mini saukar al'kur'ani can makarantar allonmu dake cikin unguwar mu duka cikinta muka yi sauka al'kur'ani mai girma a duk lokacin da masifa ta tunkaro ni nakan sanya an yi mini sauka da addu'a sannan a yi sadaka Hamusu ne ya jagoranci al'amarin sati guda aka d'auka ana sauke izifi sittin a lokacin na fara jin sanyi a zuciyata. Maigidan ya kuma zo mini da albishirin kammaluwar ginin shagunana har ya nuna mini bidiyon wurin a waya waje ne mai darajar gaske a cikin kasuwar ta wuse market gini ingantacce na zamani mai tafe da 'kawa kamar yadda ya fadi madaidaiciyar plaza ce mai d'auke da shaguna sha biyu masu matsakacin girma kasa da sama ko'ina gwananin sha'awa ga Ac ta kowace kusurwa da manyan panal na solar haske ko ta ina yanzu shawarar yadda za a yi tana hannuna sai abinda na ce haka yake gaya mini yana lankwasar da kai da murya duk a k'okarinsa na ganin ya kashe guguwar wuta mai tartsatsi da take shirin kamawa a gidansa. Ni kuwa na ce da shi yadda ya bada umarni haka za a yi amma dai ina so na yi amfani da 'bari d'aya sama da k'asa d'aya side d'in a bada shi haya ya ce hakan ya yi. Bayan kwana biyu ya shigo har d'akina ya same ni ban jima da fitowa daga wanka ba ya dinga bina da kallo har sai da na tsargu na dube shi ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Ciki ki ka samu ne?" Na ji wani bala'in fad'uwar gaba domin kuwa akan ga'ba nake ina sanya ran ganin al'adata cikin kwanaki biyun nan. Sai na girgiza kaina ina fad'in." A a mai ka gani?" Ya d'ora hannunsa saman kirjina da suke da towonsu har yanzu ba su langa'be ba ya ce na ga sun girma sosai kin d'an yi kumburi Giwa ina fahimta a duk lokacin da ki d'auki ciki kina canzawa fa har yatsunki. A sanyaye na ce." To wallahi ba zan tabbatar ba amma don Allah ka daina kira mini shi yanzu ka taimaka mini na rantse da Allah na wuce haihuwa Allah Ya raya mana wanda muka samu." Ya zuba mini ido fuskarsa ta canza da wani yanayi ya furta." Ni ba za ki taimaka mini ba kenan. Na jima ina gaya miki ina son samun uwata Halimatussadiya sai ki ce na tausaya mini indai ni ban wuce haihuwa ba Hajiya kema ba ki wuce ta ba, mu riko Allah Ya ba mu mai albarka na ce ko daga haka sai na godewa Allah." A sanyaye na ce." Ai shikkenan." Ya rike hannuna yana dan murzawa ya furta." Ki ce Amin kin ji ko Allah Ya sa shi din ne, domin a jikina nake ji hakan!" Na dube shi ganin yadda ya zura mini idonsa ya sanya na ce ." Amin Allah Ya sa shine." Ya kuwa sauke ajiyar zuciya yana fad'in." Na gode miki sosai Allah Ya yi albarka." Na amsa da Amin a takaice kafin ya sake kallona a karon da babu adadi. "A game da abinda muka sanya a gaba ni dake a yanzu nake so na ji a ina aka kwana ina so mu wuce wannan wurin ne zan je Legos ina da uzuri a can din amma ni kad'ai nake son tafiya." Na ce." Business din da nake yi cikin garin kano na zannuwa takalma da huluna nake so na kawo shi nan din kamar yadda na gaya maka da farko amma ina so shaguna biyu na zuba supplements ina so na jarraba ana samun alheri." Ya d'an yi jim kafin ya ce."Supplements kayan gyaran jiki na mata da kwalliya ko?" Na gyad'a kaina idona a kansa ya ce ." Hakan ya yi Allah Ya ba ki sa'a, amma ba ki sha'awar sayar da kayan maza ina nufin irin wanda muke sanyawa tunda harkar huluna ta kar'be ki sai ki sa hannu anan din domin mu ga abinda Allah zai yi." Na ce." Hakan kuwa ya yi sosai na gode da shawara Allah Ya saka da alheri zan yi ko nan gaba don ba ni tsammanin abinda yake hannuna a yanzu zai ishe ni yin duk abinda nake buk'ata. Ya ce." Ni zan yi miki order domin shirya shagunan tunda na bada shawarar yin hakan amma har yanzu ba ki fitar da sunan shops din na'ki ba. Ita kanta plazar akwai buk'atar a samar mata da suna na mussaman ko?" Nan fa d'aya wallahi na manta shaf kuma dai da kunya na ce masa sauran shagunana suna d'auke da AminatuAminu collocation ne. Tun lokacin da na fara bud'e shagon d'inki na sanya masa A-A fashion designer hakan na nufin AminatuAminu sai Kuma da na bud'e shaguna tukkuna na bud'a sunan kowa ya gane abinda nake nufi kuma har zuwa yanzu wannan tambarin ne a jikin duka shops dina sai dai a sabunta idan ana so a sake 'kawata lamarin. Ina so a ko'ina ya cigaba da tafiya a haka domin cirewa customer's d'inmu shakku da kokwanto....... Masu karatu ku ba mu sunan da ya kamata a kira shop's din Amina na Abuja don Allah kada a yi rashin adalci.......πŸ˜ƒ Plazar dai na yi mata suna da (GIWA PLAZA) shin ta cigaba da amfani da AminatuAminu tunda da shi a kasanta.....✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP #700 VIA 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *173* Har yanzu idanuwansa na tsaye a kaina jikina ya k'ara yin sanyi kasala ta mamayeni bakina ya mini nauyin da na kasa ce masa ga yadda nake so komai ya tafi daidai da abinda na gina shekara da shekaru ai da kunya da nauyi duk da yanzu babu shi a raye a duniya amma mafiakasari mazan mu na yanzu ba sa rasa abin kishi koda ga wanda ya mutu ne mussaman da na riga na fi kowa sanin halinsa mutum ne shi mai zazzafan kishin tsiya. Kawai sai na tsinkayi maganarsa yana fad'in." Za mu cigaba da kiran shops din da AminatuAminu ne ranki ya dad'e?" Ya fad'a yana dago fuskata da tafin hannunsa. Na dube shi cikin wani irin yanayi ya aka yi ya san abinda yake d'auke kenan a jikin banner da logon shugunana tunda ban ta'ba daukarsa na kai shi ba kuma ban ta'ba nuna masa bidiyon abinda ya danganci harkokina ba. Ya d'an yi murmushi yana fad'in." An gaya miki shashashan namiji kike aure Amina. Bari ki ji abinda ba ki sani ba tunda na aure ki idona akan harkokinki yake da cigaba da fad'uwa duk ina samun labari mussaman na samu lokaci Hamusu ya jagorance ni ya nuna mini shagunanki a cikin kasuwar kwari yana kuma gaya mini irin yadda nauyi da hidima suka yi yawa akan ki akwai abin mamaki ne a anan don miji ya bibiyi sha'anin matarsa. Tunda kina shakkar ki nuna mini ciki da wajenki ni na bibiya domin samun nutsuwa kuma na yi miki murna da farinciki kin zama mace mai kamar maza a cikin maza kashi dari kin take hamsin sauran sakarkarun su d'auki hamsin domin jajurcewarki akan neman halak ba kowane namiji ne zai iya abinda ki ke yi ba a yanzu kuma ina yi miki fatan alheri tare da addu'ar Allah Ya sa ki fi haka." Tun da ya fara maganar kaina yake a sunkuye d'agowar da zan yi sai ta yi daidai da zubowar hawayen da ya taru a cikin kwarmin idona suka fara sauka saman kumatuna bakina ya dinga rawa magana nake so na yi amma gabad'aya ya gama d'aure ni da jijiyar jikina na rasa shin godiya zan yi masa ko kuma rungume shi zan yi." Ya d'an 'bata fuska yana fad'in." Kina ba ni mamaki wasu lukutan Amina shin ni din kuwa ina da abinda zan biya ki bisa abubuwan da na samu ta dalilinki. Kada ki manta da cewa babu wani arziki madaukaki anan duniya mai sanya farinciki da annashuwa face na haihuwa tabbas Allah ne yake bada ita bayan na yi godiya a wajensa wajibi ne kema na yi miki bisa samun sanyi idaniya da kuka ba ni. Babu buk'atar godiyarki ko zubar hawaye ina so ni ma na shiga cikin ladan da kike samu don haka don na sanya miki hannu cikin lamarinki kaina na yi wa taimako babu wanda ya san gawar fari sai Allah ko bayan babu raina ina da tabbacin yarana kaf da naki da ba naki ba ba za su wulakanta ba.'' Hannuna na sanya na sar'kafo wuyansa ina kuka sosai wanda yake fitowa daga can karkashin zuciyata. Ya d'ora hannuwansa biyu a gadon bayana yana d'an bubbugawa kafin ya dago fuskata muka dubi juna da wani irin murmushi a fuskarsa ya furta." Kukan sam bai yi miki kyau ba giwa na hango muninki." Ya sanya yatsu yana ta'be mini hanci da kumatu haka dai na dinga daurewa ina cire hannunsa yana mayarwa dole dai sai da ya sanya ni dariya ya cika mini kumatu yana fad'in ." To ko kefa kuka ko mutuwa na yi kada ki yi mini kuka domin abin sai ya zai zame mini biyu na tafi na barki wata'kila shekaru kad'an ki manta da ni wasu mazan su fara zawarcinki." Na ce." Don Allah wace irin magana ce wannan ka daina ba ni son jinta." Ya gyad'a kansa yana fad'in." Gaskiya ne ai Amina idan na rasu mazan zamanin nan ba za su iya d'auke ido a kan ki ba." "Idan ka riga ni rasuwa babu yadda zan yi ba kuma zan kalubalanci Ubangiji ba domin ni ma ita nake jira amma ka sani wallahi ko shugaban kasa ne zai fito neman aurena ba zan aure shi ba na gama aure har abada zan zo na riskeka a aljanna mu cigaba da rayuwa." Yana dariya sosai ya ce."Shugaban kasa fa Amina?' Na tare shi da saurin gaske ina cewa." Ko da sarki ne wallahi ai na gama yin rashin mijin da babu wanda ya isa ya maye mini gurbinsa to me nake nema a duniya komai ka yi mini fa." Fuskarsa ta yawalta da wani 'kasaitancen murmushi yana ta 'kan'kance idonsa a tsakiyar nawa idon dad'in kalamaina sun sanya shi cikin wani irin shau'ki ya rasa ma abinda zai ce mini duk bakinsa da iya maganarsa na kashe shi a zaune sai murmushi. Na cigaba da cewa." Kamar yadda ka kawo shawara hakan za a yi Plaza ta cigaba da amsa sunanta na (GIWA PLAZA) Shops din kuma AminatuAminu na amince da hakan na kuma gode bisa wannan kara da ka yi mini Ubangiji Allah Ya bar mu tare." Ya rike hannuna na dama ya had'e yatsun waje d'aya ya d'amke sosai." Za a yi hakan in sha Allahu amma sauran shagunan ai ba ki da hurumi tunda hayarsu za ki bayar dole masu kar'ba sune suke da zabin abinda za su sayar a ciki kin gane abinda nake nufi ko?" Na gyad'a kaina a nutse na ce.'' Na gane ni dai wurina sunansa GIWA PLAZA saboda suna ne na mussaman da babylove ya sanya mini kuma ina alfahari da sunan ya fito daga bakinsa." Ya sa dariya har sai da duka hakoransa suka bayyana." Me yasa ba ki ta'ba nuna mini sunan na yi miki dadi ba uhumm?" Ina murmushi na ce." Wallahi da gaske sunan dadi yake yi mini har wani tunkaho nake yi fa?" littafin nan na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba. Aikuwa dadi ya ishe shi ya kwanta saman gado yana ta dariya sai kace wani shashasha ni ma ina ta ya shi yau na gama kashe masa karsashin jiki da 'yan kalaman da ba su wani sun kai sun kawo ba abin har ya ba ni tausayi wato ita soyayya jahilar mahaukaciya ce babu talaka babu mai kudi haka zalika babu sarakai babu attajirai duk lokacin da ta so illatarwarta sauka take yi a duk inda ta so ta yi sharafinta amma idan ba ita ba din ba ai ban ga wani dalilin da zai sanya mutumin nan yin wannan dariyar ba wallahi. **** Lamarin da ya kara dakusar mini da jiki akan sha'aninsa yadda da kansa yake yi mini tallah status d'insa da kuma babban pege dinsa na facebook da Instagram bayan an gama shirya duka shagunan shidan kowanne d'ankare da kayan masu inganci da quality shaguna biyu da ya yi alkawari sai da ya shirye mini su da lates Textiles yaduka na manya da shaddodi d'ankare kowace kanta abin gwanin burgewa shagon cosmetics d'aya na supplements d'aya d'ayan kuma na zannuwa leces atamfofi kowane nau'in da b'angaran abaya (dogayen riguna) d'ayan kuma ya zama na takalman mata da maza da kuma b'angaran huluna iri daban daban. Mussaman ya sanya masu shirya advert da muryar da lallai dole ta isar da sa'ko aka yi bidiyon na mussaman tun daga kan shagunana na kwari market har zuwa wad'annan sabbin da aka bud'e. To sanya hotonan wajan a peges din sa na sadarwa ya sanya jama'arsa yin shearing kafin ki ce me messages na 'yan uwa sun fara cika inbox dina mussaman daga maiduguri mutum kusan shida na buk'atar samun gurbi daga cikin dole ne a cikinsu zan duba wad'anda suka dace daga cikinsu. Rasa abinda zance masa na yi tunda ya ce ba shi buk'atar godiya sai dai daga zarar na kalleshi sai na ji tausayinsa ya tsirga mini har ina jin taruwar hawaye a idona da kansa yake ta yi mini tallah ya cire girman kai ya cire son a sani ya kuma cire k'yashi irin na wasu mazan ya kuma nuna shi din duk arzikinsa me nema ne ya kuma tabbatar mini da cewar abinda ya yi shine kasuwanci domin kuwa shi arziki ai ba a nemansa da sau'ki. Ban yi gangancin kwatanta abinda ya yi ba a ganina yadda jama'arsa ma suke sharing ya isa gefe guda kuma daga can kano Hamusu da Usaini suma sun dage sosai da tallah ta kowace kafar sadarwa abin ya yi ta ba ni mamaki. A daran na amsa wayar Baban Saude addu'a ce dai da fatan alheri anti Yagana Sahura Hadiza ma ta kira ni Ya Falmata kuwa kamar ma ta fi ni farinciki fadi take yi na jima da gaya miki cewa akwai haske cikin rayuwarki domin kina da nasibi gaba kad'an za ki zama abar kwantace. Washe gari da safe kafin ya fita yake gaya mini akwai wanda suka gama magana da shi gogaggene fannin kasuwanci kuma mutum ne mai kula da amana don haka ya saya mini sabbin layikan waya shi wanda ya kira da Lawan zai zama kamar manager a wajan domin sa ido da kuma kula da yaran da za a sanya a shagunan sannan akwai buk'atar samar da securities saboda dukiyar da aka zuba shaguna dai tuni an kar'be su domin a yinin ranar da bidiyon ya fita duk guda shidan kyasa da sama aka kama saboda sun yi sau'ki duk kuwa da cewar an kashe kudi an kuma yi komai cikin inganci ga soler ga Ac sannan ko'ina teis kuma akan miliyan shida duk d'aya ga wurin fuskar jama'a daf da titi jama'a na hada-hada a fannin babu cunkoso mai yawa. Wallahi cikin yammacin ranar naga shigowar kud'ina miliyan talatin da shida. Ya kira ni domin ya tabbatar da shigowarsu ya ce kudin shagunana ne yaa katse jin na fara yin godiya abinda baya buk'ata kenan. Sai da ya dawo yake gaya mini sun yi waya da Baban Saude har da Babanmu ma suna yi ta yi masa godiya na ce nima duk sun kira ni sun yi mini addu'a sosai. Anti Yagana kuma tun abin nan da ya faru a lokacin da ya yi mini kyautar kamfani suke jin kunyar juna ita dashi Ya Falmata ce dai ta kira shi a waya har ta had'a shi da Dada sukai ta yi masa godiya. Wannan shine abinda ya haddasa mummunan rikici tsakaninsa da Hauwa wanda ya kaita ga tsautsayin kunnawa gidanta wuta tunda tsabar bala'in da tashin hankali a ranar da taga abinda yake faruwa a social media da kuma status dinsa ta d'ora abinci jallop din taliya har sai ta babbake ta yi baki tana can d'aki a kwance ta manta tana ta kuka gidan ya fara canzawa da k'aurin hayaki ga mai aikinta Ladidi bata nan ta je ganin gida. Sulaimanu mai yi mata hidima gidan shi ya ankara domin masu gadi na can nesa abin bai je musu ba ya shiga gidan a gigice hayaki da kauri daga kicin tukunya ta yi jajawur gas na neman yin bindiga da ita da shi Allah ne yasa suna da nisan kwana ya yi namijin kokari sosai domin kuwa shine ya tunkari gas din ya kashe ya toshe hancinsa a gaggauce ya fita sai a lokacin ne ta fito a ki'dime ita da shi suka yi waje Ubangiji Allah Ya ta'kaita k'auri da haya'kin suka gama fita tukkuna ta koma cikin falon. To tundaga ranar suke rikici shi fad'ansa yana so ya ji dalilin da ya sanya take nema ta had'a masa gobara a gida domin dai duk b'oyenta sai da ya gane lallai akwai abinda ya faru a gidan kuma Sulaimanun bai boye masa komai ba. Ta dinga kuka tana fad'in sai ya saketa ita gaji ya ce shi kuma haka kawai ba zai yi saki ba sai da hujja. Rikicin dai har sai da ya kai su gaban Hajja anan ne ta fad'i abinda yake sasakarta Ya gina mini plaza ya ya zuba mini kaya sannan ya kuma bude mini shaguna a kasuwar kwari guda uku ita kuma ya had'a ta da wani lalataccen kamfaninsa da ya tabbatar da cewa shi kansa ya tashi daga aiki don haka wallahi idan har adalci za a yi itama a yi mata plaza sannan a bude mata shaguna. To sai a lokacin ne ya san dalilin tashin hankalinta. Ya ce yadda ya mallaka mata kamafani ba tare da ya cire na'urorin da ake aiki da su ba haka zalika don ya gina mini plaza ya sanya mini kaya a ciki ba lefi ba. Duk abinda yake yi yana sane yana kuma yin aiki da ilimi da koyarwar Annabi domin yin adalci cikin ni da ita babu wadda ta sanya shi ba mu wani abu daga cikin dukiyarsa shi ya yi ra'ayi a lokacin ya jaddadawa Hajjan cewa plaza kad'an ya yi mini a madadin kamfanin da ya bata sauran shagunan da take tunanin shi ya bud'e mini ba shi da hannu tun kafin ya aure ni nake neman kudi ita kanta Hajjan ta san da haka tunda da farko ganin yadda Hauwa ta yi bala'in shiga damuwa ta ce a samu sulhu kawai ya kar'bi kamfanin tunda ita din macace zai wahala ta iya kawo masa cigaba sai ya yi mata yadda take so. Amma jin haka sai jikinta ya kara yin sanyi tuntuni ta fahimceta zafin kishinta da ganin Ido shine zai kai ta ya baro. Kwanansa biyu a kano suna buga artabu Hajja ta ce a sayar da kamfanin a bata kudin shi kuma ya ce bai gina shi don ya sayar ba. Adalci d'aya da zai yi mata zai cigaba da kula mata da shi domin ganin ya sake yin shura yanzu ma ba wai aiki ne ba ya yi ba, kawai dai yawaitar massarafuwar kamfanin sabulun da suka yi yawa ya sanya kasuwarsa ta kwanta dama amma a rana akan iya fitar da kwali dubu ko fiye da haka ina lefi. Hajja ta ji dad'in hakan domin sai take ganin ba wani abun bane a ganinta ma wanda aka bawa kamfani guda ai ya fi morewa ta sallame shi ta ce ita Hauwan ta kwana biyu a wurinta domin a ganinta cikin kwanakin da za ta yi zata iya tausarta ta rarrrasheta ta ha'kura amma ina Hauwa ta wuce da tunaninta washe garin ranar da ya tashi Hajja na dyakinta da safe misalin goma da kwata tana sallar walha Hauwa ta bar gidan cikin matsanaciyar damuwa da tashin hankali bauci ta nufa zuciyarta cike da bakinciki da kuma neman hanyar da zata warware damuwarta.......✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *174* To duk yadda ya kai da ko'karin ganin ya b'oye abinda yake damunsa sai da na hankalta cewa lallai a cikin matsanaciyar damuwa yake wadda ma take ko'karin ganin ta ta'ba wasu muhimmanan al'amuransa mussaman da ya d'auki dabi'ar shiru da nazari. Hankalina sai ya rabu biyu daya a kansa daya kuma akan harkokina da suka fara kafuwa wanda shi din ne ya zama sila kuma ma'kasudi domin dai ya taka muhimmiyar rawa wadda ta zama tushe kuma matakin nasara shaguna har mun tsayar da ranar bud'e su wadda muke sanya ran cewa a cikinta za mu yi promo ga customers dinmu na farko mun tallata daga can kano zuwa abujan da sauran jahohi bisa jagorancin mutumin da ya had'a ni dashi Lawan wanda na tabbatar da cewar shi din za'kwakuri ne tuntuni sun yi masayar lambobin waya da su Hamusu. Kuma mun gama magana da Baban Saude kan cewa zai ba ni yaransa biyu duk da acan suna sana'ar huluna da sayar da yaduka mabambamta mussaman na hijabai da ro'ko da magiya ya amince mini domin duk wad'anda suka nemi samun gurbin zama duk da cikin family dinmu suke Ya Falmata ta ce a a daya muka d'auka daga cikinsu Halifa karamin k'aninsu Banandi sai Abahuraira da kaninsa Saifullahi yaran Baban Saude daga can kano kuma gidanmu na ce idan Hamusu da Usaini za su taho sai Ashiru ya biyo su shima tunda shi Saminu suna tare da Yusi a shago daya wanda koyaushe yake sake bunkasa dalilin kokari da cigaban da suke kawo masa a zamanance. Wannan yanayin nasa gabad'aya sai ya dakusar mini da karsashin jikina hidimar dai kawai nake yi amma gabad'aya bana yin ta cikin dadi dalili ko bai gaya mini cewar akwai matsala tsakaninsa da Hauwa ba dole na gane tunda ya fi sati daya yana kwana a gidana sau d'aya da na yi masa magana ya 'bata ransa yana ba ni amsa kamar ba ya so sai ban sake ce masa komai ba na zura masa ido amma dai yau na yi niyyar takureshi akan sanin abinda yake faruwa yanzu abinda na gama fahimta a game dashi Hauwa ce matsalarsa tunda zahiri da bad'ini Allah Ya riga ya gama yi masa komai Ilai kuwa ita din ce domin dana matsananta masa da tambaya abinda yake zuciyarsa ya furta mini Kai tsaye Amina zan saki Hauwa. Zahiri na ji fad'uwar gaba da tashin hankali lokacin da maganar ta fito daga bakinsa ban kuma yi mamaki ba domin tsananin tunani da nazarin da yake yi akan lamarin ne shin ya aikata ko kada ya aikata tsayin shekarun zamana da shi na fahimci mutum ne mai nisan tunani kuma bai fiye yanke hukunci cikin fushi ba yakan ta jujjuya lamari yana nazari a kansa kafin ya yi hukunci ga misali nan akan matarsa Hajiya Maryam da ta rasu kafin ya amince da abinda ake magana a kanta sai da aka kai ruwa rana har ya gani da idonsa ya kuma tabbatar. Jikina ya shika sosai na zuba masa idanuwana shima ya zuba mini nasa ido babu annuri ko kad'an a saman fuskarsa ya cigaba da cewa rabuwata da yarinyar nan shine kwanciyar hankalinmu gabad'aya domin kuwa Hauwa ba ta shirya zama ta gyara mini gidana ba har ta ba ni nutsuwa da kwanciyar hankali irin wadda nake samu a wurinki. Ni ba sakaran namiji ba ne don haka ban ga dalilin da zai sanya a ce wata mace na raba mini hankali ba. Abu biyu suke ri'ke da Hauwa a hannuna a yanzu kuma su nake dubawa shiyasa duk abubuwan da take yi nake kawar da kaina a kanta ba wai tsoron rabuwa nake da ita ba kamar yadda take nuna hakan. Ko yau na rabu da ita gobe ina iya auro wata a madadinta idan har ina da ra'ayin hakan don haka tunda kin nemi da lallai sai kin ji matsalata to wannan ce." A kasalance na ce." Ko zan iya sanin dalili, ai dai ka san haka kawai ba a sakin mace sai da dalili, gaskiya ka yi hakuri abin kunya ne a tsakaninku dukkaninku kun girma fa." Ya gyad'a kansa ." Dalili akan ki ne domin duk zargi da tashin hankalin da ta shiga ganin kasuwancinki tana ganin ni na kafa ki na ce mata a a ni ma cikin nema na gan ki muka yi aure kina neman ki, bata yarda ba ta kai kara wurin Hajja wai kamar ni Hauwa ke yawon kaini k'ara saboda ba ta da mutunci tana ganin na fifitaki ina kashe miki kudi ita na bata tsohon kamfani sai dai a canza mata da abinda na yi miki shin a cikinku ko akwai wadda ta sanya ni d'aukar dukiyata na baku, alheri ne kawaii na yi muku ganin tare duka aka nemi dukiyar daku tana ganin abinda na yi miki ya fi wanda na yi mata akan hakan kuwa lallai ranta zai b'aci don ban ga dalilin da zai sanya ta tsananta k'yashi a kan ki ba, kema Allah ne ya yi miki daidai gwargwado kuma kin nema ni hannu kawai nasa miki kuma sai daga karshe ko ba haka ba ne?" Na gyad'a kaina ina fad'in." Hakane amma akan hakan ka ke cewa za ka saketa ai ba hujja ba ce wannan kuma abinda ta nema ka fi karfinsa don ta tsananta kishi da k'yashi a kaina babu lefi ko ka manta kishi ne a tsakaninmu kowa fa da irin zuciyarsa, wallahi ban ji komai ba amma don girman Allah in dai zan baka shawara ka d'auka to ka yi mata yadda take so tunda kana da iko ka daidaita tsakaninmu itama ka bude mata plazar sai ka kar'bi kamfanin ka kawai tunda dama wahalarsa yawa gareta." Ya girgiza kansa." Idan na yi mata plaza sauran shops din na kwari market kuma wa zai yi mata? tana cewa ai duk ni na yi miki" Yar dariya na yi kad'an na ce sai ka yi mata menene a ciki ai Allah Ya hore maka?" Ya girgiza kansa a nutse ya furta." Babu wanda zai karya mini rantsuwa Giwa ai na ce ta bar shi a hannuna zan a cigaba da aiki da shi a madadinta kuma abinda take han'koro za ta samu rashin yarda ne kawai da ci da zucci. Ba zan yi wata plaza ba yanzu wannan shine karshen magana." "To kasan halinta da rashin yarda da kuma taurin kai kenan idan kai da kake matsayin jagora baka yi yun'kurin ganin ka nemo mafita ba lamarin zai lalace ai." "Ai na nemi mafita tuntuni aiwatarwa zan yi kawai ko kin ga na yi miki kama da namijin da mace za ta juya ne Amina. Wasu lukatan Kawai ina biye muku ne domin ba na son hayaniya wa za ta gayawa taurin kai ne ni da ita shege ka fasa." D'akin ya d'auki shiru bayan ajiye maganarsa na sauke numfashi Ina dubansa na ce." Yanzu kasan yadda za a yi tunda abin ya zo da haka me yasa ba za ka kara mata kudi akan kamfanin ba." Harara ya wurgo mini kafin ya ja tsaki yana fadin. "Ba zan k'ara mata ko kwabo ba wallahi." Rantsuwar da ya yi a karon farko sai jikina ya mutu ba wai bashi dashi ba ne bayarwa ne kawai ba zai yi ba Amma ni ina ganin idan har ya k'ara mata kudi akan kamfanin da take ganin darajarsa ba ta kai plazata ba zuciyarta zata yi sanyi ga shi kuma ya rantse da gaggawa. Na ce." To ni zan k'ara mata amma a madadinka." Ya dinga shillo mini harara kafin ya yun'kura ya tashi bai ce komai ba ya shige toilet yana tsaki. Ni kuma a ganina ai ba abin jin haushi ba ne don zan bata kud'i ba ni son ya saketa ko kad'an wallahi domin abin ba zai yi mata kyau ba daraja dai da alfarmar tana a hannunsa ta yi hakuri ta barwa Allah ikonsa kamar yadda ya fadi yanzu Ubangiji ne ya yi mini wallahi ban ta'ba tunanin zan kai matakin da nake a yanzu ba. Kwanaki biyu muna ta abu daya gabad'aya ma ya'ki ya saurare ni da shawarar da na kawo sai hanya hanya yake yi yana ta shirye-shiryen tafiya Legos abinsa ni kima ina ta damuwa ga ciwo ciwon da na fara cin karo da su na kasala da zazza'bi taruwar yawu a baki da yawan bacci ciki ne da ni na tabbatar domin ban ga al'adata ba rashin sukuni da abubuwan da suka kutso ya sanya bai lura da canje-canjen da na sake samu ba. Cikin wannan yanayin muka bude shagunanmu da bisimillah abin sai godiya da sake godiya wurin Ubangiji mun samu alheri kwarai da gaske domin yanayin yadda aka s'aukaka farashi a karon farko ya sake janyo mana suna a duniya da costumer's mabambamta. Daga cikin manema labarai ('yan jarida) har da ni Binta Umar Abbale na tafi da biro da takardata domin d'auko rahoto na samu abin rubutu a kai Na shiga cikin mutane ina ta ra'be-ra'be duk na ki'dime hankalina ya kasu kashi -kashi shin rahoton zan d'auko ko kuwa kallon zan yi kaya na alfarma kamar za su bud'e ido jama'a kuwa ga su nan hamsha'kai suna ta parking din motocinsu Allah sarki ashe ta hango ni a labe ina le'ken shagon supplements dinta da ya tumbatsa da ya kaya ni shine ya yi bala'in d'auke mini hankali na saki baki galala ina ta hango manyan supplements din da suke tumbatsar da mace da tayar mata da komad'ar jiki cikin zuciyata ina ta fad'in dama ina da kud'i zahiri da na sayi wanda zai dawo ni shamshakiyya kalar 'yan gayu irinta duk da yake supplements din kala kala ne amma dai ga dukkanin alamu duk abinda yake cikin wannan shamsh'akin shagon nata sahihi ne babu cutarwa. 08089965176 domin neman karin bayani Aikuwa ganina sai ta yafitoni da hannu da wannan fara'arta tata ta ce da ni na za'bi abinda nake so. Na dinga washe bakina don saura kad'an na daka tsallen murna na ajiye 'yar zabirata a can wani waje inda wani mutum yake zaune da Loptop a gabansa amma ban iya ajiye biro da doguwar pepper din da take hannuna ba. kai tsaye shagon na kutsa ina zagaye shi bakina ya ki rufuwa. Wani kwando nai zurfi na ciko da supplements ina ayyanawa a raina Allah Ya sa kada ta ce sun yi yawa na mayar ni kaina nasan na so zuciya amma cikin ikon Allah ta kar'ba ta dudduba tana murmushi ta ce a zuba mini a leda. Na yi ta godiya na kar'ba ina duba jikin ledar wadda ta kasance ta mussaman mai d'auke da logo da bayanai bambamta a jiki. Daf da zan fita kawai na hangi wasu mata masu kumari sun k'oshi 'kwarai daka gani sun ci sun tayar da kai suna ko'karin kutsa kansu shangon zannuwa. Kowacce rataye da jaka sai na bi bayansu ina ji suna fad'in dole kam ai Amina ta mu ce dole mu yi patronizing d'inta duk dai ta kafu ta tsaya da k'afafunta amma yadda ta yi kwasha-kwasa da kayanta irin haka ba kowane d'an kasuwa ne zai iya yin abinda ta yi ba. La'bewa na yi inda ba za su gan ni ba don da kunya ace ta sake ganina tunda ta sallame ni bayan sun shiga sai na le'ka kaina abinda ya ba ni mamaki bai wuce ganin yadda suke gaisawa cikin raha da wasa da dariya ba ashe k'awayenta ne Nahajarama Maryam Saminu Sulaiman Maman Fu'ad da Mama Hauwa zaria na yi zuru ina ta lek'ensu suna ta hira ta sanya an basu wurin zama har da lemo bayan sun gama hutawa suka tashi suka fara dudduba shops din suna sanya albarka da fatan alheri. Can na hangi wasu iyayena suma sun shigo plazar cikin annashuwa ban yi mamaki ba domin dai duk cikinsu babu mutuniyar banza mata ne nagartattun da suka mayar da d'an wani nasu Hajia Usainakaita Mommy fossima Nijar hajia Halima wada kura hajia karimatu Haladu Nasiru da hajia Halima Dalha shehu. Na kuwa ji dadin ganin yadda ta karrama mini iyaye suma kuma sun yi mata halin karamci da dattako turaman atamfofi suka saya masu yawan gaske wanda nake da tabbacin cewa ba d'aurawa za su yi a jikinsu ba rabar da su za su yi ga iyayan marayu. Ina nan tsaye da ledar kayana na hangi k'awayen nan nata sun fito kowacce da ledoji a hannunta niki-niki ita kuma ta biyo bayansu da raha da barkwanci na yi saurin b'oye kaina ta raka su har bakin motarsu suna yin sallama hannuwansu ri'ke da juna kamar kada su rabu. Na sake gyara biro da takardar dake hannu ina kallonsu da wani irin murmushi wanda ni kaina na kasa gane ko na menene lallai Amina ta cancanci k'auna da soyayya domin kyawawan halayenta.. **** To cikin sa'a aka kammala bikin bude shops wanda aka d'auki tsayin sati guda ana kai kawo da hidima da jama'a cikin k'warewa da jajurcewa ta kowane fanni anyi katari kuwa domin kuwa an cimma nasara akan abinda ake nema. Duk nisha'din da cigaban da na samu ban samu nutsuwa yadda ya kamata ba domin kuwa har yanzu maigidan ba a nutse yake ba yana dai ta yin al'amuransa ne a matsayinsa na namiji mai juria amma ni da nake tare da shi na kuma san halinsa na san a cikin damuwa yake kawai yana danneta ne. Kuma na gaya masa a wannan tsukin da shi kansa ya kasa control din matsalarsa yana da kyau ya tsananta da addu'a domin neman zabin Allah amma zahiri shirinsa da yanayin yadda yake kasancewa cikin damuwa ya fara damuna ina ganin dole na sanya hannuna a wannan rikicin duk kuwa da alwashin da na ci a baya a kan fita daga sabgarta don ganin ya fita daga cikin damuwar da yake cikinta a yanzu. Yadda Allah Ya yi mini babu wayo kuma babu dabarata dalili kuwa in banda ni da yaran shops dina a yanzu babu wanda yasan adadin alherin da na samu a cikin kwanakin nan kacal shi kansa bai sani ba kuma ina so na gaya masa na samu riba da yawa a cikinta zan cire wani abu na bawa Hauwa tunda shi ya riga ya rantse ba kuma na so na karya masa rantaywarsa. Ranar dana gaya masa zan cire 10m shima ya cire 10m mu had'a mata 20m kawai ya ji ne amma uffan bai ce mini ba har garin Allah Ya waye bai sake tayar da maganar ba ni ma ban tasheta ba sai bayan kwana biyu na sake yi masa magana. Aikuwa ya fara fad'a sosai kamar dama kiris yake jira yana fad'in kamfani ya yi niyyar bata tunda ta ce bata so kanta ta yi wa kwabonsa ba zai k'ara mata ba. Tunda nayi niyya na bata kud'ina ne amma shi ba a isa ba. Sai na kyale shi kawai bayan kwana biyu na kira Hajja a waya muka gaisa sosai na sha addu'a da fatan alheri domin Hamusu ya kai mata turaman atamfofin da na ce a dinka mata anan ta dinga godiya da addu'a har sai da na ji hawaye ya ciko idona ba zan yi maraicin uwa ba tunda Hajja tana raye bata yi mini k'yashi da ba'kinciki irin na wasu iyayen mijin ko wannan alherin ya isa ni ma na ture komai. Duk da bani da hurumi akan lamarin amma Allah ya ga nufi ne sam ba ni yi wa Hauwa sha'awar abinda take yi wa kanta hasashe yadda ya d'auki wannan zafin wallahi kiris ya rage a yi ta kare. Duk shawarar da na yanke na gaya mata domin kuwa ko anti Yagana ban gayawa ba duk da nasan bata da ganin k'yashi amma za ta iya hana ni tace babu ruwana. Wannan maganar tawa ta yi wa Hajja bazata ainun ta rasa abinda zata ce sai da na ji shurun ta yi yawa tukkuna na sake magana sannan na ji sautinta tana ta godiya tana sanya albarka tana fad'in tunda shi ya rantse ba zai k'ara mata komai ba to itama ta sanya 5m sai a had'a mata 15m na ce hakan ya yi amma da sunan duka ita ta bata kada sunana ya fito ciki. Ta ce hakan ba hujja ba ce dole a gaya mata jin ta fad'i haka sai na gane cewar ba ta fahimci azancina ba. Na jima kuwa ina yi mata bayani idan har Hauwa ta tabbatar da cewa ni ce ma na bata kudi ba shi ba ko ita Hajjan to babu shakka wutar ba zata mutu ba ruruwa ma zata sake yi tunda duk rikicin a kaina ne. Tsayin lokacin da na d'auka ina yi mata bayani ya sanya ta gane hujjata sai ta amince da hakan tana ta sanya mini albarka da addu'a akan Allah Ya ninka mini abinda na bayar ya kuma albarkaci kasuwancina.........✍️ [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK.* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *175* Bayan kwanaki biyu da kanta Hajjan ta kira ni a waya tana yi mini bayanin cewa an daidaita komai yanzu haka ma suna tare da Hauwa a gidanta da kuma mahaifiyarta kamar yadda muka yi da ita bata nuna musu da sanya hannuna ba kawai dai ta kira su ne akan su zo a tattauna domin samun maslaha kudi kuma ta kar'ba a madadin shi ya bayar domin itama ba ta nuna musu da sanya hannunta a ciki ba. Hakan ya kwantar da tarzomar da take yun'kurin tashi da uwar da 'yarta ta duka bakinsu d'aya dama tuntuni Inna Uwani ta daina b'oye -boye yanzu fili take fitowa ta nuna tana bayan d'iyarta tunda ta sha fadi cewa itace gorar gida ko ma baya. Ita Hauwa tun kafin su amsa kiran Hajjan yan-uwanta da k'awaye abokanan arziki suna ta yi mata fad'a da nuna mata daburun zama da miji da kishiya anti Zeey wato Zainab Khabir Ishak tana d'aya daga cikin wad'anda suka dinga nusashshe da ita cewar wannan abinda take yi bashi ne zai ri'ke ta a gidan aure ba domin yanzu kai ya waye an daina irin wannan kishin irin na jahilan mata da yake macace mai tsage gaskiya duk d'acinta ba ta yi shakkarta ba ta gaya mata kuskure da lefinta ta gaya mata cewa lallai ne fa sai ta gyara halinta zata cigaba da jin dad'in zama da mijinta tunda har ya iya k'ara mata miliyan goma sha biyar bayan kamfanin da ya mallaka mata to lallai hakan ya nuna yana son cigaba da zama da ita. Ita kuwa Mum Sajeeda takaicin abinda Hauwan take yi gabad'aya ya 'kumeta ta rasa ma abinda za ta ce saboda yadda take jin haushinta tana fad'in kamar wadda ba ta yi boko ba tana aikata ayyuka irin na gidadawa mata k'awar Sadiya ta wurin aikinsu nan ma ta ji labarin abinda yake faruwa har gida ta je ta samu Hauwan ta yi mata wankin babban bargo acan wajan aiki suna kiranta da anti Hally macace mara son wargi sannan tana da zafi-zafi mafiakasarin masu sunan suna da fad'a da kuma fad'in gaskiya komai d'acinta. Haka dai suka yi mata rubdugu a can bauchin Maman Ummul-kairi ta zauna da ita a tsanake ita cikin nutsuwa ta dinga jan hankalinta tana sake jadadda mata cewar ita kishiya ba a cin ta da ya'ki irin na bayyane tunda har ta fahimci abokiyar zamanta ta fita soyuwa a zuciyar mijinsu sai ta nemi hanyar ganin ta samu zaman lafiya da ita Asmau Muhammad jabbi ta sanya bakinta tana cewa kuma ta ji an ce kishiyartata bata da mugunta sannan macace mai karamci da halin girma mussaman idan an duba da irin abubuwan da ta gudanar a cikin kwanakin da suka gabata wurin sassauto da farashin kayanta. Ita kuwa Eama kallon sakarai take yi mata domin tun tana bata haushi yanzu dariya take bata tana kiranta da sokuwar mace Aishatu waziri kuwa fadi take yi ki gurgu'de auren ki dawo ki zauna a gida wallahi akwai wadda na yi masa sha'awarta kuma a cikin mu take duk yadda zan yi sai na yi kokarin ganin ya nemi auranta tunda ke baki da wayo kin gama bayyanawa miji da kishiya munanan halayenki. *** To ni dai Hajja bata gaya mini ranar da za ta dawo ba amma hankalina ya kwanta sosai jin cewar komai ya daidaita har ta kar'bi kudi to na tabbatar da cewar kuwa ba zata kara yin wasu kwanakin masu tsayi ba za ta dawo dakinta Yanayin yadda yake tafiyar da al'amarunsa ban tsammaci ya san abinda yake faruwa ba gaskiya domin kuwa da ya sani tabbas sai ya yi mini maganar amma gashi yau har kwana biyu da yin waya da Hajja ban ji ya ce komai ba. Sai da daddare tukkuna bayan ya gama cin abinci ya dube ni a nutse yana fad'in." Kin dawo da Hauwa ashe." shiru na yi ban ce komai ba sai aunar maganar da ya yi nake yi. Ya tsira mini ido kafin ya cigaba da cewa." Tunda kin dawo da ita sai ki gaya mata zamanki take yi babu yawuna ba kuma ruwana da ita." Jikina ya yi sanyi ganin ta hanyar da ya 'bullo kuma hakan bai yi masa ba kenan haushi ya ji. Na daure na furta." Ba ni da na dawo da ita ba Hajja ce." Ya d'an harare ni yana fad'in." Duk abinda ki ka aikata mahaifiyata ta sanar da ni. Ita dai kin yi mata gwaninta kuma ta yi miki addu'a amma ni sam ba ki burge ni ba." Na yi shiru ina kallonsa kafin ya cigaba da cewa." Tunda kudin cizonki suke yi mai zai sanya ba ki sayi fili kin yi k'aramin massalaci ba hadiya ga mahaifiyarki ko ki yi rijiyoyi na ruwa ko kuwa ki kai gidan marayu sam baki burge ni ba wallahi idan ma don ni ki ka yi bai ban sha'awa ba. Shiru na yi na kasa tanka masa saboda jin haushin gwaliyar da yake yi mini. Ganin ban ce komai ba sai ya cigaba da sakin maganganu na gaji da sauri na daga masa hannu ina fadin." Ni don Allah na yi ai ba don na burgeka ba tunda Hajja ta yi farinciki kuma hakan ya yi mata daidai alhamdulillahi maganar ta mutu haka don Allah." Ya tashi zaune sosai yana kallona kafin ya ce." Magana ba zata mutu ba tunda ba ni na ce Hauwa ta dawo ba na gama yanke hukunci a kanta." Na ce." To tunda ka gama yanke hukunci a kanta sai kawai ka aiwatar ni ina ruwana idan ka saketa ka tabbatar da cewar zaka auro wadda zata kula da yaranta ni ma nawa kadai zan ri'ke shikkenan karshen magana. " Na yun'kuri na tashi na bashi waje. Washe gari har d'akina ya biyo ni ina toilet ina ta kalato amai irin na sassafe majina ce kawai ke fita wani abu ya tsaye mini a wuya yana kaikayi. Ya leko toilet din ganin halin da nake ciki sai jikinsa ya yi sanyi ya rike mini hannu har na gama na wanke bakina muka fito zuciya sai hantsilawa take yi. Muka zauna ina ta sauke numfashi shi kuma ya tsira mini ido sosai a hankali ya furta" cikin ne ko?" Juyar da kaina na yi ban bashi amsa ba saboda har yanzu haushin abinda ya yi mini jiya nake yi Ya lalubi wayarsa dake cikin aljihu jikinsa na dan rawa still hannunsa na ri'ke da nawa lambar wayar Dr Sailuba yake nema. Na kar'bi wayar na ajiye saman dirowar gefan gado ya kusance ni sosai cikin taushin harshe ya furta." Ki gaya mini mana menene ba ki so a kira Dr Sailuba kin tabbatar ne?" Na d'an saki ajiyar zuciya Ina fad'in." Shine na tabbatar tun lokacin da ka fara hasashe tunda kuwa hakane ka ga babu amfanin kiran likita ni ba yarinya ba ce. " Ina rufe bakina ya zame kasan kafet sujuddur Shukur ya yi. Na zuba masa ido yayin da goshinsa yake kasa yana mika godiyarsa ga Allah sai jikina ya yi sanyi sosai anya kuwa ya ta'ba d'okonta da ciki kamar wannan da aka samu yana murna duk lokacin da muka samu ciki amma dai wannan abin ya yi yawa. cikin raina na ji nima ina son cikin da kuma ina addu'a akan Allah Ya cika mana burinmu na samun d'iya mace mu a sanya mata sunan Hajja Halimatussadiya. *** To ko da ta dawo sai da ya gama shan 'kamshinsa tukkuna don sai da ta kwanta hud'u da dawowa sannan ya je gidanta kuma kafin ta dawo din na ga ta kira shi a waya ta gaya masa zata dawo ni dai addu'ata Allah Ya sa kada ya gaya mata cewar ba shine ya bata kudin ba ni ce don nasan ba 'karamin aikinsa ba. Sati biyu ya kara akan dawowarta ya tafi Legos domin daman dawowartata ce ta sanya shi jinkirta tafiyar ya tabbatar mini da cewar ba zai wuce wata biyu ba zai dawo. Tunda ta dawo bamu hadu ba dama can tunda aka raba mana gida ita ce mai shigo mini bana zuwa gidanta sai da dalili mai karfi zuwana biyu kacal lokacin da ya yi ciwo da lokacin da ta yi 'barin ciki. Sai dai duk ranar juma'a nakan ce da yaran su je su gaisheta suka dan zauna a can dalili Ladidi mai aikinta na hillatarsu da tatsuniya da labarin kanzon kurage su kuma akwai son haka idan sun dawo gida suce mama ta ce a gaisheki. Hadiza kam takan zo mini sa'i da lokaci mu yini tare tunda tare suka tafi da Sukairaju itama cikin kad'aici take hakan ya sanya nake tura mata yaran ranar alhamis bayan sun dawo daga boko sai Masa'udu ya kai su idan sun dan jima ya je ya d'auko su. Cikin wannan yanayin Nabila ta fito tare suka zo mini ita da Nusaiba wai sallama ta zo yi mini za ta koma jos da zama dalilin abinda ya samu rayuwarta duk abinda ta mallaka ya salwance da kyar Allah Ya bayyana gaskiyar cewar babu hannunta akan abinda ya faru. Wallahi ta ba nii tausayi sosai ta yi wani irin baki fatar nan da aka kwailayeta ta toye ta yi dabbara-dabbara daka gani ta k'are mata babu kud'in cin abinci ma balle na sayan man bleaching duk wannan gayun babu shi ta susuce ma gabad'aya. Rayuwa kenan shiyasa duk abinda mutum zai yi ya sanya tsoron Allah a ciki. Kasuwanci ba za a tsarkake shi ba ya ki Haram yaki halak ko ta halin kaka sai an yi kud'i tunda an shiga hurumin Ubangiji kuma ai ba za a ga daidai ba. Wasu daga cikin kayana na tsinto mata masu kyau set biyar na hada mata da mayafai da hijabak sannan na ce lallai za ta ga sakona a kurkusa.. Kafin su tafi kuwa kuka ta yi sosai da sosai tana ta ba ni ha'kuri har na gaza gane hakurin me take ba ni domin dai gabad'aya cikin nadama da danasani take tunda duniya ta yi kuli-kulin kubura da ita. Bayan kwana biyu da zuwansa kuwa na kira Nusaiba a waya na ce ta turo mini details din Nabilan tana turo mini na sanya mata dubu dari biyu ciki. Sannan dama ina da lambar wayarta tun farkon haduwarmu lokacin rasuwar Alhaji Amadu muka yi musayar lambar a lokacin jininmu ya hadu domin ni da ita ne muka dinga tiri-tiri da Hajiya Maryam din akan 'kin cin abinci. Kuma bayan Hakan muna d'an gaisawa a wancan lokacin har idan ta yi status na bude na gani idan abin murna na yi mata murna haka zalika idan abin jaje nan ma na jajanta. Katsam na daina ganin status dinta nan na tabbatar da cewa ta yi block dina ne tunda lokacin aure ya kullu tsakanin maigidan da 'yar uwarta sai ta rufe ni, a lokacin abin ya yi ta ba ni mamaki da daure mini kai Na kira ta muka gaisa na ce ta duba na tura mata sa'ko kamar wadda na bawa miliyan biyu ta dinga yi mini godiya har muryarta tana rawa tsabar kyautar ta yi mata dadi. *** Lokaci bayan lokaci Kamalu kan kira ni bidiyo call mu jima muna hira yaro ya yi wani girma da wata haiba ta mussaman wata irin nutsuwa da annashuwa nake tsintar kaina a ciki a duk lokacin da nake kallonsa ina kara tahamdi ga Allah madaukakin sarki. Watansa uku ya dawo kamar yadda ya fad'i lokacin cikina ya shiga wata na biyar amma bai fito ba ya dai bi jikina kwankwaso da breast sun sake girma sai dai Ina jin ciwon mara kafa sa sauransu har gida Dr Sailuba take zuwa ta yi mini awo ta kuma ba ni maganganun da suka da ce. Wai shi a tunaninsa idan ya dawo zai ga ciki ya fito sosai na ce masa cikin bai ma cika wata biyar ba ai bai yarda ba sai ma ya fara zargi babu shi ya rasa sukuni ko kad'an hankalinsa bai kwanta ba sai da dr Sailuba ta yi masa cikakken bayani ya ce a je a yi scanning a ga mai za a haifa tunda nake samun ciki bai fiye matsawa ba yakan ce duk wanda Allah Ya ba shi yana so amma abin mamaki wannan kam yana dawowa ya daga mini hankali dole na shirya Hadiza ta yi mini rakiya domin yin scanning din kamar yadda ya buk'ata Ashe itama tana 'kunshe da nata cikin ban sani ba bayan an gama yi mini aka yi mata cikin ikon Allah ni mace ita namiji satikan cikinta sun haura nawa ta riga ni samu amma dai tsiraranmu kadan ne za ta riga ni haihuwa wata'kila kafin ta yi arba'in na haihu. Sosai na tayata farinciki domin can baya gidan Alhaji Halilu ta yi ta samun matsalar lalacewar ciki har dai suka rabu bata haihu ba a wannan matakin da muke ciki da shekaru suka fara nisa ko biyu ta samu sai ta godewa Allah. Mijinta ne ya kai mu bisa bin umarin maigidan shi dai tun a mota yake ta annasuwa ya rasa ina zai sanya rayuwarsa ganin result din cikin matarsa namiji kuma cikin koshin lafiya ita dashi gabad'aya sai suka ba ni tausayi. Kwanaki goma da yi mini scanning muka tafi umara ni da shi a cewarsa yana da kyau mu je mu yi godiya tare da addu'a akan Allah Ya tabbatar mana da abinda hasashe domin kuwa komai yana iya canzawa gashi ya jarabtu da son haihuwar 'ya mace mai sunan Mamansa. Mun yi addu'a sosai wadda ta shafi kowane bangare satin biyu muka dawo gida. Rayuwar ta cigaba da gurgurawa sannu a hankali ban san dai me yake tsakaninsa da matarsa ba domin tunda ta dawo ba mu had'u ba kunya ta hana ta zuwa inda nake sai dai sakon gaisuwa idan yara sun je. Shi kuma yana ta zagari tsakanin gidana da gidanta duk wadda take da girki zai je ya kwana. Tun bayan dawowarta babu wata matsala da ta sake faruwa yanzu kusan wata shida kenan cikina na da wata bakwai lafiyar Allah nake gudanar da hurd'odina babu nauyi irin nasu Hassan sannan laulayin da na yi ma takaitaccene a farkon samun cikin ne. Babu wanda ya san ina sa juna biyu tsakanin anti Yagana da Sahura tunda ban gaya musu ba muna dai yin waya sa'i da lokaci. Sai da Hadiza ta haihu tukkuna da su anti Yagana suka zo yan gidanmu suka fahimta lokacin ma ni kadai nake jin abinda nake ji nakuda ce nake yin ta a tsaitsaye Hadiza ta haifi namiji yaro lafiyayye mai kama da babansa sai ta dinga ba ni sha'awa wallahi ganinta ri'ke da jaririnta lafiya lau tiriri ya kare. Kayan da Nabila ta had'awa su Hassan a lokacin haihuwarsu sama suna saman maigidan don haka ya ce da Sukairaju ya zo ya kwashe su suyi amfani da shi ya samu takwara domin kuwa kwana biyu da haihuwarsa ubansa ya yi masa hud'uba da Tajuden. Yan gidanmu kaf sun halarci taron sunan Hadiza da yamma sai ga Hauwa da leda cike da kayan baby wai ai ta ji an ce yaro ya ci sunan maigidanta. Ta sake ana ta wasa da dariya da ita babu kuma wanda ya nuna mata komai ni kaina janta nake yi da hira yadda ta saki jikinta sosai ya tabbatar mini da cewa ba ta fahimci halin da nake ciki ba ni ma, ko da yake a zaune nake ba lallai ne ta gane komai ba. Sai daf da magriba ta yi mana sallama ta tafi anti Yagana ta ce da Fati ta zazzage kayan da ta kawo a duba tsaf kada ta kunso wata jarabar ne. Na dinga dariya ina fad'in anti Yagana kenan. Set din kayan jariri ne uku da turaruka masu tsada da wani takalmi mai ban sha'awa bayan mun gama gani Fati ta had'a kayan ta mayar da su cikin leda. Sati biyu suka ce za su yi kafin su tafi anti Yagana kuma ta ce kwana biyu kacal za ta kara ta kama hanyar gidanta na yi na yi da ita itama ta zauna ta huta sosai kamar yadda su Fati suka zauna ta ce ai ita babba ce da kunya kada lalacewar ta yi yawa mazajenmu su daina ganin girmanta. Na ci dariyata kuwa na 'koshi mussaman da na tuna yadda suke yin wasan 'buya da maigidan tun musayar yawun da suka yi akan kamfani shi yana jin kunyanta itama tana jin nauyinsa. Wannan littafin na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biyani hakkina ba. Aikuwa bayan tafiyarta da kwana biyar ciwon nakuda ya kama ni a gida ranar juma'a kaf kowa yana nan har yaran kuma da safe ciwon ya tashi ban fito daga d'aki ba na kira Dr Sailuba saboda dama tuntuni na yi nak'udata a tsaitsaya don haka zuwanta da minti ashirin da biyar na haihu lafiya lau yarinya mace ta dinga tsalla ihu da ya fargar da kowa Yara suka ki'dime suna murna Mama ta haihu Khalil ne ya ruga gidan Mamansa twin's kuma suka hau sama wajan Babansu bacci yake yi suka tashe shi da ihun murna Mama ta haihu. Dr Sailuba ba ta bud'e d'aki ba kuwa sai da ta kammala komai ta gyara ko'ina amma still kusan awa guda da haihuwar yarinyar kuka take tsalawa har dai abin ya fara ta'ba ni na fara tambayarta anya lafiya ta ce mini lafiya lau don karon farko bata tsammaci matsala ba. Tana bude d'akin suka dinga shigowa yan gidanmu su Fati da Hauwa da take jan kafa tsabar k'aduwa da tashin hankali kamar wadda ta yi targad'e a kafarta kallon farko da na yi mata na gane lallai akwai matsala domin duk yadda ta kai ga ganin ta gayyato dariya da annashuwa tasirin damuwar da ta tsinci a kanta a ciki ya danne abinda take kokarin gayyotowa duk wanda ya lura da ita zai gane cewa lallai a rikice take domin kayan bacci ne a jikinta da hijabin sallah. Bakin kowa kamar audiga tun daga kan maigidan zuwa kan masu aiki yaran da 'yan uwanana sai murna da sambara suke yi don ma dai kukan da yarinyar ke tsalawa ya d'an rage karsashi da annashuwar shi ma ya fara tambayar Dr Sailuba babu matsala da confidence d'inta ta ce masa babu wata matsala lafiya ce. Hauwa ta kar'bi babyn hannunsa tana juyyata can kuma ta dan daga mata idanuwanta tana gwalesu sosai ta dubi ta d'aga rigar jikinta tana tatta'ba jikinta da hannunta sai ta dubi Dr Sailuba tana fad'in." Ki duba sosai Dr kada ki dinga yin abu daka yarinyar nan bata da lafiya." A d'an sanyaye ta kar'beta daga hannunta har zuwa lokacin kukan take tsalawa ta dan jima tana jujjuyata Kafin ta dube ni da sanyi jiki ta furta." Za mu je asibiti domin dubata sosai kukan ya d'an so ya yi yawa sannan jikinta ya d'auki zafi akwai abinda nake zargi." Gabad'aya ni da shi sai jikinmu ya yi sanyi muka dubi juna. Ya yi saurin kar'be babyn tana tsala ihu ya d'an dubi Hauwa dake tsaye a gefansa itama shi take kallo karaf ta ce." Ku je asibitin sai a dubata gaskiya bata da lafiya." Na ga sanda ya wurga mata wata muguwar harara ya kawar da kansa cikin wani masifaffan yanayi da tashin hankali. A takaice dai a ranar a asibiti muka kwana domin dai gado aka ba mu babban likita ya bincike mana ita tsaf sikila ce dole akwai buk'atar zamanmu a asibiti na wani lokaci domin kula da ita. Tashin hankali wanda ba a sa masa rana. A daran ni da shi kuka domin dai da farko har na fi shi dauriya na dinga tausarsa da kawo masa misalai tare da gaya masa kada ya butulcewa Allah kada kuma ya nuna Allah bai yi masa daidai ba. Ya kasa jurewa hawaye yake d'igarwa domin dai bayanin da likitan ya yi mata babyn sikila ce sosai. Hauwa kuwa ta kira shi a daran sm da kyar na bashi baki ya d'auka don gabad'aya ba shi cikin hayyacinsa ban ji me take gaya masa ba sai gani na yi ya tashi tsaye jikinsa na wani irin kyarma yana ce wa." Ba ki kunya da nauyin gaya mini wannan maganar ba Hauwa." Itama na ji ta cikin 'karaji tana fad'in." In sha Allahu rabbi sai ta mutu da izinin Allah hakkina ba zai barka ba wallahi ba zan daina mi'ka kukana ga Ubangiji ba ai ba cikin haihuwar ne ba ni dashi ba ni ma, yarinya kuma nafad'a maririciya kuma mutuwa suke yi kada ma ku sanya rai a kanta domin mun ga haka ya fi sau d'ari. Jikinsa ya cigaba kyarma da wata kaurarriyar muryar da ban san shi da ita ba ya furta." Ina ce sai ina auranki tukkuna zan kwanta dake ki samu cikin da za ki haihu shikkenan na sake ki Hauwa saki biyu babu wata dangantaka ta aure a tsakanina dake yanzu na sake ki saki biyu......... Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! *A kar'ba da ha'kuri don Allah hakan tana iya faruwa da rayuwarsu ina fatan dai ba ku mance tushen labari ba. Sakon littafin gudun aure ya isa saura k'arashe in sha Allahu Ina mutukar godiya....* *GARKUWAR MATA.✍️* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *V-VIP AREWAPEN* *07084653262* *176* Na ji komai da kunne na babu buk'atar neman karin bayani ni gabad'aya ma abinda yake gabana lafiyar yarinyarta akwai tsananin damuwa da fargaba a ce ka gama goyon ciki da wahalhalunsa ka haife ka fuskanci wani k'alubalan na mussaman sai yanzu gane wannan shine babban dalilin da ya sanya likitoci suke iyakacin bakin kokarinsa wurin ganin sun dakile yawaitar haihuwar yaran da suke d'auke da wannan lalura. Doke ce a yanzu waliyya da mahukunta basa d'aura aure sai da shedar daidaituwar jini mussaman ga saurayi da budurwar da ba su ta'ba haihuwa ba akansu dai wannan dokar ta fi tsananta akwai sau'ki akan namijin da yake da iyali da kuma bazawarar da ta haihu a wani wajen tana da yara maslaha ce a tsakaninsu ko da suΓ± yi aure sai su d'auki matakin gujewa samun ciki. Duk da yake duk tsumi da dabara ba a isa a yi wa Allah wayo ba wahalar dai da tiri-tirin shine abin gudu. Na haihu ina murna ban ta'ba tunanin zan sake haihuwar sikila ba ganin na jera haihuwa har sau biyu lafiyarsu lau gabad'aya ni da shi tunda aka samu cikin yarinyar nan ba mu ta'ba zama mun tattauna mas'alar da za ta iya kasancewa a rayuwarmu ba saboda duka tunaninmu daya wata'kila Allah ya d'auke mana tunda mun yi sau biyu a jere dukkaninsu lafiya lau. Sanin gaibu sai Allah kuma duk abinda ya tsara shine daidai kuma dole a yi godiya gare shi. Lamarin Hauwa kuwa gabad'aya kaina ya kulle na gaza kuma na yi rauni akanta domin duk kaifin tunanina k'wakwalwata ta kasa hakaito mini a wane mizani zan ajiyeta a bayyane komai yake bata da abokiyar gaba sai ni kuma a duk lokacin da sarki Allah ya bata sa'a a kaina don ta d'auki makami ba wani abu ne. Asibitin na mussaman ne don haka da gari waye Baba Tabawa kawai na ce masa a kawo mini na kuma kira Fati a waya na ce ta had'a mini kaya da duk abinda zan buk'ata tunda ba su tafi ba suna nan likitan dake tsaye kan yarinyar ya bada tabbacin kan cewa a k'alla mu yi sati ko kwana goma kuma alhamdulillahi kwana daya kacal da muka yi yarinyar ta sassauta kukan da take yi zafin da jikinta yake d'auka ma ya yi sau'ki ta kuma samu bacci. Hakan ya sanya shi tafiya gida domin yin wanka tunda tare muka kwana cikin tararrabi da zullumin abubuwa masu yawa ya dinga ba ni tausayi daga zarar na daga kaina na dube shi hakika Allah ba yadda baya aiwatar da ikonsa a kan bayinsa. Ya yi addu'a akan samun haihuwa kuma diya mace wadda ya nema a wurin Allah Ya amsa masa sai kuma ta zo a maririya mai rangwamin lafiya wannan ma jarabawa ce me zaman kanta amma godiya ga Allah itake nuna cikar munini tunda ai akwai ma'auranta da duka yaran nasu suke kasancewa da cutuka mabambamta kuma daya bayan d'aya ya d'aukesu su koma gare shi bayan iyayen sun sanya rai kuma ba su gaza ba wurin nemo musu magani da kudi da lafiyar jikinsu. Ubangiji ta kowace suffa ya kan jarrabi bayinsa wanda yake so domin auna imaninsu. Da wad'annan nasihun na d'an samu kansa amma ko bayan wannan nasan damuwar ai tana jika dalilin abinda Hauwa ta yi tamkar ba jininsa ba k'iyayyar ta munana ta kuma tsananta Allah ne mai rayawa kuma shine mai kashewa shi ya ba mu don ya kar'ba ai ba mu da abinda za mu yi tunda mu da muke zaune a duniyar zaman jiranta muke yi. Wannan shine kawai abinda na bari a zuciyata maganganun Hauwa akan yarinyata ba su razanar da ni ba, musulmace ni dole kuma na yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau. Haihuwa ya ba ni ya sake ba ni ya ba ni ta mussaman wadda ba kowa ke da baiwar ba har sau biyu masu lafiya rayayyu guda shida yana kuma raya mini su cikin aminci da kulawarsa da kuma tarbiyarsa babu abinda zan ce da shi sai godiya kuma duk abinda ya zartar daidai ne. Da Baba Tabawa muka kasance a asibitin tunda gaskiya akwai tsaro sosai ba su barin wannan shige da ficen itama saboda maigidan sananne ne yana kuma da alfarma ya sanya suka barta ta zauna. Alhamdulillahi cikin kwanaki hud'u abubuwa sun yi sau'ki ta daina duk abinda take yi tana kuma kama nono ta sha cikin nutsuwa ta yi baccinta da kwanciyar hankali. Muka samu nutsuwa ni da shi mussaman da likitan yake jaddada mana cewa muddin an kula an kiyaye komai kan ka'ida ciwon ba zai dinga motsa mata ba a kai-kai. Kwananmu takwas muka dawo gida. Ya zama kamar kufai shiru babu hada-hada ta yara duk suna ma makaranta masu aiki Mairo da Taburni na kicin Hassan da Usaini na bacci bayan wankan da aka yi musu shi kuma Sultan na tare da su a kicin. Na kira Hadiza a waya na gaya mata na dawo cikin kasa da minti ashirin sai gasu gabad'ayansu suka kewayeni duk babu wata annashuwa a tare da su babyn tana ta bacci babu halin d'aukarta domin dai likitanta ya bada umarni hakan kada a yawaita jagwalgwala mata jiki sai dai ido kawai Fati take tambayata da wane suna za a dinga kiranta tunda wai Sukairaju ya gaya musu sunan Hajja ne da ita na ce Mufida haka babanta ya ce a kira ta. Yini muka yi tare da su har yaran suka dawo daga makaranta ganina a gidan ya sanya su shiga tsananin murna hankalinsu gabad'aya nakan babyn sai sun d'auketa Minal har da kuka sai da na kira Mairo tukkuna na ce ta ja ta su fita domin wani irin ciwon kai nake yi kukan da take yi kuma yana sa'bata da yanayin yadda duk na gansu cikin damuwa mussaman Khalil duk jikinsa ya yi sanyi na kasa gane shin akan menene ba ni tsammanin ubansa ya gaya masa ya saki uwarsa sai dai idan ita za ta gaya masa kuma ba na tsammanin ta tafi tana gidanta tunda na ji lokacin da yake magana da Mairo yana gaya mata sakon Ladidi tunda k'awarta ce idan Hauwan ta aikota sukan dan jima suna hira akwai wani k'aramin gari a cikin bauchi mai suna giayade anan cibiyar iyayensu take duk da ba su had'a wata dangantaka ba hirar yau da gobe ta sanya suka fahimci garinsu daya. Washe garin ranar da muka fito Hajja da yayarsa suka dira dama ya gaya mini shine ya dakatar da su tunda ko sun zo muna asibiti ganin hakan ya sanya ni ma na hana anti Yagana zuwa tukkuna can gidanmu ma haka na gayawa Babanmu a waya cewa su bari sai mun fito Sahura kuwa kusan kullum sai mun yi waya. Sai dare tukkuna muka samu ke'bewa Hajja fadi take yi Hauwa abinda ta yi muku Amina Allah Ya yi mata ba zan yi mata baki ba ba kuma zan nunawa duniya Tajo ne nawa ba amma da wahala ta sake yin katari da namiji da abokiyar zama kamarki zahiri kin yi iyakacin bakin kokarinki wurin ganin kin kawo daidaito a tsakaninku kin yi bajinta kwarai kuma kin yi da jiki da aljihunki a tarihi ban ta'ba ganin kishiya irinki ba Allah ya biya ki da aljanna Ubangiji Allah Ya dubi rayuwarki. Wad'annan yara kuma ina yi miki addu'a akan Allah Ya ba ki wuyan d'auka Allah Ya raya mana su. Na dinga amsawa da Amin Amin amma bayan haka ban iya furta komai ba akan abinda suke tattaunawa Hajiya Saratu tana ta fad'a akan zaman da take yi tunda an yi ta ta kare babu wata sauran igiya zaman me take yi kuma har tana fad'in da safe za ta je gidan ta ji dalili babu sauran wani mutunci da zumunci a tsakaninsu tunda har ta iya rufe idonta ta yi wa dan uwanta wannan cin fuskarsa. Gaskiya ne a wannan ga'bar takai-takai kawai ake yi kowa nasa ya sani domin kuwa abinda ita Inna Uwanin ta nuna kenan. Wannan karon Hajja ta saki ragamar hannun yaranta ai kuma magana ta 'kare babu sauran gyara babu amfanin zamanta a gidan ta kama hanya ta tafi yara kuma ta bar su a gidan ubansu. Da wannan suka rufe maganar ni dai magana akan Hauwa ta k'are a bakina domin ban san abinda zan ce ba ta gama goge mini hadda ta tilawa. Aikuwa kamar yadda ta kwana da al'amarin garin Allah Yana waye wa ko karyawa ba ta yi ba ta nufi gidan Hauwa. Ni dai Ina d'aki da yake kofar a bud'e take saboda yaran sun shigo mini kafin su tafi skull na ji fad'anta a falo har ina tsinkayar muryar maigidan. Fadi take yi zaman nata ai bashi da wani amfani ban kuma yarda da abinda ta fad'a ba wai juna biyu gareta ko za ta tafi sai a bari ta haihu tukkuna shin kai ka san cikin ne da ita. Cikin rashin karfin sauti na ji maganarsa amma ban ji abinda yake cewa ba. Na yi zuru ina mamaki cikin da take ta ha'kilo a kansa shin tasan dama tana dashi ta yi wannan rashin mutuncin ko kuma dai karya take yi don kada ta tafi ne. Wani sashi na zuciyata ya dinga gaya mini karya take yi da tana da ciki da kowa ya sani tunda abinda take nema ne kenan kuma ba zata zafafa bakincikinta ba. Can wajan minti ashirin da biyar a tsakani na dinga jin kuka kasa k'asa da maganganu suna tashi sai da na kasa kunne tukkuna na gane muryar Hauwan ce take wani irin kuka mai cin rai Hajja tana ta yi mata magana akan ta yi shiru amma sai kara karfin kukan take yi. Cikin babban sauti na ji muryar Hajiya Saratu tana cewa kan ki kika tonawa asiri Hauwa ba mu za'bi Amina ba saboda muna 'kin ki. Mun za'bi kyawawan halayenta ne da kuma biyayya amma tunda yanzu magana ta kare babu buk'atar a yi ta maimaitawa sai dai addu'ar Allah Ya fitar da sakamako da gaggawa a tsakaninku wanda ya cuci wani sai Allah ya saka masa ba mu da wata hanyar gyara kuma babu wata mazahaba da za a bi saki ukun ai ba a lokacin daya ya yi miki su ba an yi daya da farko ya zo ya maimaita miki biyu saboda haka baki fara yin nadama ba Hauwa kuma muna nan ba za mu fasa addu'a ba idan shi ya cutar dake kamar yadda kike yawaita fadi Allah Ya saka miki. Saboda irin bud'e wutar da Hajiya Saratu ta yi a gidan sanya kowa jikinsa ya yi sanyi masu aiki kaf ba su fito ba domin sun jima a falon suna musayar yawu tana ta jaddada mata 15m din da take tunanin maigidan ne ya bata to ba shi ba ne ni ce hakan ya kara tsananta kukanta ina daga d'aki ina Jin gurnaninta cikin tashin hankali kamar wadda ke shirin tayar da sarkin aljannu. Shi gabad'aya ma bai sauko ba balle ya tanka takaici da b'akinciki ya na ta nukurkusarsa. Babu arziki Hauwa ta kama hanyar garinsu jin zafafan kalamai raddi masu kauri da jefa zuciya cikin rud'ani da bala'in yanayin da ba zai misaltu ba dama aka ce duk wanda ya ce tukunyar wani ba zata tafasa ba tabbas ta shi ko d'umi ba za ta yi ba. Washe gari Nusaiba ta zo mini da yaranta kaf muka yini tare su kuma su Fati suna jiran zuwan anti Yagana tukkuna don ba su kai ga tafiya ba. Kwana biyu a tsakani ta iso da yamma kuma matan gidanmu gabad'ayansu har da Babanmu da Baba Sule suka kwana da yamma suka yi shirin tafiya gabad'aya amma ban da anti Yagana saboda na ce ta bari tukkuna sai nan da sati d'aya Yaran shop's dina har da securities din dake gadi a wajan Lawan ya jagorancesu a daran da su Fati suka tafi muka jima da suma muna tattauna cigaban da ake samu koyaushe. Haka na dinga samun baki daga wannan sun tafi wasu za su zo Sahura ita kadai ta zo mini wannan karon Yusura ta sake samun ciki sai kawai na ganta da yarinya jale-jale tana koyar tafiya yarinyar Idiris ce uwarta ta cire ta daga nono lokacinta bai cika ba ta yi aure a cewarta baya kawo kudin abincinta iyayanta suka ce ta cire ta daga nono a kai masa 'yarsa suka kawota suka dire babu Imani uwar ta tafi ta yi aure. Mai shegen k'iwa da rashin yarda saboda tsabar bala'i lallai Sahurar ba zata huta ba ko uban da ya haifeta bata yarda dashi balle danginsa ta ma'kale mata na dinga mamakin wannan lamari kwatankwancin abinda Minal take yi mini yanzu ko wurin aiki da ita take zuwa Hajja kuwa sai 'kara mata karfin gwiwa take yi tana fad'in kada ki sare kada ki gaji wata'kila zata ji kan ki da d'a da dukiya ba a yi musu mugunta. Muna tare da su tsayin kwanaki uku babu irin batutuwan da ba mu tattauna ba abinda Hauwa kuwa ta aikata ya yi bala'in ba su mamaki amma jin irin hukuncin da maigidan ya yanke a kanta ya sanya zuciyoyinsu suka yi sanyi. A ranar da suka shirya tafiya wasu bakin suka dira Hamusu da Usaini kowanne da iyalinsa sai kuma Yusi da Saminu. Hajja kuwa ta samu 'kawa 'yar gidan Usaini mai sunana kenan itama suna kiranta da Minal ta dinga tsokanarta da faratu haske ne da ita kau har ta so ta fi ubanta haske Hajiya Saratu na tsokanar Hajara kamar ba goyonta ba, ita yarinyar ashe mahaifiyar Ummansu Saminu ta d'auko domin duka hasken fatar ta gada musu duk da ta tsufa amma tana nan kar kar da ita Fulani ne na asali. Kwana biyu da zuwansu Yusi yake gaya mini Kamalu daf yake da dawowa gida domin sun yi magana da shi a cikin satin da ya wuce na ce bai gaya mini ba duk da kuma mun yi magana da shi kwana hud'u da suka wuce ya dai tabbatar mini da cewa daf yake da ya kammala abinda ya kai shi amma bai fada mini ranar da zai dawo ba, amma ba na mamakin kan cewa ya sanar da maigidan tunda kusan ya fi sakewa da shi fiye da ni. Kwanaki biyu a tsakani suka tafi Hajiya Saratu ma ta riga Hajja yin gaba domin ta ce ita zata zauna ta kwana biyu tukkuna har na ji Yusi yana tsokanarta wai sai ta taso sun tafi haka yake janta da tsokana irin wadda ma bai yi wa Gwaggo irinta ba tsakanin Yusi da Hajja akwai amana da kuma 'kaunar juna har da rantsuwa wai gidan babu dad'i idan bata nan ta ce masa ba wasu kwanaki za ta yi da masu yawa ba. Shi kam babu halin zama makaranta ga kasuwa ba ma shi da ishashen lokaci na kansa. Hajja ta sake sosai da jikokinta tana jan su a jiki da wasa da dariya har dai suka sake tunda sun gano cewar kakarsu ce wadda ta haifi Babansu idan suna gidan karad'insu kad'ai ake ji a falo tana ta biye musu Baba Tabawa na yi musu dariya. Minal ce take ma'kale da ni da Mufida suna dawowa daga makaranta a wasu lukutan ko uniform ba ta zuwa ta cire za ta same ni a d'aki ta'ba nan ta'ba can ta yi ta han'koro ita lallai sai na bata k'anwarta. Cikinsu har khalil babu wanda ya taba daukarta sai dai gani daga nesa Babansu ya ce ko za a ba su sai ta kara wayo tunda ga abinda likita ya ce kuma alhamdulillahi ta yi lafiya tana shan nono sosai ta yi baccinta na rana da dare babu kuka mai zaburarwa sai dai tak'aitacce dalili duk wasu sharad'ai ina bi yadda muka yanke ni dashi rainonta yana hannuna duk rintsi babu buk'atar taimakon masu aiki gudun yin abinda zai sa'ba da lafiyarta. Yau kwananmu talatin da tara ya kama saura kwana daya kacal mu yi arba'in ina toilet na din ga jin kukanta a gaggauce na fito da sauri na riski Minal kane-kane saman gado tana ta cakumarta da wannan rawar kan nata. Tsawa na yi mata irin wadda ban ta'ba yi mata irinta ba ta kuwa zabura da sauri ta juyo tana kallona wanda ya yi daidai da shigowar Khalil na cigaba da Fadin." Ba ki jin magana ko, na ce ki bari zan baki ita ba yanzu ba tukkuna." Ta cire hannunta da sauri daga kan towel din Khalil da sauri ya dube ni yana fad'in." Mama me ta yi mata?" Shiru na yi ban ce masa komai saboda kwanaki ya daketa akan haka alokacin da ta taba yun'kurin aikata abinda ta yi a yanzu. Na nufi yarinyar da sauri na dauketa aka ci sa'a kuwa ta yi shiru tana lumshe idonta baccin za ta koma. Ita kuma ta sauka daga gadon tana ra'be-ra'be tana kallon Yayan nasu na kalleshi ina fad'in kada ka daket....ban kai ga rufe bakina ba ya kwada mata wani mari ta kwallara kara a ki'dime ta yo wajena. Na rufe shi da fada sosai. Ya fara fadin." Mama yarinyar nan sai ana dukanta fa wallahi rawar kanta ya yi yawa haka ta ga 'yan uwanta na yi tuntuni ake fad'in magana d'aya amma ta'ki ji ta zo ta cakumeta alhalin ba ta da lafiya." Na sassauta sosai ina fadin." To na ji amma dukan da ka yi mata ya yi yawa kada ka sake ka ji ko?" Ya gyad'a kansa yana sauke numfashi ita kuma dadi take yi." Mama ki yi hakuri." Na ce na ha'kura ai amma kada ki sake." Ta daga mini kanta tana jan hanci. Da gaske ta sangarce shekara tara fa yanzu ya kamata ace ta rage lalata shi kuma yanzu jin sa yake yi babba a cikinsu duk wadda ta yi shirme zare idonsa yake yi bai dai ta'ba dukan su Hassana ba sai dai muzurai da tsawa idan ya ga sun yi abinda bai da ce ba. Ya nuna mata hanyar fita da hannu ta gane abinda yake nufi aikuwa sumi sumi ta fita. Na ce Kai ba ka jin tsoro ta gayawa babanku kasan 'yar gaban goshi ce. Ya d'an yi murmushi yana fad'in ai Mufida ta ture mata fada yanzu itace akan karagar mulki." Takaitaciyyar dariya kawai na yi na cigaba da jijjiga yarinyar a hannuna. kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba. Ya zauna kusa da ni a nutse zamansa ya sanya ni nazarinsa sosai yana da damuwa tuntuni na fahimta kawai shiru na yi. Ya ce." Mama ko zan iya sanin abinda ya shiga tsakin Mamanmu da Baba don Allah ki gaya mini da na tambayi Hajja ta ce mini babu sauran zama a tsakaninsu ma'ana babu damar da za a gyara ta dawo, ki yi hakuri don Allah ki sanar da ni rufe mini bashi da amfani mahaifiyata ce na yarda amma k'wakwalwata ba zata manta da abubuwan da suka dinga faruwa ba tun da k'ananun shekaruna na gane dabi'unta ba su da kyau na yi iyakacin bakin kokarina wajan ganin ta gyara an zauna lafiya amma hakan bai samu ba. Jikina ne ya mutu da jin abinda yaron ya zo mini da shi. Yaro karami da tunanin manya idan yana manyance abin har mamaki yake ba ni wallahi sai na yi saurin yin kasa da kaina To na ce masa me in banda abin Khalil Hajja ta sakaye masa saboda abu ne mai muni a ce ya ji abinda uwarsa ta aikata. Amsar ai tana wajan Babansu tunda shi ya aikata ba ni da abinda zan ce. Ya gaji da magiyarsa ya tashi ya tafi domin abinda nake nanata masa shine ni ma ban san komai ba. BAYAN WATA UKU Bauci "To tunda kina ganin akwai yiwuwar haka sai ki jarraba ki gani ni dai ba ni da wata dama yanzu Hauwa gabad'aya ma cikin nadama nake a halin yanzu dalili ban san da wace fuska zan kalli yar uwata ba abinda ki ka aikata bai yi mini dadi ba ko kad'an gashi saboda ke sakarai ce kin dawo gida hannu rabbana in banda wannan kudin da ya baki wattanin baya ina takardar kamfanin da kike ta masifa akan ba kya so kun rabu rabuwa ta har abada babu kome kamfani kuma yana hannunsa har yanzu tunda dai bai baki shedar mallaka ba kin yi a banza sakarai shashasha duk shawarwarin da k'awaye da abokan arziki suke ba ki kin watsar kowa ya gaya miki ta wannan hanyar ake ya'kin kwatar 'yanci a gidan miji shikkenan ai sai mu zauna ni dake ai mu tsotsi tsamiya kin raba da ni da 'yar uwata Hauwa gashi abinda duk muke han'koro bamu samu ba idan kun yi auran kisan wuta kin biya wanda za ku kulla yarjejeniyar shin kina da tabbacin zai sake ki, ki koma gidan Tajo. Shi din ai ba mahaukaciya ce ta haife shi ba, ta wace hanyar za mu bi koda hakan ta kasance muga bu'katarmu ta biya?" Inna Uwani ta kai k'arshen maganarta cike da damuwa mai tsananin gaske. Ta nisa yayin da take ko'karin korar damuwa da wasi-wasin zuciyarta ta ce ." Zai yiwu Inna don mun gama magana da Yaya Naziru mijin Sadiya na ce zan bashi miliyan uku idan mun yi aure wata biyu zuwa uku sai mu rabu. Maganar komawa dakina ai mai sau'ki ne in sha Allahu zan koma kuma zan yi kokarin ganin na gyara na zauna lafiya da ita da shi don yanzu gabad'aya hankalina na gidan da yarana shikkenan Amina ta zama ita kad'ai yaran ma sun zama nata saboda na riga nasan na yi sallama da yarana Inna kamar fa ba ni na haifesu ba." Sai hawaye shaaaa! suka fara kasa tsare a kumatunta. Ta takure jikinta sosai ta jingina bayanta jikin wata tsohuwar kujera dake falon nasu tana kuka mai tsuma zuciya. Ta ce." Hauwa ba ki da kunya da ta ido yanzu Nazirun za ki aura da wane idon za ki dubi Sadiya duk abinda za ki yi fa ki yi tunani akai shima Nazirun kwad'ayin me yake yi ne, ki je ki nemi wani a waje wanda babu dangantaka mana. Ta dago kanta tana kallonta kafin ta ce." Shine kawai nake ganin zai cika alkawari Inna tunda ai rashin ba shi goyon baya ne a wancan lokacin ya sanya ya nemi auran Sadiya Inna kada ki manta fa tsohon saurayina ne. Kuma ya gaya mini kudin nan da zan bashi zai dora akan kasuwancinsa da ya yi rauni tunda zahiri yanzu Sadiya ta fi shi samu tana aiki tana kuma business ni kaina na sha yin order a wajanta. Ta ce." Saboda baki da wayo ko, ba ki tunanin d'adin baki ya yi miki domin ya rama abinda ki ka yi masa a baya wane irin cin kashi ne ba ki yi masa ba da k'yamata saboda ba shi da kud'i, ki yi nazari sosai akan hakan." Shiru ta yi na d'an wani lokaci kafin ta ce." Inna ki daina wannan tunanin don Allah shi kansa fa dana gaya masa kudirina goyon baya ya ba ni ya ce yana da kyau na yi kokarin ganin na koma hannun uban yarana har yana jaddada mini cewa idan ba tsautsayi ba babu wani dalilin da zai sanya shi rabuwa da matarsa saboda rayuwar yara na shiga garari." Inna Uwani ta dinga galla mata harara kafin ta ja tsaki ta furta." Ke har wani shiga garari kike hangowa yaran da suke da uba irin Alhaji Tajo. Suke kuma da uwar riko irin Amina. Wannan ba hujja ba ce amma tunda kin ce haka ba zan hana ki ba wata'kila gaskiya ne yana buk'atar kudin ne domin d'orawa akan kasuwancinsa tunda har ya amsa tayin da ki ka yi masa sai ku yi abin a sirrin ce yadda babu wanda zai gane da wata manufar kuka shirya auran...........✍️ *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* [6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *πŸ”š ALHAMDULILLAHI* *177* *SADAUKARWA GA IYAYAN DA ALLAH YA JARABTA DA FITINANNUN YARA IYAYEN DA ALLAH YA JARABTA DA HAIHUWAR YARA MASU DAUKE DA LALURAR JINI SIKILA. SADAUKARWA GA JAJURTATTUN MATAN DA SUKA YARDA DA RUSHEWAR FARINCIKI SU DOMIN JIN DADIN YARANSU. SADAUKARWA GA MAZAN DA SUKE HAKURI DA JIMIRIN RIKON MARAYA. SADAUKARWA GA ILAHIRIN MASOYA MAGOYA BAYANA WANDA NA SANI DA WANDA BAN SANI BA BINTA NA GODIYA NA SAKE GODIYA ALLAH YA SAKA DA ALHERI LITTAFIN GUDUN AURE BIYU NE A MADADIN DAYA DOMIN YA YI MUTUKAR TSAYI SOSAI YA ZAMA COMPLETE A TELEGRAM 2K DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA SHI* *0542382124...BINTA UMAR GTBANK* *07084653262* *177* Wannan shine tunanin Hauwa wanda babu technology ko kad'an a cikinsa. Lokacin da maganar ta fasu a cikin danginsu sun yi mamaki da k'ananun maganganu amma ganin yadda Sadiya ta goyu da bayan auran ya sanya kowa bakinsa ya mutu. Ita kanta Hauwan ta yi mamaki sosai amma da ta tuna cewa auran kwangila ne sai hankalinta ya kwanta ta fara tunanin ko mijin nata ya gaya mata yadda suka shirya wata uku kacal za su yi su rabu. Gabad'aya lokacin idonta ya gama rufewa babu abinda take da buri illah a dauran auran wattani uku suka cika ya saketa kamar yadda suka yi alkawari zuciyarta bata ta'ba yi mata kokwanton wani lamari zai iya kasancewa ba. Ba mu da labari daka ni har maigidan sai saura kwanaki biyu d'aurin auran Hajja ta kira shi a waya muna tare a dakinsa take gaya masa Hauwa za ta yi aure Inna Uwani ta kira tana gaya mata nan da kwana biyu za a d'aurin auran. Bai shiga wata wata damuwa ba ya yi fatan alheri suka d'an ta'ba hira kad'an kafin su yi sallama ya kashe wayarsa. Na d'auka zai d'an nuna kishinsa ko yayane tunda sautari wasu mazan sun tsani su saki mace su ji da gaggawa ta yi aure duk da nasan babu wata soyayyar kirki a tsakaninsu amma ai sun haihu zai d'an ji wani iri sai kawai ma na ga ya d'auki Mufida yana yi mata wasa yarinyar ta yi gwa'bi babu lefi amma dai da mutukar bambanci a hallita a tsakaninta da yan uwanta tun bayan haihuwarta sau biyu kacal ciwon ya motsa mata dalili muna mugun kiyayewa da bin ka'ida cikin kowane yanayi koyaushe tana hannuna na ri'ke na goya idan ta kama. Allah Ya jarrabe shi da masifar sonta sosai saboda dalilai bambamta sunan Mamansa sannan kuma 'ya macace mai rauni mai kuma rangwamin lafiya. Zahiri ya so Minal amma kamar yadda Khalil ya fad'a kwanakin baya yanzu dai Mufida ce ke kan karagar mulki don ni kaina idan muna tare bai fiye ba ni lokacinsa ba. Idan ya d'auketa sai su yi ta wasa itama ta yi sabo dashi tana ganinsa za ta dinga mik'a hannunta tana 'bangale baki ga shi kamarsu daya bayan yanayin ciwonta ta kwashi yanayinsa ta kowane sashi mussaman k'aramin jikin shiyasa abin ya yi yawa 'kank'anuwa ce sosai amma dai babu rama ta tashin hankali a jikinta a murmure take. Na kasance sosai cikin nazari da tunanin auran gaggawar da Hauwa za ta yi k'asa da wata hud'u da mutuwar auranta babu abinda zuciyata ba ta gaya mini ba akan haka. Wani sashi na zuciyata na gaya mini wata'kila ta samu wanda take sone kuma mai wadata da wannan nazarin na yi ko'karin ganin na mantar da kaina lamarinta tunda Ubangiji ya datse alakarmu domin ba ni fatan ta sake dawowa cikin rayuwarta har abada addu'ar da a koyaushe nake yi kenan. Ina ganin status dinta jefe jefi tunda har yanzu muna da serving din lambar juna ban goge ba itama bata goge ba amma ba mu ta'ba yin magana ba idan ta d'ora ma ba ni dubawa saboda har abada ba ni buk'atar abinda zai k'ara had'a ni da ita. Dalilin da ya hana ni goge lambarta kuwa saboda yaranta a duk lokacin da Khalil ya buk'aci magana da ita zan bashi lambar tunda duk tsiya ai ba canzawa towo suna dole itace uwarsu kuma ba zan d'auki aniyar datse alakar da take tsakaninsu ba kamar yadda koyaushe Babansu ke gayawa yaron ko za su je bauci wajenta sai sun girma ba yanzu ba yaron har ya gaji da bibiyar lamarin ya ha'kura abin yana yi masa ciwo ainun yadda ya damu da ganin irin rabuwar da iyayen nasa suka yi wadda duk wanda zai bud'e baki zai gaya masa cewa babu sauran gyara kuma sun karanta karatun a islamiyya. **** To wani abu da Hauwa ba ta sani ba shine har yanzu Naziru yana sonta dama a rashinta ne ya auri Sadiya tunda a wancan lokacin ta raina samunsa k'aramin 'dan kasuwa ne yana sana'ar sayar da leda a kasuwa da abinda ya danganci buhu da bacco sai dai inda Allah ya taimake shi shagonsa ne ba haya yake yi ba. Kuma ya yi kokarin ganin ya gina gidansa mai d'akuna uku da shago a waje d'aya yake kiwon kaji biyu Sadiya take amfani da su shagon waje kuma yaransa da yake duk maza ne yanzu sun zama samari su hud'u suna amfani da shagon amma dai band'aki d'aya ne duk da shi suke amfani a cikin gidan. Haihuwar da ta yi ne a yanzu ta haifi mace wadda gabad'aya suka d'auki son duniya suka d'ora mata. D'akin nan da yake kiwon kaji shi ya gyara mata aka yi sabon fenti da sumintin kasa amma dai duk da haka d'akin yana warin kaji tunda ya jima yana kiwon shekara da shekaru d'akin ya game da wari abin sai addu'a. Ranar da aka d'aura auran ta tare suka kwana a daddafe shi a wajansa hakan ba komai bane tunda ya saba sha'kar warin k'ashin kajin da yake kiwo wanda suka hadu da dusar abicinsu. Ita kam a wajanta sabon lamari ne da take ganin ba za ta iya jura ba mussaman da wata gaisuwar kirki bata ratsa tsakaninta da Sadiya ba da gari ya waye ta yi tafiyarta wajan aiki gidan kaca kaca gashi bashi da wani girma k'udaje sai shagalinsu suke yi daga cikin d'akinta tana iya jiyo zarnin fitsarin samarin gidan da ya had'u da warin masai yake fitar da wata irin k'alla tunda na gargajiya ne. Sai shi da kansa ya zuba ruwa a bokiti ya wanke bandakin tukkuna ta iya shiga ta yi wanka yadda ya nuna ai hakan ba komai ba ne tunda ya riga ya saba Sadiya ba ta yin aikin gida sai ta dawo daga aiki to balle kuma yanzu da take ganin ba ita kad'ai ba ce matar gida. Da wannan matsalar aka fara domin dai rige-rigen shiga band'anki ake yi a gidan samarin yaransu duk nan suke uzurinsu har ma da abokansu idan sun zo wataran ma tana ciki tana uzuri za ta ji ana buga mata kofa wai ta yi sauri ta fito. Yaran da ada can suke ganin girmanta dalilin amincin da yake tsakaninta da Mamansu yanzu ko kallo ba ta ishe su balle su gaisheta. Aka dinga fafata rigima sadiya ta yi duma ta barta da yaran sai rashin kunya suke yi mata ita kuma duk abinda take yi na kasuwancinta bata fasa ba gari yana wayewa za ta tafi aiki ranar hutu kuma ta shiga kasuwa sare sare kayan da take sayarwa. Sai ya zamana Hauwa ke aikin gida ta yi girkin rana da dare koyaushe idan ta yi masa korafin cewa babu ajadanar haka a shara'din auransu sai ya bita da lallami da dadin baki yana ce mata idan bata saki jikinta ta nuna auran soyayya suke yi ba mutane za su fahimci manufarsu. Hakan ya sanya take gyara gidan har ta yi griki ta kuma wanke bandaki Sadiya na wajan aikinta ta dawo kuma ta d'ibi abinci ta ci ta k'oshi ta yi mata duma kamar babu sanayya a tsakaninsu Babu wata maganar arziki sai kame-kame sai hakan ya kara tayar mata da hankali gashi tun farkon tarewarta ta bashi dubu dari biyu da hamsin akan ya kama mata haya koyaushe idan ta yi magana sai ya ce mata gidan ne ba a samu ba. Haka ta yi wata biyu a daddafe a gidan lokacin sun yi fito na fito da Sadiya uwarka ubanka sun kuma yi wa kansu tononan silili har Sadiyan na fad'in indai Naziru ne gata nan gashi nan ai ba tomo ba ne kuma ta kama kafar wala tunda duk mazajen da suke gari ta rasa da wanda za ta yi auran kisan wuta sai da mijinta. Lokacin ne maganar ta fasu a dangi iyayensu maza kowa ya san dalilinta nayin auran kisan wuta don ta koma gidan tsohon mijinta ne. Inna Uwani sai da fita ta gagareta saboda kunya da tashin hankali irin lalataccen kallon da 'yan uwan mijinta ke yi mata sai ta zama abin kallo ma domin har gida aka dinga zuwa ana yin ala wadai da irin yadda ta bada goyon bayan aikata abinda Allah Ya haramta shi kuma Naziru ya riga ya gayawa mahaifiyarsa cewa bai auri Hauwa don ya saketa ba. Amma kuma ita sai ya ce mata idan har tana so ya saketa sai ta kara masa miliyan biyu kudi sun kama miliyan biyar da yake hankalinta a tashe yake da barin gidansa babu ja'inja ta kΓ ra masa. Da wannan hanyar ya dinga kar'be mata kudi har sai da ya zama ya tatiketa tsaf kuma ya ce ba zai saketa ba saboda yana sonta dangi kuma kaf suka goya masa baya. Lamarin da ya janyo mata mummunan ciwo jininta ya hau aka dinga tiri-tiri da ita don har kwanciya ta yi a asibiti a lokacin ne muka samu labari ni da shi mun je kano hutu zai d'an gudanar da wani aiki Hajja take gaya mana halin da ake ciki domin dai duk yadda lamarin ke yi mata zafi a ranta sai da ta je har can bauchin ta duba jikin Hauwan ta kuma ce masa lallai ya tura mata da kud'i domin jinyya saboda babu tunda har ya yi rantsuwa akan janye kyautar kamfanin da ya yi mata ya ce babu amfanin mallakawa ma'kiyi abinda zai kawo masa cigaba a rayuwarsa. Mutum ne mai bala'in riko da tsananin gaba do dai yanzu an sake girma amma dai yadda ya'ki jinin Hauwa haka ya'ki jinin mutuwarsa sunanta 'yar ta'adda a wurinsa yana rangwatawa ne kawai saboda Hajja ta nuna tsananta gaba da kiyayyar bashi da amfani tunda an riga an hadu babu yadda za a yi da juna. To ita ga da niyyar da ta yi aure amma ga yadda kaddarar takasance A lokacin kuwa ya tura mata da dubu dari biyar ya kuma kira wayarta tun bayan rabuwarsu wata biyar kenan suka gaisa 'kasa k'asa nake yin maganarta tana magana a hankali ya dubata da jiki sosai sannan ya ce ta duba ya tura mata sa'ko. Ya mi'ko mini wayar wai tana son mu gaisa babu yadda na iya haka na kar'ba nasa a kunnena na ji maganarta a raunane kamar ma kuka take yi. Zuciyata ta d'an karye kad'an amma ban bari ta gane ba muka gaisa sosai na yi mata ya jiki ta tambayi yaran gabad'aya har da k'aramarsu Mufida na ce duk nuna nan lafiya lau. Jin ta yi shiru ya sanya na mik'a masa wayarsa na ji yana gaya mata idan da buk'atar wani taimakon gaggawa ta sanar dashi daga haka ya kashe wayarsa. Ko da muka keb'e bai bai tashi zancan ba sabgoginsa kawai yake yi cikin kwanciyar hankali da nutsuwa tun kafin mu zo nasan dalilin zuwan tunda bai gaya mini ba ni ma ban nemi jin karin bayani ba Hajja ta kira ni a waya ta gaya mini yana yi wa Kamalu gini amma bata gaya mini wane iri bane shin na gida ne ko kuwa na makaranta. Sati daya muka yi a kano muka koma abuja cikin yaranmu da suke samun kulawa wurin masu aikin da a yanzu nake ganinsu kamar 'yan uwana saboda yadda sha'kuwarmu da su ta kara tsananta. Babu wani sa'bani da ya sake giftawa tsakanina da shi tun bayan fitar Hauwa muka samu wani irin daidaito da kara kusanci ga juna gabad'aya hankali da tunaninnmu yana kan yaranmu mussaman ita wannan din da muka samu daga baya. Ban ta'ba jin ya yi wata magana da ta danganci neman cikin gurbin da Hauwa ta bari ba abinda na lura da shi ma a yanzu ba wannan ne a gabansa ba amma ta fannin abinda ya danganci mu'amula ta aure babu wani abu da ya yi rauni muna shan soyayya launi-launi domin ni dashi gabad'aya mun 'ki bari kanmu ya yi murfi yadda koyaushe yake d'okantuwa da ni haka nima nake kasancewa da shi kamar wata sabuwa dalili ina kasancewa cikin gyara kaina ciki da waje yadda zai ji dad'i ya kuma yi alfahari dani tare da dakushe masa sha'awar duk wata 'ya mace. MURFI Bayan shekaru biyar abubuwa da yawa sun faru masu dadi da marasa dad'i mun yi rashin Hajja haka zalika mun yi rashin Dada mata uku da suka taka muhimmiyar rawa a cikin rayuwarmu Gwaggo Hajja Dada duka sun amsa kiran Ubangiji suna masu tuba da tabbatar da ya'kini ga Allah. Yadda kowa yake ha'kuri idan ya yi gagarimin rashi haka mu ma duka muka yi hakuri 'ya'ya da jikoki masu aiki da hadimai tare da abokanan arziki. A cikin dai shekarun ne Kamalu ya taka mataki na mussaman fannin addini tauhidi tare da da'awa. Yaro ya yi bazata to amma ba abin mamaki ba ne idan har an yi duba da irin kalubale mabambamta da aka riska tun daga farkon kuruciya har kawo wa yanzu da aka cimma manufa babu shakka addu'ar iyaye tana da tsananin tasiri akan yaransu ba ma su kad'ai takewa tasiri ba har da wad'anda ke abota da su. Na ga zahiri domin ita addu'ar a yanzu na tabbatar da cewar itace take ri'ke da ni har na riski wannan lokacin cikin nutsuwa da hayyacina. Gwani Kamaludden Aminu Salihi a yanzu yana da masters degree (gwani) bayan fafutukar da aka sha wajan neman ilimi littafan addini tun daga kan al'kur'ani mai girma babbbak'u farfaru haddace shi da kuma rubuce shi. Idan muka zo kan kan litattafan addinin musulunci irinsu fi'kihu ahlari ishmawi iziya risala askari muwad'da malik muddawara kulasatunurulmubin, arba'una hadis, zadizzaujen. Wad'annan littafan addini ne da duk wani mai neman ilimi fannin da'awa ya karance shi Gwani Kamalu ya zauna zaurukan malamai da yawa domin k'arin sani kafin malamansa su bashi izinin zama kan mumbari a katafariyar makarantarsa da uban rik'onsa ya gina da sunansa mai suna *Gwani Kamaludden tahafizul-kur'an* Ya k'ara da gina massalaci kusa da makarantar domin zaman tafsiri da warware wata mas'alar idan ta taso wadda ta shafi addinin musulunci a k'arshe kuma ya ce ya nemo aure gidan mutunci da tarbiya domin k'ara samun goyon baya da nutsuwar gudanar da al'amuransa. To rasuwar Hajja ita ta gyara zazzafar gabar dake tsakanin Inna Uwani da Hajiya Saratu domin dai Inna Uwani kuka take yi sosai da Hajiya Saratu a ganinta itace take zuga Hajja ta'ki yafe musu ta zo ta sake zuwa wurin Hajja domin neman gafara da kuka da ro'ko ba a rabuwar arziki a tsakaninta da Hajiya Saratu domin cikin ikon Allah duk zuwan da za ta yi sai ta risketa a gidan su yi ta babu kyau babu dadi ita Hauwa na can babu wadatacciyar lafiya domin yawan hauhawar jininta ya sanya mata nakasa k'afarta daya ta lanjare da 'kyar take janta a gidan Naziru ma gabad'aya ta zama maririya domin babu wani abinda take iya aiwatarwa tunda babu lafiya kwanciyar aure wannan ba kasafai yake yi da ita ba saboda babu nutsuwar yin kullum cikin ciwo yau da lafiya gobe babu adalci d'aya da ya yi a lamarinta da ya cigaba da zama da ita a hakan bai saketa ba. Ko saukar al'kur'ani da Khalil ya yi Inna Uwani ce kawai ta samu damar zuwa nan abujan tunda ran Hajjan aka yi wannan bada'kala domin kuwa da kuka ta bar gidan sakamakon irin k'yama da gudun da yaran Hauwa ke yi mata ga Hajiya Saratu ta hana ta motsi a lokacin ne Hajjan ta tsawatar mata tana gaya mata ko bayan ranta bata yarda da wannan matsanaciyar gaba ba babu yadda za a yi da juna tunda an hadu abinda ya riga ya faru sai a bar wa Allah tunda ya wuce yara kuma kada a kuskura a dasa musu kiyayyar uwarsu.. Bayan rasuwar Hajjan ne na ga sun d'an daidaita domin dai mutuwar ta ki'dima mutane da yawa. Har ita Hajiya Saratu ta je can bauchin ta duba Hauwa data na bani labarin halin da take ciki sai da ruwan hawaye ya ciko idona lallai dan adam ba abin komai yake ba Hauwa ta had'u da jarrabawa da kuma ciwo mai tsanani wanda a halin yanzu maigidan ne ke hidima da maganinta mijinta kwabonsa bata ciwon kai ina ma ya ga kudin. Gidansa dai babu yunwa zai kawo ko babu dadi Sadiya ta dafa ta sammata a kwano amma ita da yake Hajiya ce ta fi Hauwan kudi takan yi miyarta ta kaji ko ta namar rago duk ranar dai bai yi cefane Mai kyau ba ta tsakura ta ci ita da yaranta abinda ya kawo shi take bawa Hauwa tunda dai ita kacangal bata iya yi saboda babu isashshiyar lafiya kullum tana dakinta a kwance cikin zullumi da koke koke da wata kafurar nadamar da har ta mutu ba zata musulunta ba. Zuciyar imani ce ke sanya Sadiya kulawa da ita saboda tana tuna wasu alherai da ta yi mata a lokacin da take da dama a shakarun baya. Hajiya Saratu da kanta ta zo ta same ni kan cewa idan har Kamalu bai zai tsayar da matar aure ba to sun bashi Aslamiyya jikarta ce ta wurin d'anta na biyu Hafiza ce don kuma tasha wakiltar makarantarsu wurin gasar al'kur'ani k'asashen musulci. Na ce mata ba ni ya kamata ta nema da maganar ba d'an uwanta za ta gayawa tunda dashi suke yi magana ta ce ta sanar da shi kuma ya yi murna sannan ya ce zai tuntubi yaron wannan ha'kkina ne dole a gaya mini. Na ce tunda hakane sai dai kawai na yi fatan alheri da tabbatuwar al'amarin. Dama Salim matarsa yanzu tsohon ciki ne da ita haihuwa ko yau ko gobe ya yi aure shekarar da ta wuce yar gidan abokinsu Alhaji Sulaiman mai suna Suhailat amma ba Hajiya azizaa ce ta haifeta ba matarsa ta biyu ce. Nan gidansu ya gyara wani sashe ya zauna da matarsa amma karfin zamansa yana can legos kusan yanzu shi ya kar'bi ragamar zaman can din shi da Adamu, maigidan ma yakan je idan ta kama amma baya jimawa a can yake dawowa gida k'arfin zaman yanzu yana nan Abuja tunda akwai masu ri'ke masa wata ragamar a can legos din. Hamusu kuma yana da mata biyu yanzu yaransa hud'u ya sake gina gida mai girma rayuwa ta yi kyau kwarai da gaske babu wanda nake yi wa mugunta kaf cikin yarana na bud'awa kowa ya samu Turzumi ma yana tare da su a kasuwa na ce a sama masa gurbin zama ya fara kasuwanci domin kula da yan uwansa tunda shine namiji babba a gidansu. Shi kuma Adam idan an yi magana ina budurwarsa sai ya nuna Usaina ta yi ta zum'bura baki tana jin haushi yanzu suna da 16years suna ajin karshe a secondary school. Shekaru biyu da suka wuce suka sauke al'kur'ani mai girma Minal kuma tana da 14years da yake tana da girman jiki har ta so ta fi su girma da 'barage k'irjinta ma ya fi nasu fitowa uban yana fad'in daga ya kalleta gabansa yake fad'uwa aure zai yi mata da wuri idan yana fad'in haka na yi ta dariya yanzu ta yi hankali ta daina wannan rawar kan ta nutsu karatu kawai suka sanya a gaba. Nakan ce duk saurinsa sai ya bari mijin ya fito ya ce ai shi tuntuni ya yi mata miji da na matsananta kuwa Ina fad'in ba da yawuna ba don amanace a hannuna kafin rasuwar Hajja duka yaran sai da ta d'amka mini amanarsu na ce ya bari ba gaggawa ake yi ba don ni ban gaji ba idan har zai dubeta saboda ga'barar jikinta gabansa yana faduwa to ba zai yiwu ya aura mata wanda bata so ba kamar yadda ya tambayi Usaina akan Adamu ta amince tana sonsa itama ya zauna ya tambayeta bud'ar bakinsa ya ce mini ba kowane mijin da ya zab'a mata ba face Yusi. Tun daga lokacin bakina ya mutu ban sake yi masa wata magana ba a duk lokacin da ya tayar da maganar sai na rasa abinda zan ce. Haka kawai ma sai na dawo jin nauyin yarinyar duk da cewa ba ta san wainar da ake toyawa ba sabgarta take yi amma sai na tsinci kaina da 'kin barin mu hada ido a hankali na rage biye mata idan tana yi mini shirme da sangarta abinda ya zame mata jiki a gare ni tun tana yarinya domin da ta tabbatar da cewar Mufida ta 'kwace mata kujerarta wurin Babansu sai ta dawo wajena ni kuma na kar'beta tare da cigaba da lelenta Twins na fad'in su babu mai yinsu a gidan duk lokacin da kishinsu ya tashi. Khalil kuwa yana can Madina karatu makarantar da Kamalu ya yi koyaushe uban na sha'awar Kamalu yana kuma bada misali a kansa da burin Khalil ya yi koyi da shi wajan jajurcewa. Yusi dama fannin kasuwanci ya karanta don haka tun bayan kammala kararunsa kasuwancinmu ya b'unkasa dalili shine a yanzu ke fita waje yi mana order dubai chaina India da oman zamansa a najeria yakan zama ta'kaitacce dalilin wannan zurga zurgar shi da Saminu tuni sun kammala gidajensu a rijiyar zaki wajan d'ambare don shi Saminu ma har an kai kud'in aure da sanya rana. Jikin gidajen da suka gina na sanya su yi mini bhole guda biyu hadiya ga mahaifiyata na kuma gina madaidaitan masallatai uku hubusi duk a gareta Babanmu na bashi za'bi sabon gida ko kuma a sabunta masa wanda yake ciki a yanzu ya ce a sabunta masa gidansa na gado iyaye da kakkani. Gabad'aya aka rushe shi aka yi sabon gini na zamani kowacce aka sanya mata sabbin kayan d'aki. Addu'a muna shanta da ni da shi daga bakuna mabambamta dalilin hannunmu da yake zaga ko'ina. Ban san abinda yake tsakanin Abahuraira da Hassana ba katsam Baban Saude ya kira ni a waya yana tambayata menene a tsakaninsu domin kuwa da suka je ganin gida saifullahi ya gaya masa wata magana a kansu. Na ce da shi ban san komai ba amma ya tambayi Babansu ya ce shikkenan zai neme shi. A daran kuwa suka yi waya shima dai bai san suna soyayya ba sai da ya kira yarinyar muka titsiyata ta fara kame-kame daga karshe dai ta bada amsar da muke so mu ji daga gare ta tana dariya uban na taya kamar wasu shashashai haka na tsaya ina kallonsu shi da ita idan yana wata shiriritar da yaran ya yi ta ba ni haushi shiyasa gashinan sun mayar dashi kakansu tunda tsakani da Allah a ganina wannan mas'alar ai ta jin kunya ce amma babu ita shi da yarinyar yana tsokanarta tana k'yalkyala dariya. Ya sanar da Baban Saude ya bawa Abahuraira Hassana a duk lokacin da ya kintsa Baban Saude ya ce a kintse suke son samu a had'a duka dana Kamalu da Usai da Adamu. Wanda za a yi shi bayan dawowarmu daga aikin hajji kamar yadda suka tsayar da lokaci. Wanda ya yi daidai da lokacin da za su kammala secondary amma da shara'din barinsu cigaba da karatu koda an yi auran Suka tsayar da magana a haka bayan wasu kwanaki kuma yake gaya mini za a had'a da Minal kawai duk da ajinta biyar ita yanzu na ce a a ba za a tsinke mata karatu ba bayan haka kuma ba ta yi k'warinsu ba, sannan kuma shi yake sabgarsa shi kad'ai babu wanda ya gayawa a cikin yaran balle su san halin da ake ciki ba a yin haka. Ya ce ya gayawa Yusi a waya kuma ya amince. Na ce to itama a gaya mata ya dinga dawurwura alamu sun nuna yana jin tsoron rigimarta abin mamaki ko da ya gaya mata ya yi mata miji da farko zum'bura baki ta dinga yi da k'ananun hawaye amma yana gaya mata wanda ya zab'a mata ta sinne kanta tana murmushi nan ma ya dinga kyakyata dariya kamar wani sabon kamu abin ya dinga ba ni haushi da mamaki. Ta tashi ta sauka 'kasa da sauri yadda ta nuna alamu ta amshi tayin da aka yi mata kuma Yusi ya samu gurbi a cikin zuciyarta. A wannan shekaran rabon kujerar hajji ya yi anti Yagana da Ya Falmata sun rabauta da ta su. Baban Saude da kuma babamu suma sun samu tasu. Sai iyalinsa gabad'aya ni da shi da yaranmu har da Mufida da kuma Adam da Sukairaju muka d'unguma zuwa kasa mai tsarki domin yin aikin Hajji. Masu aiki muka bari a gidan. A can muka riski Khalil kamar yadda muke hasashe ya yi wata iriyar kamala ta ban mamaki kamar dai yadda Kamalu ya yi dama yaro ne mai son girma da manyance sai abinda ya k'aru balle yanzu da ilimin addini ya fara huda shi tare da shi muka yi Hajjin ya d'auki Mufida ya sa a kafad'arsa sosai na tsananta da ro'ko da addu'a akan Allah Ya tabbatar da alheri bisa wannan had'aka ta auratayya da za mu yi wa yaranmu addu'ata gabad'aya ta ta'allaka ne akan hakan tare da fatan cikawa da imani da kuma samun zuri'ar da duniya za ta yi alfahari da ita......✍️ *ALHAMDULILLAHI!* *ALHAMDULILLAHI* *ALHAMDULILLAHI!* Lefin dad'i k'arewa ga dai yadda 'karshen wannan labari ya zo. Ina ro'kon Ubangiji Allah Ya yafe mini abinda na rubuta bisa kuskure wanda na rubuta daidai kuma ina ro'kansa da ya ba ni lada tare da wad'anda suka bibiyeni. Godiyata bata da iyaka akan masoyana na gode na sake godewa wad'anda nasa ni da wad'anda ban sani ba. Comments section na gudun aure lallai kun yi bajinta kuma kun kara mini kwarin gwiwa wajan ganin na isar da sa'kon dana d'auko ba tare da na gaza ba. Na sake fadi kun yi bajinta k'warai ban cire kowa ba. Masu k'orafi kuma ban ji komai ba wannan ma cikin kulawa ne Allah Ya saka da alheri. Za mu cigaba da zumunci da gaisawa cikin comments section kafin zuwan sabon littafi idan Allah Ya sa muna raye. Ina fatan wanda zai zo anan gaba ya fiye muku wannan da muka kammala dad'i da wa'azantarwa. A yi bikin sallah lafiya aka kuma yi mini tallah a gruops na kammala a arewapen ga masu jiran karanta complete din littafin.... ALLAH YA SADA MU DA ALHERI. *GARKUWAR MATA.* *BINTA UMAR ABBALE* Downloaded from NovelsHQ.com This Novel is downloaded from https://NovelsHQ.com to download more hausa novels visits our site at www.Novels.Com For feedback and support Facebook : https://facebook.com/NovelsHQ.com Twitter : https://twitter.com/NovelsHQ.com Telegram : https://t.me/NovelsHQ.com